Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 11
kamar walƙiya.Na ja ajiyar zuciya,abin da na fahimta a family su komai nasu ba su yinsa dole sai ta daɗin rai wannan dalilin yasa ko da wasa ba su saka ƙarfi ba wurin baiwa Boss ni ba. Ina nan tsaye ina saka wasiƙar jaki Zuly ta turo ƙofa ta shigo,kallo ɗaya ta yi min ta ɗauke kai tare da yin gaba.Ni kuma na take mata baya ina mai kiran sunanta,sai da ta cire zumbulen hijabinta sannan ta juyo ta fuskance ni ta ce “Luby ban san wace irin zuciya ce da ke ba marar tausayi,duk halin da Abbanki yake ciki kin kasa haƙura ki bada kai bori ya hau.Me za ki yi da shi budurcin? Ina ce duk don da dai ki kai shi ne gidan mijinki,to ki sani a family ba a auren bare.Duk wanda ko wacce ta shigo babu aure to dole ne ya zaɓi abokin rayuwa cikin ƴan ƙungiya,kuma ina ce ai a gabansu za a yi komai ba za ki samu matsala da mijinki ba tun da ya san komai” Tamkar mai cutar dundumi haka na ji a lokacin,sai kuma na fahimci ba ƙaramar ƙungiyar asiri ce wannan ba wacce ta ɓoye sirrika masu yawa sai a sannu ne za ka dinga ganinsu suna fitowa. Ban kai ga cewa komai ba Zuly ta ƙara da “kawai ki amince ita ce shawara da zan baki” Idona wani irin raɗaɗi na ji suna yi min kamar an watsa barkono ciki,maƙoshina ya bushe ƙamas dakyar na iya tattaro yawu na haɗiye kafin na ce “ban gane ba zan iya auren wani ba? Zulaihat wai wannan ɗin duk mene ne? Wane irin dokoki ne wannan? To ki tsaya ki ji in faɗa miki daga yau a yanzu da nake faɗa miki na fita daga family har abada,ku je can ku yi tsafinku kuɗi ne dai to ban so ku riƙe abinku.Kuma wallahi kika yi ƙoƙarin ɓullo min da wani sharri to sai na je har ofishin ƴansanda na shaida musu ke ce kika kashe mijinki” ina gama faɗar haka ban tsaya ɓata wani lokacina ba na fita na bar ta cike da shock. Duk a tunanina shikenan na huta na jefar da ɗan mangoro na huta da ƙuda sai dai ina isa asibiti na tarar da tashin hankalin da ban taɓa zato ba. Jikin Abba ya rikice sai aman jini yake dunƙule-dunƙule,likitoci sun duƙufa wajen bincike amma result bai nuna alamun wata cuta ba ga jinin Abba sai ƙasa yake yi ga shi banda kuɗi,jinin kuma sai an saya. Duk da yana cikin firgici da gushewar hankali bai hana shi isar min saƙon kar na saki na bayar da mutumcina ba.Banda kuka babu abin da nake yi,ji nake kamar na je na cewa Zuly na amince sai dai fa duk shaƙiyancina na tsani zina ban ƙaunarta ko kaɗan.Ko da ace saurayina ne wanda nake so ban ji zan iya basa kaina ba ballantana sindiƙin ƙato mashuriki matsafi. A lokacin da zuciyata ta yi rauni sosai,shine ganin yadda jini ya soma yi wa Abba zuba ta hanci da kuma ido daga ƙarshe yayi shaƙuwa shikenan ashe ta fitar rai ce.Wuaren ƙarfe bakwai ne na yamma likito suka tabbatar mana da hakan,tsabar tashin hankali yasa na suma aka bani gado.Ban san abubuwan da suka faru ba sai a washegari na farka tuni kuma an kawar da gawar Abba an kai shi mankwancinsa na gaskiya.Sai a lokacin na yi kukan mutuwarsa kamar raina zai fita,kafin a sallame ni daga asibiti Allah ya ƙulla alaƙa tsakanina da wani Dr David shine ma ya ɗauki nauyin biyan kuɗin maganina har na ji ɗan sauki. Bayan na koma gida ma haka yake zuwa yana kula da ni,kusan ma in ce shi ya ɗauki nauyin gidanmu tun da babu wanda ya tallafa mana daga dangi. Cikin abin da bai wuce wata ɗaya ba wata irin shaƙuwa ta shiga tsakanina da Dr David ,sonsa ya samu matsuguni a zuciyata duk da hankalina bai kwanta ba saboda shirun da Zuly ta yi sam ban yarda da shi ba,don na sha jin yadda ƴan ƙungiyar asiri ke da mugun naci.Ashe kuwa ban saɓa lamba ba,a wani yammacin Laraba mun ajiye magana Dr David zai zo ya ɗauke ni mu je gaishe da mahaifiyarsa .Mun yi waya da shi kenan ya shaida min ya ga shi nan zuwa,bayan kamar mitin goma aka kira ni aka shaida min yayi hatsari yana can asibiti . Cike da tashin hankali na fita ko Ummah ban shaida ma ba,ina fitowa nan cikin layinmu wani mai mashin ya kaɗe ni sai da na yi sama na faɗo duk kayan jikina suka ɓace da ruwan dauɗa,dole na koma gida na yi wanka ina ƙoƙarin sake fita kuma ita ma Ummah ta soma nata ciwon abu kamar wasa sai ga mu har da zuwa asibiti. Bayan mun dawo gida na yi ta gwada kiran Dr David amma layin bai shiga,amma ban haƙura ba a cikin haka na samu ya shiga sai dai ba shi ne ya ɗaga ba mahaifiyarsa ce wacce nan take ta hau ni da masifa akan na rabu da ɗanta kar abin da nake ciki ya shafi ɗanta na je can na ƙarata da matsalata.To a nan ne fa na gane zama bai same ni ba,sam kasa bacci na yi .Tsakar dare kuma ciwon Ummah ya ƙara tashi ta soma numfashi kamar za ta mutu,a lokacin tuni na soma yin kuka na ɗauki wayata tsabar ruɗewa wai da Dr David zan kira nan ne na ci karo da saƙon Zuly tana yi min hannunka mai sanda tare da barazanar cewa in ban yarda na dawo bakin aiki ba to zan rasa Ummah tamkar yadda Abba ya tafi. Ina matuƙar son Ummana wannan yasa na aika mata saƙon zan koma a gobe,hum in faɗa muku wani abin mamaki kamar cirar ƙaya haka Ummah ta warke ta samu bacci.Sai na ji na ɗan samu nutsuwa,ni kam ban yi bacci ba har sai da na yi sallar asuba wacce zuwa yanzu ina yin sallolina. Sai wuraren ƙarfe tara na farka,na yi wanka na shirya sai kuma na shaidawa Ummah zan koma a bakin aikina. “Ni kam Lubna tun da Abbanku ya rasu ban ga wani daga cikin ƴan wurin aikinku ya zo ba,har shi ogan naki” shine abin da Ummah ta ce. Na ce “kin san na rasa wayata,kuma oga ba ya ƙasar ita kuma Zulaihat faɗa muka yi lokacin da na ce ta ara min kuɗi ta ƙiya ƙila shi yasa ba ta zo ba ko kuma ba ta samu labari ba” “To Allah kyauta,ki je Allah ya tsare ki ya kuma kare ki da sharrin dukkan mai sharri” Cike da jin daɗin addu'arta na amsa da “amen” kafin na fita.Ina zuwa bakin titi motar Zuly ta parker a gabana,zuciyata cike da ƙunci na je na zagaya na buɗe na zauna ta saki murmushi mai sauti kafin ta ce “barka da safiya” ban amsa ma ta ba har muka isa gidanta na canza kaya muka wuce. Sosai na yi mamakin yadda aka shirya min tarba ta musamman,har da yi min wankan fure aka yi min kafin kuma na yanka cake aka shiga taɓi.Bayan wannan sai muka wuce ofis ɗin oga ni da Zuly,bayan mun zauna ne ya soma yin magana “Luby duk da dai ban so kika rasa damarki ta farko ba,amma mun rarrashi Boss kan ya janye wannan dokar duba da yadda kike da ƙoƙarin aiki dakyar ya yarda amma da sharaɗin za ki kawo sperm ɗin wani wanda kika sani mai ilimi” Na ɗan yi saƙo kafin na ce “a ina kuma zan samu sperm oga?” Zuly ta yi karaf ta ce “ saurayinki David mana ,ai kin ga yana da ilimi sosai kuma ma ai kin ga ba musulmi ne ba ballantana ki sha wuya wurin shawo kansa” Shiru kawai na yi,duk da na ga sharaɗin ba wani mai tsauri ne ba amma tabbas na san da haɗari a ƙasa. “Ko kuwa dai kin fi so a dinga yi wa ahalinki ɗauki ɗaiɗaya suna mutuwa ɗaya bayan ɗaya?” Zuly ta jefo min tambayar da na ji tamkar na shaƙe mata wuya,kuma sai yanzu ma ne raɗaɗin mutuwar Abba ya fi yi min ciwo fiye da can farko. A hassale na ce “ kar ki yi kuskuren taɓa Ummana don wallahi zan shayar da ke mamaki,kun faɗi sharaɗinku ai sai ku jira in ban yi ba sai ku bijiro min ta nan” Oga ya ce “ Zuly ke ma ya kike yi mata magana haka? Ki yi haƙuri Luby ki je ki fara shirye-shiryen taron da za ki gabatar yau da dare,Zuly ki bata sanadaran da kuka fitar na taurari”cewar oga kafin ya miƙe ya shiga toilet,ita kuwa jakarta ta zuge ta miƙo min wasu kwalabe biyu ɗaya mai baƙin murfi yayin da ɗayar kuma ke da farin murfi.Na karɓa ina juya su yadda kowacce kwalba ke fitar da bata kalar hasken. “Baƙin tauraro yana da matuƙar muhimmanci ga waɗanda suka san amfaninsa,shi kuma farin yana ƙara ƙarfin power ne kawai” Zuly ta faɗa kafin ita ma ta tashi ta take wa oga baya.Ba a ɗauki lokaci ba yanayin sautinsu ya fara farmakar kunnena babu shiri na fita na bar ofis ɗin amma sam sautin ya ƙi fita da kwayanta hakan ya haifar min da zuwan wani hatsabibin feeling wanda ya fi kama da na haddasawar sheɗanu.Ido kawai na lumshe tare da ƙanƙame jikina,a inda nake zaune nake a cikin ofis ɗin Zuly nake jin wasu idon sharri na ankare da ni amma da na duba ban ga kowa ba. Ina zaune cikin wannan hali Zuly ta shigo,jan bakin da ta saka duk babu shi a leɓenta sannan zaman rigarta ma haka.Ba tare da wata damuwa ba ta ce “kafin mu isa Japan ya kamata ki aiwatar da aikinki na kawo sperm ɗin David,ki tabbatar komai ya tafi kan tsari” “Ta ya za a yi na samu sperm ɗinsa ba tare da mun yi sex ba?” “Ki yi tunani Luby,yin sex da masoyi ai bai da wata illa ya fi ki yi da wanda ba ki so” “Ba ki da hankali,sai na je na yi zina? Allah ya tsare ni” na faɗa tare da miƙewa,ina shirin fita wani abun al'ajabi kiran Dr David ya shigo wayata cak na tsaya kafin na juyo na ce “shi ne ke kirana ” sai ta saki murmushi ta ce “ki ɗauka mana” Kiran na ɗaga,bayan mun gaisa ya tambaye ni yana son mu yi magana amma don Allah ba ta waya ba mu haɗu ko da wani restaurant ne.A ranar nan rabon na rabu da alaƙaƙai ne yasa na yarda da gayyatar Dr David,wani abun mamaki kuma shine a restaurant ɗin Hajiya ne muka haɗu a nan ne na fara ganinki Haule haka kawai na ji kin yi min sai kuma na ga kina yawan kallona a duk lokacin da za ki kai abinci a wani teburin da aka buƙata.A tattare da ke na ga wasu abubuwan na daban sai dai ban san ya zan yi na yi miki magana ba,a nan ne kuma hankalina ya rabu biyu na yadda zan yi na samo sperm ɗin Dr David da kuma na mamakin yadda kike yin abu kamar siddabaru. Dakyar na iya tattaro jarumtar tunkarar Dr David kan cewa ina son sperme ɗinsa saboda an ce yana gyara fuska,bai wani musa min ba don dama ya kira ni izuwa nan ne don bani haƙuri da kuma neman alfarmar mu koma soyayya.Mun yi da shi zai kawo min sperm ɗin zuwa dare,da wannan muka rabu ya sauke ni gida.Duk yadda muka yi da shi na kwashe na shaidawa Zuly ta yi murna sosai har ta kasa ɓoye farin cikinta,sai kuma na yi mamakin haka amma na ɓoye shi har lokacin da Dr David ya zo ya kawo min abin da na buƙata cikin wata ƴar kwalba. Bayan na karɓa ya jefo min wata tambayar da ta hautsana hanjin cikina,“Lubna kin tabbata a fuskarki za ki shafa shi?” duk da a lokacin na firgita amma haka na mayar da abin tsokana na ce a'a cikin mahaifata zan ɗura shi don na samo baby mai kama da kai,nan yayi dariya muka taɓa ƴar hira kafin ya tafi. Yana gusawa motar Zuly ta parker na shiga muka lula can gidanta,cike da zumuɗi take cewa “meeting ɗinki na Japan an ɗaga shi,yau za mu je ɗakin sirrin Boss domin gabatar da sacrifice ɗinki na farko” sam ban fahimci abin da take cewa ba,sannan kuma ban tambaya ba. Yau ma ta cikin madubinta muka bi muka isa a ɗakin taron,abun mamaki kowa ya haɗu har da shi kansa Boss ɗin wanda idonsa ke jifana da kallon sha'awa.Ba a ɓata lokaci ba muka dugunzuma wani ɗaki mai shegen duhu ,babu abu mai haske ko ɗaya in kuka cire wani mirror . Cikin wata irin busashiyar murya Boss ya kira sunana,hakan yasa na ɗan matsa ba tare da na amsa ba.Hannu ya miƙo min,na san za ku ce ta yaya na ga haka duk da na ce akwai duhu a ɗakin.To abin shine da zarar mutum ya kai wani lavel yana samun wani ido a tsakiyar goshinsa mai gane masa komai da ido normal ba zai gani ba. Yana karɓar robar sperm ɗin ya buɗe ta,sannan ya dangwalo da yatsansa ya shiga yin rubutu a jikin madubin *BAƘIN RUHI* shi ne abin da ya rubuta nan take wata irin guguwa da iska mai ƙarfi suka cika ɗakin na yi tunanin duk za su yi murna sai dai fa akasin haka ne ya faru saboda kururuwa da suka soma,kafin ƙyaftawar ido wani jan maciji ya bayyana a mirror ɗin yana feshin wuta kafin kuma madubin ya tarwatse wanda turnuƙin fashewarsa ta haifar min da gushewar hankali ko da na farka a kwance na same ni kan shimfiɗa Ummah na yi min fifita.Ina ware idona sosai nan na yi arba da Alhaji wato Maheer,wani irin mugun kallo ne yake watso min yana hararena. Ummah ta ce “kin farka Lubna?” ban amsa ba sai dai na yunƙura zan tashi sai dai na kasa saboda yadda jikina ke yi min mugun ciwo. “Ki kwanta ki huta” cewar Ummah. Shi kuwa cike da mugunta ya ce “barta za ta iya tashi,ke miƙe ” Maganarsa tamkar umarni ne a gare ni,haka na ji ba zan iya yi masa muso ba na miƙe na tashi zaune duk da kuwa uwar azabar da nake ji.Wani magani ya fiddo cikin aljihu ya miƙo min,“komai za ki ci ki dinga zuba wannan a ciki,in kuma kika kuskure daidai ɗaya rana za ki koma hannun waɗanda kika fito” A lokacin da na ji Ummah na yi masa godiya sai na fahimci tuni ya shaida mata komai,ban yi mamakin yadda aka yi ya san komai ba don na fahimci yana da power.Sannan a cikin coma ɗin da na shiga haka aka yi min wahayin komai ta yadda aka yi ya tarwatsa komai,ashe lokacin da muke yin magana da Dr David Maheer ya shigo restaurant ɗin kuma ya ji abin da nake cewa.Sannan kuma abin da ba ki sani ba Haule sarai Maheer ya san cewa ke ma ba normal mutum ba ce,kamar yadda na dinga kallon abubuwan da kike na siddabaru to shi ma idonsa suna iya ganin duk abin da kike yi” Lubna na kawowa nan da dogon labarinta da take bamu ni da Aliya sai ta yi shiru,ni kuma numfashi na ja kafin na ce “amma ta ya aka yi ni ban san da cewa shi ma yana da power ba sai yau? ” “Saboda ƙarfinsa ya wuce yadda duk kike tunani,kin ga fa shi ne ya kuɓutar da ni daga komarsu tun lokacin ba su sake waiwayata ba.Haka ita ma Ummah ba ta yi sake kan kula da lamurrana ba kullum cikin yi min addu'o'i take,duk asubah in ta gama sallah kamar wata ƴar baby haka take dafa goshina tana yi min addu'o'i ” cewar Lubna. Na dubi Aliya wacce duk yanayinta ya canza kafin na ce “ya dai?” “Babu komai! Amma dai a yadda na fahimta ita ma Lubna ta shiga komar BAƘIN RUHI ne kamar yadda na saba ganin gawarwakin waɗanda suka mutu ta silarsa,su ma jini yana fita ta idonsu” Furucin Aliya ya tuno min da gawar Haidar,murya na ɗan rawa na ce “Lubna bayan an yi wa mahaifinki wanka shin jinin da ya fita ta idonsa ya wanku?” Ta ce “wallahi ban sani ba saboda lokacin ai na faɗa muku ban cikin hayyacina kuma ko da na farka tuni an kawar da shi” Na ce “da buƙatar mu samo amsa,babu kuma wanda zai bamu tabbacin haka sai Ummah.In dai hakan ta kasance to tabbas BAƘIN RUHI nada ƙarfi sosai ta yadda ya bazu a duniyar nan to amma wane ne shi?” na yi tambayar da ni da su babu wanda ya san amsarta..... My book is only 500 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 🔞Don Allah masu zuwa suce min complet suke so ku yi haƙuri Ni ma banda shi,yanzu nake typing in kina so ki biya na saka ki group. [05/04 12:15] MRS SADAUKI: *BAƘIN RUHI*🧌🐲 ```LoVe aNd HoRrOr story```👽 By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️} *SADAUKARWA :* Ga dukkan iyayenmu MATA da suka tsaya tsayin daka don bamu kariya a kan dukkan wani da ke son cutar da mu. *FCWA*☀️ ________________________ BONUS na book ɗin *BAƘIN RUHI* mai so ya tura 300 kafin na saki last free page 10 gobe in sha Allah ki tura kai tsaye ta wannan account ɗin 2670215530 ZULFAU YAHAYA ECOBABK sai ki turo min shaidar biya ta WhatsApp +22795045822 .Da zarar na saki last free page discount ɗin ya ƙare. Masu sha'awar karanta tsofin Books ɗina ku zo na yi muku discount,ga wacce ta shirya ta tuntuɓe Ni kai tsaye ta WhatsApp +22795045822 09 Dare yayi sosai wannan yasa muka jingine bayar da labarin,duk da na san akwai abubuwan da Lubna ta ɓoye wanda ba ta faɗa ba amma haka na yi shiru na samu wuri na kwanta.Ido na lumshe nan take Maheer ya bayyana cikin tunanina,zaune yake a ɗakinsa ya sha wata doguwar rigar bacci ta maza fara sol da ita.Gabanta a buɗe yake,hakan ya bani damar ganin fafaɗen ƙirjinsa mai ɗauke da suma baƙa silik ta kwanta sai sheƙi take.Duk da ban taɓa saurayi ba,amma gargasar ƙirji na ɗaya da abin da nake fatan samu a wurin mijin aurena hakan yasa na kafe gurin da ido ko ƙyaftawa ban yi. Har sai da na ji muryarsa yana cewa ,“kin ga dama kin zo” da wani mugun sauri na buɗe idona sai kuma na tashi zaune na dafe saitin zuciyata da take bugawa,sam na kasa gane shin tunaninsa ne na yi? Ko kuwa dai ban sani ba bacci ne ya ɗauke ni sai na soma mafarkinsa? Amma dai tabbas na gansa da idona sai dai irin wannan tunanin bai taɓa zuwar min ba. Cike da tsoro na ƙara kwanciya na lumshe idona zuciyata na ci gaba da matsanancin bugawa.Wannan karon jinsa na yi dab da ni har muna jin hucin juna kai kace hatta gangar jikinmu na tare da juna ne,nan kuwa iya esprit ne.A hankali na ɗaga idona na kalle shi,yadda yayi wani tsaye ƙiƙam a gabana duk ya kere ni kamar Giwa da ɗan tsako. “Yanzu kuma wannan mene ne da ka jawo ni cikin tunaninka?” na tambaye shi. Cike da shaƙiyanci yasa hannunsa mai sanyi ya wani matse haɓata tare da ɗago ta ya ce,“ni kike yi wa magana haka? Sa'anki ne ni? Wato ni ne ma na shiga tunaninki? Kin zata ban gane ba? Ke ce kika shigo tunanina,na lura tun da kika zo gidan nan idonki na kaina duk kin bi kin takura ni kin hana ni saƙat,faɗa min wa ya aiko ki?” Cike da jin haushi na sa dukkan hannuwana na tura ƙirjinsa sai dai ko gezau bai yi ba,shi ma tuni ya hassala sai ya kama hannuna ya murɗe har sai da na saki ƴar ƙara na soma fizge-fizge amma ya ƙi saki na. “Duk shegen kinibibinki ne ya jawo miki halin da kike ciki amma ko kaɗan ba ki cancanci samu wannan power ba,sam ban ga ma dalilin da yasa ƴar aike ta mallaka miki mahaɗin ƙarfin ikona b...” ban bari ya kai ƙarshen aya ba na gantsara masa cizo a ƙirji da wani mugun sauri ya sake ni tare da ja baya ,daidai nan ni kuma na tashi zaune tare da buɗe idona fayau. Saitin hannuna na duba inda ya murɗe sai na ga yayi ja sosai tamkar a zahiri ne ya riƙe ni ɗin,ƙin komawa na yi na kwanta sai na ci gaba da zama tsakiyar su Lubna da tuni sun yi bacci. Ina nan zaune na ji handle na motsi ,kafin kuma ƙofar ta buɗe kanta ƙiiiii sai dai ban ga kowa wanda ya shigo ba.Wani irin tsoro ne ya kama ni ,sai nake ganin kamar Maheer ɗin ne zai shigo a zahiri. “Haule!” na ji muryar da har na koma ga Allah ba zan taɓa mantawa da ita ba ta kira sunana cikin wani irin yanayi. Na soma waige-waige kafin na ce “Husseina? Husseina ke ce? ” ba ta bani amsa ba,sai jin wani abu na yi cikin iska ya kama hannuna yana jana sai kawai na sauko daga shimfiɗar na soma take mata baya duk da kuwa idona bai ganinta. Da muka ratso falo haka ƙofarsa ita ma ta buɗe kanta,haka ma ta ƙofar gida. Muna fitowa sai Husseina ta bayyana a gare ni,tana sanye cikin farin likafaninta har izuwa yanzu kuma kukan jinin take. Kan dakali ta ja ni muka zauna kafin ta ce “Haule sai yaushe za ki kuɓutar da mu daga cikin ƙangin da muke ? Har yanzu ba ki samo mahaɗin sirrin tarwatsa BAƘIN RUHI ba?” Jikina banda rawa babu abin da yake yi,na ce “ta ya aka yi kika zo nan? Kuma me yasa kika fito da ni waje? Ai sai ki yi min magana a can ɗakinmu” Ta ce “in muna cikin gidan nan idonki ba za su taɓa gani ba Haule,amma na tambaye ki wane ne kike so har haka wanda ya mantar da ke dalilin zuwanki ƙasar nan?” “So kuma? A'a ni ban son kowa” ban ida rufe bakina ba Husseina ta ɓace ɓat,cike da mamakin ta ya za ta tafi ba ta yi min sallama ba na miƙe da niyyar shiga gida sai dai kuma na tsaya cak sakamakon ganin mutum tsaye a gabana fuskar nan tamau fiye da kullum.Wani irin mugun tsoronsa da shakkarsa ne suka yi min dirar mikiya musamman da na gansa da kayan jikin nan irin na tunanina. “Da wa kike magana?” ya jefo min tambayar cikin tsawa kamar wani ubana. Mayafin jarumta na aro na yafawa kaina na ce “da kai mana” Ya waro ido kafin ya ce “ke kar ki raina min hankali da ni kuma?” “Eh to wa ka gani a nan bayan mu biyu?” “Me kika fito yi to?” “Abin da ka fito yi” na basa amsa kai tsaye tare da yin gaba sai dai ƙofar a rufe take ruf.Na juyo na dube shi,sai na ga yana wani miskilin murmushi kafin ya ce “ina ce dai fatalwa ce ta fito da ke waje? To ki ce ta mayar da ke in tana da izzar zama a inda nake” yana gama faɗar haka sai ya zo yana tsayuwa ƙofar ta buɗe kanta na yi wuf zan shige amma tuni ta rufe shi kuma ya shiga ciki. Tsoro ne ya kama ni,cikin magiya na ce “don Allah Alhaji ka buɗe min ” Banza yayi da ni duk da kuwa da ina jin alamun tsayuwarsa bai tafi ba.Hadari ne ya soma haɗa kansa haɗi da tsawa da walƙiya,nan tsorona ya ninku don kuwa duk jarumtata ban son ruwan sama su dake ni. “Ki faɗa min da wa kike magana sai na buɗe miki ” na tsinkayo muryarsa. Cikin kukan da ya fara zuwar min na ce “ka buɗe min na yi ma alƙawari zan sanar da kai” ai kuwa ya buɗe ƙofar ina shiga na baza a guje na nufi can ƙofar da za ta sada ni da babban falo. Cak na tsaya ina waro ido saboda wani jaririn maciji da ya sarkaye handle ɗin ƙofa,ina juyawa kuma sai na hangi Maheer yana takowa izuwa inda nake.Timmm na ji ƙarar faɗowar macijin kafin ya fara yin silululu yana tawowa,a mugun firgice na yi baya tare da rugawa na tarbo Maheer ɗin na koma bayansa tare da ƙanƙanme shi ina kuka ashe gudun gara na yi na faɗa gidan zanzaro shine mamallakin macijin. “Sahut!” shine furucin da yayi kafin macijin yayi tsalle ya ɗale kafaɗarsa hakan

Chapter 5 of 11