Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Wlh mutumin nan har yafara bani haushi ki kalla fa irin abindanake fadamiki ko tamkar wanda muke yankan naman jikinsa agidan nan baya sakin rai wa kowa sauki sauki mam da daddy sai kamriyya da abbas da ali ke nifa yakemawa wannan abun madaga karshe dana xauna nayi tunani, Hanifa tafashe da dariya ganin yadda Aysha tayi maganar kamar xatai kuka da alamar hakan kuma tunda hawaye sun taru a idaninta. Tadafa kafadarta Look my kawas kidai kara dubawa hala bakomi tunda ba abindaya taba hadaki dashi toh inagama shegen surutun ki yagane yake ganin kamar inkika samu fuska xaki rainasa Duka Aysha Mohini takaiwa hanifa tagoce sai abayan kamriyya data futo dagudu tashigo tsakaninsu mama ta aikota xubewa tayi agun tafara ehu Wayyo bayana Wayyo takashe ni mam wayyo mam Muneeb ne yafuto dasauri mama ganin Muneeb yafuto yasa takoma tabarsu Ya akayi menene sista Kamriyya na lallauyewa yana dagota Bayana uncle anty mohini taxabgan dundum, Harara yacilla mata Waya ce kidaketa me tamiki Hanifa tana kallo kawai Mohini tana kallon kamriyya da sharri irin na ta lallai yarinyar nan akwai raki Ba abindanayi mata hanifa nakaiwa dukan dayake rabonta ne saitaxo ta amsa Ran Muneeb yabaci da irin amsar mohini yajallata da yatsa Baki daki lalai ba dama na fuskanchi kina cinxalin yarinyar nan toh kikiyayi karo nadake Yaja hannun kamriyya yana lallashinta suka shige falo Jikin mama tafada Yane yane 'yar daru Muneeb karama mata ko? Ya na kokarin futa yace Sai takuma yanxu akyaleta tunda arashin sani tadaketa Humm Aysha ce fa wlh tanasani ma dokemin ita xatayi Mam nakoma Ok Allah yatsare adawo lfy Yafuce lokacin dayafuta su mohini sunbar gidan suma direba yatafi kaisu Aysha mohini kam itakadai tasan irin famin da Muneeb yayi mata yau akan yadda takesonsa yau data kalli tsantsan kamanninsa sosai yadda yake magana anutse bai da hargitsi komai nasa cikin nutsuwa kai kahadu yaya Muneeb. Tafada afili Hanifa tayi Murmushi Allah ya mallaka miki yah Muneeb kawata Amin hanifa danaji dadi kwarai inabala in son yayan nan nawa kawata inaji kuma ajikina shima ina ransa koda bayawa Sukayi dariya. ๐Ÿ˜‰amarsu ta ango dai anmaida ta yau kwana uku kenan amma bata taba ganin koda gilmawar angon nataba agidan Nu'uman kenan abin tunbaya damunta har yafara damunta xuwa yanxu tayi nadama kuma tanaso tanunamasa tayi nadamar abindatayi masa abaya amma batamagansa ba balle yaganta abinci kuwa inda ta aje haka xata xo tasami abinta saidai taci kukanta har ta hakura tai shuru, Sau daya tataba jin futar motarsa kafin taleka yacilla hancin ta waje yadda ma tafuskanta kamar baya shigowa wannan part din yana dayan wato dayake gidan part uku ne dayan shine take ciki daya na Aliyu ne dayan kuma kawai safayane saikuma dakunan baki dake gefe guda, Yau kam taci alwashin saitagansa donhaka tun karfe biyar na yamma tabuga wankan riga da da siket na kanti sunkamata sosai hula tasa mai tambarin love agaba tadan xame hular tai baya yayin da gashinta yafuto tagaba sai kyalli yake da wal wali sbda yasha gyara na musamman kasancewar sai da akasake murje ta da gyara kala daban daban sannan suka dawo da ita. Karfe shida da rabi yadawo maigadi yabude masa get yashigo da motar bayan yafaka ta yafuto hannunsa rike dajakar sa yanufi part din dayake xaune hankalin sa kwance donko kallon inda part din fujjilat yake bason yi yake ba shiyasa ma yadauke hankalin sa dagakan wajen sbda bayaso yatausaya ma ta tun yanxu yafiso saitagama gane kurenta tukunna, Murda wa yayi yashiga tare dasauke ajiyar xuciya dafurta Allahamdulillah. Kaitsaye bedroom yanufa yana cire hular kansa sbda xafin da ake yana bukatar sanyin eysin nan ya ratsasa sosai, Kokarin mopin din dakin take duk tagyara komi tsaf datagama na bedroom saikuma ta gangaro falo Cogewa yayi jikin kofar yana kallonta itakam batasan da shigowar saba sai aikinta take Gyaran murya yayi tare dakara tsuke fuska gumm Atsorace ta mike tana kallon kofa gabanta ne yafadi ganin sa tsaye yaxuba mata ido cike kuma da tambaya a fuskarsa shin metaxo yi masa daki jikinta rawa yafarayi sbda abin tsoro ba yayiwa fujjilat wahala ko kadan balle yadda ya tsatstsareta da idannan kuma rai atamke kamar xai shakota yakashe, Ahankali yataka xuwa gaban gado ya aje jakar gefe da dirowa xaunawa yayi gefen gadon Yana cilla mata tambaya Me yakawoki nan? Kanta akasa tana wasa da yatsun hannunta don tun kallonta dashi nafarko tacillar da mofar gefe, Takasa magana sai rarraba ido take daga kafarsa xuwa kofa futa kawai yanxu take bukata tayi Dake nake magana malama kinmin shuru ko har lalacewar tawa takai maganar ma baxaki iyamin ba kinga toh fuce min adakin nan kuma karki sake nakara ganin kaxamar kafar ki awajena kixauna can kedaya dakewar shi wanda kike kaunar ehhemm oya waje Jin abindaya fada yasa fujjilat kallonsa dasauri tana sharar kwallah kenan yana xarginta da har yanxu son Ubaid take me yake kokarin alakantata dashi ne wai, Ganin ta coge yasa Nu'uman fasata yatashi dakansa yafinciki hannunta xai turata falo daganan takarasa fucewa dakanta Kankamesa tayi tanasakin wani sabon kukan Dan Allah kayi hakuri kasaurareni Tafurta a wahalce tare da shashshekan kuka, Me xan saurara me xaki fadamin duk abindaxa kifadamun abindana riga nasanine saidai ko bansaniba maimaita fadamin yadda kike kina kikeso kiyi bakomi don so kam yanxu dama bana bukata kirike kayanki koma komi kike jin kina bukata agurina kitanbaya xanmiki ciki har saki inkina nema nasan yanacan yana jiranki wanda kike so din ko bakomi duk lokacin dakika shirya barin gidan nan kimin magana nasallameki vaxan danne miki hakkin kiba gwara kimai masa da gurbin sa daya rasa kingane ok?! Xuciyar sa xafi kawai take fujjilat tarike hannunsa tana sakin wani sabon kukan Nu'uman Baitabaji takira sunan saba sai yau Wlh babu abindaya faru tsakanina da ubaid narantse da girman Allah daya, kuma idan karya nake xakasani ai, dan Allah kayi hakuri nagane irin kuskuren dana tafka abaya bansan dawanne ido xan iya kallonka ba Nu'uman! Da xuciya daya nake maka wannan maganar nagane cewa gaibu nakama kai wani alkhairi ne da ubangiji ya bani shi, dan Allah karka ki hakura Xame hannun ta yayi daga nasa yashiga ciki kawai xuciyar sa cike da tausayinta kaunar ta ta motsa sai ya ji duk baikyauta ba daya kyaleta bai rarrasheta ba yanason kayarsa bagu kawai yake mata da tsoratarwa da kalmar saki amma koda Ubaid yayi mu ammala da ita baxai saki matar saba koda xaman nasu xaiki dadi kodaya futo baiganta afalo ba donhaka kaitsaye wajenta yanufa Anan ma falo ba ita bedroom dinta ya tura can yahangota kwance saman gado tana rasgar kuka, Rumgumar ta yayi tabaya tare da dagota Ya isa ya isa haka kukan kar makwafta suji suce wani abin namiki yi shuru na hakura kuma nayarda da duk abindakika fadamin insha Allahu kuma komai ya wuce kinji? Kanta kasa tana mutsuka idaninta baki ta turo tana shashsheka Karfa ki cigaba fa shuru nace Tadaga kai cikin dashewar murya tafara magana tana matsar ragowar kwallar data makale Katabbata? Kai yadaga mata yana murmushi Ga xahiri kuwa Itama murmushi tayi tana mikewa dasauri tabar jikinsa tana direwa kasa kaitsaye kofar ta nufa tana cewa Girki xanmaka maidadi yau agidannan Dariya yayi yana binta falon Aa yau angon nake kenan toh madalla da amarya yanxu bari naje na watsa ruwa sai nadawo nakira Abdul awaya yaxo yaci girkin amarya Kitchin takarasa shigewa tana dariya Shikenan ango. Tsaye yake jikin motar yana danne danne awayarsa Tabude gidan tafuto kawai tagansa ranta abace ta furta Dama wannan dan iskan ne ya aika akirani? Tab aikwa yau xaiga yadda ake wulakanci Tanufesa afasace Aisar da tun futowarta akan idaninsa sbda yana jin bude kofa yadago kai har maganar datatsaya yi yagani amma sakamakon taxarar dake tsakanin su yasa baiji abinda ta ke fadaba murmushi kawai yake yimata fuskarsa mai cike da kwarjini takara kyau kasancewar yau gyaran fuska yaje aka masa sbda yakara daukar hankalin ta, Wai kai wan.......... Yadaga mata hannu Dan Allah kisawa xuciyarki salama yaukisaurare ni koda saudaya ne Shamsiyya haba wlh xahirin manufata itace macen aure nake nema tagari 'yanmata sai Ahankali kekanki kinsani wannan shine irin gwajin danake yi musu amma bansamu nasara ba sai anan donhaka kinsan baxan barki ba muddin inada rai kinada shi pls ki fahimceni ki kuma amshi soyayya ta, Harara tacilla masa Au gwaji gwaji tab kadade bakayi gwaji ba toh koda dagaske kake nifa banaso donhaka kawai ka kyaleni nayi rayuwa na haka bana ra ayi ba irinka nake so amatsayin miji va ni donhaka kagane kaima kajanye naka ra ayin Tajuya dasauri xata koma yasha gabanta Bantaba tsammanin xaki min haka ba kalar fuskarki ba ta iirin yadda kike magana bane haba kinsan kwa irin yadda nake sonki kuwa? Humm shikenan baxan barki ba amma nabaki sati daya kikara tunani akaina daga wannan time din dai insha Allahu mutkar baki amince min ba toh xan hakura xankyaleki kuma kamar yadda kika bukata Yajuya tare da bude mota yashige yatafi Daharara tarakasa Mustww aikin banxa irinsune sungama iskanchi xasu xo su samu yara su aure wlh niba 'YAR iska bace baxan auri dan iska ba tasakai xata shige gida. Da babanta tahadu xaitafi sallar mangaruba Abba adawo lfy Yawwa Shamsiyya wanene yaron dayakira ki daxu? Abba Aisar ofisa ne Yaxaro ido Ikon Allah dakansa kuma yaya toh kinasonsa ne sai amasa magana kafin axumi nakeson miki aure insha Allah Aa Abba gaskiya dabi unsa baimin ba kuma Abba shidin kamar dan is........... Yadakatar da ita Baki da hankali ne Shamsiyya uban ki yafadamiki Aisar haka yake kwa kinsan dan wanene kuwa? Toh wannan yaron dan babban gidane kuma dan malamai masana ilimi kuma haka suke salon neman auren su yana xuwa tahanya daban daban toh ke axahiri yaxo miki akalarsa aiba shidaya xaixoba damasu takamasa baya sama da biyar shasha sha Allah yasa bakin fadamasa bakyason nasaba Taxumbura baki Banfadamasa ba lokaci dai yabani Toh allahamdulillahi haka ake so ai daya xo kice kin amince saikuma asan yaxa ayi Allah yayi albarka shige ciki bari ni nakarasa masallacin naji anfara kira Toh Abbaba Umma nagama shirya wa xantafi kayana na mota da motana xanje sbda kinsan yanxu dai bamu da kudin daxan biya najirgi san.... Ke rufe min baki tinda ninaxama abar tsokana awajenki toh yayi yanxu kubrah sbda bakin hali ki xauna kinemar mana kudi baxaki xauna ba kina kallo haka xanxauna harkokina suntsaya kenan Umma muna da sauran kudi fa samada milion uku ahannun bakaku miyasa baxaki kirasa kice yadawimiki dasu ba ni wlh nabar miki sbda yanxu nabar harkar karuwancin nan aure xan dan haka dan Allah karki ki kwarara min gwiwa umma kitayani da addu ah yadda nai istibira i Allah yasa Muneeb ya yarda da soyayya ta yadawo gida aimana aure, Humm umma tajuyar dakai sbda gaba daya bataso kubrah xataje maiduguri ba don dai kawai ta makale ne Shikenan na amince kije Allah yaba da sa ah shikuma bakaku xanje hargidan nasa nasamesa muyi wacce xami tunda yaxama dan iska yau kwana biyar kenan ina kiransa awaya yana kashe min bansan dalilin ba Nagode umma natafi kibi Ahankali dan Allah karki ja bakaku kuyi rikici umma Aikwa uwarsa xaici wlh don Allah kinji nafada miki saina kwala masa wulakanci kafin na amso kudinmu dukka kuma nayanke dik wata halada dake tsakanin mu dashi Kubrah tasakai tafuce tabar umma dabarin baki akan wanda baisan tanayi ba Amarya amarya ta ango Abdul yafara mata kirari Murmushi tayi tana cewa Anyini lfy? Lfy kalau amarya ai ina xaune tare da maman farra naga kiran mutumin nace ko lfy ina dagawa yace ai kiran amarya ne naxo naci girki nace kai ta samu kenan dan mukam aibadaga nan kwasar girki Suka sa dariya shida Nu'uman itadai murmushi kawai take sbda ta fuskanci Abdul akwai barkwanchi ga dan banxan surutu. Sunchi abinchin sosai Abdul duk ya mamaye dakin da surutu Nu'uman sai wai gi yake masa da tum tum tabaya baigani ba saboda hira taci kai Ai ina fadamiki amarya dan fulanin nan fa daya ga anata tafiya bishiyoyi na tafiya yaga ko ina akayi bishiyar wurin itama tafiya take aikwa saiya kalli direba yace asaukesa shi ga bati baxai yarda yakashe kudinsa ba akayi akayi dashi kar yasauka domin bishiya bata tafiya amma dan fillo yaki saidaya sauka sai hararar masu hanasa yake dayimusu kallon 'yan bakinciki ne kawai sunga kudinsa xasu huta anasaukesa yanufi wata bishiyar mango yahau yarike reshe daya gam yasa kayansa agabansa yana dada gyarawa Ke bishiya kano xaki kaini muje Shuru yaji taki motsa wa yayi maganar yayi amma bishiya taki tafiya daranshi yabaci saiya ce Ke bishiya yau ko baki kaunar Allah saina more ki naga kema kinacikin masu min bakincikin kudina su huta yauko ko xankwana anan saikin kaini kano da ai tafiya kike saidana hau kika tsaya donhaka yanakan bishiya har yamma tayi saida yunwa ta ishe shi sannan yasauko yana hararan bishiya Hala ma arniya ce ke don mutum mai salla baxai abindakikai ba, ๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚ Yatafi Fujjilat dariya har darike ciki tacusa kanta acikin hijabi sai dariya take haka Nu'uman labarin yamasa dadi yayi dariya Abdul kuwa yacigaba da xura faten doya wanda yasha kifi sosai juya wa yayi domin daukar wayarsa dake ringin yaga ankewaya masa tum tum wajen biyar yafahimci waigine Nu'uman yayimasa Yayi dariya Dan iska au har wani waigi kake samin bagashi ko yanxu nabaku nishadi ba Suka kuma masa dariya Nu'uman yace Toh aikaidin ne saida waigi wannan xuba baka gudun ka kware gashi sai lodar abinci kake kai ai maman farra na kokari Abdul yakallesa cikin maganar su wacce sukadai suka gane Kwarai kuwa bakaramin kokari take daniba wlh kaganni nan akwai shegen cin abinci Allah yasa kaima kaxama ni Nu'uman yafahimci inda yadosa donhaka yakalli fujjilat saiga baiwar Allah sam batagane ba sai game dinta take awaya Kaifa dan wannan maitashin ne mai yasa kake haka ne Abdul Abdul yamike yana sa hular sa Nitafiya maxanyi adaina min waigi amarya ga ango nan sai aita hakuri dan Allah kinji Allah yabada xaman lfy Nagode agaida maman farra Xataji yafuce Nu'uman yadaga masa hannu daga kofa Abdul yajinjina kai Abi ta Ahankali dai farin shiga naga sai rawar kai kake Nu'uman yamasa dakuwa tare da rufe kofar falon, Fujjilat Na am ta amsa tana dago kai Tashi muje ciki miyi sallah Toh kawai tace tamike Bayan sun idar ne sannan suka fara shirin kwanciya nace Toh saida safe ango. Ubaid Lokacin dasuka gama duba rogo sam ba fujjilat donhaka yasan xa a iya baxa nemansa jami ai donhaka yabar kasar yayi india ummi ma daga baya tabisa acan ne yahadu dawata bahaushiya 'yar adamawa ce karatu ne yakawota nan sunanta mamiyo saleem soyayya ce tashiga tsakanin ta da Ubaid abin yakai da har manya sunyi magana anbasa aurenta daxaran takammala digree inta xa asha bikinsu da ita, wannan kenan Maiduguri Ahankali Muneeb yafahimci Aysha Mohini tanada hankali kuma surutun ta bashine ke nuna batada kamin kaiba aa tanada kamin kanta sbda yafahimci tanasonsa amma taki fadamasa daga karshe ma ranar juma ah agabansa daddy yatambayeta ta amince da musab yayi masa magana dafarko Muneeb tadago takalla saikuma taga shi ko inda take bai kallaba saita yi kasa dakai Daddy shikenan na amince yafuto Hawaye suka xiraro a idaninta Daddy yadubeta Aysha menene kuma na kukan? Bakomi daddy koda kasani baxaka iya bani abindanake so dinba kamar yadda nakasa samawa kaina shi donhka kukan shine kadai abu mafi sauki daxanyi naji sanyin xuciyata ayanxu Mama takalleta Bakya son musab din ne yanxu kokwa? Aa mam Xatakuma mata magana daddy yadaga mata hannu Ya isa aliya kyaleta Allah yasa shidin yaxama alkhairi agare ki Aysha Amin daddy Tabar falon tana kuka Tundaga ranar abin yadami Muneeb yake ganin rashin kyauta warsa agareta tanuna kunya da kawaici amatsayinta namace amma yakasa mata adalchin xuwa gare ta, kuma yanajin wani abu akanta sosai kusan tun farkon ganin sa da ita amma yaki ya danganta haka da jikinsa balle yahaye sama xuwa xuciya yaxama so yayi baiji dadi ba yadda yake ji akan fujjilat haka fa Aysha take ji kenan akansa, baxaibar 'yar uwarsa tashiga wani hali ba donhaka xaimagana da daddy kawai yau, Xaune yake adakinsa yana rage wasu aikin office Muneeb yashigo da sallamar sa, Aa kaine Wlh daddy Toh yayikyau ya office din Allahamdulillahi daddy Yayi yayi ai Allah yasa lfy naga bakin naka kamar da magana ko Muneeb yayi murmushi yana sunkui dakai Hakane daddy shine ma yasa nace toh bari naxo nasameka anan din muyi maganar Umhum inajinka Yakara kasa dakai yana sosa keya Aa yadai kai maganar ka bakomi Muneeb Daddy dama akan Mohini ne nace ina baka yi wa iyayen musab magana ba Eh bansamu nayi masa magana ba sbda wasu uxirir rika dasuka hanani amma wani abin ne kuma Muneeb Um am dama daddy nine nake sonta kuma itama tanasona kawai mundan samu sabanine yasa tace kaima musab magana Daddy yayi dariya Allahamdulillahi ai haka akeso gida bai koshi ba kuwa kaga ai ba aba makwabta ba toh Allah yayi muku albarka naji dadi sosai Kamar yanitse akasa haka yakeji amma yaji dadin yadda daddy yanuna farinciki akan abin saiyaji soyayyar Mohini ta kara ninkuwa acikin xuciyar sa Ranar asabar Alhaji adamu yaje maiduguri sbda kawu isa yakira sa sunyi waya akan maganar Aysha da Muneeb yaji dadi donhaka ranar dayaje akagabatar da baiko daurin aure nan da wata biyu dayamma yadawo gida yaba mami lbar i itama taji dadi Dayake umma nafalo taji duk hirar don har sa baki tayi sbda bataji dadiba Alhaji wa kake maganar wai ansawa rana yau ne Muneeb ya akayi? Alhaji kubrah fa tatafi wurinsa yau din nan sbda maganar soyayyar su amma saikaje ayi kulla kulla dakai abasa wata ga 'yar uwar sa kuma datake sonsa fa Alhaji Waye yafadamiki yanasonta shi toh ita Aysha ba 'yar uwarsa bace kenan kinga kima ce tadawo kawai xaifi muku don duk wani makircin ku inasane dashi da duk abin da kubrah take nasani kwanan nan akagayamin komi da yadda kukasamu kudi kikai min karyar kawar ki indo ce tabaki aro kike kasuwanci yanxu nasan komi nakyaleki ne kawai sbda ishara kuke gani yanxu baku ga komi ba saima nangaba don kikwana dasanin cewa tamkar kinbar gidannan ne jibi mutkar akwana biyun nan kubrah bata fitar da miji nadaura mata aure ba wlh saina sake ki kuma duk igiyoyin xandatse nai nadamar aurenki safara u kin asara Kuka tasa tana neman yafiya dakuma yajanye maganar saki amma ko kallo bata ishe saba daga karshe tashi yayima yabar mata falon sai mami ce tai tabata baki, Ba shiri tadau mayafi tanufi gidan bakaku sbda yanxu babu wanda xai iya auren kubrah saishi Yana ta kokarin ganin yarufe gidan sbda barin kasar ma xaiyi duka sbda nemansa ake ruwa ajallo shi da hajia mamu sunje sunyi danfara agidan wani hamshakin maikudi asirinsu yatono mai nafef ya aje umma tataho gurinsa yagama rufewa xaishiga mota Bakaku bakaku bakaganni bane? Idan naganki uban me xanmiki Gaban ta yafadi jin yaxage ta kaitsaye Haba Alhaji yanxu koba nera ta daya ahannunka aibakamin wannan katon xagin ba wanda tun ina karama akagama min shi Balle nera milion uku da motsine namu ahannun ka donhka dole ka saurareni naxo gunka natarar kana rufe gida idan xaiyuwu mukoma ciki xan magana dakai wacce takawo ni daban ni yanxu Idan kuma baxai yuwu bafa kinga sauri nake komi xaki fadamin kifadamin xantafi abuna Alhaji maganar kudina itace afarko inasonsu daga yau xuwa gobe nakira ka awaya sama da ashirin kaki dagawa bansan me kuma muka yi makaba duk kawatsar damu saikuma magana tabiyu itace inaso dan Allah ka taimaka min Alhaji ka auri kubrah Idan ka amince kuma nai maka alkawarin xanma sadaki da karin kudi dubu dari biyar kadauka ma acikin kudina na gurinka abun sauri ne gobe nakeso kaxo gidan da magabatanka gun Alhaji adaura sbda aure na yakubuta daga tarkon da Alhaji yadana masa b............ Yadakatar da ita sbda tundata fara maganar ma dama akaikaice yake kallonta Baxan auri watsatstsiyar 'yarki ba kuma kudi nacinye ke bakisan wane ne nibako toh kiban gu nawuce kota shafe ki wlh Ehu umma tasa tana xubewa agun takara sakin wani ehun tare da kururuwa mai sauti kaf gun yadauka tsaki yaja yana hambareta da kafarsa yashige mota kafin yatada motar 'yan sanda suka gewayesu kusan su asharin kowanne hannunsa rike da bindiga Su biyar suka karaso jikin motar daya yabude suka jawosa dakarfi yafado kasa suka cacimesa suka mikar tsaye Ankwa suka makala masa ganin haka yasa umma maida ihunta ciki tana mikewa tsaye Baruwana wlh nima cutata yayi kukama tsinanne bayan sata ma shegen maxina ce wlh yalalatamin 'ya ya........... Wani dan sanda yakaimata hambara Kusamata ankwa munafuka tare suka oga yace damace dama umma na kururuwa haka suka samata ankwa sunxata itace hajia mamu din ehu take tanafadi ba ita bace amma ina suka dannata amota sai policetion, Maiduguri Ahotel kubrah takwana kasancewar tayi dare sbda tabiya gidansu kawarta acan tayini sai yamma lis tadauko hanya. Mohini tayi kuka harta gaji tunda tasan anyi baikonta yau kwana hudu kenan amma kullum cikin kunci take tun ranar takashe wayarta sbda karma musab din yakirata yanxu haushin sa takeji bata taba tsammanin so naxama kiyayyaba sai yanxu da lokaci daya soyayyar Muneeb tadanne ta musab har take kokarin juyata taxama kiyayya miyasa ma na amince kuka take sosai hartagaji ta share Ranar mondy hanifa dayamma taxo gidansu mohini sbda wani abin daya rikitata haduwarsu da musab amakaranta jiya da maganganun daya fadamata akan Aysha sunkusa fada dakyar sauran dalibai suka shiga tsakanin su Mohini naganin hanifa ta fada jikin ta tanasakin wani sabon kukan Wayyo hanifa wlh sonsa xai kashe ni inasonsa wlh shi kadai ninakeso amma nacuci kaina yanxu anba musab aure na Harara hanifa ta dankwala mata masha Allah dama hanifa akwai maganai kam tamkar su fado Mekikace? Mohini tafara sharar hawaye Nasan kinji kiban shawara kawai dan Allah Hanifa ahasale ta tureta gefe tana fadin Kinga wlh karki sake xub da hawaye agabana don yadda nake jin haushn nan xan iya tafiya in kyaleki da wannan rai nin wayon, wannan ai wani salon iskan ci kawai inba hakaba yaya kukeso kurabamun hankali ne eeye haba mohini aiko bansan kinada wani saurayi daban ba ke mai iyafadamin ce ko amma ashe bada musab akasamiki rana ba kikace min dashine jiya dakinga yadda muka kare dashi amakaranta dasai kince baitaba saninaba aduniya tarata yayi fa kaitsaye yana fadan munanan kalamai akanki da fadin kinyaudareshi ke ba 'yar manya bace anyi karamar magana waye yamutu waye yay rai alokacin raina yabaci nakusa kwashe sa da mari kinsan banadaukar nonses ni wlh sannan kuma yanxu nasameki kina kuka akan me wai maye gaskiyar lamarin ne kuke boye min Mohini? Mohini ta xaro ido fuskarta dauke da murmushi sbda fatan ta Allah yasa amin bada musab akamata baiko ba toh inba shiba da waye ai ita batace ma daddy gawani saurayi ba bayan musab kodai wani daddy yabata daban Hanifa dagaske wai kike ko wasa wlh iya sanina musab mukai magana da daddy amma miyasa abin yacanja Au kema wai baki saniba Wlh bansani ba amma dan Allah muje mutambayi mam Tare suka mike xuwa falon mam Koda suka tambayeta sai kallo kuma yakoma kallon kallo tai murmushi Aa yayan naki baifada miki bane? Shuru sukayi nawani lokaci kowacce tuna ni take wanne yaya kenan Mam waye yaya haka mam dan Allah kifadaman Ke nifa banason shirme da shiririta saikace dacan ba tasaniva toh waye yayan naki bayan Muneeb Ai mikewa Mohini tayi tafara dariya Mam dan Allah hanifa kinji yaya Muneeb ne xai aure ni Saikuma taruga da gudu dakinta sbda taji kunyar mam Hanifa tabita suka xube bisa cafet sai mamakin abinsuke itakam mohini murna tacikata ba abindake damunta yanxu toh amma daxai aure ta sonta yake kome? Hmmm xuciyar ta tace kedai kam tunda kinasonsa kobaya sonki ai duk nomarl ne Ahankali kin koya masa sonki Tai murmushi dafurta yesss! A office game da Muneeb shima yau yabari akan xai magana da mohini idan yadawo Kubrah na

Chapter 10 of 12