ya baiwa bindinsa bugun fuskata nan take na yi luuu zan faɗi da sauri ya juyo tare da taro ni sai dai muna haɗa ido da macijin igiyar saita numfashina ta katse ban ƙara sanin abin da ke faruwa ba sai da na ji muryar Hajiya a kaina tana cewa “ka ƙi faɗin abin da ya same ta,sannan ma wai me ya kawo ta ɗakinka? Maheer me ka yi wa ƴar mutane?”
Wani irin sarawa kaina yayi jin wani batu wai ɗakin Maheer ,ban shirya ba na buɗe idona tarau ai kuwa a ɗakin nasa nake kwance kan bed ɗinsa abin da ya fi ɗaga min hankali bai fi yadda na ji duk ƙamshin jikinsa ya dabaibaye ni ba.
Muna haɗa ido da Hajiya ta yi saurin matsowa “Haule me kike yi ɗakin Alhaji?”
Shiru na yi don kuwa sam na kasa tuna komai da ya faru ciki kuwa har da zuwan Husseina,abin da na sani dai shi ne ina kwance a ɗakinmu Lubna ta gama bamu labari.
Maheer ɗin na kalla wanda shi ma ni yake kallo da idonsa da suka kaɗa suka yi ja kamar tsohon maye.
Hajiya ta mangare ni cike da masifa ta ce “don ubanki ba za ki faɗa min abin da kika zo yi ɗakinsa ba?”
Shaaa hawaye suka fara yi min zuba,don sai yanzu ma ne nake ganin illar wanzuwata a nan uwa uba kuma ni kaina ban san ta ya aka yi na tsinci kaina a nan ɗin ba.
A karo na biyu na juya na dubi Maheer,Hajiya ta buɗe baki da niyyar yin wata masifar iya sunana kawai ta furta Maheer yayi wata irin busa mai ratsa dodon kunne sai ta yi shiru tana mai cewa “In Haule ta gama gyara maka ɗakin ta je ta shirya don Allah kafin su Lubna su gama saka kaya a mota” sai kuma ta fice.
Ya juyar da kai gefe ya ce “ki tashi ki koma ɓangarenku”
“Amma Alhaji me ya kawo ni nan?” na yi tambayar wasu sabbin hawaye na ƙara zubo min.
“Dalla Malama saukar min daga gado,ban sani ba ki je ki tambayi fatalwar da ta kawo miki ziyara” ya faɗa a hassale.
“Fatalwa kuma?” na yi tambayar,ya zo da ƙarfi ya wani fizgo ni na faɗo daga gadon amma sai na yi saurin miƙewa ina jin tsanarsa na ƙara ninkuwa a raina.Idona har wani rufewa suke na nufi ƙofar fita,da na ratsa falonsa ne idona ya sauka da duwatsun awarwarona nan ma mamaki na yi,na duƙa zan kwashe su amma tamkar yadda iska ke ɗaga leda haka duk suka tashi sama suka yi bayana,sai na juya nan na ga ashe shi ne yayi amfani da siddabarunsa ya janye su.
Hannuna na duba na ga yayi ja alamun an yi wa wurin mugun riƙo,ban tanka shi ba na fita.Ina fara taka step na ga Lubna a tsaye tana kallon benen wanda yake ɓangaren Maheer ne,a cikin idonta nake hango wasu abubuwa da suka haɗa da zargi da kuma mugun kishi amma ban kula ta ba na wuce part ɗinmu.
Sai da zan shiga toilet ne na lura doguwar rigar baccinsa a jikina,na kwance ɗaurin na jefar da rigar amma abin mamaki sai ta ƙi taɓo ƙasa.
Ban san lokacin da na furta “matsafi kawai” sai kuma na ɗauki rigar na ajiye ta cikin jakar kayana.Bayan na shiga toilet na cire kayan jikina,ina wanka amma ƙamshinsa ne ke tashi.Bayan na gama wanka na zo na gabatar da sallar asubah wacce ta wuce ni don tuni ƙarfe bakwai ta buga.
A gaggauce na kimtsa cikin kaya masu kyau sannan na ɗauki rigar da nake ɗorawa a sama mai sunan Hajiya da kuma restaurant ɗinta.
Ko da na fito tuni an jera komai a mota,cike da ladabi na gaishe da Hajiya .Yadda na ga Lubna na kauce min yasa ban takura ta ba akan sai mun yi magana,a yau tare da Aliya za mu je a nisa umarnin Hajiya hakan yasa muka shiga mota muka wuce can.
Bayan an gama jera komai a wurinsa sai kuma na fito nan inda ke teburan cin abinci na ƙara gyarawa,babu jimawa kuwa mutane suka fara zuwa Aliya ta dinga taya ni aikin har muka samu ƙafa ta ɗan tsana sai na zuba abincin da za mu ci,sai kuma a lokacin na dube ta da kyau na ce “Aliya don Allah me ya faru a jiya a gidan Hajiya na kasa tuna komai,kawai dai na tashi na tsinci kaina a ɗakin Alhaji ”
Dama tun tuni na lura ita ma da magana a bakinta,kawai dai ta yi shiru ne.
Aliya ta ce “to mu dai mun tashi ba mu gan ki ba,shine Anty Lubna ta je ta sanar da Hajiya ita kuma tana shiga ɗakin Maheer don sanar da shi ta tarar da ke a gadonsa kina bacci sai ta yi kururuwa duk muka haura sama kafin kuma mu iya cewa wani abu shi Alhajin ya fito daga wanka dole muka fita waje saboda mugun kallon da watso mana.Amma ni ma ban san me ya faru ba,na dai ji Anty Lubna na cewa kin ci amanarta kin je ɗakin Alhaji alhalin kin san tana sonsa,kuma wai don kawai ta yarda da ke ne shi yasa jiya ta bamu labarin cewa sperm ɗinsa ne ta kai a madadin na Dr David ”
Kaina ne na ji yayi wata irin sarawa,ɓacin rai ya ƙara dirar min.Tsakanin jin sperm ɗin Maheer ne Lubna ta yi amfani da shi,da kuma jin zargin da take min sai na rasa wane ne ya fi yi min ciwo.
Abincin na ji ya fita raina,na miƙe na wanke hannuna.Kuka nake son yi don samu salamar zuci sai dai ina fitowa idona yayi tozali da wata mai ciki tana aman jini duk ya ɓata teburin da ke gaban kujerar da take zaune,hankali tashe na nufe ta sai dai tana ɗago idonta na tsaya cak sakamakon abin da ya gigita ji da ganina.....
My book is only 500 amma na yi discount daga yanzu zuwa kafin na saki page 10 ta ƙarshen free.ki tura 300 ta wannan account 2670215530
ZULFAU YAHAYA
ECOBABK sai ki turo min da shaida biya +22795045822
Wacce ba ta shirya ba don Allah kar ta yi min magana
[06/04 14:24] MRS SADAUKI: *BAƘIN RUHI*🧌🐲
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga dukkan iyayenmu MATA da suka tsaya tsayin daka don bamu kariya a kan dukkan wani da ke son cutar da mu.
*FCWA*☀️
________________________
Last free page 10
Fuskarta ta yi wani irin ja kamar za ta tsage jini ya zubo,ga idonta da suke baƙi ƙirin sam babu hasken nan.Bakinta kuma jini ne shaɓe-shaɓe yana mai ci gaba da ɓulɓulo mata.A kallon tsanaken da na yi mata duk ta yi gudu ba za ta haura shekara ashirin da biyar ba,sam kasa cira ƙafata na yi daga inda nake sai ita ce ta yunƙura ta taso ta zo tare da zubewa gabana.Yatsun hannunta na taɓa ƙafata na ji wani irin yanayi ya ratsa ni,yanayi ne wanda na taɓa shiga irinsa lokacin baya shi ma ba zan taɓa mata wannan mummunar ranar ba.
Yawun bakina ne na ji sun fara taruwa da kansu kafin su soma ɗiga suna sauka kanta tamkar ana zubar da ruwan pampo ko kuma ana yayyafi.Zafin hucinta da fitar numfashinta shi ya cika wurin tamkar wacce ake zarar ranta,ƙila shi ya jawo hankalin Aliya ta fito daga can ɓangaren ta zo nan.
“Ƙwayar cutar BAƘIN RUHI,Haule ki ja baya mana contact da ke yana iya haifar da tsayawar numfashinta” Aliya ta faɗa tana mai jawo ni baya,sai a lokacin na ji wani irin raɗaɗi a ƙafata daidai wurin da ta ɗora yatsun hannunta da na kai duba wurin sai na ga tamkar an zuba min acid ne tuni ya wani kumburo ga wata uwar azaba da nake ji.
Na yi baya na samu kujera na zauna,yayin da Aliya kuma ta soma juya hannunta mai ɗauke da ƙarfin iko na power nan take ya kawo haske tare da bayyanar da wani dunƙulalen haske sai ta cillawa wannan mai cikin shi sai ya zagaye ta sai a lokacin ta nufo ni ta tsuguna ta kamo ƙafata.
Hankalinta na ga duk ya tashi,ni kuma na ce “kar ki damu zan warke hakan ya taɓa faruwa da ni ai.Amma me yasa kika jefa mata wannan hasken?”
“Ɗaure ta ne na yi ta yadda ba za ta iya motsawa ba,haka shi ma dafin jikinta zai tsaya da aiki don yana dab da raba ta da rayuwarta.Yanzu dai bari na naɗe miki ƙafarki,sai mu tattauna yadda za a warkar da wannan baiwar Allah ”
Wani tissu ta samu ta ɗaure min ƙafa,na tashi tsaye kan ƙafafuna ina kallon mai cikin wacce ta zama kamar gumki ta kasa motsi.
“Mene ne ke damunta Aliya?”
“Ya za a yi mu samo maganin cutarta ita ce tambayar da ya dace ki yi Haule,kar ki bari kuskuren da kika yi baya ya sake maimatuwa ” ina jin furucin da Aliya ta yi sai na yi saurin dubanta,ta jinjina kai kafin ta ce “na san antynki ai,kar kuma ki tambaye ni ta yaya yanzu mafita za mu nemo kuma ke ce za ki jagoranci tafiyar”
Na ja wani gwabron numfashi kafin na ce,“dole sai na samu labarin mafarin abin da ya haifar mata da wannan cutar”
Shiru Aliya ta yi kafin ta ce “in haka ne muna da buƙatar madubi ko da ɗan guntu ne”
Ban kai ga yin magana ba aka shigo,Lubna ce da sauri na nufe ta sanin kullum tana yawo da madubi a jaka.
“Yawwa don Allah ki bamu aron madubinki” na faɗa .
Inda mai cikin take a durƙushe ta duba kafin ta zuge zip ɗin jakarta ta miƙo min,sai na je kusan Aliya na tambaye ta “ya za a yi yanzu?”
“Ki je saitin idonta ki haska madubin za ta yi magana sai mu ji” cewar Aliya .
Dukka mu ukun muka yi tsaye,suka saka ni a tsakiya yayin da na daidaita madubin ita kuma Aliya ta yi amfani do powerta ta ɗago kanta sai a lokacin na yi mata magana “Wace ce ke? Mene ne dalilin shigarki wannan halin?”
“Sunana Meelat,ƴa ga masu matsakaicin hali,ba mu da kuɗi amma muna da rufin asiri.Na yi karatuna a makarantun gwamnati har Allah yasa na kai matakin University,ina shekara ta biyu yanzu haka.Tun zuwana can na ga yadda rayuwar jami'a take yadda ake challenge ɗin sutura da kuma wayoyi.To dama tun can farko ina sha'awar rayuwar luxery,ina da babban burin shiga mota ,zuwa gidajen cin abinci na manyan mutane da sauransu.Kwatsam wata rana na fito daga jami'a zan je wurin gyaran gashi wata rantsatsar mota ta parker a gabana,a hankali ya sauke madubin motarsa wanda yake baƙi ƙirin ɗin nan.Wani babban mutum ne na gani cikin shiga ta alfarma,fari ne shi tasss mai kyau mai gayu wannan yasa ban wani ja aji ba da ya nemi ya rage min hanya.Sam ban yi duba da ya haife ni ba ko kuma kusan yin jika da ni ba,abin da ke gabana kawai kuɗi.Shi ya biya kuɗin da aka gyara min gashi da aka gama min kuma na kira shi ya zo ya ɗauke ni kamar yadda ya buƙata ya bani lambar wayarsa.Kafin ya mayar da ni can jami'a sai da yayi min shopping kuma ya faɗa min ƙudirinsa na sona yake,nan fa muka fara soyayya ko sau ɗaya bai taɓa kai hannunsa jikina ba tsawon watanni uku muna tare kuma komai nake so yana yi min.Ni da ƙawayena mun mayar da shi atm ɗinmu,a takaice dai sai da muka kwashe wata biyar kafin ya gayyace ni gidansa ya ce yana yin birthday na zo mu yanka cake sai na koma sannan kuma sai na duba gidan in yayi min nan zai ajiye ni in mun yi aure .Haka na je can gidan nasa mai kamar aljannar duniya inda ake parker motoci ma kawai abin kallo sannan akwai motoci iri-,kamar baƙauya haka na yi ta kallon har muka wuce can falonsa ashe ban ga komai ba don cikin ya fi haɗuwa.Ya nuna min kujera ya ce na zauna zai yi sallah ya dawo.Duk da a lokacin bai wuce ƙarfe biyar na yamma ba amma ban tambaye shi sallar mece ce zai yi ba kawai abin da na ɗauka mutum ne mai addini.
Daga inda nake a zaune ina ɗan jin sautin muryarsa yana karatu,amma dai ba na Alkur'ani ba ne cikin wani yare ne yake yinsa.Kamar minti goma haka sai ya fito jikinsa sharkaf da gumi har goshinsa na ɗigar da zufa,hankali a ɗan tashe yake cewa “babyna zo! Taso zuwa gare ni, please ina son ki yi min wani taimako ni kuma na yi miki alƙawari zan mallaka miki key ɗin mota da gida da duk abin da kike so.Lokacin da yayi wannan furucin na yi tunanin sex ne zai nema wurina sai duk ban damu ba don na taɓa yin aure ballantana na ji tsoron rasa budurci kuma a shirye nake na biya masa buƙatarsa duba da hidimar da yake yi min,nan take na ce masa na amince in dai gaske zai ban motar.Sai ya kama hannuna muka shiga ɗakin nan da ya fito,babu komai a ciki sai wani ƙaton akwati a tsakiya yana buɗe shi na yi tsalle na ja da baya .
Ba komai ne cikin akwatin nan ba sai gawar wata mata har ta bushe da alamu ta jima da mutuwa.Jikina ya ɗau kyarma,sai ya soma kwantar min da hankali yana cewa “kar ki wani damu baby kawai ciki za ki shiga kwanta na tsawon minti ɗaya kacal sai ki fito.
Soyayyata da abun duniya yasa na yarda na kwanta a tsorace,kamar yadda ya faɗa ɗin kuwa babu jimawa na fito sai ya bani maƙudan kuɗi waɗanda ni kaina ban san yawansu ba kuma ya mallaka min ɗaya daga cikin motocinsa da kuma gida.Tun bayan da na koma can in na kira shi wayarsa ba ta shiga,da farko ban damu ba sai satin da ya wuce da na soma ganin cikina na kumbura yana zama ƙato in kuma na yi tari sai jini yayi ta ɓulɓulowa na yi yawan asibiti har na gaji amma likitoci ba su gano abin da ke damuna ba.Har gidansa na je amma yana rufe da ɗan kwaɗo ,maƙwabtansa kuma sun ce yayi tafiya.Yanzu ma daga can nake saboda na ji labarin yau zai dawo amma kuma bai zo ba,da zan wuce ne na tsaya don in ci abinci saboda yunwar da nake ji sai kuma na soma yin tari haɗi da aman jini” tana kawowa nan na tashi daga gabanta.
Ina mai kallonsu,Aliya ce ta soma magana “ina ga yayi amfani da jininta ne don bunƙasa arzikinsa ”
Lubna ta karɓe da cewa “a'a bana tunanin domin kuɗi yayi hakan,don in don su ne to zai nemi yayi sex da ita ne ko kuma ya nemi ta basa jinin period ɗinta tabbas sai dai don wata manufar”
Bayan duk na saurari jawabansu sai na ce “in dai ba don kuɗi ne ba to tabbas da buƙatar mu je can gidan nasa”
“A'a zuwa gidansa ba shi ne mafita ba,neman taimakon ƴar aike dai ya kamata mu yi” cewar Aliya tana dube-dube.
Na ce “wace ce kuma haka ?” ba ita ta bani amsa ba,Lubna ce ta ce “duk wata power ko ƙungiya akwai shugabanta Haule ”
“Ina za mu samu tukunyar laka?” Aliya ta tambaya.
“Ko a kasuwa za a samu,me za a yi da ita?” na tambaya.
“Ku fito mu je kafin wasu costumer su zo .Haule rufe ko ina,mu tafi” Aliya ta faɗa ,duk yadda na so yin tambaya kuma Lubna ta hana haka muka rufe restaurant muka nufi kasuwa tukunyar lakar muka saya kafin kuma Aliya ta ja mu can wani guri mai ƙazanta.
“Ku rufe idonku ” ta bamu umarnin da na so yin gardama amma tuna halin matar da muka baro yasa na yi yadda ta ce.
Wani irin hayaƙi na ji ya turnuƙe min hanci yayin da Aliya kuma ke karanto wasu abubuwa maras kan gado.Yanayin yadda iskan shaƙata ya canza yasa na buɗe ido,cikin wani ƙasurgumin daji ne muke duba da labarin da Lubna ta bamu sam ban yi mamakin hakan ba.
“Wannan shi ne ƙasurgumin dajin AOKIGAHARA,ana yi masa laƙabi da dajin fatale da dodanni.Duk wani da ke son kafa ƙungiyar asiri to dole sai ya biyo ta nan domin samun albarka aljanai da kuma tabarakin manya-manyan mashahuran matsafa waɗanda suka taka rawar gani wurin zalunci.Kamar yadda kuke gani dajin ya rabu biyu, wannan shi ne tafarkin haske masu kula da fararen ruhika kuma masu kyautar ƙarfin iko na power,to mu can ne za mu je” Aliya ce ta yi jawabin tana mai nuna mana wata ƙofa wacce wani ƙaton icce mai kan mutum ya raba tsakanin hanyoyin biyu ta sharri da kuma ta khairan.
“Kina nufin BAƘIN RUHI ya samo asali ne daga wannan hanyar kenan?” na tambaye ta ina mai nuna ƙofar wacce ke cike da tarnaƙin hayaƙi da duhu.
“Wannan amsar ai ke za ki bamu ita Haule saboda maɗaukakiyar ceto da ke a jikinki” Aliyar ta faɗa tare da yin gaba,muka take mata baya ina mai juya kalmar ni ce ke ɗauke da maɗaukakiyar ceto a jikina.
Can cikin muka lula kafin mu samu wani keɓaɓen wuri mu zauna,ni ce a tsakiyarsu kamar yadda Aliya ta ce na yi.Bayan duk mun zauna sai muka ajiye tukunyar lakar a tsakiyarmu,yawun bakina na tofa a ciki sai wani irin haske ya soma bayyana daga can ƙasan tukunyar .Gaba na ɗan yi da fuskata na leƙa ciki,da wani mugun sauri na dawo baya sakamakon fuskata da na ga ta rabu biyu.Ɓangaren hagu fuskar Maheer ce yayin da bangaren dama kuma yake tawa,ban san me hakan ke nufi ba sannan kuma ban tambayi Aliya ba wacce tuni ta soma kiran sunaye barkatai sam ban aje hankalina sosai ba tunanin Maheer ne ke yi min yawo a zuciya.
“Ban san mene ne matsalar ba ƴar aike ta ƙi bayyana a gare mu,Haule ko da wani saƙo da aka isar miki zuwanmu?” tambayar nan da Aliya ta yi min ya katse min tunanina,na girgiza mata kai na ce “a'a babu wani saƙo da aka isar min”
Yanayin fuskar Aliya ya nuna rashin jin daɗi,sai ta miƙe ta ce “ku tashi mu tafi ba za ta zo ba,ban san kuma me yasa ba” haka muka fito daga ɓangaren ba tare da na yi tunanin cewa hoton da aka nuna min na fuskata ta tsage gida biyu sannan ta haɗe da ta Maheer shi ne makullin nasarar da muke tunkara ba.
Da muka fito Lubna ta ce “ amma Aliya ita wannan hanyar fa? An hana a shiga ne ko da haɗari?”
“A'a ko ɗaya,sai dai ita tana da sharuɗa ne masu tsauri shi yasa ba kowa ke son shiga ba.Kin ga muddin mutum ya shiga to ko ya ga abin tsoro bai da ikon yin ihu ko ƙara,sannan duk abin da za ka gani iya kallo ɗaya ne kacal za ka yi masa ka ɗauke idonka a kai,sannan ko ƙasar cikin wurin ba a yarda ka ɗebo ba ballantana furanni ko wani abu da ke ciki” Aliya ta faɗa .
“Haule zo mu je mu shiga mu gani ko ba komai za mu ƙara ilimi”Lubna ta faɗa tana wani kamo hannuna,haka kawai na ji gabana na dokawa amma na daure na yarda muka shiga .
Tun a bakin ƙofa wani irin iska mai zafi ya dake min,kuma tamkar an zuƙo mu ne ba tafiya muka yi da ƙafafuwanmu ba haka na ga mun yi saurin shiga tsakiyar wurin.Wuri ne mai cike da furanni masu tsantsar kyawu wanda ya ɓoye sharrinsu da kuma gubar da ke ɗauke da shi.Muna tsaka da tafiya muka dinga jin kukan jarirai,Aliya ce ta yi mana bayanin dalilin kukan.
“Dayawan matan da suka rasa rayukansu suna ɗauke da ciki su ne in sun shigo nan suke haife cikin,wani sa'in jariran na rasa madarar da za su sha ne to in sun ji ƙamshin bil'adama ne sai su fara kuka.In da mace mai shayarwa to haka za ki ga madara na ta ɗiga daga mamanta tana shigewa ƙarƙashin ƙasa” ina gama jin bayanin nan sai wani tsoro ya kama ni,duk gani nake ni ma hakan na iya faruwa da ni duk da kuwa ni budurwa ce.
Wajen wani koren fure muka ratsa sai ya soma yin rangaji yana motsi tamkar wani mai rai,Lubna ta kai hannu za ta tsinko amma Aliya ta buge hannun tare da cewa “ ba ki ji na ce ba a taɓa komai ba?”
“Na manta” ta faɗa tana dariya.
Sai da muka yi yawo sosai kafin mu kamo hanyar fita,nan ne na ji tamkar na taka wani abu mai motsin rai.Ina ɗaga ƙafata sai na ga wata sarƙar diamond mai shegen kyawu sai ƙyalli take,kallo ɗaya na yi mata ina shirin kawar da idona amma wani abu ya ja hankalina a tsakiyar sarƙar harafin H ne aka zana sannan ga wasu duwatsu masu kaloli da aka ƙawata harafin.
Na duƙa na kai hannu na ɗauki sarƙar,ko da na ɗago sai na ga tuni su Lubna sun kai bakin ƙofa.Kamar wacce aka yi wa dole haka na saka sarƙar a wuyana tare da gyara ɗan ƙaramin hijabina sannan na ɗan ruga na cimmar musu.
Ko da muka fito waje sai Aliya ta ƙara mayar da mu can wurin nan mai datti.
“Yanzu ya za a yi kenan?” Lubna ta tambaya.
Aliya ta ce “mafita guda gare mu a yanzu shi ne mu je can gidansa”
Kamar wacce aka tsikara na ce “na san gidan” duk suka kalle ni da mamaki,amma tun da abin da suke so ne kawai ba su tambaye ni ta yaya ba sai muka ɗau taxi ni ce na dinga nuna masa hanya har muka isa gidan.
Bayan mun sallami mai taxi muka fito muka yi cirko-cirko,unguwar tsit take sosai ma na yi mamakin ta yadda aka yi Meelat har ta iya ganin maƙwabtan Alhajin.
Aliya ce ta soma juya hannunta mai power ta ɓalle kwaɗon da aka rufe gidan da shi,su biyun duk suka shige ciki yayin da ni kuma na tsaya ina kallon wata matashiyar budurwa wacce ke zabaya tana leƙena ta wata can saman benen ɗaki.
‘Wace ce ita kuma waccan mai farar fata kamar fulawa?’ na tambayi kaina a zuci,ban kai ga samo amsa ba na ji kururuwar su Lubna daga can cikin gidan.A guje na nufi ciki sai na tarar suna gurmuzu su da wani gogon Biri duk yadda Aliya ke da power ta kasa tsayar da shi domin shi ma an tsafe shi.Abun mamaki ina shigowa sai ya tsaya cak tare da zubewa ƙasa yana wani irin abu kamar yana gaishe ni,ƴar kallon-kallon muka fara yi mu ukun .
“Haule ke ma irin wannan protector ɗin gare ki? Na ga duk jikinsa yayi sanyi” Aliya ta yi min tambayar da sam ban ma gane mene take nufi ba hakan yasa na share ta na ce “ga ɗakin akwatin gawar nan” na nuna musu shi da yatsa sai suka nufi ƙofar yanzu ma Aliya ce ta buɗe ta.
Sai bayan sun shiga na take musu baya ina mai waiwayen Birin da har zuwa yanzu yana a yadda yake.
Kiciniyar buɗe akwatin suke amma sun kasa,don power Aliya ma ta ƙi yin aiki.Sai na zo na kama musu amma ta ƙi buɗuwa,Lubna ta ce “ina ga akwatin nan jini ne makullin buɗe shi”
Duk sai muka kalle ta,kai ta jinjina ta ce “wannan tambarin Family ne” ta nuna wani logo da ke jikin akwatin.
“To jinin wa za a tsaga?” na yi tambayar.
Aliya ta ce “in dai haka ne da na Lubna za a yi amfani duba da ta taɓa zama cikin ƙungiyar,na san har zuwa yanzu zanen hannunta bai goge a rubutun da suka yi ba” sam ba mu yi tunanin wannan babban kuskure ne za mu tabka ba,haka Lubna ta tsaga yatsanta ɗigon jininta ya ɗiga sau uku a jikin tambarin nan take akwatin ya soma buɗe kansa a hankali wari da ɗoyi yasa suka ja baya,yayin da ni kuma na toshe hancina tare da matsawa ina leƙen akwatin.Yana gama buɗewa na ji an tunkuɗa ni ciki na faɗa yayin da kuma akwatin ya rufe ruf da ni a ciki.Cike da tashin hankali na soma kiciniyar buɗe shi amma ya ƙi yi,ina jin muryar Aliya kuma na cewa Lubna “don me kika yi haka? Yanz...” ban ji ƙarashin maganar ba sakamakon ƙanƙame ni da gawar ta yi tana yi min maganar da ta birkita lissafina.Daidai nan free page ya