Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 11
kaddamar mata,, ki duba tun yanxu mun zama bola?ta kada kai, "Allah ya kaimu,,. Washegari yana fita suna fita,direct gidan su Sa'a sukace driver ya kaisu,.zai musu suka hayaiyako mai,, tuni jiki na bari ya kaisu,,Suka karewa gidan kallo,nanne Wai gidan su ma,,ciki sukai,lokacin tana brush a gindin famfo,, da doguwar Riga ta bacci mai silik,da Maman ta suka fara cin karo,,da mamaki take kallon su, ganin ko sallama sun shigo gidan,,amaryar ce mai karfin halin tambayar "BARIKI fa??ta kuskure baki ta juyo rai hade,, suna hada ido suka ga ta bala'in yi musu kwarjini,,a jinin ta yake,,mudin kaso mata wulakanci indai kuka hada ido, toh sai dai ita ta sauke maka,Allah yai mata baiwar Kwarjini... da niyar nadar ta suka zo ko su ci mutuncin ta,,suka sau baki kallon ta,, mace kira kamar ita tai kanta?ji uban gashi da fagon wani guri?hmm lalle kam Sa'a ta wuce tunanin su,,tuni ta wayan ce wa tayi,tuni ta sau fuska lokacin da ta gane ko su waye su,,ta ajiye cup din tana kade brush tare da daukar mouth wash din,," Sannun Ku da zuwa Aunty,..Hajiyan ta kalli amarya, amarya ta kalli Hajiya.. Hee hee... BARIKI Ake fada muku,,IYAWA,, ta kallo mama,."ina taburmar nan?baki sake ta nuna mata kitchen,, ta tafi tana girgiza jiki,da kallo suma suka bita..ta dakko ta shimfida musu,,ta kallo su da murmushi,, "ya Ku zauna man,,tamkar wasu masu bin umarnin ta suka dawo,, ta koma daki ta sako hijab,.ta zauna," ina kwanan Ku Aunty?a ciki suka amsa,badan sun so ba,,Ta kallo Maman nata,"mama, baki nane fa,,Matan Alhj Muktar mai naci Dana ke baki lbr...Ba suba,hatta maman tata baki sake take kalle ta da sauri,, sukwa tuni suka gyara zama tare da sakar fuska,, tana ganin haka ta kada kai da murmushin mugun ta,, a ranta tana "woo ni BARIKI. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [6/2, 6:09 PM] Feenat Ja'afar: Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 14_Sai lokacin suka gaida Maman,.da mamakin su itama ta amsa,,ikon Allah, da ganin Matan da rashin mutunci suka zo gidan,,amma dubi Sa'a cikin seconds da bai wuce 3 ba har ta shasu,,kai,al'amarin yarinyar nan ita kanta tsoro yake bata,,Hausa sunce Wai Barewa bata gudu danta yai rarrafe,,toh gaskiya a kanta ta Musa,,dan ta ko'ina halin ta bai kama da na Sa'a ba,,da de fadeela ce,,sai dai in ta tuno ance kowacce mace da irin tata kissar a ake haifar ta,,. Kai ta kada musu,,ta kallo Maman,,tai mata halamar ta dan basu waje,,ta gyada kai, "ni zan fita ma,zan leka gidan gaisuwar nan da baban Ku yaje dazun,, ta kada" sai kin dawo,, ganan abincin ki a flaks,fadeela tayi makaranta.. Ta dawo gun su,"sai anjiman Ku, Ku gaida gida,,suka washe baki,"a dawo lfy,,Kanta fita Sa'a ta tashi ta dakko musu drinks a fridge din tsakar gidan,,da cups, ta zauna,,"Bissmillahn Ku fa,.suka kalle ta., "anya kuwa,sanyi da safe,tai murmushi,"toh ya akai? nasan da magana a bakin Ku,, sukai shiru,,tai murmushi,,zama ta gyara kamar mai Tahiya,ta dafa kafafun su,," am Aunty,, bari na fada muku Gaskiya,, wlh ba son Alhj nake ba,,en kuma Ku gode Allah,, shidai yana matukar sona,,sai dai ina lallaba shine saboda abu 1,,ta nuno su da hannu,, "saboda Ku,,dan kune matsalar shi,,kuma nayi alkawarin taimakon shi,,amaryar ta tabe baki,, ta kalle ta,," amma kun San mey? Uwar gida ta girgiza kai,,"mijin Ku na kaunar Ku,,amma kun tsaya kishi,,Baku da aiki sai tada mishi hankali,, ni fa mata na bani mamaki matuka,,. Kuma musamman Matan mai arziki, a gidan shi anfi tashin hankali,, kufa kalle Ku,, da girman Ku,,ai wlh kun wuce wannan gurin,,Ku tsaya kuyi kishi akan mijin Ku,. Kwatan kwacin Matan Annabi (S A W),,Ku kanku zaku dinga rage jin haushin juna da saukaka kishin,,nan tai ta musu,tare da sanar su Alhj ya sanar ta kom,, kuma tana tausayin shi Gaskiya.. "Sai dai abu 1 zan Iya muku,,suka kallo ta tare da sauke ajiyar zuciya,,Ku gyara tsakanin Ku,,Ku zauna lfy,,idan har kukai haka,shi kan shi Alhjn zaiji aurena ya fita a ranshi,kunga kun taimake ni,, kun taimaki Alhaji,. Sannan kun taimaki kanku.. Ni kuma zanji da sauran,, tunda Alhaji ya taba fada min,mudin mace bata son shi ta furta bazai aure ta dole ba.. Suka sauke ajiyar zuciya,, amarya tace. "Hajiya,wlh sai yanxu na gano matsalar gidan mu,,Sa'adatu tai magana mai kyau,, ya kamata mu hada kai koba auren nan,,kuma dama chan matsalar taki ce,,da sauri ta kallo ta" matsalar ki dai,,ni nace ki shigo da fetsara? tace"Toh ai kema ke kika yadda girman ki,,.tuni magana zata dawo fada Sa'a ta tsayar su,, "kunga irin ta ai,,na lura duk din kune Baku hakuri,, ni dai in Baku gyara hali ba,wlh zana yarda da Alhaji ya turo ne kawai,koda bana son shi,,.Amarya ta kallo ta" ke kuma sai an gama magana ki sako wata,,ai munce munji,,ta daga kafada.. "Ku dauka ni banni matsala,, Yanxu matsalar ta Ku ce kuda mijin Ku,,in kunji bayani na kun gyara kuga mai kyau,,in kun cigaba ta kwabe muku..toh wlh Ku zargi kanku,ta mike,"zan shiga wanka,,suma suka mike.." Mun tafi, sai kin jimu,,tai musu yake,"a gaida gida,,duk jiki yai sanyi suka fice.. Dai dai fadeela ta dawo,,ta kare musu kallo har suka fita kan ta dawo kan Sa'a.., "su kuma daga ina kika yayimo su?ta tabe baki,," Wai su nan da rashin mutunci suka zo,,any way,naga sun russuna,,aikina zai zo da sauki da halama.. "So nake a siyasar nan nai motar kaina a wajen Alhajin nan,,fadeela ta zaro ido" mota??tai murmushi, "karamar Alhaki ba,,ke Wai da ina sakar wa kana nan Yan iskan Alhazan nan da yanxu ina da motoci wlh,,yanxu haka ina da alkawarin gida a kasa..fadeela ta kada kai" ai ni tsoro kike bani,,wlh wannan ba Sana'a bace Sa'a,, ina gudun kar wataran ki hadu da dai dai ke,ko ki samu mai lakada miki duka..tai mata wani kallo "duka?mtsww wlh kina ban haushi,,ko kin manta duk inda zansa kafa tare nake da sojojin daba?? Ta waro ido.." Daba Sa'a? Tai murmushi "lalle da sauran ki fadeela,, kin ganni nan.. Ta nuna kanta" wlh na Iya taku na,,duk inda nake akwai masu take min baya tun daga safe har yamma,.a lokacin yara su karbe,,kamar yadda ake biyan ma'aikata a wata,nima haka nake biyan su..kuma nasan ba wanda ya sani..kema sai yanxun..ta kada mata kai.. "Shi yasa nace tsoron ki nake ji nima.. Sa'a akwai masu mugun nufi,,masu jefo asiri..da sauri ta daga mata hannu" ke ni ban son jafa'i,, na rike Allah, babu wanda ya isa ya min komai wlh.. Tuni ta hau jaraba tai bandaki.. Fadeela ta girgiza kai.. Sa'a bazata gane ba,, amma tunda ta saka Allah, ta gama komai.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/26, 2:12 PM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 15_Sai bayan la'asar Alhaji ya koma gida,,yasan da zuwan Matan shi zuwa gidan su BARIKI a bakin Bala driver,, sai dai da mamakin shi da ya shigo gidan An hadu da yara ana kallon Namamajo ana ta cin dariya,,kowacce taci Ado,tunda yake,abinda bai taba gani ba kenan a gidan shi anyi,,Wai a hadu,uwar gida da ya'yan ta da amarya da Ya'yan ta a waje daya..tab lalle ya fara ganin sauyi,,dan Babban burin shi dama Matan su hada kai, ya samu ya'yan shi ma su hada,,amma ina,ya kasa tsawan shekara 6,.sai gashi a abinda baifi kwana 3 ba BARIKI ta fara saita gidan shi,,toh ita kwa mey ta fada musu haka?da wani harshe tai musu magana wanda shi baiyi ba?? Ya kada kai yai sallama,, da fara'a suka amsa yaran suka taho da gudu mishi sannu da zuwa,tare da karbar kayan hannun shi suka ajiye gaban iyayen,,.Matan suma suka mai,ya amsa da kyar,,dan dole ya ga sauyawar su koba yau ba,,yai daki,,amarya ta kallo Hajiyan,, "mu bishi muji.. Suka ran kaya daki,,yana kokarin cire babbar Riga suka karaso,.karba sukai dukan su suna cire mishi,,ya tsaya baki sake yana kallon su,, Uwar gida tai murmushi," Alhaji muna fa sannu da zuwa,.ya kalle su tukun ya tabe baki,, "Ku Wai nan campaign kuke ne komai?suka kalli juna" name Alhj? Yai murmushi "na karna auri Sa'a,, zasui magana ya tsayar su,, " Ba abunda zai hanani auren Sa'a in fada muku,.gobe ma za'a kai kayan tambaya.. Da dariya suka fashe mishi,harda tafawa., tuni ya fara muzurai,, kadde fa sunyi wa yarinyar mutane wani abu??suka kallo shi, "Na BARIKI manya,,inji amarya,kai kace mana tusa mata kanka kake bamu Sani ba? Ashe ma ba son ka ake ba.. Ya bata rai" inji wa?suka hada baki"BARIKI.. Yai murmushi,,"eh a haka zan aure ta,, indai zata bani farin ciki a gida na,, ya wuce bandaki ya barsu tsaye,,zama sukai jiran ya fito.."aha Wai Baku tafi bane?? Suka kalle shi,, uwar gida tai gyaran murya.. "Alhaji,, ya kallo ta" eheem,.ta gyara zama"wlh ko ba aure mun gyara zaman mu,, kuma koda aure baza mu saba ba,,kai hakuri, munsan mun bata ma a baya,, amma wlh gaba bazai kara faruwa ba,,kallon ta kawai yake ya harde hannu,,tunda suke.basu taba sanar shi haka ba,,. Amarya ce ta katse shi,. "Nifa dan Allah nayi,,wlh kama daina cewa dan zaka auro wata BARIKI.. Ehe,.inma ka auro ta in baka Sani ba Toh yanxu ka Sani,.uwar gida sai daga mata hannu take halamar tai shiru,amma ina,dan fa ita yar gaba gaba ce,, tace" in baka Sani ba ka Sani"MATA UKU.. GOBARA(Na Mrs Jabo)Ce,,ehe,,gwara ma kai Hudu,.atoh,. yace "kun gama??uwar gida ta kada kai,"toh koh aman Wuta ne saina auro Sa'a., tashi tai" Hajiya mu tafi,,kai kuma Allah ya taimake ka..yace"Amin,, Suna fita uwar gida tace"Amma kin kwafsa mana fa,,tai kicin kicin.."Hajiya yi hakuri, wlh haushi ya bani,, kamar muna ziga shi.. Yana jiyo su ta daki,,.. Da dare ya samu BARIKI.. Sai murna yake,yau kam ta biya shi,,yaga abinda bai taba gani ba a gidan shi,,tai murmushi,"toh Allah yasa sun gyara kenan,.yace"Amin,. Amma Sa'a, nifa da gaske nake son ki fa,, wlh jiya da tunanin ki nai bacci..ta kalle shi tare da yin fari da ido.."Aiya Alhaji,, ina da tsayayye, sai dai baya kasar nan,PHDn shi in ya dawo muna da alkawarin aure..yai murmushi "anya Sa'a? Ya kada kai" Any way,, yanxu dai bamu tsadan ce ba..nawa kike ga zan baki?ta rausayar da ido,, "Alhaji masu gari,,Ashe ana cini ki kuma daku?yai murmushi, itama tai,..su BARIKI anso yaudara,,, tace" Ai zamanin siyasar yanxu da abunda ke hannun Ku manya ake kyauta ba cini ki ba.. Yanxu muna da kamar Ku a centern nan amma Bariki bata ko motar hawa..bare na samu ta raly..ta kanne mai ido 1..tuni ya hau washe baki,, lalle BARIKI,harda ke a yan campaign din namu Ashe??tace "kai,sosai, ai partn mu daya..tuni ta hau tsara shi tana kara kwadaita mishi kujerar da yake nema ta senator.. Dan dadi bai San ya mata alkawarin mota ba indai ya hau mulki.. Kamar gaske ta kallo shi da mamaki baki sake.." Alhj daga wasa??yai murmushi.."karki damu.,ai irin ku muke nema,,bare gaki da mutane,.indai kuka mana campaign yan partn mu sukai jama'a zakiyi mota..inkwa banci ba,,akwai wani karamin gida na a bayan layin nan,daki 2 ne,.na mallaka miki kodan saita min iyali da kikai..Tuni tace"Auxubillah, In Allah ya yarda ma kaci ka gama..yai murmushi"Toh amin sa a,,"Allah dai ya ja mana zamanin Ku Alhaji,, ni kuwa indai haka ne,kar kaji komai, a duk arear nan kune zakui wining..ko baku sau kaya ba..yace "A zama musau kaya.. Kai a hannun ki ma zai sauka,ta dafe kirji. " Allah Alhaji?ya gyada kai.,"Alkawari ne..tai murmushi.. Bai bar wajen ba sai 9 da 15.. Da haka auren Alhj ya tabalbal ce,,in kaje gidan shi gwanin sha'awa.. Dai dai da abinci tare suke,,duk sun fatattaki qawayen su yan ziga.. Suda Kansu sunji dadin zaman nasu..yadai wayance a cewar ya fasa auren Sa'a dan bata son shi..suka hau kuwa. Sa'a ta shiga makaranta, inda take karantar Mass communications., lalle tana da sha'awar hakan tun ba yau ba,, kamar yadda Alhaji ya alkarwan ta lokacin campaign nayi saiga katuwar mota a kofar gidan su Sa'a da sassafe,,lokacin tana ta aikin bacci,,baban su ya shigo dakin nata.."Ke Sa'a,.. Sa'a.. Ta tashi a kan sallaya tana mistsike ido.."Naam baba,.ina kwana..yace"biyoni tukunna.. Tuni ta ware.."Baba Lfy?ya fita tana biyo shi,, turus tai a kofar daki,,ganin yadda ake shigo da kaya..su fridge kana na,keken dinki,keken saka..turaman Attamfa.. Buhu buhun su shinkafa da sugar da sauran tarkacen kayan campaign... Tace "Malam daga ina haka?ya kallo ta. " yauwa da drivern mai gida muka zo..Alhaji Muktar.. Shi yace a kawo miki..tuni ta sau baki,,har ga Allah bata dauki zancen da mahimmanci ba,asali ma ta manta da zancen tana ta aikin karatun ta..oh baki bai ba,, yanxu taga uban da zai koya mata campaign,,ita da ko zabe bata taba fita ba bare campaign...tab shiga 3,kishiya maiya,, Miji Barawo.. Baban ne ya katse ta, "mey kenan haka ke nufi Sa'a?? Ta kallo shi ta fara inda inda..ya dakatar ta" Kinsan bazan taba yarda da wannan halin ba koh? Siyasa a gida na?kuma Wai kece shugaba? mamata mey kike son zama da baki zama ba?har gida gare ki fa,,ta kallo shi,ta marai rai ce "Baba wlh ban zata da gaske yake ba,, amma bari zan mishi magana.. Amma koni baba mey ya kaini siyasa anan garin..kai hakuri.. Mama da ta fito itama ta sau baki..ganin uban kaya a gida..ya kada kai" ni zan fita.. Ta dan duka"a dawo lfy Baba.. Yai murmushi, "Amin,Allah muku albarka.. tai murmushi" Amin Baba..ya kallo mama.. Mu min tafi..da baki take nuno mata Wai ta raka shi zaure..Maman ta mata dakuwa "yar kare..kai Sa'a.. Allah shirye ki.. Komai zage wa take ta nunawa uwar ta..ko daki baba ya shiga in suna waje ta dinga," mama kije man,,inkwa zai fita ta dinga sai ta raka baba zaure..BARIKI Duniya...Lol. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [6/2, 6:19 PM] Feenat Ja'afar: [12/26, 11:40 PM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 16_Daki ta shiga ta kunna waya,kan ta danna calling.. "BARIKI a Baku naku daban,,tai murmushi, "Alhaji ina kwana," lfy lau,. Ya karatu? tace "Alhamdulillah, " ya kaya sun iso koh?ta kada kai,"sun iso,,Sai dai fa Alhaji da matsala,, yace"matsalar mey Sa'a?koh sunyi kadan ne a karo miki?Tai Jim"Alhaji ba haka ba ne,,ni fa Alhj da wasa nake,,wlh ban taba harkar siyasa ba,,kaga kar nazo nai muku ba dai dai ba..ya gyada kai,, "Bari zanzo anjima da yamma,,ta kada kai" Ok,,bye.. Tai ajiyar zuciya.. Bata Iya cuta ba,bare ace ta Saida tace tai campaign din,,gwara yazo yasan nayi dasu.. Da misalin karfe 5 yazo,,bayan sun gaisa ya dau waya ya kira wata mata tare da mata kwatancen inda yake,,ba'a jima ba tazo a motar ta ita da wata yar unguwar yar siyasa,,Ya gaba tar mata dasu,"sune mataimakan ki,,ganan shu gabar Ku ta unguwar nan duka,,zata tsara miki yadda ake komai,,karki damu,ba Wai za'a fita dake campaign bane fa,,I trust you ne kawai, so ki rike kayan a gidan nan,,naki kawai ki bawa wanda kika tabbatar bata da karbi,kuma tana da kuri'a,sannan kuma zata dangwala mana,, ta kada kai "Ok,nagode Alhaji,, ya Ciro kudi bandir 3,yaba Sa'a 1 mai motar 2,,dakyar in zamu kara haduwa,.. Dai dai nan su Aminu sunxo wuce wa suka tsaya,, suka fito tana ganin su ta hau fara'a, tai sallama da Alhaji,, "Oh Aminu manyan kasa,.yaushe a gari??oh sorry Assalam Alaikum,, yai murmushi" Walaikum salam,," BARIKI manya,.da sauri abokin nashi ya dago Tare da sake kallon ta,. Da tunda yai arba da ita yaji zuciyar shi ta tsanan ta bugawa,. Yanxun ana kiran ta da BARIKI yaji wani damm..yai tunanin ko ya dace da DREAM GIRL (na Deeja Abdull)din shi,,dan yana son mace mai Aji, kwarkwasa, da iyayi da kuma addini.. But tashin farko a kira ta da BARIKI? Lalle bata kwarai bace.. Katse shi tai"ina yini.."BARIKI sai kin jimu,Alhaji ya bamu numbern ki,,ta kada musu kai tare da dagawa Alhaji hannu.. Tuni abokin Aminu ya kara kulewa,.dan da ganin dayar kasan muguwar yar BARIKIN asali ce,,gaisuwar da bai amsa ba kenan yaci mur.,tamkar bai taba dariya ba,, itama bata bi ta kanshi ba ta koma ga Aminu,, "Lalle BARIKI, tana fa kai miki mutuniyar nan,harda Su Alhaji Muktar yau a gidan nan??,,tai murmushi karo na 2 ta kallo abokin nashi,, tuni ya dauke kai,,ta tabe baki,," wlh aiki na mishi,kadai gane,kuma sai ta rufta dani,, ta wani marai rai ce mishi,,n wlh i don't know what do?? Ganin yadda take wani marai rai ta ta kara bawa abokin nashi haushi,. Ya kallo Aminu, ka saman a mota,,ya kallo ta ya watsar tare da harara yai gaba,,take itama ta dauke shi ta yar,,harda dan tsakin ta kadan,,"ban San ya zanyi da baba ba,,Aminu daga wasa mutumin nan ya kawo min kayan campaign,, yanxu fisabilillahi ina ni ina siyasa 4 God sake,,dube ni fa,,ta fara gyara Riga, dama doguwar Riga ce a jikin ta sai mayafi data daura,,Aminu yai murmushi, "Yanxu da abinda zai gagare ki dama??ta kalle shi,," no ka gane, wannan da ban ne,en kasan bansan shudanya da kowa,.Shima wannan lallaba shi nake ya samu yaci ya sallame ni da mota..ya waro ido "mota Sa'a? Ta kada kai tana mishi wani feffekara,," hasko ni Kaidai,,"kuma kin yadda?ta kada kai "na yarda,.yai murmushi, "yan siyasa fa basu alkawari, da sunci suke manta da kai," No wlh wannan na daban ne...horn suka jiyo,,ya kallo ta "toh sai zuwa na 2,.tace" ina Qawata?ya kada kai,"chan muka nufa ai...tai murmushi, "da kyau..yace" au abokina ne,,tun satin chan ya dawo,bamu hadu ba sai yau,nasan baki san shi ba..munxo wuce wa na ganki nace mu tsaya mu gaisa..ta tabe baki,,Da" ganin shi dan raini ne wlh,.kai hakuri fa,atoh.. Yai murmushi,ai afuwa? Ke dai sai nazo karbar kaso na,ta raki shi har bakin motar.."Ok,see yaa,.ta dago mishi yatsun ta,, yai kwafa,,Aminu ya kallo shi,, "ya dai? Ya tabe baki"Amma dai yarinyar nan yar raini ce daga ganin ta? Take Aminu ya tariyo itama nata zancen" Da ganin shi dan raini ne..sai yai dariya,,.ya kallo shi tare da Harar shi"dariya na baka koh?ba kaga Harar da take min bane?ya kada kai, "na gani,,amma kai ka fara mata ai,,Sa'a na San tsaf,in an mata saita rama. Baka Santa bane,,amma Sa'a,, hmm ta kece raini ce wlh,,jin shi kawai yake, amma ya kasa tan kawa,, take yaji haushin yarinyar ya dadu,,wato har a kira ka da sunan BARIKI alfari ne ka amsa?? Mtsww yai tsaki,,Aminu ya kallo shi,," ya akai kuma? Indai Sa'a ce yi hakuri, abar zancen ta. "Yanxu muje na kaika wajen Ummi,kaga hadaddiyar Babyn da zan aura,,.ya kada kai, shikam bai fiya magana ba,,Aminu ne mai surutun tsiya. Ummi ta fito itama duk kusan kiwon Sa'a ne,. Dan tare suke schl yanxun,, itama akwai iyayi,sai dai bata kai Sa'an ba.." ya gaba tar mata da abokin shi Hafeez, da fara'ar ta tace"a yau kam naga Hafeez,, yau she a kasar?yai murmushi, satin chan.. Ya shirye shirye?biki ya karato,.ta kalli Aminu ta sunkuyar da kai kasa tana murmushi,.a toh da dan dama dama,tunda ita tana da kunya,a ganin shi sun ban banta da Sa'a Qawar ta, dan shi kam yana son mace mai kunya,,. Anyi siyasa lfy,dakyar baba yabar ta a gidan ma,,Allah cikin ikon shi Su Alhj Muktar sunci zabe,Shima ya samu hawa kujerar senator,, randa za ai walima har BARIKI Matan Alhj suka gaiyato,,.sai dai yau har wata da hawa kujerar senator ba mota ba lbrn ta,har ta fidda tsammani,,. Yau bikin su Aminu saura wata 3,.su Sa'a kirjin biki,,taje gidan su Ummi zatai mata rakiya siyayya super market,,. Suna tsaka da zabe zabe,tayi gefen cosmetics tana zaba Ummi na bata basket tana zubawa, sai dariya suke dirka,, gaba daya hankalin ta yayi kan zancen Ummi,, ta mika hannu zata dau turare bata kula da mutum a tsugune zai dau abuba takai hannu,,da tsautsayi,gwan gwanin turaren role on na nevea ya fado kanshi yana dagowa,, da sauri ta sa hannu a baki kan tace" am really sorry pleas..tai shiru,take ta hade rai, shi kwa ba tare da ya dago ba yace"No,it's Ok,.."Sa'a meya far..jin an ambaci sunan wace yake haushi,,tuni Shima ya hade rai"kina kallon ina kike jifo min abu kai,,tuni itama ta kankan ce ido,,"ina kallon ka ne,,yai tsaki, "au,haka ma zaki ce? Ta tabe baki,, zata wuce yasha gaban ta,, " na fiskanci yar rainin hankali ce ke,,inba haka ba..."Hafeez,, mey ya faru?Sa'a? Tuni ya ware,,"a Ummi,,ta kalle su duka"Naam,Hafeez, ya akai ne?meya faru,,yai murmushi, "no ba komai,,ya Aboki na,, Sa'a tace" uhmm,ta wuce gaba,,ya bita da kallo,."Ummi zan wuce, koh kin gama?tace"eh mun gama,bari mu biya,,suka jera suka je wajen biya,,ya ajiye nashi,,kan ya kalli wajen mai kirgen"nawa ne kudin nasu?ta kalli Sa'a "tare kuke har ita,. Ta kallo ta" wa?Allah sauka,hanyar jirgi daban ta mota daban,, tana mai wani kallon 9 saura kwata,tuni ya kule,,yace"da ke zan biya wa?ya kada kai, "u must be jocking,, yai mata wani kallon raini,, zata tanka Ummi ta sako baki" Wai kun San juna ne hala? By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/27, 12:34 AM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 17_Ta maka mishi harara kan ta koma kan mai kirge,,"ki fadan kudi na ko na bar muku kayan Ku,,mai kirge tai murmushi,, ganin fadan nasu abin dariya,,ta fada mata kan ta kallo Hafeez Shima ta fada mishi,, ta dakko kudi ta bata,. Ta suri kayan ta zatai gaba,mai kirgen kudi tace"hala dai fadan nan na masoya ne?? Ya kallo ta da sauri kan ya kalli Sa'an da ta juyo "dawa? da waccen ne masoya,,?yaja tsaki." Dan Allah ban chanji na kan ki Sani amai,,tuni ta kullo ta karaso.,ka kallen da kyau,,kasan ni ba irin Matar Ku bace,,ke kuma ki Iya bakin ki, dan he's not my type.. Ummi da tsabar takaici ya ishe ta,,ga shi har sun soma tada musu jama'a, tuni tai waje taja Sa'a,, da sai bambami take,,ya fito kan ya kalli Ummin "zo mu wuce man,,ta kallo sa'a" kiyi hakuri kizo ya sauke mu,,"kut,. Ummi,jeki,jeki kawai, na gode da rakiya,. Amma bazan shiga wannan akwarabar motar ba,,muka kalli mota nida Hauwa,,Lalle Sa'a, kin so kan ki,,shikam dariya ma ta bashi,, "Ummi,ki shigo kawai mu tafi,,ta kalle shi, ta kalli Sa'a, in ta shiga ta shiga 3 wajen Sa'a, ganin yadda take cika da batsewa,,." Kai hakuri Hafeez, inna barta ba dadi,ya daga kafada.."sai gani na 2..sukai sallama ta dawo gun Sa'a,, yazo zai wuce ya zuge glass,, "sai a hau ta haya,.tai mai gwalo" eh dai baza a shiga ba,.ya sauke glass ya wuce.. Tace"a sauka da nauyi..Ummi ta kallo ta,, "Sa'a, lfyr ki kuwa yau?meye ya hada ki da haffex har haka da zafi?wannan ai fadan yara ne wlh,..ta dallah mata harara," Dallah rufen baki kema,,Wai ke ga dadi saurayi,,. "Nan har hakuri na bashi,,ta shagwabe fuska kamar mai shirin kuka.." Wayyo haushi,, da nasan shine,da duk kayan wajen zan rikito mishi aka,,Ummi ta kallo ta lokacin tana tsaida mai taxi.."Toh naji muje,,zanji komai wajen Aminu ai,,amma dai kun bar abin fada, kuma shagon zuwan kine kinsan?tace"Toh ina ruwa na,, inna zo kar su siyar min..ta bude mota ta shiga.. Har akaje gida bambami take.. Kai ba wanda ta taba chachar baki dashi a girman ta sai wannan,,. Da dare akace ana sallama da Sa'a, ta kallo yaron da masifa, kace"Baza'a zo ba,, mama da fadeela suka kalle ta,,tun dazo take dacin rai,,yaro yace"kai,Aunty Sa'a,, dan bakiga waye bane, tace"waye,,"senator fa,. Da sauri ta zabura.."Khali ban son karya fa..yace"ba kince ince bazaki zo ba,ta harare shi,"dallah da wasa nake,,maza kace ina zuwa,gobe kazo in baka chocolate.., amma kamin nan, da mota nawa yazo??yace "2,ta doka tsalle ta dire," wayyo niii...tuni ya hau zigata kamar yadda suka saba yi mata a unguwa.."in kin ganta wata karama mey kyau,,ko pikanto naji ana ce mata..,tace " Toh naji,..da sauri tai daki,ta yayumo gyale,,ta gyara fuska.. Mama da fadeela yan kallo..fara'a kamar gonar audiga tace"mama bari na leka..kai kawai ta daga mata..Tana zuwa zaure ta nutsu,,ta dan leko,,ya hakimce a wata dalleliyar bakar jeep,ga wata karama a gefe,yana ganin ta ya hau fara'a, ta karaso, "badai Alhaji nake ga ba?yai murmushi, "BARIKI da kanta,,tai murmushi kan suka gaisa,,yadda bata nuna mai komai ba yaji dadi,.ko irin zalamar nan.." Ai hakuri an jimu shiru,, tai murmushi, "Ku yanxu aikun shiga sahun uziri,,Yace" haka ne,kika ji bayani shiru.?tai murmushi.. "Alhaji name fa?yai murmushi, wato sai an nuna mai hali?hannu yasa a aljihu,," Ga nan alkawarin ki,tun dazu take jiran ki,nine yanxu na iso,kan wanda ya kawo ya tafi,,baki sake take kallon shi kamar gaske,,"Wai Alhaji da gaske?ya sha mur,"na taba miki wasa? mu kullin ta karba,baki sake take kallon key in,,"Alhaji da wace kalma zan gode maka?yai murmushi.. "Sa'adatu, gode Allah kawai,,sai dai har yanxun na kasa fidda ki a raina,,tun ranar chan Dana ga saurayin ki yazo na saddaqar,, ta kada kai" Aiya Alhaji,,kai hakuri,ya girgiza mata kai,"no karki damu,,kin burge ni da kika rike mishi alkawari,, kodan hakan nima yasa na cika miki naki alkawarin, dan ina son mutum mai rike alkawari da mahimmanci,,. Sun dan jima sukai sallama ya tafi..tana gani yai kwana ta zufa da gudu gida.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/27, 12:05 PM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 18_"Wayyo Allah na, Mama, mama,tun a zaure take kwada mata kira,,da sauri suka mike dan sun tsorata,, tana shiga ta rukunkume Maman,,"wayyo Allah mama maidani ciki,, wayyo Duniya sabuwa.. Mama ta dago ta,,"Sa'a murnar meye wannan haka? Dagowa tai harda hawayen farin ciki,, ta miko mata mukulli tana tsalle, "mama mota,,wallahi mota nayi sabuwa dau a ledar ta,,da sauri Maman ta kai hannu baki ta rufe" Sa'adatu mota??da sauri tace "mama Ku leko kuga wlh,, fadeela da mama suka bita a baya,,ganin motar yasa mama kusan zube wa,,ita kam shikenan karyar ta ta kare,,acikin 2 dole da daya,,ko dai Sa'a ta yar da mutuncin ta? Ko kuma a yayime ya yimen ta ta kwaso dan yankan kai,,ganin Maman tayi shiru yasa ta dauka ko yadda ne batai ba, da sauri tace "mam ga nan takaddun malkakar ta in baki yarda ba.. Kai ta girgiza mata,. Kan tace"muje gida Sa'a,, ta kallo fadeela da sai zaga motar take da murna,,suka ran kaya gida,,dakin su taga Maman tayi suka bita chan,,ta zauna a kan gado"mama lfy?Maman ta sauke ajiyar zuciya, kan ta kallo Sa'an "Ku zauna ni kam,,suka zauna, ta sake kallon su" Sa'a, ki dubi Allah ki fadan Gaskiya, ta waro ido "wlh mama da gaske nake fa,ta girgiza kai, " Sa'a ba wannan ba,, kin tabbatar ba mutuncin ki kika yar aka baki mota ba koh?da sauri tace"Subhanallah mama,,wlh Tallahi alkawari yamin in sunci siyasa zai sai min mota,,da akwai aikin da na mishi,wlh mama,,ta girgiza kai, "yanxu Sa'a bama wannan ba, mey zan cewa Baban Ku in yazo?itama sai yanxun ta tuna da baban su,tai shiru,,ana haka sukaji sallamar shi,kowa yai tsam,daga inda yake y tsaya a kofar,a tunanin shi ko bako sukai,,Maman tace ya shigo ba kowa,,ya bude labule" lfy kukai tsumu haka?motar waye a kofar gida?ya zauna suna mishi sannu da zuwa,,kowa sa kallon juna yake,sai da ya kara tambaya "munyi baki ne? tukun fadeela tace" Baba ta Sa'a ce,, tuni ya dauke wuta,,ya kallo Sa'an,, "Toh a ina kuma ta samo mota? Sukai shiru,Yace" dake nake,ta hau inda inda,, "umm..amm,ba..bani akai fa Baba, ta wani marai rai ce mishi kamar zatai kuka,, yai murmushi" nasan wataran sai sun fashe dake Sa'adatu,, ta zaro ido "Mey za'a su fanshe dani Baba?? Ya sake murmushin takaici kan ya kallo Maman sun,," Bissmillah man,,ya tashi ya fita,, mama ma ta bishi,ta kallo fadeela. "Mey fanshe wa Wai take nufi fadeela? Wai kuna nufin haka banza ba'a kyauta sai anci moriyar ka?fadeela ta kada mata kai" ana yi Sa'a,, amma ba irin wannan ba,,fisabilillahi a wannan marar waye zai baka kyautar mota haka kawai?? Ta kada kai, "Ok na gane,,wato Baku San ma abunda zan Iya¿da wanda bazan Iya ba koh?,, tashi tai tai waje,,a bakin kofa ta tsaya tana sallama,, Maman tace ta shigo,,ta kalle su duk sun wani cirko cirko.. Ita abun ma dariya ya fara bata,,"ni

Chapter 3 of 11