Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Naija sbd ita, InshaAllah zata son yadda zatayi ta ga ta rabu da Ya Suraj don kawai ta kasance tare da Umar, don har ga Allah taji wani zazzafan sonsa na shigarta irin son da ba ta ta ba yi ma wani irinshi ba, ko Yaya Jawad ba ta ji shi haka ba kamar Umar Z, dukda ba ta taba ganinshi ba, taji ya kwanta mata a rai, a bangaren Suraj kuwa jira kawai yake tace ta amince ya ci zarafinta, ya kuma kai qararta ga tsoho qila hakan xaisa ya raba auren nasu... (Bayan wata daya) CAMBRIDGE ENGLAND Islahulkhair an soma karatu babu kama hannun yaro, suna tare da zaineema a ko da yaushe, tana tsare kanta da addininta, da yawa na mamaki idan tace she's from Africa, Africa din ma cikin Qasar Nigeria, Wasu kan kirata Unique, coz she is, Akwai wani Bature da ke Koya ma Zaineema abubuwan da bata gane ba, sunan sa Asad, ya na ma Zaineema kirki, Akwai mutunci a tsakanin su, tun randa Zainee taje gunsa da Islah don ya koya musu wani abu ya rude, shi wai son Islah yake, Yau ma dai sunzo ya koya musu wani abu, yana musu explanation yana kallon Islah, da ya gama ne ya ja Zainee gefe ya ke fada mata yana son Islah ya zaiyi?, Zainee tayi murmushi tace ya sameta ya fada mata yace no neema m scared, tace dont worry, talk to her ursef, tun da tazo bata taba jinta tayi waya da wani lover ba, so kar yaji komai yaje ya sanar da ita, nan ya samu qwarin guiwar tunkarar Islah, tana zaune kan wani kujera ya je ya zauna kusa da ita daf da ita,Islah tace a ranta tace tooufah meye na zama kusa danih? Har zata yi mai magana sai dai ta basar, yace Islah do u have a minute? Tadan muskuta tace yes, ya ce Islah i dont knw how to say dis, but i'm in love with u, i fell for u since day 1,i want u to pls be my Girlfrnd, Islah da taji kamar ta rufe shi da duka don takaici, taga bata lokaci ne ma ta tsaya bashi amsa, ta miqe zata wuce, yayi saurin kamo hannuwanta yana fadin wait, holdon, ta juyo cikin zafin nama ta gaura mishi lafiyayyen Mari, hankalin mutanen gurin yayo kansu, Zaineema ta nufo su da sauri ranta a bace, mesa Islah zata ma Asad haka? Asad cike da mamaki, me yayi zafih haka? Islah ta nunashi da yatsa tace dont u ever think of laying ur hands on me again. Fuuuu ta wuce kamar zata tashi sama.... 4⃣2⃣ 🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕Gidan Gandu🏠by 💕Biebee Isa💕 by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕 Zaineema ta bi bayan Islah a fusace tana qwala mata kirah, Islah ta juyo itama a fusacen, zainee tace what d hell was dat? Islah tace wat d hell was wat? D next time he attempts to touch me, he'll get something worse than dis, ta wuce ta var Zainee tsaye, straight dakinsu ta wuce, Zainee ta bita, zama tayi kusa da ita, tace haba Isii meye laifin Asad? He's handsome, nd brilliant, besides his a Muslim, y cant u accept him? Islah cikin daga murya tace I cant, coz m married, Zaineee ta tsura mata ido, tace stop lying, u knw if u dont like Asad jus tell him, kar kiyi Karya da aure, ta fita ta bar ta cikin dakin, Islah ta runtsen ido, tana tunano kalaman Tsoho, inda ya ke cewa Islah ki tsare kanki, ki tsare mutuncin ki, kar ki manta da Akwai Haqqin Aure Akanki, kar ki ci Amanar Aure.. Lagos Ta shigo gidan da Sallama, Gaban Hanifa ya buga lokacin da suka hada ido da me Sallamar, jiki ba k'wari ta amsata, Madam Atutu ta ma kanta mazauni tare da crossing leg, suka gaisa da Hanifa ba yabo ba fallasa, Atutu tace na san baki ganeni ba koh? Hanifa tace Eh Gaskia, yeah dama baki sanni ba, Sunana Fatima, nd nice keda Tanquieez Eatryz, nazo ne gun Yayanki, pls idan yana nan ki kira minshi, Hanifa tayi jimmm, ta dai daure tace baya nan Indai ce Lafia koh? Atutu tayi farr da ido, yea lafiya sai Alheri, dama maganar auren mu ne, Iyayena sun ce na gaya mai ya turo, Wata uwar ashar hanifa ta kyabo, ta miqe tace kam balaeee, Iskancin mata iri na legas ne bin mazaje gidan su na aure? Toh wlh ba zai aure ki ba, Idan ma ce miki yayi ni qanwarsa ce to ya miki babban qarya, ni matarsa ce ta aure, and kuma bani ba kishiya wlh, so fitar mun daga gida ko wlh in sa mai gadi ya fitar dake, Atutu ta hadiye wadannan baqaqen maganganun Hanifa, ta miqe tare da sabar jakkarta, tace tabbas na san ke matarshi ce, amma ni ban daukeki mata ba, matsayin ki a nan be wuce qanwarsa ba, me kike tsinana mai a gidan da kike iqirarin ke matarsa ce? Ke kanwarsa ce nikuma matarsa, ki bari idan na shigo sai kiga yadda ake kula da miji da tattalinsa,nan ba da jimawa ba zan zama mata a cikin gidan nan, kuma lokacin ba ki isa ki gaya min baqaqen maganganu na kyaleki ba, don ko ni ba sa'ar yin ki bace amma ynzu kin ci darajar Yayanki da na keso kuma zan aura, so na barki lafiya, ta juya ta fita ta bar hanifa tsaye, kamar bishiyar da aka dasa, YaZayyad zai sake aure? Kawai sai ta tsinta kanta da fashewa da kuka, da gudu ta shige dakih ta zube kan gado tana kuka, damuwa fal ranta, Saboda me zaiyi aure? Zuciyarta tace sbd ba kya bashi kulawar da ya kamata, zunbur ta miqe tace to don me zata bashi wani kulawa? Ai ba sanshi takeyi ba, zuciyarta tace toh meyasa kike kuka? Da sauri ta share hawayenta, i miss home ta ba zuciyarta amsa, ta miqe ta koma parlor, duk yadda ta so kawar da zancen a zuciyarta taka sa, tunanin hadaddiyar yarinyar da ta zo neman mijinta takeyi, wai shin menene haka? Ni ko nace Hanifa Kina Kishin Yayanki Zayyad.. K'arasawa tayi inda yayi parking motarsa, ta bude gidan gaba ta shige tare da sauke ajiyar zuciya, jikinsa har rawa yakeyi, yace Yadai besty? Ya ku ka qareh? Tayi murmushi tace i can see anger and fear in her eyes, lokacin da na ce mata ina nemanka, ta shiga fargaba, ta na kishinka, nan ta kwashe duk ynda sukayi da ita ta gaya mishi, Tana kishinka Zayyad, ita kanta ba ta sani ba, so use dis Oppurtunity, Zayyad yyi shiru yana tunani, for her to do all wat she did to u, d anger d jealousy, it only means 1thing, She loves me, Hanifa na Sonaah. Kano Allah Allah take ta gama abinci tazo ta bude Whatsapp don Chatting da wanda Zuciyarta ke bege, Umar Z, tana mai so maras misaltuwa, amma ba ta taba nuna mishi ba, So ma take ta daina tunaninshi ynz har sai Allab ya kawo qarshen xamants da Suraj, Musamman ya dawo Naija don ita, ta qi yarda su hadu, kullum sai ya matsa mata kan sai sun hadu tare da gaya mata irin son da yake mata, ta kan ce mishi u are just a frnd Umar, i cant meet wit u coz m married, sai yace haba Bilkis, ina sonki, kuma na san kinasona, pls ki bani chance din zuwa gurinki, i want to see u, musamman na baro aikin da na keyi a Dubai don ke, i prove mysef to u, please, tace frndshp is all i can give u nagaya ma m married koh? Allah idan ka a qara min maganar so Zanyi blocking dinka. Tana son ganin Umar amma ba ta son Tsinuwar Mala'eeku, kuma har Skool Suraj ya sata, NWU, bata taba using opportunity tace su hadu a skul ba, don ta san matsayinta. Akwai auren Suraj a kanta, tunda ya dawo daga tafia da kuma dawowarsu gaisuwa kadai ke hadasu, sai cin abinci, sai kuma idan da safe ta shirya zai ajiyeta skul, idan ko bata shirya ba drivernsa ke kaita ya daukota, Musamman ya siya sabon sim da waya don kawai chatting da Bilkisu, ita kadai ke da numbern, a yanzu ya san ya kamu da son Bilkisu sosai, kusancinsu a Whatsapp ya sa ya gane kalar son da yake mata, Irin son da ko Fadila be taba mata irinshi ba, Ya kuma yarda da amincinta, ya gane ta san darajar aure, duk da ya lura ta kamu da son wanda suke chatting amma bata bi son zucyarta ba, Fargaban shi daya kar ta ce zata rabu dashi idan ta gano cewa shine Umar Z, Ya sha attempting Sanar da ita gaskia, amma sai ya rasa hanyar bi gun sanar da ita. Amma InshaAllah komai yazo karshe, zai bayyanar mata da gaskia, Zai bar wahalar da Zuciyoyinsu, zai bayyana mata sirrin da ke ransa... Abuja Da karfi suke buga k'ofar parlorn shiru, ta kwalawa maigadi kirah da karfi, ya rugo da gudu, wai ba kowa ne gidan? Yace eh hjia, oga yaje aiki, madam kuma taje skul, a ranta tace Skul? Ta kalli mamarta, mamar tace dama ta fara zuwa makaranta? Diyya cikin fushi tace shine don wulqanci ka bar mu mu ka shiga ciki, baka iya ce mana ba kowa? Yace sorry ma, i tot kina da key ne, ba ta kula shi ba ta ciro wayarta ta kira zaid, ringing uku ya dauka, hello diyya nah, kunyi landing kenan? Ba ta amsa shi ba tace haba Zaid, mun dawo ba kowa gidan, gashi mama bata son rana, Zaid yace ohh sorry, ai bansan yau zaku dawo ba, da na bar muku key, Gashi yarinyan nan na skul, Cikin masifa tace ni ka kirata ta kawo ma mutane key, ba zan iya tsayuwa ba, yace O'O gashi ban ma da numbernta, amma ki yi haquri, its pass 2, nasan tana hanyar dawowa, kiyi hqr kinji Diyyata? Katse wayar tayi xuciyarta na tafarfasa, mamar ta tace badiyya, kinga abun da nake ce miki koh? Yarinyar nan ta samu karbuwa gunsa gashi har ya sata makaranta ba tare da saninki ba, ko ya fara sonta, da qarfi badiyya ta ce haba mummy meye haka? Bakiji me yace bane? Ko numverta be dashi so pls just shutup ki daina qarama zuciyatah zafih, Uwar tace ohh Sorry ny dear, Horn sukaji, Maiguard ya wangale gate din, Motace Qirar Focus ta danno kai, duk suka zuba ma motar ido, wata kyakyawan farar mace ke tuqin,, a idonsu tayi parking, ita kuwa bata san sunayi ba, ta fito sanye da riga jalabiyya mai kyan gaske, Zuciyarta ta bata ana kallonta, waigawar da zatayi ta ga Badiyya da Mamarta tsaye cirko cirko, da alama basu ganeta ba, ta qarasa gunsu da murmushi, Aunty kune sannu da zuwa, Hankalin Badiyya yayi mummunar tashi, a hankali tace Rumaisah, Rumaysah ce wannan? _Bibilicious Biebee_ 4⃣3⃣ 🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕Gidan Gandu🏠by 💕Biebee Isa💕by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕 Maysah ta katse mata dogon tunani tace bismillahnku, Yadda kuka san hoto haka Badiyya da uwarta suka maids Maysah, duk inda ta sa kai idanuwansu na biye da ita, Badiyya takasa daurewa tace wai ina kika je ne kika bar mutane wajei? Tace ohh sorry wlh daga skul nake, tace ok, erhmm yanzu mun iso da yunwa, ina so ki hada mana lunch, Maysah tace ok Aunty, bari na chanxa kaya, tana shiga dakih maman badiyya ta sake ashar, haka yarinyan nan ta xama? Har Jamiaa ya sanya ta? Iya kacin ki SS3, kin yarda kishiya ta fiki, sai nayi magana sai kice min ba ya sonta, baya sonta xai kai ta wannan makarantar turawa Baze? Badiyya tace ni dillah mama ki min shiru naji da abunda ke damuna. Da sauri mamar tace ohh Sorry... Badiyya na nan zaune tana karkada k'afa hade da tunanin clean din data ga Maysah, tunani takeyi Could it be possible Zaid is-- da sauri ta kar kada kanta tare da kawar da tunanin nan, Zaid ba zai mata haka ba, zaizo ya sameta, idan ko taga abu zai gagareta, gurin bokanfa kawai zata kai Maysah ya gama da ita. Ba a jima ba, sai ga Maysah ta fito da tray a hannu, har ta ajr kan dinning, maman badiyya tace ke kawo shi nan, tace toh Mama, Ta kwaso abincin ta dire musu tsakar carpet din parlorn, ta juya xata tafih, Badiyya tace keh, ni kikeso na zuba abincin? Kamar Maysah ta juya, amma sai ta juyo ta shiga xuba masu, Ganin Doya yasa Badiyya cewa, uban wa zaici doyan nan? Allah ya sa bani kikeso nacin wannan farar doyan ba kamar wata bakatafa, Maysah tayi shiruuu, dallah dauke wannan abun daga gabana, ki kawo min wani abun, ji tayi ance why dont u go cook for urself? I think zaki fi sanin abun da kikeso, kiyi shi yadda kikeso. Gabaki dayansu suka juya suna kallon me maganan, Zaid ne sanye da Riga da Wando na Ash suit, Tana ganinshi taji duk wani bacin rai ya yaye, ta miqe ta nufe shi da sauri Oh My Zaid ta rungume, shima dai rungumetan yayi, tare da fadin hows my baby diyyah? ta shagwabe fuska tace I miss u, i miss u more diyyah na, Kan Maysah a qasa, gabanta sai faduwa yakeyi, ta rasa me ke mata dadi, miqewa tayi ta wuce dakinta, Don yau ko gaisuwa be samu ba. Sannan ne Zaid yazo yana ma mamar Badiyya ya jiki, sun sha India, tayi hquri be kira ba, don badiyyan ba ta nemesa ba, tace sorry myzayd, we cudnt get a sim, jinta kawai yayi tare da daga kai ba wai don ya yadda ba, ya wuce dakih don chanzawa. Badiyya ta kalli mamanta suka sheqe da daria, tace shegia diyata, kina Indian Kaduna, suka chafe, tace ai mama Halinki na kwaso kaff, ynz ma dai bari na kira Alhaji Haladu nahh Bauchi Yau ya kama Weekend, Samir na zaune kan kujerar parlornsa yana waya, Amira ta fito sanye da riga da skirt na English Wears, tun kafin ta fito jikinshi ya bashi ga lil sismeeranshi nan fitowa, a kwanakin nan wani abu yakeji game da ita me wuyar fasaltuwa, shariyar da ta ke mishi ya fi komai daga mai hankali, Ya so ya dauke ido daga dubanta, amma sam ya kasa, don ta mai wani irin kyau, Iya rayuwarshi a kasar waje, be taba ganin macen da Riga da Skirt ya mata kyau kamar Amira ba, ji yayi sonta na fizgarshi, kasa jurewa yayi ya miqe ya janyota jikinshi, Murtuk ta daure fuskanta, ta hade girar sama da na kasa, tace meye haka? Mamaki ta bashi, Gani yayi ta rikide ta koma Amirar daaa wacce bata Mutunci idan an takata, amma da yake shima namijin dunia ne sai yace Haba Lilsismeerah, me bigbrosamir dinki ya miki da kika daina mai magana? Ki ka daina kallo nah ko ta gefen ido ne? Wani mugun kallo ta watsa mai, tace ohh so daman jin dadin wulaqantani kake idan na magana? Dama so kake na dinga binka kamar mayyah kana shareni? Ba so daya ba so biyi nake binka ka kulani amma kayi kunnen uwar shegu dani. For 8th good months, Samir ya rintse ido, m so sorry Amira, wlh i truly regret dis, i can make it up of u, just let me, tace its too late, ba zaka qara gani na ina roqon ka min magana ba, or ina roqon ka sanar dani laifin da ban taba aikata ma ba, sannan ta lura da wannan riqon da ya mata, tace let go off me, ka cika ni, ka qyale ni mana, yace Amira kiyi haquri, Wallahi nayi nadama, dama i was angry nd Miserable, but not anymore, tace hmm lallai, saboda Islah ka chanza, saboda tace ka chanxa shisa ka chanza, da sauri ya girgiza kai, yace wlh dis isnt about islah, i dint do it for her, ki yarda danih, nan da nan zuciyarta ta karaya, dama da qyar ta ke gaya ma bigbrosamir dinta magana mara dadi, sai da ta kai zuciyarta nesa, ta dai daure fuska tace Najih sake ni, yace Na dai qyaleki for now. Komawa tayi ta zauna chan nesa dashi tana latse latsen waya, ya zuba mata ido kamar sabon maye, Sonta na shigarshi, ta mai kyau matuqa, kasa jurewa yayi yace Lilsis? Kallonshi tayi ba tare da ta tankashi ba, yace Kinyi kyau wlh, kayan nan sunyi fitting dinki, ta miqe ta qare kallon jikinta tace Allah koh? Da sauri yace Ehwlhh, inason kayan sosai, a ranta tace Oh kayan kakeso? Ba tare da tace komai ba tayi hanyar dakih, da sauri ya sha gabanta don be son ta katse mishi wannan jin dadin kallonta, yace Ha'an ina zakih? Tace zanje na cire kayan nan ne na zubar, cikin mamaki yace saboda mey? Cikin halin ko in kula tace sabida kanaso, ta raba ta gefenshi ta shige dakih, shi ko Samir ya ji zafin kalamanta, Waiyo Allah, shikenan Amira ta gama tsanenshi, ya ja ma kanshi, yanzu me zaiyi ya wanke kansa gun lilsis dinshi? Taya zai nuna mata matsayinta cikin zuciyarshi? Yace bakomi, i wont give up zan shanye duk da zaki min Amira, coz ni na ja ma kaina, amma Wlh Amira ina sonki. Amira na kallonshi ta windown dakinta, dadi ya lullubeta sonshi na qara ruruwa a ranta, nd taji dadi da yayi nadama, ta yafe mishi but sai ta rama abunda ya mata, sai tayi proving dinshi wrong,sai ta gwada mishi she's not a cheap person, and ba zai sameta a sama ba... Kaduna Wayarta tayi qara, ta rugo da gudu don ganin ko waye, TSOHONMU ta gani a Screen, da sauri ta dauka tare da Sallama cikin jin dadi. Ya amsa tare da kirarin da ya saba yi mata na Almasifatu, ta shagwabe fuska kamar a gabanshi tace zaka fara koh tsoho? Yayi dariya, yace kewanki ya cika ni, kin watsar dani a bola shisa nace bari na latsoki, ta marairaice tace wlh ba haka bane, ko shekaran jiya ai na kiraka da Asuba, jiya kadai nefah, yace da yau ma, tace ai gashi ka kira, yace ai naxata mijin na kine ya sa kika manta da mu, kamar yadda ya manta da mu, ya mance yana da yanuwa a Maiduguri, fadila ta tabe bakih tace shidai ya sani, ni ko kallo be isheni ba, sai yayi tayi ai, tsoho yayi shiruu yana tunani, dama hannunka mai sanda ya ke mata, yana so ya fuskanci halin da take ciki da mijinta, Fadila wani irin Zama kukeyi da mijin naki? Cikin halin rashin damuwa tace ko wa harkar gabanshi yakeyi, ai ni ina jin magana be taba hada mu ba, sai wata rana da ya gaya min baqah gaban qawata, Ran tsoho ya baci, wata 8? Magana be hadasu ba? Shifa beyi hadin nan ba don ya kara tarwatsa tsakaninsu, yayi hadin nan ne don ya hada kansu, Yace idan na isa da ke, idan ya dawo kice mai ina nemanku, kuzo Gida, tace Yo tsoho satinshi 3 rabonshi da gida, sai bakin direba nakejin tafiar nashi, Tsoho cikin bacin rai yace Zan ga Ubanshi, ke dai kiyi haquri, zan kamo bakin zaren... _Bibilicious Biebee_ Gidan Gandu 4⃣4⃣ 🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕Gidan Gandu🏠by 💕Biebee Isa💕 by💕Biebee Isa💕 Biebee Isa💕Biebee Isa💕 Lagos Tuni take jiran dawowarsa, bashi ba alamunsa, gashi yanzu har qarfe 11 da rabi na dare, abunda beyi kenan tsayuwar dare, sai ta samu kanta da shiga damuwa, zuciarta na mai mata saqe saqe, toh ko zance yaje? Nan da nan ta tuna wannan me suna Fatima data zo neman sa, ta tuna kalamanta inda take shaida mata xata shigo gidan, kaii sam ba zata ta bari wata ta shigo gidan Zayyad ba, jin tsayuwar motarshi ya tabbar mata da shine ya iso, ts sauke naunauyar ajiyar xucia, ta miqe tayi parlor, anan sukayi kicibus, kallonta ya tsayayi kafin nan ya rabata ya wuce, bin bayanshi tayi tace kajih, yayi gaba, ta qara cewa kajih, ya juyo ya dan hade rai, wai nih? Duk tayi tsuru tsuru, ta rasa yadda zata fara mai magana, ganin bata da niyyan magana ya sa shi yin gaba ya shigewarsa dakih, zama tayi kan kujera game da fashewa da kuka, ta miqe da sauri ta shiga dakin, lokacin har yayi kwanciyar shi, gadon ta hau a hankali tace Ya Zayyad, wani abu ya ji ya dirar mai a tsakiyar kai, tunda yake be taba jin ta kira sunan shi ba, ya juyo yana me fuskantar ta, bakih na rawa tace YaZayyad dazun wata tazo nemanka, ya hade fuska yace mun hadu, kun hadu kace? Yace eh daga gurinta ma nike, ta zaro manyan idanuwanta tace dagaske ita zaka aura?Yace InshaAllah, Kuka yajih ta fashe dashi, tace pls Yazayyad ka kaini gida, i really want to see my Mum, i missed home, be son kukan nan, yace kiyi shiru, ba yanzu za muje Maid ba, sai nan gaba, cikin fada tace for how long yazayyad? Tunda akayi auren-- sai tayi shiru ta kasa cigaba da maganan, yace Ehen ina jinki, ta dan muskuta, tunda na zo lagos din nan, wata8 kenan ban taba zuwa gida ba, kawai ka ajiyeni a nan don ka kuntata min, don kawai ka ga banda kowa, yanzu har aure zaka qara, ta sake fashewa da wanih kukan, miqewa zaune yayi, yana kallonta ta ma rera kuka bi hakki,Yau sai yaga duk tayi sanyih, ta qara kyau, beyason kukan nan da takeyi, amma yanaso ya tabbatar da sonsa da takeyi, yace kinaso kije gida? ta gyada kai da sauri, ya qara cewa bakya so nayi aure? Nan ma ta gyada kai, yace ki bani reasons not to marry again, tayi shiru, yace Hanifa, ina so na aure fatima, sabida tana sona, nan da nan ta sauya fuska, kar ya bata shirin sa ya sa yace i will take u home in two days, amma da sharadin zakiyi min biyayya nd zaki kula da all responsibilities na da ke kanki, only den i will decide if m to marry again or i will take u home kin gane? Ta gyada kanta a sanyaye Yace oya zo ki kwanta, ba gardama ta matsa kusa da shi ta kwanta tana ajiyar zuciya, shi ko Zayyad godia yayi ma Allah da ya sauko masa da hanifa cikin ruwan sanyih, Allah ya sa hakan ya dore Amin Kano Tana kichin tana hada lunch taji wayarta na ringing, ta fita don parlo don duba me kiran nata, Umar Za tagani, mamaki tayi, don tsawon taraiyyarta da Umar be taba kira ba, Sai chatting, kuma rabonsu da chatting tun shekaran jiya, bata ankara ba wayan ya tsinke, bata gama tunani ba wani kiran ya sake shigowa, ta dauka jiki sanyaye, Asssalam Alaikum My Angel, ta lumshe ido don taji muryan nan very familiar, ta amsa mai sallamar, yace Zuciyata ta kasa jurewa da fushin da kikeyi dani don nace kituro min hotonki, naga ai ba laifin na bane, laifin zuciyata ce da ta kamu da sonki Bilkisu, Ki daina min irin wannan hukuncin, ta bude lumsassun idanuwanta, tana jin dadin muryan shi, tabbas idan ta cigaba da sauraronshi, zata karaya har ta fara bayyana mai sirrin da ke ranta game dashi, amma ba zata taba barin hakan ya faru ba, tunda har yanzu akwai auren Suraj a kanta, cikin masifa tace kai mallam wai baka da hankali ne? Na gaya maka ni matar aurece, da mijina, wani alaqa ba zai taba qulluwa tsakaninmu ba, saboda haka ka kyaleni, kar ka sake kirana, Suraj yayi Murmushin jin dadi yace wlh ba zan daina sonki ba, kuma kina iqirarin kinada aure abinda mijin bai da mu dake ba, mijinki solobiyo me sakarai muna maza, ran Bilkisu yayi matuqar baci jin Umar ya zagi ya Suraj, tace ba wawa muna maza solobiyo, sakarai kamar ka, kasani mijina yafi karfinka, idan kayi zuciya kar ka qara kirana, yace ai ba zan taba zuciya Ba har sai kinzama tawa, don ko gani a qofar gidanki, ki fito muyi zancen soyayyah, tace kan ka dai akeji yace ba ki yarda ba koh? Shin ko ba gidan bane No 3 Nassarawa GRA gida me black gate with brown roofing, hantar Bilkisu ta kada, gabanta ya fadi, yace ki fito naga sanyin Idaniya or else zan shigo wlh, tace wlh yau sa kayi dana sanin sani ka jira gani nan zuwa, yau sai ka ga karshenka me bin matan aure, ta latse wayar tare da lalubo wayar suraj karo na farko a rayuwarta, sai dai har ya kaste suraj be dauka ba, yana ganin kiran yaqi dauka, Bilkisu ta kalli Agogo 6 saura na yamma, lokacin dawowan Suraj yayi, kar wannan shegen umar din ya shigo ciki suraj ya dawo ya ganshi ya mata mummunar fahimta, da sauri ta shiga dakih ta fita wajen gidan bayan ta sanya hijabi. Zaune ta ganshi kan mota, gabanta ya fadi, yaushe ya Suraj ya dawo? Da sauri ta qarasa ginshi, yasuraj, dama dama wanih ne yake ta damuna, yanzu wai yace yazo nan gidan, shine shi-- Sshhh Bilkisu, suraj ya katseta, theres noone here just me, duba kiga, sai a lokacin ta kalli unguwar ba kowa kamar anyi shara, ba kowa, suraj ya diro kan motar, tace ya Suraj sunanshi Umar, wlh he's bin disturbing my life, suraj ya riqo hannunta yace Bilkisu, look at me, ta dago ta kalleshi, yace Do u love him? Dont lie to me, murya na rawa tace Yes i do, but its u m married to, i have no intentions of cheating on you pls believe me, ya qara riqe hannuwanta gam, fuskarsa dauke da murmushi, yace listen to me Bilkisu, Ni neh Umar Z, ni ne muke chatting dake tun tafiar Islah, Na tsaya a dubai ne, anan muka fara chatting, everything data happened was All me, Tsananin mamaki ya lulube Bilkisu, zuciyarta ta shiga zafih, hawaye suka wankr mata fuska, ta daga hannu ta kamtse Suraj da marih, how could u do dis to me? Ta juya ta shige gida da gudu.. 4⃣5⃣ 🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕Gidan Gandu🏠by 💕Biebee Isa💕 by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Bayanta ya bi da sauri, yana kwala mata kirah banza tayi dashi, kichin ta shige inda take ji qaurin abincinta, ta ma manta ta bar abu a wuta, da sauri ta kashe gas din, ta shiga kwasar Abinci, Suraj yazo ta bayanta ya na mata magana, Bilkisu kiyi haquri mana, this is d only way i cud think of, i want u to love me like d way i do, ta juyo da sauri tana kallonshi, yace yes Bilkisu ina sonki, son da ban ta ba yi ma ko wacce mace ba, ana da ina tunanin Nayi so, a yanzu kuwa nagane a baya ba so nayi ba, Hauka nayi, yanzu kuwa ke nake so, Shisa na bullo ta haka, don ina tsoron rabuwa dake, don a ganina kin tsaneni, duk abunda na fada a matsayin Umar gaskia ne, ban miki karya a kan komai ba, duk abinda na fada miki a chat haka yake a zahiri, Fargaba na daya, kullum shina ke tarrabi, ina tsoron ki amince ma Umar,

Chapter 12 of 20