tun da haka suka zaɓawa kansu ai shike nan, amman yana tausayawa Zareenah, ba komai yake jiye mata ba nan gaba, domin kuwa dukkaninsu basu da tabbacin abin da zai faru a gaban."
EL MU'AZZ
Yana ajiye Sulaiman ya juya zuwa asibitin da aka yiwa Zareena aiki tun da ya doso ɗakin da aka kwantar da ita yake jiyo muryar mahaifiyarta tana ta masifa, dan haka ya dakata bai shiga ciki ba.
"Kin cuci kanki Zarina, kin wulaƙanta rayuwarki, ba baki nake miki ba amman ina da yaƙinin akwai ranar da zata zo sai kin zubar da hawayen nadamar abin da kika aikata,nadamar da zata kasance mara amfanin a gare ki, wallahi da na san abin da zaki aikata kenan bazan barki ba, amman saboda kada na hana shiyasa kuka ƙulla kuka rufe ke da mijinki da mahaifinki, saboda duk ƙwaƙwalwarku ta kifaye ce, idan shi baya son jikokin ai ni ina so ke kaɗai Allah ya mallaka mana ai dole zamu so ganin wani abu da ya fito daga gareki amman soyayyarki ta rufewa mahaifinki ido ya kasa gano hakan ai shikenan,duk zakui nadama ranar da shi mijin naki ya buƙa ci haihuwa ya kawo wacce zata haifa masa."
Tun da ta fara faɗan ba ta faɗi kalmar da ta girgizata ba irin kalmar nan tata ta ƙarshe ai kwa ta saki wani uban ihu haɗe da faɗin.
"Ammi dan Allah kada ki mini baki, ya riga yayi mini alƙawarin bazai mini kishiya ba,in fact ban yankewa kaina wannan hukuncin ba sai da yayi mini wannan alƙawarin."
"Zarina kenan, gata da soyayyar da aka baki yasa sam ƙwaƙwalwarki ba ta aiki,idan El yayi miki alƙawarin bazai miki kishiya ba shi ke da ikon kansa?
Ko kwa tafiyar rayuwar a tafukan hannunku take?
Ko kwa daga sama ya faɗo?
Idan shi ba ya buƙatar 'ya'yan ai iyayansa zasu so ganin jininsa ko kwa zuba muku idanu zasu cigaba da yi?"
Wani gumi ne ya zirarowa Zarina ta shiga kurma uban ihu iya ƙarfinta, mahaifinta da ke gefenta ne a zaune ya shiga rarrashinta haɗe da rufe Ammi da faɗa ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba,duk da jikinsa yayi sanyi da maganganunta, amman ai baici tazo tana gaya mata wa'yannan magan ganun ba a yadda ake buƙatar lafiyarta yanzu, shi fa soyayyar Zarina na rufe masa idanu a abubuwa da dama wan da sam baya lissafi yake biye mata su aikata wani abun,kamar dai yanzu da haka ta kasance.
Ƙarar turo ƙofar da aka yi yasa Zarina buɗe idanuwanta da ta rintse tana kuka Abie na faman rarrashi, akan EL suka sauka daman tasan shine saboda jin mayataccen ƙanshinsa da ya kaiwa ƙofofin hancinta ziyara.
"Yauwwa bie, zo dan Allah ka gayawa Ammi ta daina yi mini baki, kayi mini alƙawarin baza ka mini kishiya ba, kuma baza ka gayawa mahaifanka cewa na cire mahaifata ba."
Lumshe idanuwansa yayi kafin ya warasu akan Ammi, kamar bazai magana ba kafin can kuma yace.
"Ammi dan Allah komai ya wuce."
Numfashi ta sauke me nauyi kafin tace.
"Ai shike nan, na bar wannan maganar daga yau, dama ai shishshigi na ne tun da ba'a saka da ni ba."
"Afuwa Ammi, mun yi kuskure."
"Ya wuce."
Ta faɗa tana jin ciwon abin da Zarinan ta aikata, ciwon da ta tabbata bazai taɓa warkewa ba, da ace tana da wasu yaran to ta tabbata abin zaizo mata da sauƙi to ba bu Zarinan dai ita ce wacce ta kassara rayuwarta dan ita da haihuwa hai hata hai hata.
Ta rasa wannan makauniyar soyayyar da Abie ke wa Zarina da har tasa yake biye mata a dukkan abin da ta nuna tana so ko da ba akan daidai ba ne, duk da kasancewar ta ƙwara ɗaya da Allah ya basu ba ta cancan ci irin wannan soyayyar ba mai rufe idanuwa, ba haka ta so tarbiyyantar da 'yarta ba ko kaɗan sai dai ba yadda za tayi da Abie da yayi uwa yayi makarɓiya da kuma samun goyan bayan Zarinan tun da komai za tayi mata ita a gurinta a zuwan takura ne.
SULAIMAN
Yana shiga sai da ya fara kiran wayar Najj suka ɗan taɓa hira, kafin ya kira Mommy da Daddynsu ya sanar musu ya sauka lafiya,har lokacin ransa maƙale yake da abin da kunnuwansa suka jiye masa EL ya faɗa yana tausayawa Zarina har ga Allah don ta El me sauƙi ce don san da ya buƙaci haihuwa yana iya rufe idonsa ya kawo wacce zata haifa masa, sam ya rasa in da suka aro wannan halin yahudancin su da ke tsakiyar birnin makka cikin larabawa,musamman Zareena da ta kasance haifaffiyar garin tun da shi El zuwo ne, sam rayuwarsu kamar ba wa'yanda ke cikin larabawa ba idan kuna jin labarin rayuwar sakewa to ita EL MU'AZZ ALIYU FANDA ke gudanarwa da matarsa ZAREENA TAHIR ABDUSS SALAM.
Wanka yayi ya gasa jikinsa sosai da ruwa Mai zafi, bayan ya shirya kansa cikin shigar shan iska kana ya bi lafiyayyen gadonsa ya haye ya hau baccin gajiya,dan ya gaji da damuwar Zarinan da ke ganin daidai ta aikatawa rayuwarta ya azawa kansa.
ku kallla."Fatma tace da 'yan tawagarta, gaba ɗayansu kuwa suka juya idanuwansu ya sauka akan Sajda,tana taku ɗaiɗai cike da yauƙi da yanga wan da ya zame mata jiki domin kuwa duk in da gayu yake Sajda tasan gayu ta kuma san ta kansa. Abin da ya bawa su Fatma mamaki ba komai ba ne sai yadda Sajda ta samo mayafin da ya mugun shiga da leshin da ke jikinsu gaba ɗaya,anko ne na class mate ɗinsu, sun zaga kasuwanni da dama haɗe da super market suma da dama amma basu samu mayafin da ya mugun shiga da leshin ba kamar yadda na Sajda ya shiga, abin da suke gudu ya faru (Sajda ta fisu ɗaukan wanka) Har ta gifta su ta ankara da yadda suka zuba mata ido kamar su cinyeta ɗanya, basa shiri shiyasa bata shiga shirginsu, su kullum burinsu su fita ɗaukar gayu amman hakan ya gagara saboda ta fisu sanin takan gayun.
"Lafiya dai ko na ci muku bashi?"
" Muna mamakin yadda akai kika samu mayafin da muka gama karaɗe kasuwanni da dama ba mu samu ba."
"Hmm shine matsalarku?"
"Eh"
"To matsalarku tazo ƙarshe in sha Allah zan haɗa ku da NEEHAL COLECTION daga yanzu wahalar neman mayafai ƙare muku da yardar Allah, dan nima tun da aka haɗa ni da ita na huta, duk mayafan da ake so ana samu a gurinta ko wani irin kala ne, kuma masu kyau da ɗaukar ido cikin farashi mai sauƙi."
"Au wai kina nufin mayafin na gida ne ?"
"Eh mana ɗan hannu ne."
Amma ta iya mayafai maza maza haɗa mu da ita dan baza mu shiga gurin bikin nan ba sai da irin mayafin ki muma mu ƙure gayu.
https://wa.me/message/AD4MDTQJLXIRD1
Ku bi wannan link ɗin zai kaiku in da zakui magana da NEEHAL COLECTION daga yau matsalar mayafai ta ƙare muku zaku samu duk kalar mayafan da kuke so cikin farashi mai sauƙi ina mai tabbatar muku zaku ji daɗin muamala da ita.
Ga masu bukatar a tallata musu hajarsu kofa a bude take cikin farashi mai sauki.
#09037093702/08082007142
#BR
[10/1, 10:01] RASHUNA: BEBEE'ARTH
Wattpad@Rashuna
KANA NAKA
(Allah na nasa )
20
ZAREENA TAHIR ABDUSSALAM
'Ya ɗaya tilo gurin mahaifinta TAHIR ABDUS SALAM (Abie)da mahaifiyarta OUMAIMA OUMAR (Ammei)wan da haifafun Saudi arebia ne za kuma mu iya kiransu larabawan garin.
Sai da suka shekara goma da aure kafin Allah ya basu cikin Zareena,murna da farin cikin da suka shiga ba ya misaltuwa,yayin da haihuwarta tazo musu da buɗi na alkhairi,domin kuwa dukiyar Abie haɓɓaka ta dunga yi kamar ana ƙara izzata,ɗan kasuwa ne wan da yayi fice cikin ƙasashen duniya,kuma gogaggen ɗan bokon da ya wadatu da ilimi ya ratsa shi,wan da hakan yasa yake rayuwarsa tamkar ba balaraben saudiya ba domin kuwa al'adun yahudu da nasara sun shiga jikinsa sun zauna daram wan da zamu iya cewa a gurinsa Zareena ta kwaso nata ɗabi'un.
Wannan buɗi da ya kuma samu a haihuwar Zareenah shi ya kuma makantar da shi a soyayyarta, ba ya ji ba ya gani duk abin da ta nuna tana so sai yayi mata shi ko da ba ya ra'ayin hakan, a haka ya raineta a kuma hakan ta tashi, wan da hakan ke soya ran Ammei domin kuwa ba haka ta so tarbiyyantar da tilon 'yar tata ba, amman rashin mafita ya saka ta kawo ido da kunne ta zuba musu,domin kuwa ba ta samu goyen baya gurin Zareenan ba,ita Zareenan gani take Ammin takurawa rayuwarta take saboda ba ta sonta Abei yafi sonta da ƙaunarta.
Daga pre nursery har zuwa seneor secondary tayi su ne a CALCUTA.Wani babban birni a arewa maso gabacin india.
Daga ita sai nanynta Hussa suka tafi dan Amminta tace babu abin da zai sakata barin ƙasarta ta haihuwa,idan har makarantun da ke cikin Saudiya basu wadacesu ba to itama babu in da zata bi su.
Ba ta da wani buri da ya huce bayan gama secondary ɗinta ta tafi HONG KONG domin cigaba da karatunta domin kuwa tana matuƙar son ƙasar,suna yawan zuwa yawon shaƙatawa da Abei idan ya kawo musu ziyara anci sa'a kuma lokacin suna hutu.
Babu abin da ke burgeta irin abubuwan ƙayatarwa da bugewarsu ba ma kamar Repulse bay hotel da Aberdeen hotel in da zaka ga kifi mai rai irin wan da kake so daga wani tabki da ke kusa a dafa maka shi nan take ba tare da ka ƙagara ba, sai dai kuma shigowar EL MU'AZZ cikin rayuwarta ya sauya mata wannan burin daga ranar da ta fara ɗora idanta a kansa daga ranar taji zata iya ajiye ko wani buri ne domin ta kasance tare da shi.
Tashi tayi idonta na mata ciwo da ƙaiƙayi dama kuma tun tana yarinya tana fama da ciwon idon sai dai kuma yakan jima bai tasar mata ba,to dama anwa Abie ɗinta kwatancen likitan idon da ya fara aiki a Muwadda hospital cike da ƙwazo da nasara har yace zai kai Zareenan ya duba idanuwanta ko za'a dace,sai kuma gashi yau ta tashi da ciwon idon dan haka ya ɗauketa suka nufi asibitin.
Kasancewarsa sanannen mutum babu wani jira ko dogon layi suka shiga office ɗin SULAIMAN ALIYU FANDA,yayin da EL MU'AZZ ALIYU FANDA ke cikin office ɗin yana duba masa idonsa da yau ya tashi yana masa matuƙar ƙaiƙayi,sanye yake da wata arniyar jallabiya blue da ta ƙara haska farar fatarsa ta kuma yi masa masifar kyau,sai kuma baƙar p cap da ta bada damar bayyanar kyakkyawar sumar kansa wacce daga gani kasan ba ƙana nan kuɗaɗe take lashewa gurin gyaranta ba.
Bayan gama duba idon nasa da Sulaiman ya yi ya sanar masa idonsa ba shi da wata matsala, may be dai ko jiya ya daɗe bai bacci ba kuma ya zubawa kansa ruwan sanyi.
Tabbas jiya ɗin ya daɗe bai bacci ba yana ta aiki akan cumpuiter, kafin can cikin dare kuma yanayinsa ya sauya gaba ɗaya,wata gigitacciyar sha'awa ta addabi rayuwarsa wacce bai taɓa tsintar kansa a cikinta ba duk da fahimtar kansa da yayi yana cikin mazaje masu yawan buƙata,tsarewar Allah da kiyayewar sa ce ta kawo shi yau gurin kaucewa dukkan matan da ke bibiyar rayuwarsa.
Sai da ya sakarwa kansa ruwa mai matuƙar sanyi ya kuma daɗe yana sauka tsakiyar kansa kafin ya samu ya ɗan ji dama dama wan da yake tunanin hakan ne ya haddasa masa ƙaiƙayin idon.
"Ka sha wannan maganin bayan ka ci abinci sai ka ɗiga wannan a idanuwan naka sai ka kwanta ka samu bacci sosai, dan Allah yau kar ka fito ka samu ka huta sosai yadda zaka samu sakewa."
Fara maganar Sulaiman ce ta dawo da shi daga zancen zucin da ya tafi ya lumshe idonshi ya warasu kaɗan akan fuskarsa kafin ya miƙa hannunsa ya karɓi magun gunan da Sulaiman ɗin ke miƙo masa a daidai nan kuma Abei ya murɗa handle ɗin ƙofar ya turo ya shigo Zareena biye a bayansa idonta bai fara sauka a ko ina ba sai akan Mu'azz wan da zuciyarta tai wani irin bugun da ba ta taɓa ji tai mata irinsa ba lumshe idonta tayi ta kuma sauke shi a kansa a daidai lokacin shi kuma ya miƙe ya cewa Sulaiman.
"Thanks."
a saman laɓɓansa kafin ya fara takunsa na cikakkun maza zai bar office ɗin ba tare da ya kalli fuskan wanda suka shigo office ɗin ba, yayin da Zareena tai mutuwar tsaye tana binsa da kallo,ganin yana ƙoƙarin barin office ɗin ba ta san san da bakinta ya furta.
"Hey." Ba ganin ko juyowa bai yi ba bare ya nuna ya jita yasa ta saurin zuwa ta sha gabansa yana gab da isa bakin ƙofar,a jikin ƙofar ta jingina ban da haka kusacinsu zai yi kusa sosai duk da haka suna jiyo ƙamshin turaran junansu da ya fara saukar musu da kasala,barema Zareena ta ji labari dan ƙamshin turaran El ɗin ya taimaka ƙwarai gurin ƙara matar mata da jiki da jin ƙaunarsa na narkar da jini da jijiyarta.
Bugu zuciyarta ke yi tana tsalle a ƙirjinta amman haka tayi ƙundin balar miƙa masa kyakkyawan farin hannunta dan idan ta bari a yau ya kubfce mata ba ta san inda zata samo shi ba wanda hakan ke nufin hautsina kyakkyawar rayuwar da take gudanarwa.
"ZAREENAH TAHIR ABDUS SALAM."
Ta faɗa tana ƙarewa kyakkyawar fuskarsa kallo,idanuwansa ya sauke a kanta wanda har lokacin basu koma ainihin yadda suke ba,cike suke da buƙatar wanda zai ɗebe musu abinda suke ji cikin jini da jijiyarsu.
Kallonta yake sosai kallon da bai taɓa yiwa wata mace makaman cinsa ba ko don halin da yake ciki ne,ko kuma kyahun Zareena da kyahun surarta ke fisgarsa oho?
Zareenah kyakkyawa ce sosai kyawun da yakai a kira shi da kyau,kyawun da ta yo gadonsa gurin iyayanta har ta so ta zarta su a kyau,farinta har wani shaiƙi yake yana ɗaukar idon mai kallonta.
Har ta fara sarewa zai kulata ganin yadda yayi bakam da ita,kallon da yake mata ma ba ta ankare ba saboda na ƙasan ido yake mata sai dai tana jin yadda jikinta yake mata rawa sosai,yayin da Abie da Sulaiman suka zuba musu ido suna ganin sarautar Allah.
Kyakkyawan farin hannunsa wanda ke cike da gargasa baƙa wuluk tana zuba shaiƙi ya miƙo mata yayin da ta saki kyakkyawan murmushin da ya bayyana kyawawan haƙoranta farare tasss da suka ƙara ƙawata kyakkyawar fuskarta ta sanya hannuta cikin nasa wanda a lokaci ɗaya suka ji sauyawar yanayin jikinsu musamman ma shi da yake cikin halin buƙatuwa dan haka da sauri ya zare hannunsa daga cikin nata kamar anai masa dole ya furta.
" EL MU'AZZ ALIYU FANDA."
Murmushi tayi kafin ta furta.
"Nice name."
Ta buɗe hand bag ta ciro wani kyakkyawan kati ta miƙo masa,kamar bazai ansa ba sai da ya gama shan ƙamshinsa kafin yasa hannu ya ansa, can ƙasan maƙoshi ya furta."Ba ni hanya na wuce."
Tana bin fuskarsa da ke kuma matar da ita cikin soyayyarsa ta lokaci guda ta matsa ta bashi hanya kafin ta furta.
"Pls ina jiran kiranka."
Ba tare da ya nuna alamun ya jita ba yasa kai ya bar office ɗin yayin da Sulaiman ya sauke ajiyar zuciya cikin ransa yace.
"Ki ma godewa Allah da kika samu ya saurareki har ya haɗa hannu da ke daga dukkan alamu shima yana da interest a kanki."
Ita ko Zareena gurin Abei ɗinta da ke tsaye ta nufa ta rungumesa haɗe da lumshe idanuwanta cikin kasalalliyar muryar da soyayyar El ta saukar mata da ita tace.
"Abei ina son shi,wallahi Ina ƙaunarsa Abei ka ji zuciyata."
Ta kamo hannunsa ta kai saitin in da zuciyarta ke mugun bugawa.
"Subhanallah, ina burin karatun naki Baby?"
"Na ajiye shi daga yau Abei aure nake so ba da kowa ba kuma da shi,idan yaso karatun ya biyo bayan komai."
Numfasawa yayi, kafin yace.
"To zauna likita ya duba ki tukunna idan munje gida ma ƙarasa maganar."
Murmushi tayi a ranta tana jin daɗin wannan ciwon idon da yayi sanadiyar haɗuwarta da El kafin ta ƙarasa gaban kujerar da aka tanada dan zaman mara lafiyar da zai gana da doctor, yayin da Sulaiman da Abei ke gaisawa yana masa bayanin ciwon Zareenan ita kuma idonta ya sauka a in da sunan doctorn ke rubuce.
Sulaiman Aliyu Fanda. nan tayi rewending sunan da El ya gaya mata.
"El mu'azz Aliyu Fanda. Murmushi tayi yayin da ta fahimci 'yan uwa ne da wannan likitan ko ba komai ta samu yaƙinin ko bai kirata ba tana da tsanin da zata hau ta lalubo shi.
Magani itama ya bata na sha da na ɗigawa ya kuma ce ta rage ta'ammali da ruwan sanyi,dan kwa gwana ce gurin wasa da ruwan sanyi,duk tsananin sanyi wanka ma da ruwan sanyi take kuma duk wani abu na sha ba za ta sha miki shi dalan dalan ba sai mai matuƙar sanyi shiyasa wani zubin Ammi takan kirata da kwaɗuwa gurin son wasa da ruwa,dan zata iya wuni cikin swiming ba tare da damuwar komai ba.
A mota ban da zancen El babu abin da takewa Abei,suka je gida ta ɗorawa Ammi ma har sai da ta gaji ta hau ta da faɗan rashin kamun kai da kunyar da aka san ɗiya mace da ita.
Sai da Abei ya shiga ciki ya nuna mata cewar ai ba laifi ba ne don mace ta nuna tana son namiji da zata hauta da faɗa ai ba kanta farau ba kuma kanta ƙarau ba asali ma sunna ta daɓɓaka tun da hakan ya faru da Annabi Muhammad (S.A.W) da matarsa ta fari Sayyadatuna Nana Khadija.
Tun daga nan ta kawo ido ta zuba musu kan lamarin El da shi da 'yar tasa dan taga alamun anan ɗinma bayanta zai bi gurin yi mata auren da ta nuna tana so duk kwa tsananin so da burin zurfaffan ilimin da zai bawa Zareenan da ya ci a kanta....
"Ku kallla."Fatma tace da 'yan tawagarta, gaba ɗayansu kuwa suka juya idanuwansu ya sauka akan Sajda,tana taku ɗaiɗai cike da yauƙi da yanga wan da ya zame mata jiki domin kuwa duk in da gayu yake Sajda tasan gayu ta kuma san ta kansa. Abin da ya bawa su Fatma mamaki ba komai ba ne sai yadda Sajda ta samo mayafin da ya mugun shiga da leshin da ke jikinsu gaba ɗaya,anko ne na class mate ɗinsu, sun zaga kasuwanni da dama haɗe da super market suma da dama amma basu samu mayafin da ya mugun shiga da leshin ba kamar yadda na Sajda ya shiga, abin da suke gudu ya faru (Sajda ta fisu ɗaukan wanka) Har ta gifta su ta ankara da yadda suka zuba mata ido kamar su cinyeta ɗanya, basa shiri shiyasa bata shiga shirginsu, su kullum burinsu su fita ɗaukar gayu amman hakan ya gagara saboda ta fisu sanin takan gayun.
"Lafiya dai ko na ci muku bashi?"
" Muna mamakin yadda akai kika samu mayafin da muka gama karaɗe kasuwanni da dama ba mu samu ba."
"Hmm shine matsalarku?"
"Eh"
"To matsalarku tazo ƙarshe in sha Allah zan haɗa ku da NEEHAL COLECTION daga yanzu wahalar neman mayafai ƙare muku da yardar Allah, dan nima tun da aka haɗa ni da ita na huta, duk mayafan da ake so ana samu a gurinta ko wani irin kala ne, kuma masu kyau da ɗaukar ido cikin farashi mai sauƙi."
"Au wai kina nufin mayafin na gida ne ?"
"Eh mana ɗan hannu ne."
Amma ta iya mayafai maza maza haɗa mu da ita dan baza mu shiga gurin bikin nan ba sai da irin mayafin ki muma mu ƙure gayu.
https://wa.me/message/AD4MDTQJLXIRD1
Ku bi wannan link ɗin zai kaiku in da zakui magana da NEEHAL COLECTION daga yau matsalar mayafai ta ƙare muku zaku samu duk kalar mayafan da kuke so cikin farashi mai sauƙi ina mai tabbatar muku zaku ji daɗin muamala da ita.
Ga masu bukatar a tallata musu hajarsu kofa a bude take cikin farashi mai sauki.
#09037093702/08082007142
#BR
[10/3, 20:47] RASHUNA: BEBEE'ARTH
Wattpad@Rashuna
KANA NAKA
(Allah na nasa )
21
KANA NAKA FREE NOVELL NE.
Yanzu nake typing nasa shi yasa wani zubin kuke samun delay kafin nayi post saboda abubuwan rayuwa aka ce yau da gobe ta fi ƙarfin wasa Ma su buƙatar compleet ni kaina ba ni da shi ku biyo ni a sannu har mu cimma ga cinyewa mu siɗe gaba ɗaya.
Da ƙyar ta ga wucewar kwanaki biyar tana jiran tsammanin kiran waya daga El amman shiru kike ji tamkar maye ya ci shirwa.A kwana na biyar ɗin ne ta kasa jurewa haƙurinta ya gaza ta nufi asibitin Muwadda.
Direct office ɗin Sulaiman ta nufa, ta same shi ba ya tare da marasa lafiya, yana dai rage aiki a computer ɗinsa,sai da ta zauna akan kujerar da ke gabansa kana ya ɗago kansa ya sauke idonsa kan fuskarta, sarai ya gane ta, amman kwanakin da ya basu ai bai idda cika ba, ko kuma ba ta samu sauƙin idon ba ne?
Ya tambayi kansa,ya kuma bawa kansa amsa da..
"Bari dai to naji me ke tafe da ita ta bakinta."
Hannu ta miƙa mishi su gaisa, ya girgiza mata kai,dan shi irin wannan gaisuwar idan ba da namiji ɗan uwansa ba ba ya yadda yayi da kowa.
Murmushi tayi dan ta gane nufinsa kafin tace.
"Ya ka ke, ya aiki?"
"Lfy Alhmdlillah, da fatan dai ba idon ne ya matsa miki ya sakaki dawowa ba?"
Girgiza kai tayi kafin tace.
"Wannan karan zuciya ce ta matsa mini Doctor,ido tuni ya warke dan na ji daɗin maganin da ka bani sosai."
"Alhmdlillh to haka ake so,amman kuma nan ba sashen masu ciwon zuciya ba ne,idan kika fita daga nan ki tambayi ɓangaran masu ciwon zuciya idan kinje sai ki tambayi office ɗin EL MU'AZZ ALIYU FANDA in sha Allah yadda na baki maganin ciwon ido kika ji daɗi zai baki na ciwon zuciya ki ji daɗinsa fiye ma da haka."
Wani murmushin zallar jin daɗin abun da yazo mata a sauƙaƙe ta saki,kafin ta tashi cike da zumuɗi tace.
"Na gode Doctor, ina da yaƙinin idan na ganshi ciwon zuciyar zai raba ni da ita gaba ɗaya. Allah ya baka abin da kake so duniya da lahira."
Tana kawowa nan ta bar office ɗin cike da karsashi.
Bin bayanta yayi da ido cike da nazarin maganarta sai lokacin ma ya tuna abin da ya faru tsakaninta da EL ɗin ranar nan,ta yuhu abin da ya kawota kenan ta kuma same shi cikin sauƙi.
Kai tsaye ta murɗa handle ɗin ƙofar office ɗin nasa ta shiga wani sanyayyen ƙamshi ne ya doki hancinta da ya samar mata da nutsuwa kaɗan kafin ta sauke idonta a kansa nutsuwar ta zo mata gaba ɗaya.
Sanye yake da wasu arnayen suit blue da sukai matuƙar dacewa da farar fatarsa, ina ga dai ya fuskanci yadda blun abu ke yi masa kyau shi yasa yake saka shi, dan siririn glass ɗin idonsa ma blue ne da yayi matuƙar ƙarawa fuskarsa kyau, fuskar nan a haɗe ba wani annuri yana rubutawa mara lafiyar da ke gabansa magani a jikin kati, kyakkyawan farin hannun nan nasa mai cike da gargasa ɗaure da wani arnen agogo blue shima sai ɗaukar ido yake.
Lumshe idonta tayi ta buɗe ta fara takowa cikin office ɗin cike da kuzari da shauƙin soyayya, a kan ɗaya kujerar da ke gabansa ta zauna haɗe da sauke wawuyar ajiyar zuciya ganin ko in da take bai kalla ba yanawa mutumin da ya rubutawa magani bayani.
Ko da ya gama da shi bayan ya fita ma wata mata ce ta shigo, haka ya dinga duba marasa lafiyarsa ba tare da ya nuna alamun wanzuwarta a gurin ba, ita kam hakam bai dameta ba sai morewa kallonsa kawai take zuciyarta na sanyaya da farin ciki.
Can da ta ji ƙishi ta tashi ta nufi in da ta hango fridge ɗinsa yake ta ɗauko gorar ruwa da lemo da ɗan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 17