m a t a d a u k i c i k i n g a g g a w a e m e r g e n c y a k a n u f a d a i t a s aboda asamu a ceto ranta".............
"Yayin da yaran abun duniya ya ishesu Farha ta karasa gurin da daddy yake akwace kamar kace dashi tashi ya tashi cikin shesh shekar kuka take magana daddy nah nasan kana jina dan Allah ka tashi kada ka manta da alkawarin da ka daukar mun kace zaka rayu tare damu bazaka taba rabuwa damu ba me yasa zaka karya alkaqwarin da kayi
Muna matukar bukatar ka a kusa da Allah ka tashi ta fada jikin gawa ta cigaba da kuka kamar ranta zai fita
Ashrab t matso kusa da ita cikin kuka ta janyota jikin ta Kiyi hakuri autar daddy duk irin alkawarinda mutun ya dauka baya ta'ba cika shi saida izinin Mahaliccin sa dan haka kiyi hakuri daddy ya tafi kuma bazai ta'ba dawowa ba saidai muyi masa addu'a Allah ya sadashi da rahma"
Ta janye daga jikinta a'a Ashrab kada muyi haka dake da bakinsa ya gayamun haka dan haka ki bari naje na tayar dashi ninasan yana sona zai tashi
Wallahi ina son daddy bazan iya jure rashin shi ba shi isa bazan bari zuciyata ta sabu da yarda da yatafi ba jikina yana bani da daddy na yana nan da ransa doguwar suma yayi
Kuka mai karfi ya subuce mata katashi daddy dan Allah katashi gidan mu zai zama kamar kango idan har baka tare damu kada ka manta da yanda muka shaku muke rayuwa mai dadi cikin so da kaunar junan mu daddy dan Allah ka tashi......
Likitoci suka shigo farha na ganin sun doshi gurin daddy ta cikin sauri ta taso cikin daga murya tace kada ku kuskurah kuce zaku taba mun daddy daya daga cikin su ya masto kusa da ita kiyi hakuri Farha daddy ya rigada ya rasu abunda zai zamar masa gata ayanzu a kai shi makwancin shi kiyi hakuri ki fawwalawa Allah komai saiki ga ya sanya miki sassauci acikin ranki
Ta dago jajjayen ida nuwanta tace kana tunanin na yard da daddy ya mutu, to idan ma kana tsamanin haka tunanin ka yagayamaka ba dai-dai ba dan ni nasan yan nan da ransa......
Tausayin yarinyar yagama cika zukatan su domin kuwa sukansu sun san irin shakuwar da family yayi amma ba yanda aka iya hakan nan za'ayi hakuri
Baba direba ya kasa cewa komai tausayin yaran ya gama dabaibayeshi ya matso kusa da Farha da ta kankame gawar daddy ta hana kowa yaje kusa da ita har Ashrab tsaye take tana kallon yar'uwarta tana kuka ta kasa aiwatar da komai....... Cikin dabara ya matsa kusa da ita ya tausasa muryar shi yace yarinyar daddy ni nan ina bayanki bazan bari atafi da daddy ba saboda nima ban yarda da ya mutuba kinga karbi kisha ya mika mata lemo mai sanyi kamar jira take take ta karba ta sha sosai kafin yan mintina tafara ganin mutane dishi-dishi can kuma ta sulale kasa bacci mai nauyi yayi gaba da ita
Baba direba ya taimakawa Ashrab suka daurata agadon da yake kusa dana gawar Alhaji cikin sigar rarrashi yace kiyi hakuri hakan da akayi shine kawai mafita saboda idan har tana gani bazata yarda ayi komai ba bada wata manufa nayi hakan ba hasalima banyi hakan ba saida umurnin likita Ta dago na fahimta baba nikaina nasan hakan shine kadai mafita
Ta ja dogon ajiyar zuciya tace ya jikin mum ya jijjaga kansa jiki kam ba'a cewa komai saidai addu'a amma hajiya tana cikin wani hali
Ta share hawayen da suka gangaro mata tace baba direba wannan wace irin jarrabawa ce tazoh mana alokaci daya.
Kada ki damu Allah yana iya sauya rayuwar kowane bawa alokacin da yaso yakuma ga damar hakan ita jarrabawa Allah yakanyiwa bayinsa ne saboda ya gwada imanin sa idan kayi hakuri ka jure sai Allah ya buda maka ta inda bakayi zato ba
"Ta kara goge hawayen da suka gangaro mata wallahi baba direba dauriya kawai nake ji nake kamar nima mutuwar zanyi, ......."haka mutuwa take ya'ta musamman ta iyaye sai dai hakuri amma akwai d'aci ya mike bara naje likitoci suna jirana ya fice daga dakin yana goge hawaye"..... 'Kafin kace meye wannan duka yan'uwa da abokanan Alhaji musaddiq sunji rasuwar sa na kusa da na nesa kowa ya zoh ba'a samu yin jana'izar saba sai washe gari alokacin hajiya salma ta farfado Farha ma haka sadai ita hajiyar zaune kawai take bata cewa da kowa uffan sai hawaye dasuke zuba tamkar fanfoh......
Bayan an kammala shiryashi aka kawashi gurin iyalansa suyi bankwana hajiya salma ta kasa cewa komai sai kuka da takeyi farha tayi zaune kamar mutun butumi itama dai kamar bata cikik hayyacinta dan maganganun da take kadai sun isa su tabbatar da hakan..... Kusan kowa da yake gurin saida ya zubar da hawaye domin kuwa iya tausayi wad'anan iyalan sun bawa mutane tausayi matuka haka aka dauke shi aka fitar dashi domin sadashi da makwancin sa na gaskiya........
Gidan yayi shiru mutane sai kaiwa da kawowa suke yan zuwa gaisuwa.... Mahaifiyar munubiya itama tana gidan saidai wani abun mamaki da daure kai duk wannan abun da akeyi munu bata sani ba domin kuwa tun jiya bata gidan tana can hotel tare da abokin sha-shancinta suna sheke ayarsu tun adaren jiya maman ta take neman wayar ta amma akashe
Haka uwar takwana acikin kunci da kuma Allah wadarai da halayyar munu ace gidan da kake zaune ayi rasuwa amma kai bakada ko labari Allah dai ya kyauta.....
"Washe gari sai 10:00 pm na dare ta dawo gida tun a gate din gidan taso ta gane akawai abunda ke faruwa amma saboda batada mutunci ta share da baba direba tafara haduwa tayi masa kallon wulakancin da ta saba tayi shigewar ta ciki batare da tayi masa magana ba kamar ya sanar da ita amma kuma yanda yake cike da jin haushinta sai ya fasa yaga to meye amfanin hakan dama ita hakan zata soh tunda dama ba wani jituwa sukayi ba.... Ta baya tabi saboda bata son kowa ya ganta baran tana a dameta da tambayar ina ta kwana tana shiga ta yi wanka tabi lafiyar gado kafin yan mintina bacci yayi gaba da ita".....
Wannan ke nan
Tun asuba maman munu ta nufi dakinta tajima tana buga kofar amma shiru zuwa yanzu hankalin ta yafara tashi anya munu tana da hankali kuwa..... Can taji anbude kofar cikin masifar da tasabayiwa delu amamakinta taga maman ta ta tsaya cike da mamakin ganinta lafiya tace da ita kekuma yaushe a gari me kika zoh yimun da sassafe daki...."maganar ta kona mata rai matuka ta dake ta dannah kanta cikin dakin batare da tace da ita komai ba,..... "Tana mai jin haushin maman zata takura mata tace wai yaushe kika zoh ne kuma ma me kika zohyi nifa wallahi bana son takurawa nan dinma bazaki barni na huta ba sai kinbiyoni ki takura mun"....
"Ta dago jajayen idanuwanta tace bazaki taba gyarah rayuwar ki ba kenan munu banzoh gidan nan dan na takura miki ba hasalima dalili ne ya kawoni ta share hawayen da suka gangaro mata tace,
" Kina da masaniyar abunda yafaru kuwa? ta dago tana mata kallon raini tace ni ki gaya mun kawai sai wani janrai kike yi me kuma yafaru? "
" Allah yayiwa Alhaji Musaddiq rasuwa yau kwan biyu kenan
Babu kunya ba tsoron Allah munu ta daga hanu tasoma magana Alhamdulillahi nayarda kwallon mangwaro na huta da kuda"
" Kan Aisha yayi mugun kullewa da zantukan munu me kike nufi da hakan me kike nufi dayin hamdallah rasuwa fah nake gaya miki amma naga kamar ma hakan kikaso
"Ta dago bazaki ganeba bantaba tsintar kaina afarin cikin da na tsinci kaina ba yanzu zanbaki goron Albishir ta bude baki zata k a r a m a g a n a t a d a k a t a r d a i t a y a i s a h a k a s a r k i n z u b a k i t a f i i n a s o n z a n k a r a y i n b a c c i k a f i n n a z o h n a g a i y a l a n A L H A J I M U S A D D I Q . . . . . . n a g a k u m a w a y e y a k a m a t a y a z a m a n e x t t a r g a t e "
" T a s h e k e d a d a r i y a k a m a r w a t a b o s s "
" T o o o o o o o =?D?w a n n a n f a m i l y ' s k u n h a d u d a b a l a ' i s a d a i a d d u ' a c e z a t a f i d d a k u d a g a t a r k o n m u n u b i y a "
" K u y i h a k u r i z a n d i n g a y i m u k u k a d a n s a b o d a z a m a n t y p i n g d i n y a n a y i m u n w a h a l a y a n z u "
T A K U C E A K U L L U N
L A U R A T M B E L L O
S H A R E
V O T E
C O M M E N T . . . . . . . . . . . . . . . . . . . .
=؞?=ؕ?=؞?=ؕ?=؞?=ؕ?=؞?=ؕ?=؞?
B A N G A R E N A H
( p a r t o f m e )
=؞?=ؕ?=؞?=ؕ?=؞?=ؕ?=؞?=ؕ?=؞?
S T O R Y &