Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
wata murya na cewa Myzyd, myzyd, sai kuma sukaji wani irin qara daga dakin da gudu suka shiga dakin, Zaid ya kalli wacce ke kan gadon, da alamu rai yayi halinsa, ya tsura ma gawar ido yana so ya gane wacece amma ya kasa, fuskar ta chanza kamanni sosai Fusksrta duk yayi baqi fatarta ta fara kwayewa, kuraje duk sunyi fanchami a jikin, jikinta ba kyan gani, Zaid ya cire baki ya kira nurse, yace haka kuke barin patients? I dont think dis one is Alive now, nurse tace sorry sir, ta mutu, ai mutuwa hutu ne a gareta, patients din HIV+ ce, tunda mamarta ta kawota bata sake dawowa ba, kwanaki sai da mukayi cuffing hanayenta don cizgar gabanta takeyi ta na yagan fatar jikinta, Zaid ya girgiza kai waye likitan patient din? Tace ai Dr Maikudi ne, yazo ya dubata? Tace aa bezo ba, yace haba mana call him, dis patient needs RA, ya kamata a kaita Murtuary before ta koma wani abun, Rumah ki basu sadakan mu tafi, da alamu Zaid be gane ko wacece ba, Maysah da ta ganeta ta fashe da kuka sbd tsoron Duniya, dubeta da yar gayu, yar kwalisa mai iko da kasaita, dubi yanda Allah yayi da ita, tcae Yazayd baka gane ko wacece ba? Yace kinsan ta ne? Tace Badiyya ce, badiyya matarka ta da, wani uban tsaki Zayd ya buga ya ma badiyya wani mugun kallon tsana, yace die, Go to hell and burn to ashes, ya fizgo hannun Maysah yace mu tafi, haba Yazayd, lets help her, she needs us, Zaid yace me zan mata rai zan dawo mata dashi? Uwarta ta ajiyeta ta barta mu sai mu kwasa? Ka yafe mata pls, ta riga da ta mutu, ka yafe mata ko za ta samu wani saukin, yayi tsaki yace ke ya ka mata ki yafe mata sbd ke ta azabtar ni da taso azabtarwa Allah be ba ta iko ba, so sai ki yafe mata tace ni bata min komai ba, Allah bai barin irinsu, tace yazayd a dauketa a mata sallah, Da karfi zaid yace Rumaysah, shige mu tafi, sum sum Maysah ta wuce ta na kallon yadda gawar badiyya ya wulaqance lokaci guda a ranta tace Allah ya gafarta miki, ya ji kanki nidai na yafe miki. Zaid ko wurin be kara kallo ba, ya rufa mata baya, yace u reap wat u sow. Maiduguri Karfe 2 na dare, Zuciyarsa ta buga, da sauri ya bude idon sa saboda zafin da yaji, ya sa hannu ya dafe kirjinsa, rabon da yaji ko da ciwon yatsa ne an fi shekara 40, amma yau gashi zuciarsa har ta dara Zafih, tun bayan dawowarsa hajj yake jinsa wani iri, Musbahu Zailani yayi dan gajeran murmushi, a hankali yace wannan Ciwon Ajali ne. Gidan Gandu 6⃣2🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕 ⃣ Gidan Gandu🏠by 💕Biebee Isa💕by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕 Har karfe 4 Tsoho ya zauna zaman jiran mutuwa, ba mutuwa ba alamun shi, har ya far ji ana kiran Assalatu mutuwa ba tazo ba. Ya miqe jiki a sanyayaye ya nufi masallaci, sukayi sallah, ba wanda zai kalleshi yace yana da damuwa, amma shi yasan me ya ke gani. Dawowa yayi ya zauna kan kujerarshi a parlor, yan GIDAN GANDU suka dinga shigowa gaisheshi kamar ko wacce asuba. Be nuna ma kowa wani abu ba don be son ya tads hankalinshi, kuma be yarda suyi dogon gaisuwa kamar da, da suka fahimci kamar be son magana da sun gaisheshi suke tafia, Hajia Babba ce ta shigo, ta zauna gefenshi, Alhaji barka da Asuba, yace karime ta musbahu, tayi murmushi yace zauna kiji, ta zauna, ya shiga mata fira yana bata labarai masu sanyaya zuciya, cikin dabara yace wai idan na mutu ya zakiyi? Tace chap Alhj ai bana son ma tunanin mutuwarka, na fiso na mutu kafin naga mutuwarka, don na san ina iya zaucewa, yace haba karime, sai kace ba musulma ba, ai kinsan Qaddara koh? Ashe ba so na kikeyi ba tunda mutuwata zata sa ki hauka, ya turo baki, tace Alhaji ni na san ba wanda ya kaini sonka, yace Ahap, ai in kina sona bazaki taba bari wasu suyi man kuka ba balle ki, Addua kadai ce mamaci ke buqata, tace wai tsaya Alhaji, wannan maganganun na meye ne? Yace in banda abinki karime waya san gawar fari? So ake ko da yaushe bawa ya zama cikin shiri, Hajia Ama da Umma Hajja sukayi Sallama, suka amsa musu, suka zo suka gaids Tsoho, suka gaisa da hajia Babba, Duk yanda Hajia Ama taso ta hada Ido da tsoho ta kasa, tsoho ya qi yarda su hada ido, haka kurum taji gabanta na faduwa, ta daure tace Alhaji lafia kake? Murmushi ya fara yace Kalaw nake Aishalle, tace Anya? Hajia Babba tace ke ma kya fada, yanzu ya ke min magana me kama da wasiyya, duk na rasa gane inda maganar tashi ta dosa, Umma Hajja tace Alhaji ko wani abun ke damunka? Ka fada DonAllah, kar kayi nauyin baki, yace ku saurara kuji, shi fa bawa so ake ya zama cikin shirin mutuwa a ko da yaushe, balle mu da mu ka kwana biyu, mun tsufa, ba a sa gawar fari ba, ko ba haka ba? Duk suka gyada kai, to ku kasance masu dangana, ku kasance masu, tsoron Allah, ku kasance masu tuna mutuwa, tsoho ya saba musu irin wannan nasihar, to sai suka share fargaban da ke ransu sai suka dauki wannan nasiha ce kamar wacce ya ke musu kullum. Kuma ina roqon Allah ya hada min Hajjo, Aishalle da karime a matsayin Mataye na na Aljanna, ko a Aljanna baku ba kishiyoyi, ku din kenan duk suka yi murmushi, sukace Amin Alhaji Allah ya hada mu duka a chan, yace Amin Matayena, sanyin idanuna. Ku tashi ku tafi ina so na dan koma bacci, duk jikinsu yayi sanyi, sun san cewa idan tsoho ya farka da Assalatu be koma wa wani baccin sai wani daren, Amma yau yace zai koma, basa son sa abun a ransu ne shiyasa suka fita jiki a sanyaye. ****** Ya kalle su su sha takwas, tara maza tara mata, ya kalli yanuwanshi da ya riqa su biyu tun suna yara, ya juya ya kalli yaran Danuwansa Rabiu, su 5, yan ukku da yan biyu, sannan ya juya ya kalli yaransa. Sai ya saki murmushi, yace Alhamdulilah, duk suka zuba mai idanu, yace kunsan ba abun da ya kai Hadin kai dadi? Hadin kai wani abu ne idan da akwai shi a wuri, to ba abunda ya kaishi dadi, idan anaso a samu hadin kai to dole ku zama rufa ma juna Asiri, Dole ku zama masu yarda akan shawara daya, dole ku bi na gabanku, dole ku so junan ku, dole ku zama daya, dole ku zamo tsintsiya ma daurinki daya. Sai abu na karshe, dole ku tsaya akan junan ku ina nufin masu taimaka ma juna, idan kun hada wannan to kun samu hadin kan junanku. Jikinsu yayi sanyi, Aunty Abida ta fashe da kuka, tace Baba wani abu ya faru? Ko baka da lafia ne? Tambayar da sauran ke son yi kenan, yace bakomai Abida, Nasiha ce da na saba yi muku yau da kullum, Aunty Nuratu tace amma ta yau ta sha bambam, Baba ba ka lafia, ko a kira Dr Munnir? Yayi murmushi yace idan mutuwa ma zanyi Dr Munnir ya isa ya hana? Suka girgiza kai, ba wanda ya san gawar fari, ni dai ku hada min kanku, ko da ace wata ran bana nan, a duk inda nake Zan kasance mai Alfahari da ku, ku bi manyan ku, Mudassir da Labaran, sai yan 3, na baku Girma, na baku shugabbancin wannan Gida, Ku kasance Adalai, ku cire son kai, ku kasance masu son junanku. Baba Hassan da ya gane inda zancenshi ya dosa, ya rarrafo ya kama kafarshi yana kuka, yace Baba, kar ka tafi, ban mu taba kukan rashin mahaifi ba, kaine mahaifin mu, kai ne gatan mu, kaine katangar mu, kar ka tafi baba, idan ka tafi ya zamuyi,? Wa zai ciro mu daga baraka idan mun fada, Tsoho yayi daria sosai, yace kai hassan, wai kai yaro ne? Ka manta kuna da yara masu girman Zayd da Zayyad? Ku zaku kula da kanku, ni na gama nawa, ku ya rage kuyi naku, Hankali na na kwance ne saboda nasan kune manyan gidan nan, ba zaku taba bari Zuriyata ta gaiyara ba, zaku tashi tsaye kamar ina raye. Abunda nake so daga gareku shine Adduarku, da neman gamawa lafia, Aunt Sadiya na kuka tace ai wlh ka ma gama da dunia lafia, don ni na fi sa ka a cikin Shariffai, tsoho ya katseta, yace Aa Halimatuwa, kar kice haka, ba wanda ya san gaibu, ni dai Adduarku nake bukata, kuma bansan yan kuke kuken nan, ba zan ji dadi ku dinga min asarar hawayenku ba, bana son kukan ku, Baba Abbakar, ya fashe da kuka yace baba ka yafe mana, yace kul Abubakar, ba ku taba bata min rai ba, amma duk da haka na yafe muku Allah ya muku Albarka, ku tashi ku tafi, suka tashi jiki ba kwari. Sukayi Gaba, ya kira baba hassan, a hankali yace mai Be Strong Hassan, u are d Man here, kuma banason zaman makoki kaji? baba hassan ya kasa cewa komai sai daga kai da yakeyi kamar kandagare, ya fita da sauri. Magana ta zagaye Gidan Gandu, duk iyaye sun kira yaransu da ke wajen gari sun sanar dasu, wurin 7am Aunty Abida ta sanar da Zaid, murmushi yayi yace tsoho na son cimma wani abu ne, tace bangane ba, wlh abunda yake bari is more like wasiyya, zaid Tsoho na fama da internal pain, but becoz he loves us dat much ya kasa sanar damu, Zaid m scared to loose him, i love him, gaban zaid ya fadi, yace Mom noone is loosing Anyone, gamu nan zuwa. Hankalinsa ya tashi, ya shiga tada Maysah a hankali yace tashi mu tafi tace ina? Maid, lafia? Yace tsoho ne, wai be lafia, wani tsalle tayi ta fada toilet, donyi wanka, Zaid ya kira Jawad, jawae a rude yake yace ai gashi nan sun dauki hanyar Maiduguri, tun dazu Samir ya kirashi ya gaya mai, Zaid yace nima ga mu nan tahowa. Be safe brother ka kwantar da hankalinka kayi driving kajih? _Bibilicious Biebee_ Gidan Gandu 6⃣3⃣ 🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕Gidan Gandu🏠by 💕Biebee Isa💕 by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕 Da Tsoho akayi Sallar Azahar, mamaki kowa yakeyi, har sun fara tunanin ko dama nasihar ce ya ke musu dazun da asuba, gashi har anyi azahar dashi, nan suka fidda shakkun mutuwa, kawai dai nasiha yake musu, jikoki duk sun hallara, na nesa da na kusa, banda Zayd da Maysah, harta Zayyad da hanifa da ke lagos sun iso. Dama Islah da Mu'ammar ba su dade da dawowa Naija ba sbd Islah tagama Exams Wannan kenan. Tsoho kwance kan gado, yana kallon sama, jikokin nashi su 10 sukayi sallama, ya dan kallo su yana kokarin tashi, dama su yake jira, yace ga su gasu, duk suka bi suka zagaye shi, Ina Zaid Da Rumah? Jawad yace suna tafe don sun shigo maiduguri, sun kusa isowa gida, tsoho yace wani irin gudu Zaid keyi haka, Allah dai ya kiyaye, suka amsa da Amin, yace yauwa ku saurara kuji abunda zan fada muku, kunsan ance ba a son gawar fari ba ko? Toh bari na bar wasiyya incase na rigaku mutuwa, gabansu duka ya yanke ya fadi, yace, ina so d'a ko d'iyar Zayyad ya auri da ko diyar Mu'ammar, ina so d'a ko d'iyar Suraj ya auri da ko d'iyar Jawad, ina so d'a ko d'iyar Samir ya auri d'a ko d'iyar Zayd, wannan shine burina akan yaranku, idan anyi wannan hadin, sauran kuma na baya, na bar ma iyayenku, don bnsan iyakan zuriar da zaku haifa ba, iyayenku xasu zaba musu waenda suka dace dasu, kun gane wannan? Duk suka daga kai sama, yace yauwa, sai kuma magana ta biyu dangin turawa, bari muga idan akwai sauran turanci akaina, duk sukayi murmushi yace Afternoon tips, Love One Another, be there for one another, stand together side by side. Kunji? Suka daga kai, yace wato idan anyi mutuwa ba'a so ayi kuka, kuka kamar saukar garwashi ne a jikin mamaci, Addua kadai mamaci ke buqata, kun ga kamar ni nan idan dayanku ya mutu, kunsan me zanyi? Suka girgiza kai, yace zanyi murmushi ince Alhamdulilah, bazan yi kuka ba, ya kalli Islahulkhair ai ke ma bazakiyi kuka ba ko idan na mutu? Ta daga kai tace InshaAllah ba zanyi ba ya juya ya kalli fadila yayi murmushi sannan ya murguda baki yace ni bazanyi kuka idan kin mutu ba, kema ai ba zakiyi ba koh?tana kuka tana murguda baki tace bazanyi ba, yace hanifa fa? Itama kukan takeyi tace bazanyi ba, Bilkisu me gadon zinari fa? Tana kuka tana cewa eh tsoho bazan ma kuka ba, yayi murmushi ya kalli mazan da duk fuskokin su suka rikide sukayi ja, masu karyayen zuciya kamar Mu'ammar, Suraj, jawad da samir kuka sukeyi kamar mata, Zayyad kuwa fuskarsa ce tayi jaaa, Tsoho yace haba mazaje nah, be strong mana, m not dead already, just take care of ur wives, be there for them, value them, love nd cherish them, i will be there watching u all. I am proud of u all. Ina sonku duka ***** Ko parking be samu yayi da kyau ba, suka fito shi da Maysah, A sittin suka kwasa a guje, ba shi ba ba maysan ba, sukayi sashen tsoho, mutanen tsakar gida suka mimiqe don yanda suka ga zaid da maysah na relay sun zata tsoho ya mutu. rige rigen shiga cikin dakin sukeyi Lokacin da Maysah da Zayd suka hada ido da tsoho a tare suka saukar da Ajiyar zuciya, tsoho yayi murmushi yace sannunku da zuwa likita bokon turai da matarsa. Ruma matso nan kinji? ta matsa kusa dashi jiki a sanyaye, Zaid ma ya matso kusa dashi, Abunda Tsoho ya gaya ma su Suraj shi ya sake maimaita ma su Maysah, hankalinsu ya tashi, yace Ruma ai ba za ki min kuka ba koh ta toshe bakinta hannhn bibbiyu don wani kuka mai karfi ya zo mata, ta shiga daga kai tana bazan ma kuka ba tsoho, yace promise? Ta gyada kai tace eh tsoho, Ta ja da baya tana kuka. Lokacin dakin ya cika makil, Tsoho yace ku zo muyi musabaha, Assalamu Alaikum ya miqa musu hannu daya bayan daya suka zo suna bashi hannu suna amsa sallamar da ya ke musu, maza da matansu, manya da yaransu, kuka akeyi, duk yawan su sai da tsoho Yayi musabaha dasu, yace MashaAllah, kar ku manta, ku riqe zumuncin, Allah ya raya ku ya muku Albarka, Allah ya sa ku gama da dunia Lafia, Assalam Alaikum warah--matullah muryar tsoho ya sarke. Baba hassan ya shiga karanta mai kalmatush shahada, duk dakin aka amsa, ko wa ya shiga maimaita kalamatush shahada, Cikin ikon Allah tsoho ya amsa, ya maimaita kalmar shahada, yana kaiwa karshe malaika ya ida zare ransa, Allahu Akbar inji baba hassan, yace Allah ya masa cikawa, Maysah ta yi saurin kallonshi tace aa baba kalla fa, idonshi biyu, duba kagani murmushi yake mana, tsoho yi musu magana kaji, baba Mudassir ya matsa gurin gadon, ya shafe idon tsoho, ya rufe shi da zannin gado, Innalillahi wa ina ilaihir rajiun, kullun nafsin zaikatul maut, Luuuu, Maysah ta fadi kasa summamiyah, luu fadika ta fadi, bilkisu ta bita, hajia Babba ta zube itama, karan faduwan mutane kawai kakeji, haka suka dinga zubewa, wasu fargaba wasu tsoro. Allahu Akbar mutuwar tsoho tayi kyau, Uncle umar kadai ya yi karfin halin kiran dr munnir yace yazo da nurses gida ba lafia, Zaid tsaye gaban gawan tsoho, ko gezau beyi ba, fuskar nan tayi jaa, jijiyoyin kanshi suka mimiqe kamar zasu fito, tsigar jikinsa Suka tashi, be ma san wainar da ake toya ba, hajia Ama na kusa da zayd, ta tsura wa gawar ido, ta rungume hannuwanta saman kirjinta, ta shilla duniar tunani, Dr Munnir ya zo da emergency, hankalinshi ya tashi ainun ganin gawar tsoho, shima kukan yasa, nan nurses dinshi suka fara farfado da waenda suka suma, su jawad ds sauransu duk suna cikin masa suma, Maysah na farfadowa ta sake zubewa kasa, Hajia Babba ma ta farfado ta taso cikin zafin nama tayi gadon, Oh daman mutuwa zakayi shine ka barmin wasiyya dazun?ko banyi kuka yanzu ba Dole zanyi kukan rashinka nan gaba, amma nasan nima ina nan tafe, na kusa bin ka bazan iya rayuwa bakai ba, tayi saurin share hawayen idonta tace kuyi sauri a suturceshi akai shi makwancinsa na gaskia, Allah ya jikanka, ta ba kowa mamaki, Baba Hassan ya kalli Hajia Babba yace Mama ku za ku mishi wanka. Cikin Rabin Awa an gama yi ma tsoho ko mai, nan suka dinga shiga one by one suna mai addua, A lokacin yanzu suman Maysah 3, aka hanata shiga inda gawar take amma fir taqi tace sai ta shiga ta mai Addua, Uncle umar yace a barta, ta shiga ta dade ta na mai Addua, tana fitowa ta kara zubewa kasa. Mutuwar tsoho ya cika gari da ma kasar gabaki daya, yan unguwa suka cika gida, har shehun borno ya hallarta, Manyan mutanen kasa sun zo, kowa fadan halaiyar marigayin yakeyi, A Lallai sunyi rashin tsoho, mutum mai girma da karama, mutumi ne gatan talakawa, shine gineginen Masallatai da Islamiyoyi, kowa ya dauko matsalarshi kan tsoho suke saukewa don ya magance musu, duk fadin Girman Gandu haka aka cika gida Dam da mutane don sallahtar Gawan tsoho, aka gama sallah aka daukeshi aka kaishi gidan shi na gaskia, mutanen da suka suma a makabartar da yawa suke, sai dai kaji tim, kafin a ceto wannan wannan ya sake faduwa. Sun ga tashin hankali ba kadan ba. Mutane Suka fara watsewa, aka bar yaransa da jikokinshi kadai a maqabartan, suka dinga zuba mai Addua, da kyar aka raba su Zaid da kabarin tsoho. Suka koma gida. Hankalin a tashe, ko wannaensu na sonyi kuka, amma da sun tuna maganganun tsoho sai su shanyen kuka, amma hawaye basu daina xuba a idanuwansu ba, don wadannan hawayen ba za su iya tsaida su ba. Allah ya ji kan Musbahu Zailani, Allah ka sa Aljanna ce makomar shi, Allah ka ba zuriyarshi haqurin jure rashin shi Amin😪.. Gidan Gandu 6⃣4⃣ 🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕Gidan Gandu🏠by 💕Biebee Isa💕by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕 Ba su yarda sunyi zaman makoki ba, don yana daga cikin wasiyyun tsoho da anzo an musu gaisuwa suke saurin sallama bakin, Baba Labaran ya shaida ma yan unguwa cewa zasu cigaba da ga inda tsoho ya tsaya, duk me neman tallafi kar ya ji shamaki yazo ya sanar dasu. ***** Baza'a a iya bayyana tashin hankalin da yan Gidan Gandu suka shiga ba, duk yanda ake tunani abun ya wuce nan, bayan kwana biyu baba Mudassir ya umurci kowa ya koma bakin aikinsa, su koma garuruwansu, haka ko wannensu ya kwashi matarsa ya tafi, su hajia Babba kuma sai ince Allah ya sa a fita Takaba lafiya. Allah ya baku ikon jure Rashin Tsoho. 6months later Bauchi Football suke yi a dan karamin field din gidan, ko da Amira ta harba kwallon nan, be tsaya ko ina ba sai kan cikin Samir, da sauri ya fadi hannunsa riqe da cikinsa, yana fadin Wash Allah, ai tuni ta ruga gurinsa inda ya kwanta, oh no bigbrosamir, m sorry, shi kuma ya fara ihun karya, ta na duqowa yayi saurin dagowa ya rungume ta, yace thats all folk's, na rama jiya haka kika sa na rude da kikace na bugeki da kwallo, tace haba bigbrosamir ba haka akeyi ba fa, kai u seem serious, dis is cheating, ba zan yarda ba, yace sorry ma, a min haquri, ta maqe kafada tace nidai sai ka goyani,n yace done, ya duqa yace oya hau, ta danne bayanshi ya tashi yana guda da ita, ita kuma sai palla daria takeyi.ta manna mai kiss tace ina son bigbrosamir dina, yace inason lilsismeerahnah... Kano Billy nah, m home, Queen? Where are u? tana jin shi, ta boye bayan labule, ya ajiye brief case din shi ya shiga duka dakunnan bata nan, har toilet ya leqa be ganta ba, ya shiga kichin ba alamunta, hankalinshi ya soma tashi, Toh ina ta shige?while tasan bana so na dawo ban ganta ba, Bilkisu ta toshe bakinta sbd daria na son kubce mata. Hango kafafunta yayi ta labule, yayi murmushi ya miqe, ganin ya nufota ne ya sa ta fito tana kyalkyala daria. Ta yi hugging dinshi tace sorry my king, ya ja hancinta yace kina so ki wahalar dani ko Queen? Tace na tuba, ya maqe kafada kamar wani yaro, yace naqi din sai kin min kiss, tace oya kulle ido, ya rufe ido, ta daddage ta gantsara mai cizo ya saki kara da gudu tayi dakih tana daria, yace lallai yarinya kin kai kanki, yau sai na rama duk cizunan da kika min. Daga ciki tace haba king sorry mana u know i love u ryt? Yace i love you more shiyasa xan rama ya biga ciki tare da kullo kofar😏 Cambridge England Tana dawowa daga skul ta shiga kitchen, tasan Haniebunch is on his way home, noodles ta shiga dafawa, yana shigowa yaji alamun akwai mutum a kichin, a hankali ya lallaba ya shiga kichin din, ta dage sai juya abincin takeyi ba tasan da shigowan shi ba sai ji tayi an rungumeta ta baya, dan guntun ihu ta sake don ta tsorata, a hankali ya rada mata shhh, honeybunch, its me, murmushi ta sake, tace welcome honey i've missed u, i missed u more, ya juyo da ita ya sake rungumeta, yace i love u so much, i love u too, yayi hada bakinshi da nata ya fara kissing, abincin ya fara kwari alamun konewa, ina samm basu san yanayi ba, Islah ta fara jin kaurin yayi yawa da sauri ta dan bubbuga mishi baya, yayaya saketa, suna leqa tukunya sai suka fashe da daria, don noodles din ya qone qurmus, ta shagwabe fuska yaya u see ur life ko? Yace aa kice dai u see iur lives ko? Tace ni me nayi? Yace toh ni ma menayi? I was jus kissing my wife, Islah tace frm now on, ba ruwanka da shiga kichin especially idan ina ciki, yace wlh baki isa ba, duk inda kike nima kafana na nan, nd guess what, i've been hired at d IATA Training center, i will b part of d trainees, nd i will be paid thousands of pounds, Islahulkhair ta rungumeshi tare da sakin ihu, tace This calls for a celebration, yace je ki shirya, kizo muje mu dauki Zaineema Da Asad (sunyi aure) then we'll have our lunch. Tace okay honeybunch i love u, me more. Gombe Kwance take kan cinyarshi suna kallo, yace hanie nah, da Gombe da lagos ina kika fi jin dadin xaman? tace kai ma ka san nan ya fi dadi, gashi muna kusa da su Amira, nan ina ganin mutane, chan ko ba na ganin kowa, ai Wallahi na fi kowa jin dadin wannan trsnsfer din da aka maka, atleast i dont have to worry about that fatiti, Zayyad yayi daria harda riqe ciki, Hanifa kin ciki rigima, kinsan Atutu is my best frnd, ba komai tsakani na da ita, Plan mukayi ni da ita shisa tazo nan gida, ba wacce nake so sai ke Hanifa, an halicce ki ne don ni kadai, don ki zama matata, ina miki so mai yawa, i love u so much, theres noone in my heart just you nd u alone, hanifa ta rungume Zayyad, tace Yayanah, ina sonka nima sosai, i cannot live without u, sonka a jinin jikina yake, i dont knw wat my life wud be like if uo not in it, tace yaya tell dat ur besty if i see her leg in my house again, m going to cut dem all of, coz u are mine nd mine alon, Zayyad yayi daria, yace karki damu da Fatiti, coz she's married, kar ma ki damu da ko wacce mace kar ki manta no kishiya in ur Family's policy, tayi daria, yace one more thing kin kusa fara GSU, an samo admission din, tayi saurin rungumeshi tana i love u wallahi, thanks yayana, ina farincikin sanar dakai dat m two months pregnant, wani ihu Zayyad yayi ya tashi ya godema Allah, ya rungume matarsa kamar zaa kwace mishi ita yana fadin Thanks so much sweety, Atlast we gonna have a Musbah junior, tayi saurin rufe fuskanta tana daria. Kaduna Zaune take a kan carpet tana kallon indian Series, Jawad ya zo ya tsaya a kanta yana murguda mata baki, yo ita ina ma ta sani tana chan ta na kallo, Ya zo ya tsaya yace Ni wallahi sai nayi disconnecting dukka Wires din TV dinnan, idan ana kallo mantawa akeyi na dani, bama a da lokacina, ta miqe da sauri oyoyo baby, yace dont baby me sai ynx ki ka ganni? tace sorry mana, zo kaji, ya maqe kafada kamar wani karamin yaro, yace kuma idan nayi mafarki sai na gaya ma Tsoho abun da kike min, da sauri ta narke tace haba baby, kayi haquri ba zan sake ba, in short bazan kara kallon ba ma, kayi haquri kajih, yace to nayi a min kiss sannan a min wanka, sai a shafa min mai sai a zo a lallabani inci abinci kuma sai a lallabani nayi bacci, m a baby dats wat i do always, tayi daria tace yes u ar a baby, dole zan maka komai, don kasan i love u so much, ya ce amma kinsan cewa nawa son yafi naki yawa, da sauri ta girgiza kai wallahi nawa yafi, yace nawa yafi, ta bata rai kamar zatayi kuka tace wallahi nawa yafi, Ai Allah na kallona, ya zauna ya fara zuba mata shagwaba, hardasu a kasa tirjetirje kamar wani yaro yace ni bazan yarda ba, ni kice nawa yafi naki yawa, idan ba haka ba i will go for a hungerstrike, nd i wont bath again, tace lalala babban magana, naji naka yafi yawa, shikenan? Ya rungumeta yana daria yace yauwa baby, shisa nakesonki, kin san son da nake miki yayi yawa da yawa, ta mai gwalo tace amma nawa yafi yawa, ta zura a guje ya bi bayanta, suka dinga zagaya parlorn suna daria karshe ya samu nassaran chapkota, suka zube kan sofa, i love u baby, i love too baby. Abuja Ta shiga dakinsa hade da sallama, taji shiru ba amsa, Sweetie, where ar u? yana toilet yace here,get me d towel pls, tace me na ce maka kan shiga toilet ba towel? Kince na dinga shiga da shi, ayi haquri mallama a kawo mun, ta girgiza kai, ta dauko towel din ta yi knockimg tace gashi, yace oh no, na sa sabulu a fuska na, pls ki shigo ki kawo min, tace Yazayd isnt going to change, hop uo not planning something, yace no my love, i cross my heart, tana shiga ya danna ma kofa key, tsaye ta ganshi a bayanta yana daria, ta shagwabe fuska tace Yazayd plsss, wallahi yanzu nayi wanka, bakaga har kwaliyya na maka ba? Yace nagani kinyi kyau whch is y xan kara

Chapter 19 of 20