Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
10 / 11
fitsarin ya wuce,sai a lokacin na ji kunya tare da gyaɗa masa kai alamun na yarda. Murmushi ya sakar min kafin ya fita,sai a lokacin na cire rigar baccin da hijabi.Wankan tsarkin na yi kamar yadda ya umarce ni kuma sai na ga ya kyautatu ɗin na yi shi.Bayan na fito sai na ga yana bai wa Inna A'i magani da murfin roba,ya fi kala uku maganin kafin kuma ya miƙe ya fita. ★Uncle Salem Jiya a lokacin da Inna A'i ta ɗauki wayar Nafisa ,a cikin muryarta kawai ya ji hucin wani ruhi da ke jikinta.Bai kuma yi wani dogon tunani ba ya fahimci tabbas da matsala,can gida ya koma ya tattaro duk maganin da ya san zai buƙata kafin ya ɗauki hanyar garin Ƙwargwam.Abu guda ya sani shine ba zai iya rabo su daga ƙauyen can ba tun da har Innarsa Delu ta yarda ta bar su suka wuce alhalin kuma ta fitowa Nafisa a siffar ruhi. Ko da ya zo kuma bai ga Inna A'i bai yi mamaki ba,ita kanta Naf ɗin ƙwayar idonta kawai ya kalla ya hango yadda guba ke son game dukkan jikinta.Abu biyu ne yasa ya bata maganin,na farko don ya ji wane ne ya ciyar da Inna A'i don samo mafita,na biyu kuma don karye abin da aka baiwa Nafisar a cikin shayi ta sha. A jiya ba don yana son ceto Inna A'i ba babu abin da zai hana shi ya mayar da Nafisa cikakkiyar mace,sosai moment ɗin ya ja shi zuwa ƙarshen shauƙi.Ba tare kuma da ya fita ba daga nan inda yake kwance da taimakon zoben hannunta ya lalabo Inna A'i a can wani ƙasurgumin daji tana yi ta tafiya ita ɗaya kamar mahaukaciya saboda tun bayan fitarta zuwa mayar da kwanukan gidan headmaster a nan bakin ƙofar ɗakinsu ta ji kamar ta zurma cikin rame kafin kuma ta tsinci kanta wani wuri.Dukkan detail ɗin nan Uncle Salem ya gansa daki-daki,wanda kuma ko ita Inna A'i aka tambaye ta ba za ta kawo shi ba. Yadda ta ji muryarsa kamar daga sama shi ya sa ta juyo baya ta fara dawowa gida kuma,ko lokacin da ta buga ƙofa daga cikin ramen ta fito sai dai Uncle ya toshe duk wata ƙofa da zai sa A'in ta fahimci wani abu. Yanzu kuma da ya fito, tsugunawa yayi ya ɗiga wasu ruwa cikin ramen kafin ya rufe kwalbarsa ya saka a aljihu. Masjid ɗin makarantar ya nufa wanda ake ta kiran sallah,yana isa ya shiga sawun gaba bayan yayi nafiloli sai ya zauna har lokacin sallar yayi .Tuni kuma masallacin ya cika aka tayar bayan an gama ne Uncle Salem ya juyo yana kallon headmaster wanda ya zauna kafaɗa da kafaɗa da shi.Ya saki wani murmushi kafin ya ci gaba da yin Azkhar ɗinsa,har sai da ya gama kafin ya basa hannu ya ce “ Assalamu alaikum ” Headmaster cikin mazgewa ya miƙawa Uncle hannu suka yi musabaha wacce yayi da na sanin yin ta,don kuwa akwai kumfan magani a hannunsa na karye sihiri. “Wa'aleykum Salam ! Fatan an sauka lafiya?” ya amsa tare da saurin janye hannunsa. Uncle Salem ya ce “ lafiya lau alhamdullah ! Na zo duba wurin da matata ne za ta yi aiki ita da Kakarta sai kuma na ga wuri yayi kyau” Cike da takaici headmaster ke kallon Uncle ,don kuwa tun zuwansa jiya akan idonsa na ɓoye ya sauka.Sannan sarai ya san da shi ne ya warware zare da abawar da ya ƙullawa Inna A'i,amma saboda ya iya munafurci shine zai ce masa wuri yayi kyau. Cike da iya tako shi ma headmaster ya ce “ ai kuwa dai school Ƙwargwam na kula da malamanta har ma da ɗalibai” Uncle wani murmushin ya sake yi kafin ya ce “ ni ne shaida,amma me yasa kuka bata ɗaki mai lamba uku bayan ita sabuwar zuwa ce?” “ Ɗakin nada matsala ne?” “A'a kawai na tambaya ne” “In ba ta sonsa ai sai a canza mata” “ A'a na faɗa ma wuri ne mai kyau,kuma lamba ukun ai ita ce daidai da ita surukar Inna Delu guda” Uncle ya faɗi haka ne ya na saka idonsa cikin na headmaster don yi masa gargaɗi kan cewa kar ya sake cutar masa mata in kuma ya ƙara yin kuskuren haka shi da shi shege ka fasa.Da sauri kuma ya miƙe ya barsa nan. ★ Bayan na gama sallah haka na tsure Inna A'i da tambayoyi sai ta faɗa min inda ta je amma sai kwana-kwana take yi min daga ƙarshe ma ta shige kitchen tana cewa “bari na haɗa mana breakfast ” Na ce “ yau fa Litinin ko kin manta azumi muke ni da Uncle ” “ A'a yau ba za ki yi ba,ki bari har Alhamis ” Uncle ya faɗa wanda ke shigowa.Na dube shi da mamaki jin yau shine ke cewa na ajiye azumi,“ Uncle ina yi fa” na faɗa kamar zan yi kuka ina kallonsa.Ya ɗauke kafin ya ce “a'a akwai maganin da za ki sha yanzu kafin ki ci komai” sai yayi gaba ya ƙarasa gaban jakarsa ya fiddo wata kwalbar zuma. Ido tab hawaye nake dubansa,ya ɗago ya kalle ni kafin ya ce “za ki zo ki sha ko sai na zo nan na ɗauko ki na matse miki baki tare da ɗura miki shi?” Jin ya fito a Uncle Salem ɗinsa mai tsanani yasa na ƙarasa gabansa na yi zaune tare da tanƙwashe ƙafafuna.Da wata ƴar ƙaramar cokali ya soma bani zumar har sai da na sha bakwai da ita kafin kuma ya soma bani wasu sauran maganin,ɗaya kuma ya ce “ wannan kuma sai in kin ci abinci za ki sha” sai ya miƙo min na karɓa ina gunguni. Yayi murmushi mai ɗan sauti kafin ya ce “ Naf sai yaushe za ki girma?” Kamar suɓutar baki na ce “ ranar da ka yi min aure” Shuru yayi bai ce komai ba,ni ma sai na rashin kunyata.Na ɗaga kai da niyyar satar kallonsa sai na ga ashe ni ɗin ce yayi ƙuri kamar mai kallon tv.Zan yi ƙasa da kai yayi saurin tallabo haɓata ya ce “ da gaske kin shirya zaman auren?” Na lumshe ido ina dariya,ya ce “ faɗa min na ji saboda in na koma gida na yi wa Daddynki magana a soma shirin biki” Na ɗan cinno baki gaba na ce “ni da ko saurayi banda” kamar daga sama na ji bakinsa kan laɓana, wannan karon dai kam cikin hankalina nake.Cike da razani na buɗe ido kafin da sauri na tashi daga gabansa jikina na ɗan yin rawa,duk da ba yau ne ya saba yi min kiss ba amma a goshi ne ko a kumatu ya saba min sannan an ɗauki lokaci mai tsayi rabon da yayi. “Nafisa?” na ji muryar Inna A'i,da sauri na nufi kitchen ɗin ina jin daɗin kiran nawa da ta yi.Ina shiga ta yi min wani kallo sai na ji na tsargu na yi tunanin ma ta gani ,a ɗan daburce na ce “ ni ma ban san me yasa Uncle yayi haka ba,shi ba giya yake sha ba ballantana na ce bai cikin hayyacinsa ” “Ungo ni ki je ki sha ya fi wannan surutun da kike yi min marar kan gado,duk duniyar nan akwai mai sonki sama da shi Salem ɗin da har za ki yi tunanin zai yi abin da zai cutar da ke” Inna A'i ta faɗa . Na karɓi kofin kunun tare da komawa can gefe na soma sha sam na ƙi yarda na koma can,ita ma ba ta matsa min amma ina shanyewa sai na fito don tuni gari yayi haske sannan lokacin da za mu je bakin aji ƙarfe bakwai ne. Ina fitowa na gansa a zaune ido rufe yana wani jan numfashi tare da ɗan game fuska haɗi da yamutsa ta.Toilet na shiga na yi wanka,da na fito sai na tarar ba ya nan.A gaggauce na shirya tsaf,na zuba takardun da zan yi amfani da su da abin rubutu. Inna A'i ta fito tana min wani kallo kafin ta ɗauke kai,“ki je yana mota yana jiranki ku yi sallama” Jiki a sanyaye na fita ganin irin yadda ita Innarmu ta canza min fuska wacce nake ɗauka uwa ta biyu.Hijabi na saka kafin na fita,gidan gaba na buɗe na zaune na sunne kai tare da yin shuru ina wasa da zoben hannuna.Kujerar da nake zaune a kai ya ɗan buɗe ta ja baya,da sauri na kalle shi yadda na ga idonsa sun kaɗa sun yi ja yayi bala'in bani tsoro.Murya na ɗan rawa don duk a tunanina kuka ne yayi,na ce “Uncl...” sauran maganar ce ta maƙale jin bakinsa kan nawa abin ma bai tsaya nan ba ya soma shafar hijabina ta sama .Hawaye ne suka soma zubo min ,ba yau ne farkon jin cewa uba yayi mu'amala da ƴarsa ba na sha jin ire-iren labarun nan a kafar BBC amma ban taɓa tunanin akwai ranar da abin zai zo kaina ba don ban taɓa banbance Daddy da Uncle ba.Duk abin da yake yi ko motsi ban yi ba da yatsana ballantana na yi yunƙurin hana shi ,hawaye kawai nake yi don babu bakin kuka saboda Uncle ya mayar da shi sweet ɗinsa.Sama da minti goma kafin ya janye daga gare ni amma ina jin hucin saukar numfashinsa kusan fuskata da na rumtse idona.Shashekar kukansa da na ji ta yi kuma bala'in tayar min da hankali fiye da abin da ya gama yi min,na buɗe idona ina kallonsa shi ma hawayen yake fitarwa kafin ya kama hannuna dukkan biyun ya ce “ don me Naf? Me yasa kike horar da ni da yawa? Me yasa ba ki ganin zazzafar ƙaunar da nake yi miki? I love Naf! Ina sonki,ina buƙatar ki a kusa da ni haƙurina ya ƙare” Tamkar wacce aka bugawa guduma a kai haka na ji ,kalamansa kuwa kusan tarwatsa min kwanya suka yi sam kasa fahimtar abin da yake nusar da ni na yi.“Wuce ki tafi ki kula min da kanki”ko ida rufe bakinsa bai yi ba na ɓalle murfin motar na fito..... My book is only 500 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 [06/04 15:24] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️ ```LoVe aNd HoRrOr story```👽 By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️} *SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta. *FCWA*☀️ ________________________ 09 Ƙafafuwana har harɗewa suke saboda kalaman da Uncle Salem ya fesar min,ruhina kuwa yayi wani irin sanyi saboda zazzafan romance ɗin da yayi min wanda ya toni duk wani sirrin zuciyarsa da muradinta na shekara da shekaru.Ta ya zan so Uncle soyayya ta aure? Ta ina ma zan fara wannan cakwakiyar da sam ƙanƙanuwar kwanyata ba za ta iya ɗaukar wannan rikicin ba.Ina shiga ɗaki na tarar da Inna A'i tana jera min takardun da ni ce na fidda su a jaka,ta ɗago ta dube ni kafin kuma ta kawar da kai.So nake na shaida mata kalamai da kuma abin da Uncle yayi min ko zan samu sukuni amma sam ba ta bani fuska ba.Wannan yasa kai tsaye na shige toilet,ga mamakina duk jikina ya ɓace saboda abubuwan da yayi min har sai da na canza pant na kuma wanke fuskata.Ina tsaka da maida kwalliyar fuskata na ji ƙarar tashin motarsa,na ja ajiyar zuciya tare da motsa laɓana kaɗan na ce “Allah ya sauke ka lafiya!” sai na ɗauki wani sabon hijabi saboda wancan duk Uncle ya cukuikuye shi sannan hawayena sun jiƙa shi ta gaba. “Na tafi sai na dawo”na faɗa dakyar,ta ce “a dawo lafiya” jakata na ɗauka tare da fita daga cikin gidan na nufi can ɓangaren makarantar. Ina zuwa gaban ajin da zan koya na tarar tuni ɗaiɗaikun ɗalibai sun zo,haka suka gaishe ni irin yadda ake yi.Wani sanyi ya ratsa ni duk sai na ji ƙuncin ya sauka daga zuciyata har da murmushi,ina nan tsaye kamar sauran malamai bakin aji aka soma kawo yaran sai a lokacin na dinga cewa su shiga aji su zauna.Ina nan tsaye wani ya kawo ƴarsa sai kuka take,da sauri na kama hannunta ina mai rage tsayi na ce “yi shuru mana babyna ko ba ki so na baki alawa?” Cikin murya ƙurciya ta ce “ina so” Na ce “yawwa to yi shuru sai na baki ,me sunanki?” “Firdausi”ta bani amsa,na gyara mata zaman ɗan guntun hijabinta kafin in saɓe ta kamar wata ƴata na ce “to yi wa Daddy bye bye sai mu je aji na nuna miki inda za ki zauna” da murmushinta kuwa ta yi masa alama da hannu,ya ce “na gode Madam ” Na ce “bai komai ai aikinmu ne” sai kuma na shiga aji na zaunar da ita a kujerar gaba ta kusa da kujerar da aka ware domin zamana. Bayan nan na ƙara komawa can bakin ƙofa,ban shigo ba har sai da ajin ya cika zuwa lokacin tuni ƙarfe takwas ta buga.Ina shiga na yi zaune ina kallonsu ɗaya bayan ɗaya ina jin wani sanyi na ratsa min zuciya,kafin kuma na tashi na bi ɗaya bayan ɗaya ina tambayar kowa sunansa.Dukkansu yara ne da ba za su wuce shekara bakwai ba,wasu ma ba su kai ba,ina cikin zagayen ajin sai ga headmaster ya shigo shi da mataimakinsa. Takarda mai sunan ɗalibai ya miƙo min da kuma alli wanda zan yi rubutu da allo,liste ɗin na ɗauke da ɗalibi ɗari cicif.Bayan fitarsu ma sai da na sake kiran sunayen yaran kafin na je na soma yin rubuta a jikin baƙin allon wanda yake goge fesss,kwanan wata na rubutu da kuma ABCD sai na soma koya musu suna yi duk bayan na faɗa.Haka muka ta yi har lokacin shan iska yayi,sai dai kamar yadda meeting ɗin jiya ya sanar da mu dokokin makarantar hakan yasa ban fidda su waje ba. Grand Maa ce ta shigo ita da wata budurwa ɗauke da wani basket,cike da girmamawa na gaishe ta yayin da kuma budurwar nan ta soma raba wa yara abincin da za su ci.Bayan ta gama a gaban idona Grand Maa ta miƙawa wani yaro biscuit kafin su fice. Bayan an gama cin abinci duk suka je suka jefar da abin take away ɗin a shara nan na ci gaba da yin cours ina aika kowane ɗalibi ya zo ya rubuta harafi ɗaya daga cikin ABCD ɗin da na yi musu.Ƙarfe sha biyu na rana cif aka kaɗa ƙarar rawar tashi ,nan aka zo fara ɗaukar yara ba ni na baro ajin ba sai da kowa ya watse . A gajiye na shiga gidan,Inna A'i ta yi min Barka da zuwa na amsa ina mai rage kaya na shiga toilet.Bayan na yi wanka ta gabatar min da abinci,na saka plate ɗin gaba tare da ɗaukar waya na kira Ammy bayan mun gaisa cike da alfahari nake bata labarin yadda ranar farko ta kasance ,sai murmushi take kafin mu yi sallama ina gama cin abinci na ɓingire bacci wanda tamkar jirana ake aka ƙara yi min maimaicin duk abin da suka faru a yau ɗin tun daga lokacin da na je na yi tsaye gaban ajina har zuwa lokacin shan iska na yara.Yaron nan da Grand Maa ta baiwa biscuit na ga yana ta kuka yana kallona yana kiran “madam? Madam cikina ciwo! Madam mutuwa zan yi ,wayyo cikina” amma sam wai na kasa tashi daga kujerar da nake zaune,a gaban idona jini ya soma yi masa zuba ta ƙofofin hanci kafin kuma ya faɗi babu rai bayan yayi wata irin ƙara wacce daga nan na tashi daga baccin. Na yi miƙa tare da duba agogo sai na ga tuni lokacin sallah yayi,kawai na miƙe na je na ɗauro alwala na gabatar da sallar.Sam ban wani bai wa mafarkin da na yi muhimmanci ba sai ma takarda da na ɗauka na soma rubuta abubuwan da zan koyar da su gobe,bayan nan kuma sai muka hau yin hira da Inna A'i lokaci lokaci kuma ina chating abina. Ana kiran sallar magrib na tura wa Uncle saƙo kamar haka “barka da shan ruwa!” Sai ya maido min da amsa da “ azumin da kika yi sanadin karewarsa?” “Kamar ya?” “Eh mana Naf ɗanɗanon yawunki ma kaɗai ya isa ya karya min azumi,uwa uba kuma tattausan ƙirjinki” da ya turo min saƙon nan na karanta shi ya fi sau goma,ina ta juya kalaman cikin tunanina ina jin tabbas Uncle nada buƙatar ganin likita don kuwa na sha jin ana cewa in mutum ya daɗe bai yi aure ba to hankalinsa na yin rauni .Da wannan na yi masa uzuri na ce kawai bai da lafiya ne kuma na yi alƙawarin zan sanar da Daddy a sama masa magani. ★Uncle Salem Ikon Allah ne kawai ya kai shi gida lafiya,duk yadda azumin nasa ya zama gurgu hakan bai sa shi ya ajiye shi ba.Wanka kawai yayi ya ci gaba da yin abinsa har aka kira magrib ya ajiye shi,ya dawo daga sallah kenan ya tarar da saƙon Nafisa .Cikin son nuna mata fa eh haƙurin nasa ya ƙare yasa duk ya cire nauyi ya soma yi mata magana cikin wannan salon.Yayi jiran amsarta amma shuru,kawai sai ya kira Daddy ya sanar da shi ya kamata a fara shirin yin bikinsu da Nafisa amma sai Daddy ya ce ya je can gida su yi maganar ido da ido tun da tuni ya sanar da shi bai samu damar zuwa dajin ba. Sai bayan sallar isha'i ya tafi can,a babban falo suka zauna Ammy ta kawo musu gasashen naman kaza da kuma shayi.Suna ci suna tuna baya, Uncle ne ya soma da cewa “ Abdul Hameed ka tuna lokacin da muna yara kai ne ke son gashen nama irin haka? ” Daddy yayi murmushi ya ce “a lokacin ai tantabaru ne muke gasawa,sannan muna samari ne ba yara ba” Uncle Salem yayi murmushi ya ce “ai kuwa dai ” “Kamar sati nawa kake ganin ya kamata a sa ranar bikin?” “Zuwa wata uku haka, lokacin an yi musu hutun makaranta a ranar da ta dawo sai a saka ta lalle” Uncle ya faɗa yana hasko tuni ga lokacin nan ya zo. “To babu damuwa ,amma ka samu ka sanar da Nafisar komai?” Daddy ya tambaya. “A'a tukuna dai amma ...” sai kuma ya ji nauyin abin zai ce kawai sai yayi shuru,shi ma Daddyn bai damu ba sai ma kiran Ammy da yayi ya sanar mata ,sosai ta nuna farin cikinta kafin ta fita.Bayan sun gama tattaunawa Uncle ya fito ya nufi flat ɗinsa,an gyara komai an share an goge.Wanka yayi ya shirya cikin bacci sannan ya soma yin wuridin da ya saba a kullum kafin kuma ya ɗauki wayarsa ya soma kallon hotunan Nafisa wanda a iya kallonsu kawai hankalinsa sai tashi yake yana jin buƙatar kasancewa da ita. ★ ƘWARGWAM Yau ma ban ci abinci da dare ba kawai cake na ci da chocolat,sai na saka wasu a jakata wanda zan baiwa Firdausi kamar yadda na yi alƙawari.Ina yin kwance na ce “Innarmu don Allah ki yi min gatana irin ta dogon ƙarni mai abin tsoro” “A'a Allah ya tsare ni Nafisa ,kin ga bacci ma zan yi don gobe ina son yi mana dambu tun da safe” ta faɗa tare da yin kwanciyarta gefe da ni.Na turo baki tare da lumshe ido,hoton abubuwan da Uncle yayi min duk suka dawo min.Sai wani abu nake ji yana bijiro min na shauƙi amma ban ma san taƙamaimai mene nake buƙata ba,amma sosai nake jin daɗin tunanin don abin da nake ji yana bani shauƙi sosai.Sai laɓana nake motsawa kamar wacce ke son Uncle ɗin ya ƙara shan su,a haka bacci ya ɗauke ni mai haɗe da mafarkinsa muna having sex.Yadda duk jikina ya amsa kamar a gaske yasa na buɗe idona dakyar da suka yi min nauyi,na duba lokaci a wayata sai na ga ƙarfe uku da minti uku na yunƙura na tashi zaune daidai nan hasken ɗakinmu ya ɗauke don dama ban iya bacci cikin duhu.Fitilar wayata na kunna sai dai tamkar wata wutar kyandir haka ta soma yin rawa kafin kuma ta ɗauke ɗif.Ban wani damu ba na sake ɗaukar wayar don sake kunnawa wannan karon cak screen ɗin ya ɗauka kafin kuma ta mutu da kanta. Daga bakin ƙofa na hango wata mace mai fararen kaya a tsaye gashin kanta na tashi cikin iska. “Wace ce?” na tambaya. “Deborat” ta bani amsa kai tsaye,kafin kuma ƙyaftawar ido tsundum na ganta kusa da ni a zaune muna kallon juna. Ido sune ƙofar hango ruhi, wannan yasa nake kallon ruhinta tun daga wajensa har cikinsa.“Ke ce kike yi min gatana kullum” na furta bayan na gama lalubo dukkan asalinta.Ba ta bani amsa ba sai jawo ni da ta yi ta kwantar ni kan cinyarta ta soma shafar sumar kaina,na lumshe ido don kuwa shafar irin dai ta matar da nake ji ce tana yi min haka duk dare.Sai dai wannan karon shafar ta babanta don tsintar kaina na yi a wani wurin, dube-dube na soma yi har na ci karo da allon sanarwa inda aka rubuta “DARASIN SANIN RUHANIYA” ina shiga ciki abun mamaki duk sai na tarar da kaf malaman nan da muka yi meeting da su,ga kuma su headmaster da principal su ma duk suna zaune yayin da Grand Maa ke koyar da karatu.Kamar wancan lokacin haka na zauna kusan Adama,na mayar da dukkan hankalina ga Grand Maa inda take cewa “kamar yadda vice headmaster ya faɗa muku lokacin meeting wannan school Ƙwargwam ta kasu kashi uku primary,da Sakandari sai kuma kuma Ajin Ƙwargwam wanda iya malamai ne kawai muke koyarwa” tana rufe bakinta na jefa mata tambaya,“Grand Maa me Ƙwargwam ke nufi?” “Matsafa!” ta bani amsa kai tsaye,sai na yi shuru ina tunanin zuci na ce ‘Ƙwargwam school na nufin MAKARANTAR MATSAFA? to amma su wane ne matsafan?’ Tamkar Grand Maa ta shiga zuciyata kuwa sai ta bada amsa ta hanyar cewa “darasinmu na farko shine chapter ruhi da gangar jiki,ta wannan hanyar ce ake gane matsafi” tana gama faɗar haka sai ta yi wani abu da hannunta nan take sai ga wani table ya bayyana a gabanmu,sannan a samansa wani yaro ne kwance babu kaya jikinsa da na dubi yaron sai na ga ba kowa ne ba face ɗalibina wanda ta baiwa biscuit a ɗazu ..... My book is only 500 vi 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 [06/04 15:24] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️ ```LoVe aNd HoRrOr story```👽 By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️} *SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta. *FCWA*☀️ ________________________ Last free page 10 Ganin Grand Maa ta ɗauki wuƙa za ta tsaga cikin yaron na yi saurin rumtse idona,ina jin sautin kururuwarsa yadda yake kuka yana cewa “madam ki cece ni kar ki bari su cutar da ni ” na buɗe idona da suka yi jawurrr na sake zuba su kan Grand Maa wacce ke zuba jinin yaron nan a kofi ta hanyar saka ludayi tana wani kwaso shi. Bayan ta gama sai ta kai kofin bakinta ta sha sannan ta miƙawa principal shi kuma da ya sha ya bai wa headmaster daga nan sai vice principal da kuma vice headmaster.Grand Maa ta ƙara karɓar kofin ta ce “lamba ɗaya sha ka bai wa lamba biyu,haka za ku dinga yi har kowa ya sha” wanda aka kira da lamba ɗaya na duba, kyakkyawan saurayi ne irin sosai ɗin nan kuma sai na ga yana kama da headmaster da dukkan alamu ɗansa ne,bayan ya sha sai ya miƙawa lamba na biyu shi kuma ya miƙo min na karɓi kofin ina kallon yadda jinin ɗalibina yake kwance a ciki mugayen matsafan nan sun mayar da shi lemun sha .Na kai kofin kusan bakina na yi kamar na sha kafin na miƙawa Adama wacce ita kuma ita ce lamba huɗu,so nake na ce mata kar ta sha amma idon Grand Maa ƙurrr suke kanmu ina ji ina gani Adama ta sha jinin kafin ta ba na kusa da ita a haka har kowa ya sha aka mayar da kofin. Daga nan sai Grand Maa ta yi wani siddabarun sai ga yaron da aka feɗe cikinsa ya tashi zaune daram da buɗaɗen ciki idonsa na shatatar da hawayen jini yana kallon tsakiyar idona har yanzu kuma bai gushe da neman taimakona ba sai dai sam ban san ya za a yi na taimake shi ɗin ba. Wasu kwalabe ta jera saman table ɗin,ta yi wani alama da hannu a nan take duk suka buɗe kansu.Bakinta na furta ɗalasiman tsafi ta dinga umartar ruwan da ke cikin kowacce kwalba da su je su shiga buɗaɗen cikin yaron,nan ya soma yin wata irin zabura kamar an jona shi da lantarki abin da na kasa jura kenan na ce “ōvovār̃ī” hakan yana nufin komai ya tsaya wato stop cak duk komai ya tsaya kuwa

Chapter 10 of 11