Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tashi takarbi wayan tace “naji I don’t want you to tell me anything and nima I will not tell u anything Hawwa, but just tell me kina Ina yanzu naji kina hanya, ina zaki”? Shiru tayi kaman bazatai magana ba tace “wajen Ammi zani a zaria” faduwa sosai gaban Ni’ima yayi tace “Hawwa going to zaria da daddaren nan ke kadai a mota are you okay? Kin manta yanda ake kidnapping ne a hanyan” ahankali Hawwa tace “I will be fine karki damu” cikeda damuwa Ni’ima tace “Hawwa why can’t you come to me eh kika kama kik……” key mota dataga Baban Yaseer yadauka yayi kofa yasa dasauri tazare wayan daga kunnenta ta katse tace “Baby ina zaka”? Slippers yashiga sawa yace “zaria” tahowa wajen tayi dasauri tace “zaria this night”? “if anything happens to Hawwa wani abu zai iya samuna!” Yafadi da karfi dayasa chak Ni’ima ta tsaya shima ya tsaya yana kallonta jin abinda yafito daga bakinshi saikuma yadan dafe kanshi yace “just stay with the kids, text me her aunt home address” yana maganan yafice tana tsaye awajen taji ana budemai gate, hannunta da aka rike yasa tai firgigit tajuyo tab dinta Yasmeen tabata tace “Mommy I want to sleep” dan murmushi ta kakalo ta mata ta kalli Yaseer ma tace “okay muje ku kwanta” kama hannunsu tayi tawuce dakinsu dasu bayi ya kaisu sukai fitsari sannan tahau gado dasu tace “addu’an bacci” addu’a sukayi taja bargo ta rufesu tana kashe musu wuta ta rungume su, wasu hot tears taji sunabin kuncinta hannu takai ta share amman sun kasa daina fitowa jin alamun sunyi bacci yasa ta tashi tafito daga dakin tazo falon ta zauna tana kallon system nashi very important aiki yake da Oganshi yasashi yayi yaturomai by 11 na daren nan, gashi yanzu 11 saura, zama tayi tasake fuzar da ijiyan zuciya sannan tadauki wayan nata hannu tasa ta goge fuskanta tass sannan ta shiga turamai address din, kafin tai dialing number Hawwa amman harya katse bata dagaba message ta shiga ta turamata. “Be safe Hawwa, I’m worried about you, Allah tsare hanya” kusan 2min saiga reply na Hawwa tace “I know you are worried, don’t be nakai zan kiraki, love you Best” love you best din takalla sai taji wasu hawaye masu zafi sun sake zubomata tashi kawai tayi tafada dakinta iPad dinshi dake saman drawer side nashi na bed ta kalla yawanci yana daukanshi da daddare yadanyi karence karance, samin kanta tayi da dauka, hoton family portrait nasune ne as wall paper, tadade tana kallon Baban Yaseer a hoton sannan tai kokarin duba wayan taga password shiru tayi tana tunani sai kawai tasaka birthday na su Yaseer taga yabude tashiga cikin wayan, tana dube dube chan ta shiga gallery wayan, hotunan Hawwa taci karo dasu a gallery, dasauri ta shiga ciki hotunan duka na wayanta ne wanda ko Hawwa batadasu dan ita ke snapping nata, tun hotunan su na primary and secondary school, da hotunan datake mata occasionally, da hotuna datama Hawwa adakinta tana sanye da rigan bacci mai kyau ga boobs nata da sukai showing dasauri takai hannu tai deleting wannan, saikuma hotunan datagani wayanda Hawwa nafitowa daga gidansu da hotunanta in different places kaman stalking dinta ma yake yana bibiyanta batare data sani bama ita Hawwan, ganin zuciyanta zai buga yasa tashiga marking pictures din tai deleting everything ta maida iPad din ta ijiye tana sauke ijiyan zuciya saikuma tafashe da kuka sosai na tausayin kanta. Sosai Hawwa ke gudu akan titi da daddaren nan zuciyanta gabaki daya yazo mata wuya, bini bini take goge hawaye, she can’t even explain d kind of pain datake ciki today has been a bad day for her, daidai ta shigo kaduna around 12 tayanta ya faci gangarawa gefen hanya tayi kawai tai parking tadaura hannayenta asaman fuskanta tafashe da kuka sosai tace “Ya Allah maisa ban sami mijiba? Nayi imani da kaddara mai kyau da mara kyau, I accept whatever you choose for me Ya Allah, ina salla, ina azumi, ina nafilfilu, ina karatun Al Qur’ani, bantaba fasikanci ba, bantaba shan giya ko wani abu na maye ba, inama iyayena biyayi, ina taimakon mutane, daidai gwargwado ina bautamaka Allah” cikin murya mai rauni sosai tace “Ya Allah kaji tausayina kaji Ya Allah, Ya Allah kabani mijina nima, Ya Allah ka kawomin mijina nima, Ya Allah ka aurar dani da gaggawa banson yanda hankalin Babana yake atashe sabida ni, nazaman mishi abin kunya, dani ake kwatancen shi, Ya Allah ka tausaya mini kaji” tafashe da kuka sosai she missed mamanta she missed her, kusan 1hr ita kadai a motan nan babu tsoro ko fargaba aranta koma yatakama takama din kawai, idanunta a lumshe bawai bacci takeba but jikinta duk ya saki taji ana bubbuga marfin motanta “Hawwa Hawwa, Hawwa talk to me, Hawwa” kaman ana kiranta daga nesa hakan yasa tadan bude idanunta kadan, ganin hasken flash na haskota yasa gently tajuyo da rinannun idanunta ta kallo glass na motan shima ganin haka yasa Baban Yaseer ya haska mata fuskanshi sabida taga shine, wani irin kafeshi da idanu Hawwa tayi batun yauba taga soyayyanta a idanun Baban Yaseer but koda mistake bata taba saran zamata bashi chance ba saisa bata cika zuwa gidansu ba saidai ta sami kawarta awajen aiki kosuyi outing tare, She will never ever betray her friend koda baban Yaseer ne d last man aduniya, but yau for the first time ganinshi cikin tsakiyan daren nan yazo yabi wannan hanyan tundaga Abuja yazo nemanta bayan he came to her rescue earlier today yasa ta tsareshi da idanu tana tambayan zuciyanta could Baban Yaseer be the man she just finished asking God for? Is Allah testing her? Mijin best friend dinta? She rather hakura da auren gabaki daya aduniya tayi alahira, sosai take kallonshi hankalinshi amugun tashe yake buga kofan ganin yanda take kallonshi yana Hawwa open, kusan 2min tadauka tana kallonshi kafin gently ta danna lock motan yayi unlocking kanshi yabude motan da sauri yaduko yana kawo fuskanshi daidai nata cikeda tsantsan so da kulawa da damuwa yace “Hauwa’u! Are you okay?” Tsare shi da idanu tayi sai kawai hawaye ya gangaro daga idanunta dasauri yashiga ciro handky daga aljihunshi jikinsa har rawa yake yace “don’t cry and don’t be afraid I’m right here, Aliyu is here”. [9/18, 5:03 PM] M Shakur: 💫GARGADAN SO💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣4️⃣ LUKUKU GENERAL ENTERPRISE gidan spices kenan da abubuwa daban daban, babu kalan spices din da basuda shi, tundagakan su ginger, garlic, tea different kind da sauransu, this is tasted and trusted brand, chat them up kisai spices now!!!!! wa.me/+2348095660030 EPISODE 2️⃣4️⃣ Kawai tausayi taji tabama kanta saisa takasa rike hawayen dan tana cikin jarabawan rayuwa, she’s 30 batai aure ba babu miji, kowa is pressuring her, her biggest support, her biggest fan is her best friend Ni’ima da tun suna yara suke tare, kawancen amana da iyayensu sun zama daya ma, she’s not a small girl when she sees love she knows love, wani irin kaddarane wannan? Baban Yaseer can never be her amsa nooo please Ya Allah not my best friend’s husband, ganin hawaye yakasa tsayawa daga idanunta asanyaye Aliyu yace “I’m here for you, I will forever be right here! Ina taredake Hawwa in good times and bad times, dare da rana, I’m right here” ahankali yadaura hanky kan fuskanta wani sanyi taji dayasa ta lumshe idanunta da sauri takai hannunta i ta karbi handky tana goge fuskanta, tadanja majina dadan ragowan karfin zuciya tace “maisa kabiyoni Baban Yaseer? Nace kabiyoni ne must u follow me everywhere? Must you get involved in my issues? An gayamaka I can’t take care of myself ne ko I need your protection”? Ataushashe yana kallonta ganin ranta abace, cikida zazzafan kauna yace “sabida bazan taba iya bacci ba bayan nasan kina irin wannan hanyan, I care for you” ahankali Hawwa tace “wat if something happens to you”? Asanyaye yace “I don’t care koma menene yasameni I just wanna keep u safe” abu tahadiye a wuyanta sai kawai ta juyo ta yunkuro tace “I need to change my tire, spare tire na booth” matsamata yayi tafito tai booth yabi bayanta tana bude booth din takai hannunta zata dauki tayan yarigata dauka yace “let’s go muje motana ki zauna” tsayawa tayi tana kallonshi, “muje dan Allah Hawwa dare ne mu kadai a titi” batai musu ba yayi wajen motanshi da ita yabude mata gaba ta shiga ta zauna ya maida yarufe sannan yadawo booth nata yaciro supanu yaje gaban motan yana kwance tayan dayay less, sosai Hawwa take kallonshi kaman yauta fara ganinshi abubuwa da dama suna yawo aranta, tana zaune awajen saiga yan sanda sunzo wajen fitowa tayi ta nuna musu ID card dinta tayasu gyara tayan sukayi, suna gamawa Baban Yaseer yabar musu motanshi yabasu kudi su tsaremai sannan yashiga na Hawwa, hakan yasa ta zagayo ta zauna ya kunna motan yaja waje tajuyar da kanta tana kallo ahankali yace “do you think is right kije kidan Anty ki middle of the night? Kodai idan mukaje zaria namiki booking hotel, idan gari yawaye saikije”? Tana kallon waje batare data juyoba tace “zan iya zuwa wajen Ammi na anytime anyday” gyadamata kai yayi bai sake magana kusan 30min sai chan yace “Hawwa it’s okay not to be okay” lumshe idanu tayi tabude anatse yace “you got this! Karki bari kalaman Baba natabaki, karki karaya, I hate seeing you like this” yadan kalleta yanda take kallon waje yace “kinji” gyadamai kai tayi daganan basu sake magana ba harsukakai zaria, nunamai hanya tadingayi har zuwa wani gida a wani anguwa mai dan kyau da mutunci, saukowa tayi ta zagayo tadan kalli Baban Yaseer dake kallonta tace “dan bani car key” zare key motan yayi yabata yana kallonta, a gate tasaka wani key dake jikin motan tabude kofan tashiga ciki tana sallama tsakar gida ne mai fadin gaske, tourchlight taga an haskewa taji muryan yan dattijuwa na “waye awajen gate din nan” ana bude kofa da gudu Hawwa tai wajen kofa matan na bude kofa dadan charbi a hannu Hawwa ta rungumeta da karfi tace “Ammiiii na” ririketa matan tayi tace “Hasbunallahu wa ni’imal wakeelu Hawwa kece da daddaren nan, ke tashi kiga na ganki lafiya Hawwa” tadago Hawwa daga jikinta murmushi Hawwa tayi tace “Ammi baban Naseer na waje bani key gate na bude ya shigo da mota saiya dan zauna zuwa safiya yakoma Abuja” wani dan kallo Ammi tamata tace “Baban Yaseer kuma? Aliyun Ni’ima”? Gyadamata kai Hawwa tayi Ammi tabata key fita tayi Ammi itama tafito tana haskawa bude gate din Hawwa tayi yashigo da motan ta maida gate din tarufe Ammi tace “maraba da Baban Yaseer, sannunku sauko sauko” Saukowa yayi kanshi akasa cikeda kunya yace “Ammi mun sameku lpy” cikeda fara’a tace “Alhamdulillah ina jikokina? Da y’ata Ni’ima hope duk suna lpy”? Akunyace ya gyadamata kai yace “Alhamdulillah” murmushi tayi tace “muje nakaika side din su Baffa ka kwanta bazakabi hanya da tsakar daren nan ba sai idan Allah ya kaimu da safe akawo maka abinci ne”? Dasauri yace “a’a Ammi dare nayi bana iya kara cin abinci” satan kallon Hawwa yayi dake gefen Ammi tana wasa da hannunta yamika mata car key ta yace “take” dan dagokai tayi kafin tasa hannu ta karba Ammi tace “muje” suka wuce suna hira itakuma tawuce wajen motar ta booth taciro akwatinta ta gu huri ta shiga dashi ciki, bayin Ammi tafada tana cikin wanka Ammi tashigo tasami waje ta zauna yanda ta ganta haka tasan dawani abu. Towel din Ammi ta dauro tafito Ammi ta kalleta tace “zonan Jidda” kayan shafanta tadauka tazo kusada Ammi ta zauna tana bata cream dinta a hannu Ammi ta karba tana sauke ijiyan zuciya tace “meya faru?” Dan shiru tayi sabida kawai taji komi yadawo mata sabo, hannunta Ammi takama tana shafa mata mai kafin takalleta strictly tace “ya akayi kike tare da mijin kawarki at this type of time and day Hauwa’u”? Baki tabude zatai magana saikuma tadan sauke ijiyan zuciya Ammi tace “speak” anatse tace “Ammi wlh I don’t know cus ni ko kiran Ni’ima ma banyi da abun yafaru ba, probably Baba ne yakirasu to check ko ina gidansu, saita kirani daga gayamata ina hanya zanzo wajenki hala to shine ta turoshi” Ammi na kallonta ta sauke ijiyan zuciya tace “Hawwa babu wani naki dabaisan relationship dinki da Ni’ima ba, yarinyar nan kawar amana ce, yanda kika daukeni haka tadaukeni, don’t ruin friendship naku under no circumstances, you know maganan danake” gyadamata kai Hawwa tayi tace “nasani Ammi” saikuma ya tashi daga gadon ahankali zuwa akwatin nata tadauki dogon riga na bacci tasaka ta zare zanin wankan ta shanya ta dawo gadon tahau ta daura kanta kan cinyan Ammi tareda sauke ijiyan zuciya tabude watsapp tama Ni’ima chat “Just got to Ammi’s place, Ni’ima why did you send Baban Yaseer? Why” tura chat din tayi taga yayi layi biyu alamun datan ta a kunne amman ba’a budeba jira tayi ta amsata but shiru ijiye wayan tayi ahankali tana lumshe ido kafin kaceme bacci yayi awon gaba da ita dan tagaji yau. Yanda bacci ya shigeta yasa Ammi bata tadataba ta shiga dakin yammatan ta su biyu Amina da Ramla ta tadasu don salla itama tayi sannan tasa suka shiga kitchen cus taji Baban Yaseer yafice salla. Wuraren 7 yashigo gidan a tsakar gida yaga Ammi tareda Ramla datake gwadama yanda ake buga kosai sun hada gawayi dan basu soya kosai a gas, ganinshi yasa Ramla tace “ina kwana Baban Yaseer” murmushi yamata yace “lpy lau” yace “ina kwana Ammi” murmushi tamai tace “an tashi lpy sannu da kokari fa Aliyu, Allah ya maka albarka, bari yanzun nan zan kawoma kosai nariga an dama kamu saina kawoma kayi karo kafin kashiga hanya” girgixakai yayi yace “no Ammi bazanyi kari ba bana kari da wuri yan sanda na barma motana chan hanyan kaduna dole nafita yanzu Ammi” yayi maganan yana ciro kudi daga aljihunsa daya samo a ATM fitan nan nasa a kujeran tsakar gida dake gefen Ammi ya ijiye kudin yace “aba Hawwa idan ta tashi, wannan kuma aba su mai girki” cus baisan sunan Ramla ba, hade fuska Ammi tayi tace “kaga dauki kudaden nan karna saba maka Baban Yaseer” dasauri yajuya yayi gate yace “Ammi nagode” yafice dasauri dudda har ranshi yaso yaga Hawwa kuma sarai ta tashi tun dazu har salla ma tayi kawai bataso ta ganshi ne kawai yasa bata fitoba, tanajin fitanshi tafito falo Amina dake gyaran falo na ganinta tai ihu sosai “Ramla Ya Hawwa ta tashi” tawani zo dagudu tai tsalle tafada jikinta Hawwa tai dariya sosai Ramla tasaki kosan datake ta rugo dakin aguje itama tai tsalle kawai Hawwa tai kasa suna kanta, Ammi ta shigo dakin ta kwadamusu duka abaya tace “Oya ku dagamin ita bance ku karyamin diya ba” kankamesu Hawwa tayi tace “Ammi I missed my babies” hararansu Ammi tayi tawucewarta tafito tashiga soya kosan da kanta tunda taga shirme suke Hawwa tafito tareda su tana Ammi wai ina su Hamza da Ahmadu? “Hamza na school, Ahmadu yace anjima zaizo da matarsa su gaidake, Baffan ku na dayan gidan sai gobe zai dawo nan amman hala anjima ki gansa” murmushi tayi ta karbi kosan tana soyawa su Ramla nabata labari she looks so happy Ammi tayi murmushi ganin ayanda idanunta sukadan kumbura jiya sabida kuka sun sauka sosai yanzu kaman batayiba. Wuraren 12 Ni’ima taji ana bude gate, tunda tasan Hawwa bata taba taga miss call na Hawwa taki kiranta back ba sai yau, nor tai replying message nata, jiya tamata message shiru, da safen nan takirata sau biyu ba amsa sai tamata magana tace “call me idan kin dawo daga hospital Best, su Ramla nata tambayanki”. Jin ana bude gate yasa ta tashi dagakan kujeran tawuce da sauri tashiga kitchen, ita kadaine agidan su Yaseer na school sai though 1 suke tashi on Friday, sallama taji yayo yashigo abu kawai taji yatokare mata zuciya tama kasa amsa sallaman, kofan bedroom nasu taji yabude ya shiga sannan tasauke ijiyan zuciya tashiga fito da flasks da plates tana ijiyewa a dinning tazauna a dinning din saikuma chan tamike tawuce bedroom din nasu ta zauna bakin gado tanajin karan zubam ruwa ba’a wani jimaba yafito daure da towel a waist yadan kalleta hada idanu sukayi tana kallonshi kaman yau tafara ganinshi dauke kai yayi da sauri yawuce wajen wardrobe nasu yace “wife ya gida? Su Yaseer basu dawo daga school ba”? Tana kallonshi kaman gunki tace “basu dawo ba tukunna” gyadamata kai yayi ya tsaya gaban mirror yadau mai yana shafawa yakasa wani maganan, kalulu ta hadiye a wuya tadan bude bakinta kadan saikuma tarufe sai chan kuma tace “ka kuwa sanar da Hawwa kana sonta?!” Dum! Haka maganan yadaki kunnenshi man daya diba zaikai jikinshi yashafa kasa shafawa yayi yajuyo yakalleta suka hada ido yace “wace irin magana haka kikeyi Ni’ima”? Mikewa tayi a fusace ta nunashi da hannu tace “don’t you dare lie to me, nasan son Hawwa kawata kake why are you hiding it? Eh maisa kake boyewa bayan ka kamu da mugun sonta” hade giran sama dana kasa yayi yadan dafe kanshi yace “kinsan mene? I don’t want your drama this afternoon I had a long journey I just want to sleep peacefully, dan Allah ki kyaleni I don’t know wat you are talking about” yajuya zai wuce yanda abu kecin zuciyan Ni’ima batasan sanda tai ihu ba tace “Namiji munafuki, namiji mara amana, namiji butulu! Aliyu I know everything! I know about hotunan Hawwa dake wayana da duk ka sace suna wayanka, I know kana stalking friend dina kana biye biyenta kana mata hotuna without her knowledge, how dare you kana karyata cewa sonta kake don’t be a coward, kaji be a man for once mayaudari kawai” “Ni’eematullah!” Baban Yaseer yakirata azafafe idanunshi sun kada sunyi ja, yace “yes yes yes I love Hawwa! Yes inason kawarki! Yes I love your best friend Ni’ima and so what!?” Hannu Ni’ima takai tadaura kan bakinta tana kallonshi completely heart broken hawaye masu jarababben zafi na saukowa daga idanunta, yace “do you think I’m happy with the fact that I’ve fallen in love with your friend? Kin dauka choice dina ne? Kokin dauka son Hawwa ya tambayi izinina? Why are you insulting me calling me names mena miki? Tayaya na yaudareki? Kinga na sanar da ita ina sonta ne? Ko kinga nayi wani abu ne? I love Hawwa yes and I also love you! Sabida I don’t wanna hurt you saisa all this years ban auri Hawwa ba, I can’t bring kaina into to hurting u that much, nasan yanda zakiji, I know wat kishi is! Yes I love Hawwa, and I also love Ni’ima, nima I don’t know mesa Allah zai dauramin soyayyan kawaye biyu kuma best friends, I know this same reaction kikeyi maybe na gayama Hawwa ina sonta zatamin more than yours, so just let me be, ban miki komiba ban yaudareki ba, and bance zan auri Hawwa ba cus nasan bazata yardaba, but all I know is harna mutu bazan taba daina son Hawwa ba, son danake mata yawuce tunani na, when it comes to Hawwa banmasan me nakeyi ba, I just want her to always be happy, I want to protect her, and always be there for her and make her happy, that’s just it” yayi maganan yana komawa wardrobe yadauki kayan dazaisa yafice daga dakin, Ni’ima tafashe da kuka bana wasaba gwanin ban tausayi tana zubewa akasan dakin……. TOH JAMA’A IMAGINE MIJINKI NA SON BEST FRIEND DINKI, YAYA ZAKIJI??? HOW WOULD YOU HANDLE THE SITUATION??? KAI YAYA ZAKIYI NE???? IDAN KECE NI’IMA MEZAKAYI KO YAYA ZAKIYI DA HAWWA??? THINK AND TELL ME🥰 [9/18, 5:03 PM] M Shakur: 💫GARGADAN SO💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣5️⃣ FOLLOW MY WATTPAD ACCOUNT AKWAI FREE COMPLETE NOVELS DAYAWA AWAJEN KUSHA KARATU💃 https://www.wattpad.com/user/MSHAKURworld?utm_source=ios&utm_medium=link&utm_content=share_profile&utm_campaign=invitefriends&wp_page=home&wp_uname=MSHAKURworld Ni’ima kuka kawai take bana wasaba, tana ganin tunda aka haifeta bata taba feeling wannan kalan zafin da zuciyanta kemata yauba, for years sunyi aure itada Baban Yaseer basu taba having issues ba like babban issue haka, batada wani complain akanshi but yau yayi hurting nata kwarai, kalan soyayyan datagani a idanun Aliyu ko ita baitaba mata shi ba, duk soyayyan dazaisa kafara stalking mace kana bibiyan hotunanta harda na kusan tsiraici ma dan kayan bacci ne ba karaman soyayya bane, soyayya ce ma dakana bukatan kaga therapist, he is sickly in love with Hawwa that’s idan akwai word din, ciwon son Hawwa yake, yanzu Hawwan ta Baban Yaseer zaiso? They’ve been through so much together with Hawwa, Hawwa is her biggest support bazata taba manta sanda Hawwa tasayo mata form na school of Nursing takawo mata ba, sabida lokacin Babanta baida lpy basuda kudin daza’a saimata form agida haka Hawwa tadinga dinki tahada kudin tasayo mata form 5k takawo mata that day was the happiest day of her life, Hawwa tarakata taje tai entrance exam na shiga school of nursing din, dataci Hawwa was happier than her ma datai jarabawan, bayan 2days aka kirata zuwa interview still Hawwa tabita sukaje tajirata awajen tayi tafito suka tafi gida dagabaya aka saki admission taci an bata admission, babu kudin registration Hawwa tadinga dinki day and night, tasaida babban wayanta alokacin tasa sim nata akaramin waya takawo mata 30k itama Maman Ni’ima tasaida sarkanta da dankunne aka hada 20k daga wajenta aka hada mata taje tai registration da 50k, the first ever book da pen datai rubutu dashi a school of nursing Hawwa ta siyamata su, hawaye ta share tana tuna rayuwansu da Hawwa duk yanda mutum zaiyi tunanin friendship, kawancenta dana Hawwa yawuce haka, sabida kawance ne mai asalin amana, Hawwa harda Maman Ni’ima take fada akanta just like yanda take fada da Baba akan Hawwa tanajin haushinsa kan Hawwa haka sukema junansu wajen iyayensu, they supported each other like better half, kawance su babu ha’inci, babu kyashi ko rowa, babu bakinciki, they’re always happy for each other, dudda tayi aure Hawwa bata taba mata bakincikin wani abuba, datana da ciki wlh wlh ko Baban Yaseer mai cikin baikai Hawwa kula da ita ba, idan tana craving wani abu Hawwa zata iya barin aiki taje ta nemo takawo mata, yanzu haka yaranta su Yaseer sun fison Hawwa kan mahaifiyarta grandmother su sabida aminci da kaunan dake tsakaninsu, she’s just crying bitterly bamatasan ina zata saka kanta ba, kawai taji ta bama kanta tausayi bamatasan inda zatasa kanta ba wannan wani irin intertwine situation ne haka? Wani irin kaddara ne wannan? Ita da Hawwa started friendship ana maganan tun suna around 6yrs old cus primary one suka hadu, yanzu suna 30yrs, 20yrs plus friendship kifa kanta tayi akafanta tana shesheka tajiyoshi an budemai gate yafita tasan mosque zashi yau juma’a. ** Har yamma na rannan Friday din nan shiru ba kiran Ni’ima which is so unlike her, dudda su Ramla dake damunta da labarai but still binibini Hawwa na duba wayanta ko Ni’ima tamata watsapp message ko kira ko wani abun amman shiru, tasake kira but still ba amsa dan damunta abin yafarayi sosai. Bayan sallan magrib suna zaune sunacin abinci duka tare harda Hamza wayan Ammi yahau ringing wayan ta kalla taga Baba ne hakan yasa tadauki wayan tafito daga dakin dan bataso yaran especially su Ramla susan maisa Hawwa tazo tawuce ta shiga side nasu Hamza zama tayi kan katifarsu tayi dialing number Baban ringing daya yadaga ya buga mata sallama yace “ya wajen naku Rukayya” Ammi tace “Alhamdulillah” ijiyan zuciya Baba yasauke yace “Baban Yaseer ya sanar dani Hawwa na wajenki kice mata ni ban koreta ba ta tattaro tadawo gidan nan” anatse Ammi tace “sabida kacigaba da tallatata a masallaci kana neman kai da ita” dan shiru Baba yayi saikuma chan yace “kinga Rukayya ni ba kira nayi fada dake nayi ba, tun fadanmu na farko bayan rasuwan mahaifiyan yarinyar nan kikaso tafiya da ita nace a’a kika dinga bala’i dani nasan ba kaunata kikeba da akwai yanda zakiyi ma da rabani zakiyi da yarinyar, ni duk wannan ba itace matsalata ba kawaidai kice mata tadawo gida kar fushina yabita” dan sauke ijiyan zuciya Ammi tayi tace “yarinyar nan kawai sabida kaine mahaifinta saisa muka barmaka, wlh

Chapter 10 of 35