Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 11
ida in kina son ci gaba sai ki tura 500 via2670215530 ZULFAU YAHAYA ECOBABK sai ki turo min da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822 🔞Yanzu nake rubuta shi Ni ma banda complete in kin biya group ne zan saka ki 06.Apr.25 [06/04 15:24] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️ ```LoVe aNd HoRrOr story```👽 By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️} *SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta. *FCWA*☀️ ________________________ 01 Ra'ayi riga in ji ƴan magana, wannan haka yake a lokacin da matasa sa'anina ke sha'awar fita waje domin yin dogon karatu tare da burace-buracen ababen ƙyalƙyalin duniya ni kuma shiga ƙauyuka ne ra'ayina domin koyar da yaran da ke cikin duhun jahilci.Sunana Nafisa,matashiyar budurwa ƴar kimanin shekara ashirin da biyu a duniya.Na fito gidan sarauta,a jinin masu izza da taƙamar dukiya sai dai ni sam ba wannan ne a gabana ba.Duk da na sha wahalar shawo kan mahaifina kan ya bar ni na yi karatun zama malamar makaranta amma kuma fafur ya hana ni fita aiki wanda hakan ba ƙaramar barazana ba ce da cikar burin nawa. Fuska shaɓe-shaɓe da hawaye na nufi ɗakinsa,shine kaɗai tilo da na san zai iya yin magana mahaifina yayi amanna da ita ba tare da gardama ba.Ko sallama ban yi ba ballantana neman izini kawai na tura ƙofar,kamar kullum yana zaune kan dadduma yana jan casbi.A gabansa na zube kamar raƙumar da ke jin ƙishi,ya ɗago fararen idonsa ya zube su a kaina kafin cikin tattausan furuci ya ce “Naf !” Baki na turo gaba idona na sake zubo da wasu sabbin hawayen. “ Yau kuma wa ya taɓa ki?” ya tambaye ni cikin nutsuwarsa wacce ke ƙara masa ƙwarjini. Cikin kuka na ce “Daddy ne wai ba zan yi aikin gwamnati ba” Yayi murmushin da ya bayyana fararen haƙoransa waɗanda kullum suke shan gugar asuwaki kafin ya ce “ki je zan yi masa magana” da sauri na girgiza masa kai na ce “ a'a Please uncle ka tashi mu tafi yanzu kafin masu hura wuta su ƙara masa ƙaimi” na faɗi haka ne saboda ahalin gidanmu suna da ɗagawa sosai ta yadda suke ganin kamar ƙasƙanci ne a ce jinin gidan ya je yana aikin gwamnati,aikin ma koyarwa. Ya buɗe baki zai yi magana na yi saurin kamo tafin hannunsa wanda yake lutuf da tsoka sai taushi kamar na mace,hannun nasa ya duba da sauri na sake shi saboda ba tun yau ba ya yi min hani da hakan ba wai iya gare shi ba kawai a'a hatta ƙannaina maza ya hana ni raɓar su ko kuma taɓawa a tsakaninmu. Na sunne kai wasu hawayen na sake surnano min suna ɗiga kan farin hijabina. “Nafisatu?” ya kira ni cikin wani salo,ba tare da na ɗago ba na ce “ na'am uncle” “Me yasa ra'ayinki ya banbanta da sauran danginki? Me yasa kike son yin aiki alhalin mahaifanki sun tanadar miki komai na rayuwa?” Na ɗago na dube shi kafin na ce “ uncle kai ma ba ka son na yi wannan aikin jahadin na shiga ƙauyuka ina wayar da kan al'umma? Saboda me uncle? Kawai don iyayena suna masu arziki shi kenan sai na yi kwance na dogara da dukiyarsu? Me yasa ni ba zan yi aiki ba?” “ Saboda ke mace ce!” ya bani amsa yana kallon idona,ji na yi kamar ya watsa min ruwa zafi kawai sai na tashi na fita a guje ina gwanjin kuka.Ina shiga babban falonmu duk sai na tarar da ƴan uwana kuwa suna ta cece-kuce akan maganar,ɗakina na wuce direct na haye gado na kwanta rub da ciki amma abin mamaki sai na ji tamkar kan cinyar mutum ne kaina yake amma sam ban bai wa hakan muhimmancin ba na ci gaba da rera kukana,har na fi jin haushin rashin goyon bayan Uncle Salem kan na Daddyna.A hankali na soma jin ana shafar gashin kaina wanda ke luluɓe da hijabina,ido na soma lumshewa ba tare da na shirya ba yayin da kuma na soma sauke numfashi akai-akai.Ban sani ba ko na shiga duniyar mafarki ne ko kuwa zahiri ne amma sai na tsinci muryar wata dattijuwa na yi min gatana haɗi da bani tarihin ababen tsoro kamar yadda na fi ƙaunar kallon horror film. ★A can ɓangaren Uncle Salem kuwa Nafisa na fita da gudu yayi saurin tattare littafansa kafin ya gyara zaman hiramin kansa ya fito.Direct ƙofar da za ta sada ka da babban falon ya nufa bakinsa ɗauke da sallama,tsit duk falon ya ɗauka kafin duk su yi ƙasa da idanunsu saboda yadda yake da matuƙar muhimmancin da kuma girma a idonsu.Cike da girmamawa suka soma gaishe shi “ Barka da fitowa Daddy ƙarami“ domin haka suke kiransa in ka fidda Nafisa da take ce masa Uncle ita ma ɗin shine da kansa ya koyar mata da hakan. “Fatan dai ba ƙara ta ba aka kai wurinka,a toh don na san ba kasafai za a gan ka a nan ba” cewar Daddy yana ɗan murmushi yana kallon babban abokinsa,amininsa kuma ɗan uwansa.Uncle Salem ya ce “tun da ma ka sani ai shi kenan sai a fara shirya mata abubuwan da za ta buƙata in ta je can” Daddy ya ɗan nisa yana kallon yaran wurin duk sai suka tashi suka kama gabansu,sai a lokacin kuma Uncle Salem ya zauna suna fuskantar juna. Duk shuru suka yi na wani ɗan lokaci kafin Daddy ya ce “ ba wai yadda kake tunani ba ne aboki,ina da dalili na daban da yasa ban so Nafisa ta yi nisa da gida” Uncle Salem ya murmusa ya ce “tun muna makaranta ake faɗar wannan kalmar akan kana da dalilin ƙin yin wani abu amma har yanzu ba ka taɓa faɗa min mene ne dalilin ba.Abdul Hameed ka sani cewa su yara da kake gani sun fi son bin zaɓinsu kan na iyayensu,kuma kai ma in ba ka manta ba...” sai kuma yayi shuru. Yanayin fuskar Daddy ta ɗan sauya kafin ya ce “babu damuwa zan bari ta je ɗin, Allah ya bada sa'a ya kuma tsare ta akan abin da nake tsoron faruwar” da “amen“ kawai Uncle Salem ya amsa kafin ya miƙe tsammm ya nufi ɗakin Nafisa,ya tura ƙofa tare da yin sallama sai kuma yayi tsaye cak yana buɗe ƙofofin hancinsa saboda kalar wani ƙamshi da ya dake shi da bai taɓa jin irinsa a wannan duniyar ba.... [06/04 15:24] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️ ```LoVe aNd HoRrOr story```👽 By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️} *SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta. *FCWA*☀️ ________________________ 02 Tsaye yayi yana kallon yadda take bacci tana wani taɓe baki kamar mai kuka yayin da goshinta ke fitar da gumi.Ya furzar da wani huci kafin ya ƙarasa ya zauna bakin bed ɗin,a hankali ya cire mata hijabin nata wanda ya ɗan jiƙe saboda zufa.Sumar kanta wacce take baƙar ƙirin ya soma shafawa yana tofe ta da addu'a,a hankali ta soma sauke ajiyar zuciya tana wani motsa idonta kamar mai son buɗe su. Kamar wanda ke wasa da maciji haka ya soma shafa farar fatar fuskarta wacce ta yi ɗan ja saboda kukan da ta yi.Wata irin azababiyar ƙaunarta ce yake jin tana bijiro masa,ji yake tamkar ya ɗauke ta ya haɗiye tsabar so. Sam bai san abokin nasa ya shigo ba don ya lula sosai a duniyar tunanin muradun ruhinsa,sai jin saukar muryarsa yayi “ sai yaushe ne za ka sanar da ita ɓoyayyen sirrin da ka binne abinka?” Uncle Salem yayi saurin ɗagowa ya dubi Daddy ya saki ɗan murmushin da ya zame masa jiki kafin ya ce “ har yanzu Naf yarinya ce aboki,zan ƙara mata lokaci ” sai kuma ya mayar da duban nasa ga fuskarta a iya kallon da yake jifar ta da shi ya isa ya fallasa ma sirrin da ƙunshe a zuciyarsa. “ Shekarunta ashirin har da biyu fa,lokaci na ƙurewa girma na sake zuwar ma amma har yanzu ba ka ajiye iyali ba aboki” Daddy ya faɗa cikin rashin jin daɗi. “ Shi aure ai ba sauri yake so ba,a'a fahimtar juna aboki.Ka yi tunanin yadda Naf za ta ɗauki lamarin ne in ta ji cewa ni mijinta ne alhalin a uba ta ɗauke ni?” Daddy yayi murmushi kafin ya ce “ to ai kun fi kusa,ban iya na sani” Uncle Salem na shirin yin magana aka shigo haɗi da sallama,Ammy ce hannunta riƙe da kofin ruwa.A mutumce ta gaishe da Uncle Salem wanda a girme ya girme mata sannan ta dubi mijinta hasken idaniyarta ta ce “ ga maganinta yau ba ta sha ba sam” ya karɓa ita kuma sai ta fita. Kan dakalin gado Daddy ya ajiye maganin yana mai kallon Nafisar wacce har zuwa yanzu take baccinta yayin da kuma hannun Uncle ɗinta ke kan sumarta. “ Aboki me kake ɓoye min dangane da Naf?” yayi tambayar cike da kulawa. A ɗan rikice Daddy ya ce “ no babu komai zan je na duba wasu takardu in ta tashi ka bata maganin” yana gama faɗa ya fice,shi kuwa Uncle Salem kai ya girgiza tun suna yara suke tare amma har izuwa yanzu bai san dalilin da yasa abokin nasa ke ɓoye masa wani babban sirri da ke ɗawainiya da rayuwarsa.Tun da Nafisa ta soma tasowa yake lura da yadda hankalinsa kocokwam ke kanta hatta makaranta in ta je ya dinga kiran waya kenan yana tambayar labarinta,yana ɗaya daga cikin abin da yasa kuma ya basa aurenta tun ba ta san kanta ba amma har yau ya ƙi sanar da shi mene ne sirrin. Ganin kamar baccin nata irin wancan ne da ta saba yi ,sai Uncle Salem ya ɗauki kofin maganin ya cika bakinsa da shi kafin ya taɓe bakinta yana ɗura mata shi kamar yadda tantabaru ke ciyar da junansu,a hankali kuma take haɗiye ruwan maganin da shi ne ya haɗa mata shi a haka har ta shanye shi tasss.Da ya kai ƙarshe sai da ya ɗan lashe mata lips kafin ya miƙe ya fita,sashensa ya nufa ya rage kayan jikinsa yayi wanka ya fito ya shafa turare kawai sai ya ɗauki system ɗinsa ya soma aiki yana duba saƙonnin sojawan da shine ya tura su mission a daji.Reppot ne iri-iri wasu na murna wasu na jimame,tuni kansa ya soma yin hayaƙi yana jin cewa da buƙatar ya je can ɗin da bada wata sabuwar atisaye. ★ NAFISA Ban san iya lokacin da na ɗauka ina bacci ba,ko da na tashi da ƙamshin turaren Uncle Salem na soma cin karo wanda ya game ko ina na ɗakin.Na turo baki gaba kafin na dubi hijabina wanda na san da shi ne ya cire min shi ko shakka babu.Wanka na shiga,bayan na fito na yi sallar azahar don sallah na ɗaya daga cikin abin da na fi so a kaf cikin abubuwan ibada ita da azumi wannan kuma horarwa Uncle Salem ce tun ina ƴar shekara sha uku yake saka ni yin azumin Litinin da Alhamis,tun ina kukan yunwa har na kai na saba. Ina zaune kan dadduma Ammy ta shigo,“yawwa kin sha maganin ashe ” shi ne abin da ta fara cewa. Shiru na yi ina tunanin yaushe na sha magani amma ban tuna ba,amma tabbas da na tashi na ji bakina na zaƙin zuma.Na sake turo baki don kuwa tuni kwanyata ta hasaso min ina baccin ya bani magani. “ Ammy ni yunwa nake ji” na faɗa kamar zan yi kuka,“ Sai ki je ki ci mana,ki taso ki kaiwa Daddy ƙarami abincinsa” ta faɗa tare da ficewa .Ina kukan sangarta na fita zuwa falo,cikin gunguni nake cewa Ammy “ duk ga ƴan aiki nan amma shine ba za su kai masa ba sai ni ” Ta dube ni da mamaki kafin ta ce “ au! Dama can ƴan aiki ke kai masa abinci?” Ba tare da na ce komai ba na nufi dianing na ɗauki ƙaton tray ɗin da aka jera komai nasa,na ɗauka tare da fita ina tafe ina turo baki har na isa sashen nasa dakyar na lalubo sallama can ƙasan maƙoshi na yi. Bai amsa ba sai ɗagowa da yayi yana kallona kafin kuma ya mayar da dubansa kan system ɗinsa.Hakan yasa na ji haushi na ajiye tray kan table har na juya zan tafi na ji ya ce “ Naf!” na tsaya cak ba tare da na juyo ba ina jiran abin da zai ce sai kawai na ji tsayuwarsa a bayana.Da sauri na juyo muna fuskantar juna,idona tab tsoro nake kallon nasa da nake hango tsantsar ɓacin rai a cikinsu. “ Ka yi haƙuri!” na faɗa murya na ɗan rawa.Bai ce komai ba ya kamo hannuna ya zauna da ni kan kujera,“ ki zuba abinci ki ci” shi ne abin da ya faɗa sam babu wasa a maganar sai ya je ya zauna ya ci gaba da aikinsa. Ni kuwa kallo na soma ƙarewa kyakkyawar fuskarsa mai cike da yalwatacen saje da ɗan madaidaicin gemu,kan jajayen laɓansa na tsayar da ƙwayar idona waɗanda ke yin furucin da babu sauti da alamu wani abu yake karantawa. Tamkar wacce aka yi wa dole haka na ƙanƙance ido ina karanta bakin nasa,na waro ido jin tamkar har da muryarsa ke yi min raɗa a kunne tana sanar da ni abin da yake cewa ɗin. “ Ba ki ji abin da na ce ba?” ya jefo min tambayar,da sauri na mayar da hankali kan abincin haka na zuba na soma ci lokaci-lokaci ina satar kallonsa har na gama. “ Kawo min wanda kika rage ɗin” ya faɗa ,sai na dubi plate ɗin yadda duk abincin ke cakule saboda miya da na zuba dayawa don ina son haka. “ Uncle bari na zuba ma wani” na faɗa tare da ɗaukar wani sabon plate ɗin. Ya ce “ wanda kika rage nake so” Na ɗan ɓata fuska cike da kunya na ɗauka na kai masa,ya amsa ya ajiye shi kan system ɗin kafin ya soma ci hankali kwance . “ Uncle wannan wane ne?” na tambaya ganin wani matashin soja baƙi an naɗe kansa da bandeji. “ Wani ne” ya bani amsa,da ido na ƙara kafe hoton don kuwa ni dai yayi min kyau sosai har ban san lokacin da na ce “ yana da kyau sos...” yadda Uncle ya ƙware ya shiga yin tari ya hana ni ƙarasa abin da nake son faɗa,da sauri na je na kawo masa ruwa ya karɓa tare da rufe system ɗin ya soma sha kafin kuma ya miƙa min kofin ya je ya kwanta kan kujera mai zaman mutum uku yana wani jan numfashi tuni na tsure wuri guda ina kallonsa.... [06/04 15:24] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️ ```LoVe aNd HoRrOr story```👽 By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️} *SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta. *FCWA*☀️ ________________________ 03 Jikina na ɗan rawa na isa gare shi ina mai zube wa ƙasa daidai kusan kansa na ce “ Uncle?” shuru yayi min bai ce komai ba haka ya ƙi buɗe idonsa,hakan sam ba ƙaramar barazana ba ce a gare ni don gani nake na yi masa laifi ne har ya sa shi ƙwarewa amma ban san taƙamaimai mene ne ba. “ Uncle?” na ƙara faɗa wannan karon ina mai kai hannu ina gwale fatar idonsa a dole so nake ya buɗe su ya kalle ni,na kuwa ci nasara ya buɗe su sai dai yadda suka yi ja sosai har sai da na ji tsoro na ɗan ja baya. Murya a disashe kamar wanda ransa zai fita yana kokowa da numfashinsa ya ce “ Nafisa me na faɗa miki? Ban ce kar na saki ko da wasa kin ce wani namiji yana da kyau ko kuma ki kalle shi ba?” Na ɗan ja ajiyar zuciya tare da matsowa na ce “ ka yi haƙuri Uncle ba zan sake ba,amma saboda me Uncle? Ka ga fa duk ƙawayena suna da samari ni amma ka hana ni kuma...kuma kamar mai baƙin jini maza sun tsane ni ” shaaa hawaye suka zubo min tuna yadda ko a makaranta ƴan ajinmu ba su shiga duk abin da ya shafe ni,kusan kuma malamanmu maza ma haka ba kasafai suke saka ni yin wani abu ba,in an zo nan ta wurin ƙannaina da kuma mazan da suka zo karatu a gidanmu su ma duk hakan ce ke faruwa. Ba tare da ya ce min komai ba ya tashi zaune haɗi da ɗan duƙewa ya dafe saitin zuciyarsa,ina ganin haka sai na miƙe da sauri har ina tuntuɓe na nufi bedroom ɗinsa na ɗauko masa maganinsa.Na cika kofi da ruwa tare da ɓallo ƙwaya biyu na miƙa masa ya karɓa tare da sha,cikin ƙanƙanin lokaci ya soma yin wata ajiyar zuciya kafin ya ce “ ki je ki haɗa kayanki,zuwa jibi sai na kai ki can ƙauyen da za ki koya” Duk ƙuncin da ya cunkushe min zuciya ne ya tafi ban san lokacin da ƙawa zuci ya ja ni ba kawai na rungume shi ina cewa “ na gode sosai my Uncle,kenan har ka yi magana da Daddy ya amince wayyy!” na yi ihun murna ina jijiga bayan Uncle da na rungume tsam a ƙirjina kafin kuma na sake shi da gudu na bar falon. Ina shiga ɗaki na tarar da family na cin abinci,ɗakina na nufa na shiga sauko da akwatina ko taimakon masu aiki ban nema ba na soma shirya kayana ina yi ina murmushi ina jin daɗi na luluɓe min ruhi.Sai hoton kaina nake gani a cikin aji ina koyar da darasi wa ɗalibaina,ban zauna ba sai na haɗa duk kayana na jiki da kuma jaka da takalma. Takardu da littafaina ma trolly daban na ware musu kafin na miƙe ina yawo cikin ɗaki ina magana ni ɗaya kamar irin yadda malamai ke yi.A hankali na soma jin ciwon kan da ya zame min aboki tun na ƙurciya na ziyartata,tun ina daurewa har na kai na kasa jurewa na haye bed na kwanta.Mafarkin da na jima ban yi ba tun shekaru kusan uku shine na soma yi kamar ana jirana. Tsaye nake kan ƙafafuna na mage ina juya idona masu matuƙar haske da hange nesa tamkar na Alhuduhudu. Manyan-manyan dabbobin daji ne a tsaye a gabana suna buɗe min bakunansu masu manyan haƙora yayin da ni kuma ke ankare da kowanne daga cikinsu kafin mu soma yin dambe ina jibgarsu duk na yi musu jina-jina da jini kafin wata halitta mai siffar babban sauro ta caka min bakinta daidai cikina .Azabar da ta ratsa ni ce yasa na saki wani razananen ihu,daidai nan na farka sai dai abin mamaki daidai wurin da aka cake ni ɗin har a zahiri ciwo yake yi min. “ Lafiya Nafi?” Ammy ta faɗa wacce ta shigo yanzu hankali tashe,ido na soma juyawa amma na kasa faɗa mata don ko na ce zan faɗi abin da na gani a mafarki kamar abin tsayi sam bakina ba zai iya furtawa ba. Hawaye kawai nake yi,sai shi ma Daddy ya shigo yana tambayar lafiya.Kai kawai na girgiza masa ,ya zo ya kamo hannuna ya ce “ kina ji na Nafisa faɗa min mafarkin me kika yi?” da sauri na janye hannuna daga cikin nasa,na diro daga kan bed na nufi ƙofa. Sai kuma na yi tsaye ganin Uncle shi kuma zai shigowa gemunsa na ɗigar da ruwa da alamu alwala ce yayi. Haɓata ya tallabo ta yadda zai iya kallon fuskata da kyau ,tsakiyar idona ya dinga duba yana wani motsa baki kafin ya ce “kin kuwa yi Azkhar yau?” Idona na soma juyawa ina son kauce kallon nasa da ba ƙaramin takura min suke ba,sam babu daɗi ji nake kamar yana zuƙo raina ne. “ Kin yi Azkhar na ce?” ya sake tambayata. Kai na girgiza alamun a'a,don kuwa ban yi saboda tun asubah na samu saƙon cewa sunana ya fito a jerin waɗanda za su je bautar ƙasa wannan zumuɗin ya shagaltar da ni yin Azkhar kamar yadda na saba. Ya sake ni kafin ya ce “ biyo ni” sai ya juya,haka na take masa baya ina waiwayen su Daddy muka fita zuwa can sashensa da yake waje. Ɗakin Uncle Salem ciki biyu ne da falo,ɗakinsa guda na bacci guda kuma wanda yake zuba kayan maganin aljanu na ruƙiya.Direct ɗayan ɗakin muka shiga,kaina ne ya juya da na shaƙi warin magani iri-iri yayin da gefen cikina daidai inda aka soke ni ya soma motsi har sai da na danne wurin. “ Zauna a nan” Uncle ya nuna min wata doguwar kujera,babu muso sai na zauna ɗin.Wata kwalba ya ɗauko tare da zuwa kusa da ni ya zauna kafin ya buɗe ta,tun kafin ya ce min na sha na soma hawaye don ni kaɗai na san irin abin da nake ji a duk lokacin da ya bani ire-iren maganin nan. Bakina ya taɓe tare da ɗura min maganin,jikina ya ɗauki rawa kafin cikin fitar hayyaci na soma basa labarin mafarkin da na yi tiryen-tiryen.Kwantar da ni yayi yana mai jan doguwar rigar jikina sama,da sauri na rumtse ido lokacin da ya janye hannuna ya ɗora nasa a daidai wurin da ake ta yi min motsi. Teburin da ke ɗauke da tarkacen da shi kaɗai ya san na mene ne ya jawo,ina ji ina gani da raina Uncle Salem ya soma tsatsaga fatata da reza.Banda wani zaɓi banda hawaye don tuni maganin da ya bani ya kashe min dukkan jijiyoyin jiki sai kaina da ke faman juyi tamkar an jefa ƙwarya a ruwa. Wata kwalba ya ɗora daidai wurin ya soma tatsar jinina har ƙarar fitarsa kake ji,kamar minti biyu kafin ya cire kwalbar ya ajiye ta kan teburi.Wani magani ya shafa min a daidai ciwon mai bala'in zafi,har sai da raina ya kusa fita kafin da sauri ya cika bakinsa da wasu ruwa ya zo ya fara shayar da ni su.Duk ɗigo ɗaya na ruwan da zan sha to tamkar ana warware azabar da yake jikina ne , wannan yasa nake shan maganin cike da zalamar da ta haifar min da soma shan yawunsa da kuma laɓansa. Jikin Uncle Salem ne ya ɗauki wata irin rawa jin Naf ɗinsa na sumbatarsa kamar za ta cinye leɓensa,duk wani tsohon feeling nasa da yake faman yin ƙasa da shi a kowacce safiya ya soma taso masa.A daidai gaɓar da ya soma mayar mata da martani kuma tuni bacci ya ɗauke ta,idonsa na fitar da wasu irin hawayen jaraba ya soma sunsunar wuyanta yana jin tamkar ya mayar da ita cikakkiyar mace ko zai samu salamar ruhi. Dakyar ya rareashi kansa ya janye daga jikinta,daɓas ya zauna yana duban yadda take baccin wahala . Ƙonannen jinin mai tattare da guba yayi baƙi ƙirin a cikin kwalba,sai ya ɗauke shi ya je ya zubar toilet ya wanke kwalbar. Sai da ya je ya sake wata alwala sannan ya nufi masjid,a can ya samu Daddy bayan sun yi sallar sun fito ne Uncle Salem ya dubi abokin nasa ya ce “ Abdul Hameed ban san me yasa ka zaɓi ka ɓoye min rufaffen sirrin Nafisa ba,amma hakan bai da wani amfani don kusan na fahimci matsalar junun da ke jikinta ya samo asali ne daga can tushe ba wai gamo ta yi da su ba” Cak Daddy ya tsaya yana kallonsa, Uncle Salem ya jinjina masa kai ya ce “ tabbas ko yau sun ziyarce ta,saboda sakacin addu'ar da ba ta yi ba” Daddy ya ce “ mu je can gida zan yi ma bayani” haka suka wuce suka isa,a keɓaɓen falon Daddy duk suka zauna tare da yin shuru Uncle Salem ya matsu ya ji labarin yayin da shi kuma Daddy ya rasa ta ina zai soma.Can ya nisa tare da furzar da huci kafin ya ce “ to da farko dai kamar yadda na faɗa ma ni ɗana ga sarauniya Ayodele Ayush,kafin zuwan Musulunci a Victoria Falls suna bautar ababen bauta iri-iri ,yin tsafi kuma sai ya zama adon garin.Sai dai sannu a hankali duk komai ya canza saboda yadda mahaifina sarki Ameer ya taka muhimmiyar rawa ganin ya kawar da duk wani fasadi sai dai kash zuwana duniya kuma aka tsiro da wasu sabbin canfi wai alamomi sun nuna za a sake yin maimaici wato daga cikin tsatsona za a samu wacce za ta jagoranci mulkin ƙasar.Amma tabbas ni ba magajin sarki ba ne,sosai na ji tsoro da jin haka don tamkar karatu haka ake biya min maganar nan har na mallaki hankalin kaina” Uncle Salem yayi saurin katse shi da cewa “ haba aboki ta ya za ka yarda da wani canfi?” Daddy yayi murmushi wanda ya fi kuka ciwo kafin ya ce “ dole na yarda mana,duba da tun ina ɗan shekara ashirin a duniya na ajiye iyali saboda yadda kullum nake kasa bacci ina harin neman abokiyar rayuwa wacce zan jefar wa da ƙwan haihuwar shugabar gobe ko zan samu sukuni ” Uncle Salem

Chapter 7 of 11