Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tsaye bakin get din gidan maigadi yahanata shiga motar Muneeb tadanno kai layin murmushi tasaki sbda taganesa wannan motarsa ce tun agida Ransa abace yakaraso sbda yahangota shima tsayawa yayi tare da xuge glass yaleko dakansa Tamatsa gunsa Yah Muneeb barka da yamma Saukar yaushe kekuma? Yajefa mata tambaya Daxu naxo ina nan tsaye getman yahanani shiga Ok yace yana danna kanmotar cikin gida dama tini maigadi yawangame masa kofar get din Saida yayiwa baba akram magana sannan kubrah tashigo Muneeb ne yashigar da ita wajen mam time din Mohini anata buga game atv ita da abbas aliyu nayimusu alkalanchi Ganin Muneeb da mace yasa tatsaya sai harara take kwalawa kubrah musamman yadda taga tana kallon Muneeb kamar ta hadiyeshi danye, Afasace tabar falon tai waje sbda hawaye sunkusa xubo mata Muneeb yakula kwarai yabi bayanta yana danyin murmushi kasa kasa kai wannan yarinyar rigima fa xatai ni daban taba cewa inasonta bakuma take kishina har haka inakuma da munyi aure tasamu soyayya ta, kai haka yakarasa futa yana maganar xuciya kubrah tarakasa da ido sbda kamar takusa fahimtar wani abu Jikin katanga ta labe tana sharar hawaye bataji motsin xuwansa ba saijin maganar sa tayi gefen ta Me yafuto dake waje Aysha? Kasa tayi dakanta sbda batada amsar basa sbda itadai alal hakika son sa takewa kuka kuma baxata iyafada masa hakan ba Bakomi Tafada muryar ta narawa Yakara matsawa kusa da ita Aysha karki min karya mana ba dalili ana kukane? Tagirgixa kai Yacigaba da cewa Karki damu daganina da kubrah kanwata daga kano gidan baba Adam nasan kinyi xaton ko budurwa tace ko aa aini banda budurwa bayan Aysha Mohini Idaninta akansa kamar amafarki take jin wadannan maganganun donhaka take kokarin farkar dakanta yah Muneeb dakansa kenan yagane inasonsa har ina kuka Kamar tanitse agun haka taji da gudu take kokarin xubawa yatare hanyar Aysha inasonki kuma tunfarkon ganina dake nake sonki nine naje gurin daddy nafadamasa inasonki kema kina sona shiyasa kikaga wancan labarin ya chanja Yah Muneeb wannan wasa ne ninasan basona kake ba kanaso kai amfani da damarka ne kawai taganewa dakakeso kayi inasonka kamar yadda kake xargi ko Yagirgixa kai Ko daya ninariga fara sonki kawai nadanne ne araina sakamakon wahala dasoyayya tabani Tarufe fuska Karka damu insha Allahu xanbaka mamaki yah Muneeb xakasameni mai biyayya da soyayya agareka nidai fatana ka rike ni amanaka lallashi sona tamkar kwai Ya lumshe idaninsa yanajin tamkar yasamu fin fujjilat kam yanxu Bakomi kanwata Allah yasa mudace dik inda kikesona xanxam miki haka da yardar Allah Amin yayana, Saikuma suka kalli juna suka sa dariya. Kwanan kubrah daya tafahimci soyayyar dake tsakanin Aysha Mohini da Muneeb tagane kota kanta baya bi yaki bata lokacin sa balle yasaurari abindata xo dashi yau dasafe taji mam namaganar bikin Aysha da Muneeb biki ya matso saida ta suma sau biyu aikuwa tana farfadowa tace gida xata taho bayadda daddy da mam basuyi da itaba akan taxauna amma taki dakyar ta iya kawo kanta kano amai take sosai harda jini jini mahmud ne yakai ta hospital game da umma kuwa tana can hannun 'yan sanda tasha bugu sosai duk kamannin ta sun sauya Abba kuwa bai jeba haka mahmud sbda yahana umma wannan shige shigen namutune batasan ko wa 'yanna iri bane tarika hulda dasu, kwanan umma biyar ahannun hukuma aka kamo mamu sannan aka saki umma Alhaji bakaku duk da yadda yake ciki nahalin jina jina saidaya yiwa umma dariyar mugunta sbda yana sane tunfarko yaki fadar ba ita bace hajia mamu sbda aci ubanta Tana shigowa gida Abba yabata takardar saki kuma saki uku tasha kuka da birgima dakyar ta iya karasawa gidan hajia lami Haisam na kofar gida yana ganinta yanufota tare da xare balet sbda itace tajaja masa duk abindaya faru dashi akan fujjilat juyawa tayi tana sakin kuka Basai ka dakeni ba xan tafi Tanufi titi tana nadamar rayuwar datayi da mutane ba aji dadin xama da itaba ko ina ta raba hali kenan kaitsaye gidan hajia indo taje ita tabata gu takwana dagari yawaye tabata kudin mota tadau hanyar sakkoto asalin garinsu kenan wanda shima silar barinta garin cikin shege datayi sau biyu yasa babarsu ta dawo da ita hannun hajiya lami anan Abba yagahadu da ita. Kubrah satin ta uku tasamu sauki Dr Naufal ke kulada ita sosai tana birgesa yanason mace mai ibada da sanyi duk da bata da lfy amma akwai kokarin yin sallah kan lokaci kuma dan xaman datayi ahospital dinsa yaji yanasonta kuma aurenta xaiyi daya tinkare ta da maganar tayi kuka sosai tace ita baxawara ce kar ya aureta yace shidai yanasonta kuma komi cece ita xai iya aurenta mutkar tana sonsa kuma ta tufa, take tai masa alkawarin ta amince, ranar monday aka sallameta amotar naufal yamayar dasu ita da mahmud Abba ko sannu baimata ba gaisuwar naufal kawai ya amsa sannan naufal yane mi xaimagana dashi bayan sunkebe yake sanar masa abindaya kawosa Abba yaji dadi kuma yace bakomi yaturo manya Dr Naufal yaji dadi sosai donhka yakoma gida cike da farinciki yasanar da babansa. Game da Shamsiyya kuwa andai dai ta da Aisar har manya sunshiga antsai daranar biki donhka ma fujjilat nahango taxo ana shirye shiryen kamun Shamsiyya daxa ayi gobe Amarya sarkin kamshi Shamsiyya takalli fujjilat Kinga kwata kwata bantaba xaton xan auri Aisar ba wlh Fujjilat tace Ikon Allah kenan ai bakya gani ni da my husband yadda Allah yahada abin bawanda yayi xato gashi kuma xaman mu lfy ina alfahari da miji na Shamsiyya mijine nagari mai son farinciki na Allah yabarku tare kawata Amin wai gobe xamu jeren ko sai jibi? Um um gobene daxu daya kirani awaya yace xai xo da daddare sai a amsar muku key kawai Ok shikenan aituro wa xai adauke muko don kinsan baxan yarda da tukin mace na ganganci ba sbda babyn baba kar ya wahala Shamsiyya tai dariya Kai kawata dan Allah fa kice naxama umma nima Fujjilat tashafa cikinta dake shafe lakam tamkar batacin abinci Kinsan Allah dawasa nake miki haba yau she ma akayi auren duka duka tsokana ce irin tamu da muka saba Shamsiyya tace Hmm nidai banyarda ba Allah baxaki rasa ciki ba fuj kingakwa yadda kikayi kumari sosai gawani asirtaccen haske daya bayyana aboye humm ciki dai dan dumane dakansa xai futo Sukayi dariya Ok ai kwa da my miji yaji dadi sbda yanason ciki sosai wai so yake yaga yadda xan rinka tura cikin yana turani Suka kyalkyale da dariya Kyau xaimiki Allah fuj wlh ciki xaimiki kyau Allah ko Kwarai makuwa Dayamma Nu'uman yaxo yadauketa tun amota yarumgume kayarsa da hannu daya dayan kuma yana tuki dashi, Nagaji baby Tafada lokacin dasuka sauka agida sunfito daga mota cak yadagata sai afalo ya ajiyeta saidaya hada musu rruwn wanka abaho sannan yadauko ta yatsinbula saidariya take yana mata chakulkuli tana dariya da wasa da wasa har suka gama wanka yasabota suka futo yana shafa gadon bayanta tare da kalaman soyayya masu dadi daratsa xuciya. Ubaid Ubaid tare da amaryarsa mamiyo anyi biki anan adamawa sun dawo india anan gidansa dake cikin birnin delhi abindayaso hadasa da matar tasa shine yadda yaji ta ba budurwa ba yayi fushi da ita sosai saidakyar tasamo kansa dayake itama wayayyiyace tasan kan maxa kullum saiyayi tinanin fujjilat daga karshe har mamiyo saidaya bawa labarin fujjilat itama tajinjina labarin sannan taji kishin fujjilat aranta matsananci ummi tarasu lokacin taxoma yole xiyara ciwo yakamata anan tarasu, Mamiyo cikin ta wata uku Ubaid yaji dadi badan kadanba fatansa ahaifi mace yasa mata sunan fujjilat koxaisami saukin abindake damunsa kullum akanta. Haisam yayi aure matarsa bilkisu habeeb yau wata biyu dabikin Fujjilat tahaifi danta namiji yaci sunan MU'ASSAM, shekarsa biyu tamasa kani MUKARRAM, soyayya tsakanin ta ko da Nu'uman allahamdulillahi saiyanxu tagane abinda iyayenta suka hango mata tabbas Nu'uman jajirtaccen namiji ne mai kulada iyali dasanin yakamata dan manya mai ilimin addini da na boko jaleel shekarar sa shida duk hutu agidan fujjilat yakeyi idan akasamu hutun makaranta shida Nu'uman tamkar yaya dakani haka yake daukar jaleel har mamaki fujjilat take yadda Nu'uman ke kaunar jaleel haka jaleel ma yake kaunar MU'ASSAM da MUKARRAM. Shamsiyya tahaifi 'yaranta biyu 'yan biyu kyawawa duka mata gwanin sha awa sunci suna fadeela da fahima, Ubaid Mamiyo tahaifi 'yarta mace aikuwa ya rattaba mata huduba da fujjilat ko uwar baifadawa ba sai ranar suna yake sanar mata aikuwa sunsha rigima daga karshe tayi yaji baiko kokarin binta ba yakyaleta kawai sbda haushi dama take basa akan yadda yasameta har yau burinsa kawai fujjilat karama tayi shekara uku ya amso kayarsa donbaxai barmata 'yarsa ba Bayan shekara biyu bilkisu matar Haisam tahaifi 'yarta mace Shima fujjilat yasa kuka bilkisu tayi sosai sbda sunan babarta takeso yasa amma yasa sunan budurwar sa ta dah satinta uku bata kulasa kuma bata kiran yarinyar dasunan fujjilat Momy take cemata. Kubrah da Dr Naufal amare yau wata uku kenan da bikinsu ita da fujjilat sun dai dai ta sbd kubrah har gidanta taje tanemi gafara suka shirya kansu watan ta hudu Naufal yace tashirya suje sugaisa da abbansa taji dadi donhka tashirya cikin kayan ta masu kyau Alhaji kaseem dake xaune babban falo hajia mairo gefensa tana basa labarin kubrah ai yarinyar kirki ce ga biyayya ko ido bata iya hadawa dani Alhaji Masha Allah aihaka akeso yaro yasamo 'yar mutumchi kwarai sunanta khadija ko Eh ai sunama hanya yanxu xakagansu sunkaraso Yayi kyau ai Sallamar su tasa Alhaji kaseem dagowa Kubrah! Itama ganin Alhaji kaseem yasa tadafe kirji tana kallon Naufal Shi shi shiiiiii shine daddynka? Naufal yadagakai Lfy menene shine kinsansa ne Alhaji kaseem ne yadabe agun tamkar matacce Naufal dama wannan karuwar ''YAR HANNU ka aura karasa matar aure kaf girman kano sai wannan 'yar barikin inna nillahi wa inna ilaihir raji un, Daddy miyasa kake aibata ta ni matata ba karuwa bace Mari Alhaji kaseem yasauke masa To dan ubanka wannan tasan ubanka tunda dai saina fada xaka gane ko toh sakata yanxu nace saketa yanxu konaci ubanka Naufal anan Kuka kubrah take sosai Naufal yakalleta Kubrah menene gaskiyar lamarin wai Hakane Naufal kasakeni kawai dan Allah baxan iya cigaba da xama dakai ba Alhaji kaseem shine mutum nafarko daya fara lalata min rayuwa yasani aharkar bariki tubana ma danayi ba ason ranshi ba shine y...... Ya isha kubrah nasake ki saki uku kije ki kwashe kayanki Abba kacuceni kagama da rayuwata dama abinda kakeyi kenan Abba hajia mairo ce tarike Naufal wanda yanagama maganar yayi baya luuuuu asume mugun kallo take jifan Alhaji kaseem dashi Wlh nima saika sakeni kuma saki uku mugu axxalumin miji natsaneka maxinaci mai cutar 'ya'yan mutane ke kuma xaki futa ko sai na illataki Kubrah takwasa da gudu tana kuka maitaba xuciya tatsani rayuwar ta gabadaya batakuma fatan tacigaba da numfashi kodata sanar da Abba abindaya faru bai bata raiba hasalima ita yafara kwantarwa da hankali yace karta damu Allah yakwo mata wani wanda yafi alkhairi, Dr Naufal yabar gida kuma yace kar Alhaji kaseem yanemesa Ubaid yaje hargidan su mamiyo yadauko 'yarsa mamiyo nakuka haka yatafi da fujjilat karama yanamata wasa Gidan Alhaji adamu yaxo domin neman gafarar sa akan abindayayi Alhaji adamu yahakura kuma yaji dadin jin Ubaid yayi aure har da 'ya takwarar fujjilat mami tagoya yarinyar sbda yadda tajita tamkar tata fujjilat din, Hayaniya tajuyo daga kofa MU'ASSAM ne yashigo jaleel kuma yariko hannu MUKARRAM bayansu kuma Nu'uman ne tare da madam fujjilat dake dauke da jaririyar 'yarta Amima, wacce batafi wata shida ba aduniya Aa yau kune agidan namu kuduka akai kai yau ango nake harda amaryar tawa Abba yace yana amsar amima daga hannun fujjilat Nu'uman ne yatsuguna yagaidasu harkasa Lfy kalau baban yara mami ta amsa tana kokarin xama Dariya sukayi fujjilat tace Mami inakika aro goyo kuma Sai lokacin mami takalli inda Ubaid yake xaune hankalin yatafi kan fujjilat tnda suka shigo yadda taxama babbar mace wacce tasamu hutu dajin dadi hade da kwanciyar hankali 'Yar Ubaid ce daxu suka xo gashinan ma kugaisa Kafin fujjilat tajuya Nu'uman ya juya danufan shakarsa amma kafin nan Ubaid yaxube bisa gwiwar sa yana basa hakuri akan abindaya faru Bayadda Nu'uman ya iya dole ya hakura suka rumgumi juna kasancewar su dama abokai Fujjilat jin labarin ummi tarasu yasa tayi kuka sosai. Yasunanta Fujjilat tatambaya Takwarar ki ce ai Dariya tayi tana amsar ta Masha Allah kagakwa har kama mukeyi Abba yace Aa amaya ta tafi hanchi Suka kuma sa dariya Haisam ne rike da hannun fujjilat baby bilkisu nabayansu sukayo sallama shidama duk juma ah yanaxuwa gaida Abba da mami Mami tace Yawwa dahna karasa shigowa mutuniyata ya akaje gida Taruko fujjilat baby tana mata magana yarinyar tayi dariya tana gwarancinta Haisam da Ubaid da Nu'uman suka gaisa cike da farincikin ganin juna fujjilat harda kuka ganin yara biyu duk sunanta akasa kuma kowacce domin ita akasa ta Ubaid itace fujjilat karama ta Haisam kuma fujjilat baby Ita da bilkisu hira tabarke har kubrah da tashigo badajumawa ba daga makaranta tadawo Mami ce dakanta tashiga kitchin tadafamusu abiinchi mairai da motsi fujjilat da bilkisu da kubrah kuma suka hada kala kalan lemo sannan akayi da ira ababban falo MU'ASSAM akwai rigima gashi babba amma akwai shagwaba yadage sai fujjilat ce xata bashi abinci abaki bayadda ta iya abba na tsokanarsa yaana make kafada yahaye cinyar fujjilat tarumgumeshi Kyale abba my sweety kaci abincinka Yaxobo baki Ammy kibani abaki Ok karkadamu dama wannan ai aikina ne ko agida Sukayi dariya Ubaid yakallesu saiyaji yaron yabirgesa sosai haka haisam ma fujjilat baby ce tadebi abincin tatafi bakin MU'ASSAM xata basa Akayi dariya shikuma MU'ASSAM saiya hangame baki xai amsa sai fujjilat baby tamayar kwano tana dariya saishikuma yasa kuka Dariya akata musu abba yace Aa toh nafasa baka ita tunda kuka kake mata tun yanxu kai bakasan wasaba gaskiya kuna shagwaba MU'ASSAM dayawa Nu'uman yayi murmushi Abba itace donni kaga nagidana nan MUKARRAM yafisa hakuri Fujjilat tace Hmmm kowa dai kansa yasa ni . yamma har Ubaid xai tafi Haisam ma sunfito mota tashigo Gidan Muneeb ne da matarsa Aysha Mohini saiciki haihuwa yau ko gobe Jaleel yadaka tsalle yadafe sa mami ta rumgumi Aysha Fujjilat sai fara ah take Muneeb yaharareta Madam ya iyali tunda kinmanta gaisuwa Taidariya Badole ba yah Muneeb kaxama uban gida sosai matar ka kyakkyawa wlh amma yah Muneeb kadaukota da wannan nauyin dakabari tahaihu inmukaje suna muka dawo saikubiyo mu bangajiya Sarkin surutu kawai ai itama a ce saiku hadu kuyi tayi Abba anyini lfy? Lfy kalau Muneeb ya hanya aibaku sanar ba xaku taho Wlh Abba naji inaso naxo kawai naganku ne Toh ai yayi kyau Juyawa yayi suka gaisa da Ubaid da Haisam sannan suka gaisa da Nu'uman. Ubaid ne yafara tafiya sannan Haisam Nu'uman kuwa saikarfe goma suka tafi sbda Aysha da fujjilat gayyar surutu anhadu bilkisu ce dama batakaisu surutu ba Kwanan su Muneeb goma shabiyu Aysha tahaihu namiji anan akayi suna 'yan maiduguri saixuwa sukayi yaro yaci sunan Adam suke masa lakabi da Abba karami. Mamiyo tadawo dakinta inda Ubaid yayi gininsa dankarere akano suka dawo fujjilat baby 'yar wajen Haisam da MU'ASSAM sun shaku sosai sbda duk juma ah sai sun hadu agidan mami abin kamar wasa fa yara son junan su sukeyi ga fujjilat karama itama tana son MU'ASSAM, Abba kuma yayi alkawarin aura masa su duka biyun fujjilat baby da fujjilat karama daxaran sun girma sun mallaki hankalin su. Zuminci ne yakullu tsakanin Muneeb da Nu'uman da Ubaid da Haisam abota ce mekyau da fahimta atsakanin su yayinda shawara ma tare sukeyi musamman akan harkokin su nakasuwanchi Haka bangaren matayensu fujjilat da bilkisu da mamiyo da Aysha kansu yahadu idan xa a maiduguri gidan Aysha sai ahadu duka aje abarwa mami fujjilat karama da fujjilat baby da MU'ASSAM da MUKARRAM sbda duk iyayensu cikine dasu fujjilat kuma goyon amima take, Mami nashan dariya da yaran musamman fujji karama da take dayawan jan magana daxaran taga MU'ASSAM da fujji baby sun xauna gu daya suna karatu xata shiga tsakanin su kota daki baby itakuma baby tabita da gudu MU'ASSAM yay ta sheka dariya yana yimusu kidi da roba saidai mami taxo tarabasu kowacce na kuka tabi MU'ASSAM saidai yagudu kotakama kunnensa ta murde yasa kara ko in 'yan tabarar na kusa yasa kuka shima yau ma hakace tafaru yau friday suna gidan mami gashi jaleel bayanan yaje gidan inna habi xiyara yanxu jaleel anxama 'yan samari kamar su daya da fujjilat saidai yafita tsayi ne shi, Mu assam ne rike da hannu fujji baby yana samata wani xobe da abbansa yasamasa shi jiya nagwal ne saidaukar ido yake takallesa Yayan mu (dayake suduka haka suke kiransa) Yakalleta Inajinki baby wannan xoven danasa miki ko Tadaga kai sbda gabadaya lokacin shi shekarar sa bakwai ita kuma hudu Eh yamin kyau yayan mu kabar min shi ne? Murmushi yayi irin nasu nayara Eh mana alkawarine wannan xoben baby inmun girma xaki aure ni? Tarufe fuska tana mikewa tana tsalle Laaa yayanmu dagaske xamu yi aure toh menene auren yayanmu? Dayake shima jiyayi anafada baisansa ba saidai yanajin dadin sunan abun amma toh menene auren yataba ji baba Alhaji yanacewa xai masa shida fujji karama da fujji baby Bansaniba amma baba Alhaji yace xaimin Sai suka kyalkyale da dariya Fujji karama ta na xunbura baki tataho Yayanmu mekukeyi anan Dariya sukayi tadau sanda tabisu sai gewaye gidan suke suna dariya har itama abin sai yaxama kuma wasa mami tai dariya tana komawa ciki sbda tanajin duk abinda sukeyi. Musahna Ayman ta aura kanin Haisam yau wata biyu dayin bikin Aliyu kuma luba don bikin Nu'uman da wata biyu akayi nasa yaransu biyu mace dana miji mumina da sageer watarana yaxo daukar yaransa dasukaxo part din fujjilat yadawo daga office dama luba batanan taje garin danginta nijar 'yar boko ce luba batasan yawo dayara har karamin sageer bata tafi dashi ba mumina ce ke taimaka masa yagyara wajen nasu yakwan kwasa falon kubrah tabude masa Sungaisa tace fujjilat ana magana yace Aa mumina xaki turomin kice abbansu yadawo Ok tajuya tana kiran Mumina cikin kashe murya Aliyu harkara lekenta yake sbda yadda take iyaya tsakanin ta da Allah dama yana yawan ganinta agidan amma baita mata kyakkyawan kallo irin nayau ba Mumina ce tadafesa yarike hannun tasuka tafi Tunda yahadu da kubrah yaji yanasonta gashi kuma mumina da sageer kullum basu da labari saina anty kubrah sun saba da ita sosai kusan duk lokacin dasuka shugo part din fujjilat suna saminta agidan Tana son yaran sosai sbda mumina akwai kwakwalwa tana kallo idan akasa musu gasar karatu ita da mu'assam yadda take kusan kuresa yadda take ma yaran yasa Aliyu yaji yakara fadawa asoyayya da kubrah baitsaya boyewa ba yabayyana ma fujjilat ita dakanta tayima kubrah magana kubrah ta amince ba adau lokaci ba kasancewar ta baxawara sati biyu akasa ranar lahadi aka daura aurenta da Aliyu tatare agidansa daya part din danayi bayani abaya part ukune agidan dama ansha daru da luba kasancewar itama kubrah bakanwar lasaba yasa abin yayiwa Aliyu yawa dakyar yasamu kansu sabda yakula luba itace tafi tsokana kuma amatsayenta na babba don haka yayi mata gargadi mai xafi wanda yabata tsoro sbda tasan laifin tane karin auren nasama duka sbda bata basa kulawa yadda yakamata sbda tana gudun karta tsufa da wuri. Nu'uman xaune amima rumgume akirjinsa mu assam yana karatun sa MUKARRAM kuwa sarkin cin abinci yana dani yana xubi shida Anwar dan wajen abokin Nu'uman Abdul hannun mu assam Nu'uman yakalla yana xare ido Mu assam xo ina xobenka danasa ma Yana dariya yace Abba nasama baby shi Fujjilat kafin Nu'uman yasake magana ta amshe O o ni fujjilat kaiyanxu wai yaron nan kalau kake kuwa bagwara kace itama asiyo mata ba inso kake kabatan Ya rike hannun Nu'uman yana wasa dashi Shikenan kabari kai xan siyo maka wani kawai kaji Toh Abba Miyasa toh ita kabata sai karama tagani tayi kuka kuma Yace Alkawari nabata mommy itakuma karama baruwana dakukanta tunda ita sa ido gareta Dariya sukayi Nu'uman yace Shikenan xansiyo musu suma ai har MUKARRAM da Anwar kitina min gobe sbda gudun rigima xansiyowa ma mumina da sageer. Shikenan abban yara dadina dakai gudun rigima bakason kukan yaran nan Yayi murmushi Maman 'ya'ya na kenan karfa kimanta xaman lfy yafi xama dan sarki, ba abindaya ragemin samada naga farincikin iyalina kullum mama na min addu ah akan al amura na na yau dagobe daneman min tsari daga sharin mutum da aljan agurin Allah , haka kema matata ina alfahari dawannan sannan kuma karki manta nikuma banda hanyar sakamuku samada in kyautata muku insaku farinciki dafatan alkhairi agareku, Lumshe idaninta tayi sbda bakadan bataji dadin kalaman sa Hakane abban yara amma kayi amfani da manya manyan maganganu wajen kara tabbatar min da nutsuwar mijina da kara cire shakku akansa ko tamtama babu mijine daya amma tamkar da dubu samun irinsa kwa ayanxu akwai wahala tunda axamanin bayan ma bakasafai ake samu ba Mu assam yace Mommy mommy Abban mu ko kin manta bakice kyakkyawa ba Abba mommy kyakkyawa ne idan mukafuta shopp mata sai suyi ta kallonsa shikuma yana shamusu kamshi Dariya tayi tana karasowa taja kunnensa Ja iri dakallonsu kake so yayi ko me MUKARRAM da Anwar suka kyalkyale da dariya ganin mommy da dan hannun dama andan samu kwafsin Mommy kunnena Tacikasa tana komawa kusa da Nu'uman taxauna Kajifa yaron nan fa da alama yaga amarya abangaren baban sa ali har yafara sha awarta a bangaren abbansa Yayi dariya Aa shifa yarintansa yana nufin bana kulasu Tahararesa Ummm tohm kare kanka Xankaresa mommy daxaran yagaji Abba kaji MUKARRAM kenan yafada yana tasowa tamkar boss kaikace afilm ne yadda yake hura hanci da jiki yatako irin tafiyan aftawa afilm idan xasuyi fada Nu'uman yasa dariya mu assam yarikesa Karya kake nine dai dai dakai ba mommy ba kuma mu bamason wani anty awajenmu MUKARRAM yayi kara Mu muna so abva indai kanaso Mu assam yarike kwalarsa Karya kake boss baxaiyuwuba kaikayi kadan kaja da ixzata karkamanta wannan shine yankina ni da sarauniya baby katattara akwalayen bayinka daga nan MUKARRAM akayi kara tare da darewa Hhhhhhh Yaro mankaxa kamanta waye dodon gomurxu wanda yaki ma tsoransa yake ji ko toh yau xantaka ixxar taka nahau saman isar ka nayi linkaya dan kasan isata akantaka take Tafi fujjilat da Nu'uman suka shigayi anwar kwa kudin Nu'uman dake bisa table yadauko yarinka watsa musu sbda actin din yayi kyau kuma Rumgume MUKARRAM mu assam yayi fujjilat ta rumgume su Nu'uman yarumgumo su duka jikinsa yana dariya Ashe kuna da kokari haka Fujjilat tai dariya Acikin littafin MUGUN MULKI sukaji wannan takaddamar tasarki shaddad dasarki sharman Masha allah na wacce Marubuciyar ne Kawata mana Shamsiyya Aa Shamsiyya danasani matar Aisar Aa wannan akofar ruwa take Shamsiyya Adam yumnah kenan littafinta ne kamar dawasa danaje gidanta nadauko nadaya Yaykyau aibansan taba ne kina boyeni Taharare sa Mu assam da MUKARRAM suka kara rumgume iyayen nasu Muna alfahari daku mum and dad.😇😇 ALLAHAMDULILLAHI WANNAN SHINE KARSHEN LITTAFIN 'YAR HANNU ALLAH YASAKA MUKU DA ALKHAIRI MASU BIBIYAR LITTAFIN SHAMSIYYA ADAM MATAR YAYA ALLAH KUMA YABIYA MANA BUKATUNMU GABA DAYA, DOMIN KI UWA TAGARI 😘❤ UMMA UWA TAGARI UWA MAI TAUSAYI 😇DA KYAKKYAWAN RAINO, ABAR ALFAHARIN MU😁 AKULLUM ADDU AH TA ALLAH YABIYA MIKI BUKATUNKI YAHADAMIKI KANMU👪 YABAKI FARINCIKI 😁 MAI TARIN YAWA DUNUYARKI DA LAHIRA INA KAUNAR KI UMMA NA💚 UMMA INASONKI💛 SO MAI TARIN YAWA.💏 Ku girmama iyayenku Ku so iyayenku sama dakanku Ku yi musu biyayya tamkar bakwa son kanku Ku mutum tasu kuga darajar su Karka xama mai sa bakinciki acikin xuciyar su Mahaifiya tafi karfin komi agurinka donhka katabbatar ka share hawayen ta daduk karfin ka na kudi ko addu ah ko kyakkyawan furuci kowanne da amfaninsa kuma darajar ka da martabarka karike iyayenka dakyau. ALLAHAMDULILLAHI. Littafi nagaba kuma shine ABOKI KO MASOYI Nanda sati biyu xamu fara antayo muku shi. Saidai nakudine batsada dari biyu kacal

Chapter 11 of 12