Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 11
da kunya,. Ina,Zahra in ta cigaba da tsayuwa a tana kallon su zata Iya hawan ruwa,tuni ta juya Tasleem ta daura bayan ta tana waiwayen wannan BARIKIN, kai ko ita ta tafi da imanin ta wallahi,, duk ba Wai kyau tafi Zahran ba amma da gani ta fita sanin kan ta Duniya..sai dai ba yadda za ai Yayan su ya kaso musu yar BARIKI.. Tab, bari suje gidan. Gidan su zahran da ba'a je ba kenan sukai gida,in banda hawaye ba abinda Zahra take, Tasleem tayi tayi ta kasa dai nawa,. A parlour suka tarar da Hajiya,itama ta tsunduma tunanin Wai Hafeez da mata 2,,kukan Zahra ne ya dawo da ita,,tuni ta hau tambaya,, kan Tasleem tace komai Zahran ta amshe,tana kuka tana tsarawa Hajiyan. " Kuma Wai yar BARIKI fa Hajiya?da sauri ta waro ido waje,,tace "wallahi Hajiya Wai ma sunan ta" BARIKI,Tasleem tace"Hajiya kinga yadda yake mata dariya, tamkar wacce ta mishi ishara da Aljanna.."Ni ya ishe ni haka,,ni dama nasan yaron nan ba haka kawai yake ba,,Ashe yana chan an dauke hankalin shi, kuma Wai Karuwa yar BARIKI?? Ta kallo Zahra,"yi shirun ki,bari baban naku yazo,,bazata sabu ba Sam,,da hankali na bazaa auro min sirika yar BARIKI ba wallahi.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 6:31 AM] Feenat Ja'afar: [1/9, 1:03 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 31_Hafeez na dira gida Hajiya ta fara sauke mishi,,da tsananin mamaki ya sauke kai kasa,yasan bai isa wanke kanshi da Sa'a ba yau a wajen Hajiya,.."Saboda ta dauke maka hankali har ka gagara ban bance tsakanin Aya da Tsakuwa,,Yace"Hajiya Wallahi ba haka Sa'a take ba,,wannan sunan daban,kuma.."Rufe min baki shashasha kawai,, in baka Sani ba toh ka Sani yanzun,Zahra kawai na Sani,ba ruwana da da wata BARIKI,Macen kwarai ce za'a kirata da sunan BARIKI ta amsa??. Mita take har Abba ya ritsa ta bayan ya dawo,,yana hawa ta bi bayan shi. Hafeez ya juyo yana hararar Zahra da Tasleem,,"Yaushe na zama abin wasan Ku da har zaku Bini a baya?? Sukai tsurutsuru,ya nuno Zahra da yatsa, "Bari ma kiji,wannan abun bazai hanani auren Sa'a ba,sannan Gobe kisan nayi ki tattara ki koma gidan Ku,,.Ya tashi yai daki,,ta bishi da ido,Tuni ta fara hawaye,abun harda gori?Ita kwa mita tsinana a zaman gidan banda takaici?Bari taje gida,har gidan Aunty salma zata,karya ne a gama ta zaman aure da wata,,. Shikwa yana shiga daki ya jawo waya,ita kanta Sa'ar haushi take bashi,,dan dazun suna tsaye Ali yazo,, saboda tsabar rashin so Wai tace mishi " Excuse me"?,..Tai wajen Ali,duk da bai ji mey suke cewa ba,amma ya gano wanda suke waya dazu ne,tuni koh ta kanta bai bi ba ya shiga mota..shine kuma yana zuwa Hajiya ma ta sauke mishi,.Yai dan tsaki, Lalle sai ya dage,,Ashe da gaske take Wai Bai karbi soyayyar taba? Toh ya take so yayi??Ya fidda zuciyar shi kan Yace"Sa'adatu I luv u,komai??ya sake tsaki,,a hankali ya furta "Sa'a matsala,.. Ita kuwa tunda taga Hafeez ya zuciya ta rasa sukuni,gashi ta kasa kiran shi, a nata tunanin ajin ta zai zube,. Tai kwafa,amma Alin nan sai ta sa kafar wando daya dashi zai ki yayi zuwa wajen ta, in takamar sa gidan na uban shi ne,toh itama tana da gidan daya taka wannan na bulo ma..ta kara tsaki,,ta juya ta dau waya kan ta tashi zaune..tai dailing numbern Hafeez din,da sauri ta katse,," Oh God,,ta rike kai,"Wai Sa'a mey ke damun ki ne akan Hafeez??Tun farkon haduwar su da Hafeez shine kadai Namijin da ta taba mafarki,,shine kadai wanda ta taba chachar baki dashi dan Dabarar ta takare, shine kadai ke sawa ta bata lokacin ta wajen tunanin shi, Shine kadai a yanzun in suna tare take jin wani nishadi kadan kadan na shigar ta..Sannan yanxun yayi fushi ta damu,ji yadda take gwara kan maza,manya da kana nan su,,yau 1 wanda taki jini ya hana ta sukuni.." Ya Ilahiii", "Mey kenan hakan yake nufi?? Ta kalli agogo 9,kwanciya tai kamin ta hau Mishi text da bata San ma ta fara ba..Da sauri ta goge na ban hakuri ta rubuta. " Shine ka tafi ba koh sallama?? Tasa halamar shagwaba.. Tai murmushi, kan ta kishingida. Text yaji ya shigo wayan ya kara tsaki kan ya kwanta,chan ya jawo wayan,dan yana zata koh Alert ne na contact na Zane da aka bashi,,da mamakin shi yaga Sa'ada,.yai murmushi, take yaji kuncin shi ya yaye,tuni yai reply.. Taji text itama,tai murmushi dan tasan shine,."Munyi fada ai,, tai murmushi da har hakwaran ta suka fito, tai rufda ciki kan ta mishi Reply.. "Ai bama fada..Triple sorry" ..Shima yai rubda cikin yana karanta wa,,yai murmushi,,"No banyi ba..ban Aron minti 5 naji muryan ki sai nai sorryn..ya tura..chan itama ta bude,,tai murmushi tana duba sling,, kan ta kada kai tai reply"An baka. Ringing 5 tai kan ta katse ta dauka da sallama,,yai Jim,,tace"koh ba'a yafe ni ba??ya sauke wata ajiyar zuciya,, kan Yace"u know what?? Kina da dadin muryar sosai,,Tai murmushin jin dadi,. Kan tace "kaima haka?..sai kuma ta datse harshen ta da hakorin ta,bata ma San ta furta ba,,yai murmushi,." No,ke ai ta daban ce,,Tace"Koh,? Yai shiru,"Sa'ada waye Ali nan ne??tai dan murmushi,, "Dan mai gidan Baba ne,,Yace" ehm,sai mey kuma??ta kada kai "shikenan, Yace" Ba So??tai Jim, kan tace"akwai,.tuni ya mike zaune,,sai ta kara da"Shi yake kayan shi amma,,ya sauke wata ajiyar zuciya da taji ta,, Yace"Toh Ni fa Sa'a?? Tai shiru tana,tace"Hafeez ne kai,Yace"ehm?Toh ana son Hafeez din?? Tai Jim,gaban shi ya fara faduwa,,ita kwa murmushi take a hankali,. Sai da ya kara magana,"Ko har yanzu ban karbi Son ba Sa'adatu?? Wallahi believe me,I am madly, deeply in love with you ...Sa'a I really Love you, en u know?? Tun farkon haduwar mu na kamu da son ki,sai dai a wancen lokacin ban San so bane Sa'ada, nasan dai ina tsananin kishi na ganki da gyale shara shara,,sai naji zuciya ta na tafasa,,in na tabo ki mukai ne kawai nake samun relief.. Tunowa take da lokacin, tabbas tun ganin Hafeez na farko ta ji sauyi a tare da ita. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/9, 1:43 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 32_Ya cigaba, "Kin tuna ranar da na watsa miki lemon strawberries a jiki??? Tuni ta rintse ido dan tuna wa da wannan rana,ba zata manta ba har kuka tai,,.ya katse ta" nasan ke a zatan ki dan tsokana nai,,Ya girgiza kai, "Ganin mai shagon nan fa nai yana ta kallon ki sai ga kin dame Riga,ga nan gyale a kafada,,shine yasa na tashi na harare shi yana sosa kai,kan na baki baya na watsa miki,nasan Ummi ta gani,en dole ki nemi agaji,sai kwa gashi ta baki kin suturce jikin ki da abayar ta,,.Jin shi kawai take..ta katse shi da" Mey zakace da Marin da kamin kuma??Ya sauke ajiyar zuciya,, "Sa'adatu.. Taji kiran har kwakwalwar ta,.," Naga shigo war ki kina ta wani yauki,,ga kayan sun dame ki,ga wani Wai shi gyale da kika dakko kin maka shi a kafada,baki sa maraba da wacce ta fito haka,,ga duk kusan ke ake kallo,,amma ke na fuskan ci baya ma damun ki,haka kika kutso taron nan kika shigo fa,,da zaki kula,da zaki gano tsabar haushin da nake ji, hararar ki nake tayi ko zan samu saukin zugin raina,,ina fa jin wani a yan uwan su Ummin yana cewa wani "Woow,,she's Beautiful!! Kamar na cire babbar Rigar Aminu na rufa miki naji,.sai dai nasan ba laifin shi bane,,naki ne,. Dan na rage zugin dake raina na koma baya,,juyo war da zanyi naji ki kusa dani,kuma kamar ki shige min jiki,,bazan boye miki ba,a lokacin nan ji nan kamar ma na rufe ki da duka,,dan na tsani mace mai chudanya da maza,.ban Ankara ba naji saukar sanyi a jiki na,,...Yai shiru tare da rintse ido,,." Sa'ada ban so tuno Marin nan da na miki,, duk da har gobe kowa yana kallon kece kika mare ni in kika cire Ummi da Aminu,tanan kawai na gode Allah. Tai ajiyar zuciya,, Lalle sai yanxu ta kula da kishin da Hafeez ke nuna wa,,ya katse ta,, "Da fatan kin gamsu zaki yafen,..yaji shiru,, Ashe kudin ya kare.. Shi yana ta zuba ko warning din bai jiba,,ya dau wayan Glo ya kira..dai dai zata kira.. Yace" kiban dama gobe nazo gida da safe,yanxun dare yayi,. Ta kada mishi kai,,"Ok.. Yace"Mey toh zan samu??tai Jim,dan bata gane nufin shi ba,,sai tace*Sai dai kazo gobe,,Yace"Promise?,, ta kada kai "Promise.. Haka suka sallamar kowa ya kwanta da tunanin Dan uwan shi..barin Sa'a yau da taji duk wwani haushi ta daina ji na Hafeez,, a ganin ta ko a haka ya barta ta gamsu da Lalle So ne ya Jawo Haka. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 6:38 AM] Feenat Ja'afar: BARIKI...IYAWA 33_Tun safe Zahra tai niyar gida,.ko jiran Tasleem batai ba,, tana zuwa ta zube a tsakar dakin Mamyn nasu,, Aunty Sadiya ta kallo ta,"Lfyr ki kuwa??Kinzo kin wani zube min ba koh sallama??Tuni ta marai rai cewa Mamyn tasu tana hawaye,, "Mamy,,Na shiga 3 wallahi,,.sai ta barke mata da kuka,,Da jin haka ta waro ido waje,, Ta tashi ta kamo yar ta ta,tasan dai tatsuniyar gizo bata wuce ta koki, Amma sai ta tambaye ta" Meye kin shiga 3?? Nifa ban son wautar nan taki ta yan fari?? Ta lafe jikin shi tana kuka,,"Mamy Wai Fa Hafeez mu 2 zai aura,, kuma ya rasa da wacce zai hadani sai yar BARIKI mamy,, Mamyn tai Jim,ita dai dama wannan hadin na Zahra da Hafeez kwata kwata bai mata ba,,duk da Hafeez da yake a gurin ta,amma tasan ba abunda yar tata zata tsinta a gidan shi sai ciwan rai, toh amma ita batta da wani power a gidan,tunda itace auta a cikin gidan su kakanin Hafeez din,, haka itama aka mata wannan auren hadin,, gashi za'a sake da yarta tilo mace,dan duk sauran kannen Zahra maza ne,,. Rarrashi ta fara,,"Toh meye ne abun kuka anan Zahra?Ta sake magana cikin kuka"Mamy Abban su fa Wai ya yarda,,Hajiya ce kawai tace bata yarda ba,, Dan Allah mamy ki Taimaken ki samu Fodio da maganar,tunda Abban yana jin maganar shi,,.. Ta sake fashe wa da kuka"wlh mamy ban son zama da kishiya.. Da sauri ta kwade mata baki,,ta rike bakin tana cigaba da hawaye "Wato kaddarar ki a hannun ki take koh Zahra?Ta hade fuska mamyn,,"Da hankalin ki kike furta irin kalaman da wanda basuyi makaranta ba kadai ke fadan shi??tai kwafa,"Sannu autar mata,,Toh ki sata a ranki,,sannan ki daura damarar zama da ita tun yau,.Da sauri ta kalli Mamyn nasu,, "Anya mamy kuwa tana son ta??,,Bari Abban yazo,shi zata tsara mishi komai ya shige mata gaba,,.kamar tasan tunanin yar tata,,sai ta dawo mata Nasiha,,kan tana saukaka kishi,dan duk yadda ka dauki Kishiya toh fa a haka take zuwa maka,," Ki duba ni da auntyn Ku,da yawa mutane basa gane kishiya tace,dan tsabar muna zaman mutunci da girma ma juna..ki cire wanna akidar taki tun wuri Zahra,,Dan kin fini sanin halin Hafeez, bare akan abinda yake so,,sannan duk Family nan suna matukar yaba dashi,hakan yasa suka zaba mishi ke suna ga da hankalin Ku zai zama daya..kar ki fara bata rawar ki da tsalle tun yanzun,, tai ta mata,amma ina,ita gani take Mamyn bazata gane ba,. Karfe 9 da rabi yana gidan su Sa'a,, ita duk daukan ta wasa yake,yai katari kuwa Baban su yana waje,,Har kasa ya gaida shi cikin girma mawa,. Da fara'a Baban ya amsa,,Take yaji Hafeez ya kwanta mishi,dan ba kasafai yaran yanzun suka Iya girma ma manya ba haka..Ya kalle shi da fara'a, "Hala ka wani kake nema??Ya sunkuyar da kai kasa cikin girma mawa,, Da halamar kunya Yace"Baba dama wajen ka nazo,,Yace" Toh mu shiga daga ciki,Ya Sosa kai,Daga zaure ya cire musu farar kujera,suka zauna,sai leken cikin gidan yake ko zai hango sahibar shi,,Baban ya dan kula da hakan,"Allah dai yasa lfy?Ya sunne kai kasa cikin kunya,"Amm Baba sunan Hafeez, muna chan kasa daku kadan, dama,Amm,Sa'adatu na gani Baba,shine nake Neman izinin fara Neman auren ta a gun ka..Baban yai murmushi, a ranshi yana ambaton "Allahu Akbar,,Lalle zabin shi Dana Sa'an shi Yazo,,Dan duk wanda zai cika sharudan mulunci na Neman aure Hafeez ya fara,.Bai manta zancen shi da Sa'a ba akan Tara samari ba na aura,,bai manta amsar da ta bashi a lokacin ba,," Baba duk saurayin da ya fara zuwa Neman aure na wajen ka toh ya cika sharuddan aure na,,ka shaida hakan Baba,,nasan zaka fini sanin dawa na dace Baba..Da irin kalaman nan Sa'an take kara shiga ranshi,, ga daga gani daga gidan mutunci Hafeez din ya fito,,Ya kada kai, "Tabbas kayi abinda ya dace Hafeez, hakan ya nunan daga gidan da ka fito,,Allah yasa alkairi a ciki,,.Tuni ya fadada fara'ar shi yana sunne kai,, Baban ya tambaye shi iyayen shi,ya dai gamsu da duk bayanan shi,sai kuma bincike ya rage.. By Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 34_Baban ya shiga dashi ciki,yai wa mama magana,,ta fito da kamalar ta,Ya dan duka ya gaida ta, itama da fara'ar ta ta amsa,,kan tai dakin Sa'an da ta koma bacci,,. Ido waje take kallon shi, tunda mama tace tana da bako ta sa hijab,ta zata Ali ne,dan tama manta da Yace safe,,ido 1 ya kanne mata,, dai dai Baba ya fito zai tafi,yai mai sallama,, Ya dawo da kallon shi kanta,,Ta zauna tana mai mamakin jin sallamar shi da Baba kamar sun San juna,," Ina kwana,, yai mata wani kallo, ta kauda kai tana murmushi,,A hankali tace"Allah sa ma kai break irin wannan sammako,,ta dan harare shi,, yai murmushi,Tare da kama ciki, halamar yunwa..Ta make kafada,,ya marai rai ce fuska,,"Wajen Baba nazo,kuma na dace,,harma ya ban auren ki,harda dan duko kai a hankali kamar mai rada,,Ta kara dukar da kanta,,kan ta tashi ta debo mishi abinci,,ta zauna,,kunun gyada ne mai cous cous, yasha madara da lemon tsami,sai Doya da kwai,,Ya kalle ta yana nuna dakin mama,,yana yin halamar kar ta fito,,Tai dariya,,Ya dau cup din kunun yakai baki yana kara kallon dakin mama,ita dai sai dariya take mishi,,ya rintse ido,dan jin dadin kunun,ita kwa da sauri ta waro ido, ya bude ido a kanta,fuskar shi ba yabo ba fallasa,zatan ko bai mishi dadi bane,Yace"Hope ke kika dama,,ta [10/27, 12:11 PM] 💍🛍🍬Salma🍬🛍💍: [6/2, 5:38 PM] Feenat Ja'afar: Feenat Ja'afarSalma🍬Salma🍬🛍💍: [6/2, 5:38 PM] Feenat Ja'afar: Feenat Ja'afar🛍💍: FEENAT JAAFAR'S MOBILE BLOG JUST ANOTHER BLOG  BARIKI IYAWA 5  [10/2, 6:51 AM] Feenat Ja'afar: BARIKI...IYAWA 38_Ta daga mishi kai tana sunne kai,, "Tunda Baba ya sanar dani zuwan ka da abunda kazo nema wajen shi na amince maka,,." Hafeez, buri na ka cika a gun Abba,,Ta kallo shi," I'm inluv with you than I ever was...I love you too Hafeez,, Da sauri ta rintse idon ta da murmushin kunya, dan jin wata kunya da bata San tana da ita ba ta rufe ta,, Kallon ta yake yana murmushi,, kai shikam baiga abunda Sa'a ta rage shi ga mace da yake son aure ba.. " Kunya " "Addini: "Class" Kyauu " Da Iya kwarkwasa.. Shikam ya gode Allah, Sa'a ta mishi komai da ta so shi.. "Tnks much My Unique,,Yaushe zan turo a mini Tambaya?? Baki ta fara kunshe wa tana dariya kadan kadan,Tuni ta so zautar dashi,.. Yau sun buga luv,tamkar kar su rabu, Dakyar ta samu ta gudu gida dan magriba tayi,,Ashe haka "So" din yake??..Ashe Haka masoya suke ji amma a baya take ganin wautar su??..ita kam indai haka ne,toh itama sai ta sarrafa zuciyar ta, dan gujewa so mai zafi,,Ji take kamar dama ta girma ne da son Hafeez,,. Mama ma sai da ta gano yau Sa'a na cikin farin ciki matuka,,Dan komai ta ke sai kaga tana murmushi ita kadai,,. Shikam daga nan wajen Zahra yaje dan cika hukuncin Hajiyan shi,Da Tasleem ta sanar mata murna fal ranta,Wai yau Hafeez ne yazo gidan domin ta??.. Suna zaune bayan ga gaisuwa ta kasa ce mishi komai,dan jinsu take wani iri.,Shikam kallon ta yake yaga ta ina ta Gaza,, sannan mey Sa'a ta fita?..Ya kada kai,, "Amm Zahra magana nazo muyi ta fahimta,. Ta kallo shi fuska sake,,.Yace"Nasan kinji maganar ba ke kadai zan aura ba,,ina fatan tun yanxun ki rike ta yar uwar ki tun kan azo ga batun zama,,dan Sa'adatu she's simple, baki da matsalar zama da ita.. Tuni Annurin fuskar ta ya kau,,tai tsagal ta mike," Ya Hafeez kar muyi haka da kai,,Ban San wata Sa'adatu ba kai na Sani,,sannan ni kishiya,wallahi kishiya na dauke ta, ba Wai yar uwa ba..akan mey an gama magana tashin farko ka watgazan tsari..Kallon ta kawai yake yana murmushi,, Sa'an shi kawai yake tuno wa,mace mai Iya lafazi da kawai ci,,Akallah a haihuwar kaji zai haifi Zahra,amma dan fitsara shi ta tasamma aka tana mishi haka..Kyale ta yai sai da tai mai Isar ta harda hawaye,kamin ya taka mata birki. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/14, 6:30 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 39_Tuni ya hade rai,, Yace"Bafa shawarar ki nazo nema ba da zakimin fitsara,aure na da Sa'a kuwa zan Iya cewa shi yafi zame min dole,,so tun wuri kisan inda kika dosa,dan gaba bazata mana kyau ba,,.Nan ya barta tana ta kuka,A ganin ta magana ya fada mata, wato ita auren ta dashi bai zama dole ba??,,.Mamyn tata ta shigo dakin ganin Ta fito daga parlour tana kuka,.Lalle yar ta tana da aiki a gaban ta ja,don tana son tusa kanta a inda bata kwarjini, tasan tabbas kukan ta bazai rasa nasaba da Hafeez ba,, Gashi ta nace da sauran dangi sai anyi auren nan,amma tana tausaya wa rayuwar auren yar tata data ki jinin kishiya... Soyayya ake yi tsaftacacciya a tsakanin Hafeez da Sa'a, a yanxun kam ya maida gidan su Sa'a kamar gidan su, tun yana jin nauyin zuwa har ya ware,,sai dai abu 1 dake kawo musu cikas Ali,,Ali ya nace sai Sa'a,, tashin farko yazo da Baban shi Wai a bashi Sa'a,, kai ranar tai dariya har taji ba dadi,,sai a ranar ta kara tabbatar da Lalle Ali ba tsaran ta bane,, duk da Abban yaso tun wuri hakan ta faru,bai rufa wa mai gidan nashi ba ya sanar shi Sa'a Nada Miji,,sai dai a bawa Ali hakuri,,dake shi Dattijo ne mai dattako ya amince da Allah baiyi Matar shi bace,amma shifa Ali fir yaki daina zuwa,,duk da ko yazo ba kula shi take ba,da yaga baci ya dawo gori,inda alkawari ai Baba bazai ki bashi auren ta ba,kodan muhallin da Abban shi ya basu,,Take Sa'an tace"Indai wannan gidan kake wa toh ka kwantar da hankalin ka,amma aure ne ka kara lalata shi,dan ka nunan kai ba na kwarai bane,kuma dole mubar muku gidan Ku... gori har yaje kunnen Baba,.Tuni ta bawa mutanen da suke mata haya Notice, ta hau gyaran gida,,shi Baban bai zata ta dau zafi haka ba,,sai ranar Laraba bayan anyi da wata tazo Wai gobe zasu tashi,,da fari Baban dariya yake mata,sai dai ganin ta fara parking yasa ya tsayar ta,,"Sa'adatu ba fa Ali ya bani gidan nan ba,kinga bai kamata muyi wa Alhaji haka ba,, tace"Baba ai ko ba gori yaci karan nan ka yarda mu shiga gidan nan, Ina da gidan zama,amma fur kunki zama ciki,sai dai nasa haya,Baba chan gashi na zamani,nan na kasa,ya kamata inn ka samu dama Baba kai amfane ta,,kawai ce mishi zakai tashi zakai,daga baya ni nasan abin yi...Duk da haka Abban bai yarda ba,sai dai kamar yadda ta fada Washegari ta dakko mai katuwar Daf, Baban baya nan aka fara kwasar kaya,sai gidan Sa'a,, gida ne mai daki Uku,,biyu kana na,daya katon parlour, duk da baida wani girma,amma na bulo ne,kuma na zamani,daya dakin mai bandaki a ciki nan ta jera wa su mama kayan su da gadon ta,tasa aka sa carpet a pparlourn da manyan tuntu,,sai fridge da Katuwar TV,,Ita kuma ta hular da katifa da sauran tariki cen ta..Lalle gaya wa mai zuciya,bamai Dukiya ba,,,sai da kudin account dinta yai kat.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/14, 11:41 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 40_Baki sake su Baba suke kallon Sa'an,basu isa musu ba,dan har kuka ta sau musu,,Mama ta lallabi Baban,,ta kira Fadeela ita tazo,Gidan ya musu dai dai,Dan tsakar gida ne mai dan fadi kadan,anyi mishi siminti,suna da ruwan su,komai dai dai sauki akwai shi,Fadeela ma tai farin ciki sosai,,. Da yamma Baba ya sanar da Alhaji cewa sun tashi,yai hakuri abinne yazo musu a bazata,,yai mishi Allah sanya alkairi, ai gida kam nashi ne duka,zai yi duk yadda yaso,sai yazo ganin gida,,.yaji dadin yadda ya fahimce shi kwarai,yai mishi kwatancen inda suka koma,.kan ya dawo yana fada ma su mama yadda sukai,Sa'a tace Baban ya bata mukullin tsohon gidan toh,za ai mishi aiki,zuciya 1 ya bata,yana mai shi musu albarka. Tai ma Hafeez text, cewa sun tashi da address, dan tasan zai Iya zuwa bai same su ba,,5da rabi kuwa yazo, yana ta yiwa mama murna,,da Allah sanya alkairi,, Nan take sanar shi ai Sa'a ce ta tada ballin sai sun tashi,ba shiri,,yai murmushi, Yace "Toh ya kikai da yan hayar cikin??Da mamaki take kallon shi, Ya akai yasan nata ne?,Sai da suka je parlour yana yaba tsarin gidan,komai a saukake, amma da kyau,,yadda suka zauna a Chinese carpet din ma ya kayatar shi,ya jin Gina a tun tun,kamar wani basarake,,nan ta sanar mishi abinda Ali Yace, " Shine na basu Notice, bawai kora na musu ba,tana murmushi, ya kada kai, "Good,kin min dai dai,nan din tunda ba na uban nashi bane naga kafar mutum,,Tuni ta hau kunshe baki tana dariya,,Fadeela ta shigo suka gaisa,yana mata itama Allah sanya alkairi,.. Alhaji yazo daukan Fadeela yaga gida,,yana ta son barka,,nan yai wa Sa'a zata ga gudun mawar shi,,. Ko minti 3 ba ai da tafiyar Fadeela ba,Ali yazo,Baban shi ne Wai Yace yazo yaga gida kan suzo,,Allah yasa baban baya nan,Sa'a tace ya jira ta a waje toh,,Da dariya suka fito,da ka gansu kasan suna cikin nishadi,in ran Ali yai dubu ya baci,,a zuciyar shi yana,,"shifa kota ya ya sai ya samu Sa'a, atoh, yama ji da kyau,,..Ba ko magana ta mika mishi key, Ya karba yana kallon ta,,. Hafeez Yace" Ganan keys na gidan naku,,an bar muku shi sarkin yan gori,,en ya zamo last da zan kara ganin kafar ka a gidan nan,, dan bazata mana kyau ba,,Suka juya Sa'a na daga mishi hannu da shakiyanci,,ya kulu Iya kuluwa,,. Direct Baban shi ya kaima key in,,. Washegari sai gashi yazo da kanshi ba'asi,, Baban ya kira Sa'a,ba ko dar ta korowa Alhaji bayani,kan danshi ne ya Goran ta musu,Alhaji ya girgiza kai, "Sa'a in banda abinki, ai ni nai kyautar nan ba Ali ba,,Ya ajiye musu kan ya basu hakuri,tare da sanar shi zai ga Alin. Sa'a sun gama schl,sai Attachment,Zancen aure sai karfi yake,yayin da Zahra sai baudewa take,Da son abun Sa'a take attachments din,daga dan wannan sukai sha'awar daukar ta bayan ta gama.. Ansa bikin su zuwa Hafeez din ya gama ginin shi,,Duk bangaren kowa na shirye shiryen biki. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 7:13 AM] Feenat Ja'afar: [1/19, 1:13 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 41_Matsala 1 da ta fara fuskan ta shine kana nan maganganu da dangin Hafeez suke a kanta,,dan sau daya da ya taba kaita ta gano basa yi da ita,,tun daga ranar ta kudiri wani abu a ranta,burin ta kawai Allah kai Damo ga harawa. Makarantar zama da Miji mai mata ta bazama nema,,duk wani wa'azi mai kyau da ma'ana, mai taken mallakar Miji Sa'a Nada shi a waya,,duk wasu littattafai da tasan tabbas zata kara Sani akan su ta neme su,, Matakin farko data fara shine Bincika yanayin kayan Dakin da Hafeez yake da muradi,cikin wasa sukai abinsu,nan kwa bai son satar amsa tai ba,,a haka in fira tai dadi a wasa da wasa sai da tasan mai Hafeez yafi so na daga abinci, sutura,color, best perfumes da sauran su,,kan ma ta shiga ta gama karantar daga A har Z.. Tanan tai wa Zahra zarra tun kan su shiga,ita kullum batta dabara sai ta yaya zatai Hafeez ya zama nata ita kadai?? Duk abinda aka sa mishi lokaci toh tabbas zaizo da sannu,babu wanda yakai Hafeez da Sa'a farin ciki, duk da Zahra tana farin ciki, amma Sa'a ce ta tsokane mata ido,,ganin har yanxun yadda yake rawar kafa a kanta,duk da tayi nasarar sanya dangi yadda da cewa Lalle Hafeez zai auro musu karuwa,,kuma tabbas sun yarda,,. Hakan yasa dai dai da lefen ta a dangin Hafeez din sai yan tsirirai ne suka kai,,yai kaya na azo a gani,duk dunsu ba banbanci,,,Ware kunya Sa'a tai ta hau gyaran kanta da kanta,,.Tsohon gidan su sukutum ta maida gidan gyaran ta,Tun kamin sati da biki ta kammala duk wasu jeka ka dawo na hidimar ta,,ta hada nutsuwar ta waje guda,,dan kwarai tunda taji wa'azin Malama zuwaira ta dau darasi,,don tabbas itama ta fahimci yawancin amare basa cikin nutsuwar su ake kaisu gidan Miji,,kenan duk wani gyara da za'a miki kadan ne zai tasiri a gare ki,dan komai yana bukatar nutsuwa.. Kaflas din fenti babba tasa aka nemo mata madarar shanu,dan tasan takamar da za'a gwada mata kenan su Zahra, dangin Fulani,tasha tai wanka ..,sai da tai ta wankan amare na Lalle kullum a daura Dana madarar shanu da turaren Durot,,,Wata kwararriya ta samu,tazo har gidan tana biyan ta,,su fresh Nonon Rakumi, Su ganyen Tumfafiya,tai,duk wani sirri ta nemo su ta hada anyi mata,kan satin biki yazo in ka kalli Sa'a tamkar wata yar black Indian nan masu kyau,sai shining jikin nan yake,ga wani dan karan kamshi da laushi da fatar ta take,,kai kace daga Maiduguri ta fito,,Dan tun kan biki tasa wata Qawar ta yi mata hanyar wani mai hada turarurrukan mata masu kyau da kamshi,,Dan ita akwai son kamshi,musamman na turaren wuta.. Yau Juma'a, ta kama gobe za'a dauro auren su Hafeez da Matan shi,sun shirya kyatattiyar Dinner,, Kowa ya halatta Sa'a kawai ake jira,,in kaga ango sai wage baki da ido yake yaga ta ina zata ratso,,Zahra an hakimce a kusa da Hafeez, an Gaji da kyau itama,,gashin nan an zubo shi baya,duk da taiwa Hafeez din kyau amma shi burin shi yaga Sa'an shi,,duk sunyi waya tace suna wani room ne a hotel din 5 mint's,,. Hargowa da fadin MashaAllah shi ya juyar da hankalin Hafeez da Zahra,,tafi ake mata,ganin gasu Tj yan kanan Bodyguards dinta na unguwa sunyi wankan bakaken suite, kowa yasha bakin glass,yaran sunyi kyau matuka,sun shassha kunu su a dole masu tsaran Aunty Sa'a, sai abin ya kayatar,Ga nan Qawayen ta yan karya da wanda sukai Turkish suma sunsha kyau,,sanye take

Chapter 6 of 11