Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 11
da iyayena” na faɗa ina kafe ta da ido. Ta ce “ke ba fa komai ne ba,ina so dai ki yi wanka ki canza kaya ko kin ji sanyi” “Amma daga nan fa?” “Za mu wuce kamfani” ta bani amsa.Kafin mu shiga mota mu koma can gidanta,da isarmu kuwa wankan na shiga bayan na fito na shirya cikin ɗaya daga cikin abayar da muka siyo jiya.Ina tsaka da fesa turare ta shigo sanye cikin kayan atamfa har da luluɓa uban mayafi kamar ta ƙwarai,ina shirin yi mata tambayar ya na ga ta yi shiga ta kamala daga can falo na ji muryar wani gardi yana kiran sunanta cikin tsawa “Zulaihat?” murya na rawa ta amsa kafin ta kama hannuna ta ce “in ya tambaye ki wace ce ke sai ki ce ƴar uwata ce ke kun zo nan ne domin jinyar mahaifinki” ba ta bani damar cewa komai ba kuma ta ja ni muka fita can falo. Yadda duk ta nutsu cike da tsoro yasa ni ma na kama kaina tare da gaishe shi cike da ladabi,dakyar ya amsa kafin ya ce “wace ce ke?” Sai da na saci kallon Zuly kafin na ce “ƴar uwarta ce,jiya muka zo nan garin domin jinyar mahaifina da ke asibiti” “Ita kuma ta ce min yau ne kika zo” “Eh nan gidan ba,amma ai tun jiya muka zo ni da iyayena suna can asibiti” “Wace asibiti?” “Private asibitin nan da ke kusa da babbar kasuwa” na basa amsa,bai ƙara cewa komai ba sai ya je ya zauna kan kujera yayin da ita kuma Zuly ta je jikinta na ɗan rawa ta fara zuba masa abinci tana gamawa ta zo ta kama hannuna tare da jana muka koma can ɗakina.Bayan ta rufe ƙofa sai ta ja ajiyar zuciya,ni kuma na ce “wane ne kuma wannan?” Cikin ƙasa da murya ta ce “mijina ne,ki bari daga baya zan yi miki bayani” tana gama faɗar haka sai ta fice ta bar ni sake da baki ina mamakin kenan Zuly tana da aure amma ta rasa wanda za ta aura sai babban mutum kuma irin mai zafin kai. Bakin bed na zauna ina tunanin ni ma ai lokaci yayi da zan bai wa maza dama ,saboda can baya gani nake in ba aiki na samu ba to fa ba zan taɓa kula namiji ba. Tsawon lokaci ina wasiƙar jaki kafin Zuly ta shigo ,“ taso mu ci abinci” ta faɗa .Tashin na yi na mara mata baya,ita ce ta zuba mana sai da muka fara ci sannan ta soma bani labarinta. “Lubna kamar yadda kika sani ba duk abin da mutum yake so yake samu ba,to ni ma hakan ce ta faru da ni.Bayan mun kammala karatu na fara neman aiki ,duk inda na je babu nasara sai na samowa kaina mafita wato ita ce ta auren miji mai kuɗi shine fa na auri Alhaji ” tana kawowa nan ta yi shuru ban matsa mata da sai ta ƙara cewa wani abu ba lura da yadda take bani labarin a takure.Bayan mun gama cin abinci daga nan kuma kamfani muka wuce,kafin nan bisa hanya sai da ta ƙara gutsura min labarin nata. “Akwai wani group mai suna sugar Daddy ,a can muka haɗu da Alhaji ta hanyar wata ƙawata na samun link ɗin.Tun da na tura hotona na gabatar da kaina ya biyo ni pc ya ce na yi masa ban kuma ja aji ba muka fara soyayya kar ki so ki ga yadda yake yi min batal ɗin kuɗi.Ba a ɗauki lokaci ba kuma ya zo gidanmu suka yi magana da iyayena waɗanda kafin auren sai da suka tambaye ni ai dai ina sonsa ko ? Na kuwa ce eh.Amma a zahiri ba haka abin yake ba,kawai saboda in samu gidan hutu ne yasa na amince da aurensa.Muna yin aure hannunsa ya koma na jariri hahaha! Ya bar bani kuɗi sai dai fa duk abin buƙata yana zuba min su a store kuma bai damu ba don na ɗiba na yi kyauta da su,ana haka sai na fara haɗuwa da manyan mata .In an je biki su yi ta liƙen kuɗi,wata don ta ɓarar da 200k ba wani abu ba ne ,to abin sai ya fara damuna har na soma tunanin ko rabuwa zan yi da Alhaji .Da na kai wa waccan ƙawata da ta bani link kokena sai ta haɗa ni da oga” tana kawo wa nan da labarin ta yi parking duk muka fito,duk da a lokacin na so jin yadda ta kaya amma na yi shiru muka shiga ciki. Cike da girmamawa aka dinga gaishe ta,direct kuma ofis ɗin oga muka wuce.Yana ganinmu yayi saurin tasowa ya shayar da ni giyar mamaki don kuwa rungume Zuly yayi ƙyam a ƙirjinsa tare da feso wasu kalamai waɗanda suka sa na zauna ban shirya ba. “Ya haka Baby? Na ji an ce mijinki yau yayi saukar asubah,shine ba ki faɗa min ba.Me ya kawo haka ko yayi miki wani abu ne?” Ita kuwa ƙoƙarin fizge wa take,tana satar kallona da sauri na kawar da kai. Ina jin lokacin da oga ke ci gaba da cewa “faɗa min kun yi wani abu da shi ne?” “A'a ! Please ka sake ni mana ” ta faɗa. “Luby ki ɗan fita ina son yin magana da Oga” ko kallonsu ban ƙara yi ba na fita,direct kuma ofis ɗinta na shiga wanda ke kusan na oga.Kaina na ji yana sara min a fili nake tambayar kaina “wai da aurenta take kula wani? Da aurenta take zina? Innalillahi wa'inna ileyhi raji'un! Ya Rabb ka tsare ni daga sharrin zina Allah kar ka jarabce ni da ita,kar ka kuma nuna min ranar da zan yi ta Ya Rabb kafin ranar nan ta zo Allah ka aiko tirela ta markaɗe ni na huta” haka kawai na ji hankalina ya ƙi kwanciya da wannan aikin,sai nake jin kamar na je na shaida musu ban so. Bayan wajen minti talatin ina zaune sai ga Zuly ta shigo ,kallo ɗaya na yi mata na ɗauke kai. Ta zauna tare da soma magana ba tare da na tambaye ta ba,“sai haƙuri Luby,ni ma na fara gajiya sai dai ba a komawa baya.Kin ga a ranar da ƙawata ta haɗa ni da oga da farko iya aikin yi masa lissafi kawai ne nawa,amma sannu-sannu sai ya fara bijiro min da ainahin zuwan nawa.Cike da tako yayi nasarar kai ni kan shimfiɗarsa har sai bayan komai ya kammala ne na fahimci kuskurena,don da soyayya ya ɓullo min .Amma yana bani kuɗaɗe masu mugun yawa sai ya girgiza tunanina,sai kawai na biye masa kusan kullum in na zo aiki muna keɓewa yayin da shi kuma yake cika min jakata da ƴaƴan banki” “Ita kuma alaƙar tsafi?” na jefo mata tambayar. “Shi ne ya bani power ya kuma nuna min yadda ake yin komai” “To amma me yasa ba ki rabuwa da Alhaji ki auri oga ? Ai hakan ya fi nake gani tunda da dukkan alamu shi oga kina sonsa” Wani kallo ta yi min kafin ta ce “ki shirya za mu fita zuwa yawon ƙauyukan da za a soma aiki” “Aikin me fa?” “Na gina banɗakunan kan titi mana” ta bani amsa. Ko da muka fito tuni motar da za ta yi yawo da mu ta zo,haka muka shiga mu da wasu sauran ma'aikata.Yawo sosai muka yi muna duba wuraren da za a gina banɗakuna,wasu cikin kasuwa wasu kuma kan titi.Sai bayan sallar azahar muka dawo,Zuly ce ta yi wa oga bayanin komai kafin ta sauke ni asibiti. Ina shiga daidai nan Abba ya rufe idonsa ya soma bacci,bayan na gaishe da Ummah sai na zauna na tambaye ta jikinsa ta amsa ana ta samun ci gaba. Nan na wuni,har dare amma Abba bai tashi ba har likitocin sai da suka yi mamakin irin baccin nan da yake alhalin ba a yi masa allura ko magani mai sa haka ba.Saƙon Zuly na samu kan ina iya tafiya gidanmu ba sai na je can gidanta ba,da wannan na yi wa su Ummah sallama na je can gidan.A daren ne kuma na yi wani mafarki mai matuƙar firgitarwa,ga Abba nan yana kuka yana kiran sunana yayin da kuma wasu mutane masu baƙaƙen kaya sun ɗora shi kan garwashin wuta suna gasa shi tamkar wani tsire. A firgice na farka wanda yayi daidai da kiran Zuly,“ki fito ina ƙofar gidanku” shine abin da ta faɗa min ta kashe wayar. Cike da mamaki na duba lokaci,ƙarfe biyun dare ne.Amma haka na fita na same ta cikin mota,ina shiga ta fizge ta kuwa ta soma yin gudu kamar za ta tashi sama tambayar duniya kuma ta ƙi bani amsar abin da ke faruwa . Gidanta muka wuce,tana yin parking duk muka fito hankali tashe take jan hannuna zuwa ciki.Wannan dai ɗakin muka shiga wanda na yi laƙabi da ɗakin sirrinta,ko da muka shiga sai ta buɗe madubinta ta tsaga yatsanta jini ya soma zuba ta kamo nawa da niyyar tsaga shi kenan mijinta Alhaji ya shigo ɗakin yana salati tare da jefo mata tambaya “Zulaihat tsafi cikin gidana? Dama ke MATSAFIYA (Mrs SADAUKI) ce ban sani ba? Ai kuwa yau...” bai ƙarasa kai ƙarshen maganarsa ba Zuly ta jefa wuƙar hannunta tare da furta furucin tsafi nan take wuƙar ta sauka daidai tsakiyar ƙirjin Alhaji a nan take ya faɗi jini na yi masa malala...... My book is only 500 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 [02/04 12:10] MRS SADAUKI: *BAƘIN RUHI*🧌🐲 ```LoVe aNd HoRrOr story```👽 By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️} *SADAUKARWA :* Ga dukkan iyayenmu MATA da suka tsaya tsayin daka don bamu kariya a kan dukkan wani da ke son cutar da mu. *FCWA*☀️ ________________________ 07 Ban taɓa shiga tashin hankali irin na yau ba,kisan kai ne aka yi a gabana ga gawa kwance cikin jini.Tsabar ruɗewa da na yi yasa na soma zagayen ɗakin ina ihu,yayin da ita kuma Zuly ta soma tsafe gawar tana barbaɗa mata wata hodar tsafi kafin ƙyaftawar ido gawar ta ɓata ko kumfan jini babu,a wannan lokacin ne na ƙara ganin bala'in da na tsoma kaina a cikinsa.Zuly ta nufo ni da niyyar kama ni amma na yi tsalle na koma can gefe ,idonta ta juye tamkar wata zakanya kafin ta soma yi min magana cikin wata irin murya “Luby ki zo mu wuce ba mu da sauran lokaci,in kuma kika jinkirta duk abin da ya biyo baya babu ruwana” Ina kuka ina ƙari na ce “amma Zuly kisan kai fa kika yi,mutum ne fa kika kashe kuma mijinki” “Babu ruwanki da wannan matsalar ki zo mu wuce” ta yi furucin tare da yin tsalle ta zo ta cabko ni muka tashi cikin iska kafin mu ratsa ƙofar da ke cikin mirror. A wani ɗaki muka bayyana,da na duba da kyau sai na ga wancan dai ne na ƙasar waje.Duk yadda na so na bijiro da zancen kisan kan da ta yi ta hana,a gaggauce ta tirsasa ni na shirya cikin kayan arna kafin mu fito.Yanzu ma buɗe mana mota aka yi muka shiga ,muna tafe ina duban hanya sai na ga wata ce aka ɗauka ba waccan ba.Mun yi tafiya mai ɗan nisa kafin mu isa, wannan karon a tare muka shiga ɗakin taron mai ɗauke da ɗumbin jama'a daga ƙasashe daban-daban.Ciki kuwa har da oga shi ma ya haɗe cikin wasu baƙaƙen suit kamar sauran mazan,wuri muka samu muka zauna oga ya dubo inda muke zaune fuskarsa ta nuna alamun damuwa. Can kamar minti biyu wani zabaya ya fito sanye cikin jajayen kaya kansa ya ɗora wata hulla kamar ta sheɗan,gashin kansa da idonsa duk wasu iri ne kamar wani makaho haka ya ƙanƙance su yana ƙarewa kowa kallo ,da ya zo kaina sai ya tsayar da dubansa gare ni.Gabana ne yayi wani irin mugun faɗuwa ,so nake na kauce idona amma tamkar wacce aka yi wa dabaibaye na kasa. “Mansoor fatan ka yi wa ɗalibarka bayani?” shi ne abin da ya faɗa . Muryar oga na ɗan rawa ya ce “a'a tukuna dai Boss ” Bai ce komai ba sai ya zauna kan kujerar ya soma yin wasu maganganu da ban gane su ba saboda kogin tunani da na abka,ban farga ba sai da na ji Zuly ta zungure ni sai na dawo hayyacina nan kuma na ƙara jin wani zancen banza wanda kuwa hankalina ya kasa ɗauka. Oga ne ke bayani kamar haka “Luby a family muna da wata ƙa'ida,babu virgine a tsarin tafiyarmu in ma ta shigo to dole a yi amfani da ita don kawar da budurcinta.In irin wannan damar ta samu to Boss ne yake yin wannan aiki ,kamar yadda tsarin yake zai yi amfani da ke a gaban dukkan family bayan nan kuma sai ki karɓi zoben ƙarfin iko da kuma madubinki wanda zai sauƙaƙa miki yin balaguro zuwa ƙasashen duniya da kuma in an tsara meeting” Wata irin bazawarar dariya na yi,don abin jin shi na yi kamar wasar kwaikwayo sai na miƙe tsaye kamar mahaukaciya ina mai ci gaba da yin dariya kafin na ce “wato na basa budurcina? Akan wane dalili kenan? To ba zan yi ba,sai dai ku cire ni daga cikin family ɗin amma ba zan taɓa aikata zina ba” Da wani mugun sauri oga ya zagayo ya zo inda nake ya kama kafaɗuna ya ce “ Luby wannan dolenki ne! Kin ga ki ajiye hankalinki babu fa wata matsala sau ɗaya tak ne zai yi shi kenan ” Hawaye suka zubo min masu ɗumi,ji nake kamar na shaƙe wuyan oga har sai ya mutu na sake shi . “Na bata nan da sati ɗaya,ta je ta yi shawara don ina da ayyuka masu muhimmanci a gabana kowa zai iya tafiya” Boss ya faɗa tare da miƙewa ya koma hanyar da ya fito. Nan kowa duk ya watse,Zuly ta kama hannuna muka fito muka bar oga can.Har muka isa gida tana yi min nasiha haɗi da shawarwarin banza wanda in sun shiga kunnena sai su fita ta ɗayan kunnen,sam ban ji zan iya yin abin da suka ce ba. Na yi tunanin da zarar mun je za mu koma can Kamaru ne,amma sai na ji wata sabuwa wai zan sake yin wani zama da mutanen da na tallata musu hajarmu. Cikin bahon wanka na shiga na lumshe ido,tunanin iyayena da kuma abubuwan da suka faru suke ta min yawo a kwanya.Har sai da ruwan suka huce na zuba wasu sannan na yi wanka na fito,cikin kayan bacci na shirya sannan na kwanta sai dai fa na kasa yin baccin haka na yi ta yin juyi bisa gado.Can sai ga Zuly ta shigo hannunta riƙe da ƙaramin tray ,tashi na yi zaune ita ma ta zauna bakin gado tare da miƙo min kofi ɗaya na madara ita ma ta fara shan guda. “Wacce shawara kika yanke ?” ta jefo min tambayar. “Game da me fa?” ni ma na tambaye ta. Da ɗan mamaki ta dube ni kafin ta ce,“maganar Boss ɗin ce kika manta?” “Shi wane ne?” ban ida rufe bakina ba kofin da ke riƙe da hannuna ya tarwatse har sai da kwalba ta shige min hannu nan take jini ya soma zuba. Jikin Zuly ya ɗauki rawa,sai ta dubi madubin da ke a ɗakin kafin kuma ta taimaka min ta tsayar da jinin ta naɗe min shi da bandeji. Sosai na tsorata ban taɓa tunanin Boss nada power har haka ba,don babu tantama shi ne ya tarwatsa kofin.A tsorace nake kallon Zuly kafin na ce “don Allah ki mayar da ni gida” Muryar Boss ta fito ɓaro-ɓaro ta cika ɗakin “duk inda za ki je ba za ki taɓa boyewa ganina ba,na soma bibiyarki kenan” Da sauri na rungume Zuly ,sai aka ƙwanƙwasa ƙofa ita ce ta bada damar shigowa.Ƴar aiki ce,cikin Yaren turanci ta ce “oga na falo yana jiran ku ” tana gama faɗa ta fice. After dress na ɗauko na ɗora a sama kafin mu fita falon,Oga na zaune ya hakimce fuskar nan kicin-cikin kamar za ta tsage. Na sunne kai tare da samun wuri na ja na tsaya ganin irin mugun kallon da yake jefo min. “Zuly kin ga saboda ke ina shirin samun matsala da Boss ? Ta ya za ki kawo wacce kika san za ta kawo mana cikas? Faɗa min wace shawara kuka yanke yanzu?” “So take mu koma Kamaru,kuma ni ma na ga kamar hakan zai fi.In mun je can za ta fi samun damar yin tunani in tana ganin Abbanta ” Zuly ta faɗa ,ban san dalilin da yasa ta kawo Abbana a cikin wannan lamari ba. Oga ya ce “babu matsala za ku iya komawa,amma ki bari har zuwa gobe don yanzu haka an tsinci gawar mijinki ƴan sanda sun soma yin bincike.Kin ga in suka biyo ta kanki za su samu ba ki ma ƙasar,kuma in kin je ki nuna cewa labarin mutuwar ne ya maido da ke” “Kenan in haka ne sai dai mu bi jirgi ba ta madubi ba?” Zulyn ta faɗa sam babu wata damuwa a tattare da ita. Oga ya miƙe tsaye ya ce “eh hakan za a yi,na riga da na tsara komai” yana gama faɗa ya murza zobensa nan take ya ɓace ɓat. A ɗakin Zuly na kwana, washegari kuma tun da safe muka shirya tsaf zuwa aeroport,jirgi ne na musamman wanda bai da buƙatar sai mun nuna wasu takardu.Tamkar zan fita daga wuta haka nake ji,don na lashi takobin da zarar mun sauka Kamaru ko ƙasa da sama za su haɗe ba zan ƙara shiga sabgar Zuly ba na fita daga family kenan. Jirginmu na sauka ƴan sanda suka tarbe mu,nan na ga ikon Allah yadda Zuly ke kuka idonta duk sun yi ja sai wani rangaji take kamar za ta faɗi sai na taro ta .Daga nan police station muka wuce aka yi mata tambayoyi kafin ta nemi tana son ganin gawar mijinta. Duk yadda ta so mu je tare zillewa na yi na tafi can asibiti,a zaune na tarar da Ummah tana kuka.Tana ganina ta taso ta ce “ina kika shiga tun jiya muna nemanki a waya ba mu samu ba? Auta kuma ta ce min kuna kwance tsakar dare kika fita kika bar gidan,ina ne kika je?” “Wurin aiki mana Ummah,amma ai gani na zo.Ya jikin Abba?” Hawaye ta goge da mayafinta kafin ta ce “ɗazun nan aka kawo masa kwara-kwara wacce zai dinga yin tafiya kawai sai kwacaaa na ji ya faɗi.Likitoci sun ce aikin da aka yi masa a ƙafa ya lalace sannan ya samu shanyewar ɓarin jikiii ” ta fashe da wani kuka mai tsuma rai ,nan take jikina ya ɗau rawa.Ban ida rikicewa ba sai da na je na ga yadda Abba ya koma ,kukan ni ma na dinga taya Ummah ga likitoci sai rubuta sabbin magani suke. Cikin wuni guda suka rikita mana lissafi don kuwa an kai gaɓar da kuɗin hannun Ummah sun ida dama oga ne ya bata su. Wuraren sallar magarib kuma babban likitan ya fito da wani zance,“kuɗin gadonku sun ida ku je ku zuba wasu kafin nan da ƙarfe goma na dare ” Ummah ta dube ni ta ce “ Lubna ki je ki biya,ko har yanzu ba a baki ko dala ba sai aikin?” a cikin kalamanta sai nake jin kamar har da ɓacin rai,wato gani take na ɓoye kuɗin ne musamman suturar da ke jikina da ke tsadadiya babu wanda zai yarda kan cewa banda kuɗi. “Bari na je na dawo” shi ne kawai abin da na faɗa kafin na fito,tafiyar ƙasa na soma yi ina tafe ina tunani har na isa gidan Zuly .A falo na tarar da ita,muka gaisa sama-sama kafin na shiga ɗaki na ɗauko wayata iphone wacce zuciyata da ruhina suka yarda da na sayar da ita na yi wa Abbana magani. Har na kai bakin ƙofar fita na ji muryar Zuly na cewa“kina tunanin kuɗin sayen magani su ne za su warkar da mahaifinki? To in dai haka ne kin makaro ” Da sauri na juya ina kallonta,ta sakar min wani murmushi tana mai kankare akaifarta. “Me kike nufi a nan?” na samu dakyar na tambaye ta zuciyata na ɗan dokawa. Ta miƙe tare da zuwa dab da ni sannan ta ce “ina nufin ko duniya za ku yawace babu asibitin da za ta iya warkar da cutar mahaifinki,ke ce maganinsa in kina so ya warke dole ki bai wa Boss haɗin kai” tana gama faɗa ta bar ni nan tsaye.Na jima cikin shock kafin na fice,wajen wani mai sayar da wayoyi na je na karɓi kuɗi tare da bar masa wayata jingina. Ko da na isa asibiti na tarar ana yi wa Ummah tijara,haka dai na biya kuɗin gado da kuma na sauran maganin da ba a siya ba. Na yi tunanin na kawo ƙarshen matsalar duk da kuwa furucin Zuly bai bar kwanyata ba,ashe nan duk shimfiɗa ce aka yi min mamakin na gaba. Ƙanwata auta ita ce ta kawo mana abincin dare mun ɗan taɓa hira kafin ta koma gida ni kuma na yanke shawara zan zauna tare da Ummah. Dare ya tsala bayan duk kowa ya kwanta,na ji motsin buɗe ƙofa wanda yayi daidai da farkawata daga bacci sai dai tamkar gawa haka na sandare na kasa motsi.A gabana oga da Zuly suka shigo ɗakin suka yi tsaye kai ga Abba,can kuma Boss ya bayyana su biyu suka danne Abba yayin da shi kuma yayi masa wata allura wacce ta sa shi soma yin ihu da kururuwa yana kiran zai mutu su tausaya masa su bar cutar da shi,cikin ɗacin rai Boss ya ce “ƴarka ce duk ta ja maka masifa ba za mu taɓa barinka ƙalau ba sai ranar da ta amince da ƙudirina” Ina jin lokacin da Abba ya soma magana cikin azaba,“Lubnata ba za ta taɓa aikata abin da kuke so ba,na gwammaci na dawwama cikin wannan masifar kan na ga ta gurɓata rayuwart...” Zuly ce ta ɗauke Abbana da wani mari wanda hakan yasa sauran maganar ta maƙale masa,suna gamawa suka fice sai kuma a lokacin kawai jijiyoyin jikina suka ci gaba da yin aiki. Dakyar na iya tashi na je na yi tsaye gaban Abba ,idonsa ya zuba min yana kuka.Bakinsa ya juye ba zai iya yin magana ba,amma a haka ina fahimtar abin da yake son sanar da ni.Na faɗa jikinsa na saki wani irin kuka mai cin rai wanda yayi sanadiyar tashin Ummah ita ma sai ta soma yin kukan don ta yi tunanin mutuwa yayi. Sai da likitoci ne suka shigo suka tabbatar mata da ransa,allura bacci suka yi masa saboda wani irin abu da ya soma yi kamar mai cutar hauka. Jikin Ummah na je na ƙanƙame ta ina mai ci gaba da yin kuka yayin da ita kuma ta soma rarrashina tare da kwantar min da hankali Abba zai samu lafiya. Da gari yayi haske suka sake shigowa suka duba Abba,suka ce jikinsa ya ƙara mutuwa da buƙatar a yi masa gashin ƙashi .Haka suka tura gadonsa aka shiga da shi wani ɗaki,ni da Ummah iya bakin ƙofa kawai muka tsaya.Daga nan muna jin yadda Abba ke ƙwallowa yana ihu da ransa. Sosai kururuwarsa ke taɓa min zuciya ,sai nake ganin duk laifina ne.A haka dai na fita don zuwa mu yi cinikin wayata da na baro jiya,nan ɗin ma wata masifar na tarar shagon wayoyi ya ƙone ƙurmus sai gawawarkin wayoyin ga su nan jere ringis duk sun ƙone.Yana ganina ya ƙara ƙaimin kuka,ni ce na basa haƙuri don da ace ya san ta dalilina ne yayi asarar nan ƙila kotu ce za ta raba mu. Idona sun rufe,babu komai cikinsu sai ɓacin rai.Gidan Zuly na nufa don so nake a yita ta ƙare,ko da na isa na tarar da ita a zaune tana karɓar ta'aziyar mijinta ga mutane duk sun cika falon.Ɗakin da aka ware domin ni na shiga bayan na yi mata alama da ido ina son ganinta,sai dai ina shiga na tarar da Boss a hakimce kan gado yana murmushi... My book is only 500 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 [04/04 11:00] MRS SADAUKI: *BAƘIN RUHI*🧌🐲 ```LoVe aNd HoRrOr story```👽 By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️} *SADAUKARWA :* Ga dukkan iyayenmu MATA da suka tsaya tsayin daka don bamu kariya a kan dukkan wani da ke son cutar da mu. *FCWA*☀️ ________________________ 08 A lokacin da na ga Boss kwance kan bed sam babu sutura a jikinsa,wani irin bugawa zuciyata ta yi sai dai na kasa ɗaga ƙafata ballantana na koma baya na fita daga ɗakin. Cike da shaƙiyanci yake cewa “ki gama gujegujenki ni ɗin nan ne zan raba ki da budurcinki,in kuma kin fi ƙaunarsa kan mahaifinki ai shi kenan” yana gama faɗar haka ya ɓata

Chapter 4 of 11