ba kurma ba ne."
"Ehh". Nace ina turo baki gaba haɗe da kautar da fuskata gefe.
"Tun da kina son abina,nima ai kina sona."
"Ni dai wallahi ban ce ba." Na faɗa cike da shagwaɓa ina diddire ƙafafuwa kamar wata ƙaramar yarinya, wan da ni bansan ma nayi hakan ba."
"Bina kawai yake da kallo, kafin ya lashi leɓansa na ƙasa,cikin ƙasa da murya yace."
"An jima ki haɗa mini coffe zanzo na karɓa."
Gyaɗa masa kai nayi alamun na ji shi,ganin yana kallona kuma bai sake ni ba yasa nace masa.
"To."
Ina faɗa kuwa ya sake ni haɗe da lumshe idanuwansa yaci gaba da sippisig ɗin kununsa yayin da na fice daga kichin ɗin da mugun sauri....
"Ku kallla."Fatma tace da 'yan tawagarta, gaba ɗayansu kuwa suka juya idanuwansu ya sauka akan Sajda,tana taku ɗaiɗai cike da yauƙi da yanga wan da ya zame mata jiki domin kuwa duk in da gayu yake Sajda tasan gayu ta kuma san ta kansa. Abin da ya bawa su Fatma mamaki ba komai ba ne sai yadda Sajda ta samo mayafin da ya mugun shiga da leshin da ke jikinsu gaba ɗaya,anko ne na class mate ɗinsu, sun zaga kasuwanni da dama haɗe da super market suma da dama amma basu samu mayafin da ya mugun shiga da leshin ba kamar yadda na Sajda ya shiga, abin da suke gudu ya faru (Sajda ta fisu ɗaukan wanka) Har ta gifta su ta ankara da yadda suka zuba mata ido kamar su cinyeta ɗanya, basa shiri shiyasa bata shiga shirginsu, su kullum burinsu su fita ɗaukar gayu amman hakan ya gagara saboda ta fisu sanin takan gayun.
"Lafiya dai ko na ci muku bashi?"
" Muna mamakin yadda akai kika samu mayafin da muka gama karaɗe kasuwanni da dama ba mu samu ba."
"Hmm shine matsalarku?"
"Eh"
"To matsalarku tazo ƙarshe in sha Allah zan haɗa ku da NEEHAL COLECTION daga yanzu wahalar neman mayafai ƙare muku da yardar Allah, dan nima tun da aka haɗa ni da ita na huta, duk mayafan da ake so ana samu a gurinta ko wani irin kala ne, kuma masu kyau da ɗaukar ido cikin farashi mai sauƙi."
"Au wai kina nufin mayafin na gida ne ?"
"Eh mana ɗan hannu ne."
Amma ta iya mayafai maza maza haɗa mu da ita dan baza mu shiga gurin bikin nan ba sai da irin mayafin ki muma mu ƙure gayu.
https://wa.me/message/AD4MDTQJLXIRD1
Ku bi wannan link ɗin zai kaiku in da zakui magana da NEEHAL COLECTION daga yau matsalar mayafai ta ƙare muku zaku samu duk kalar mayafan da kuke so cikin farashi mai sauƙi ina mai tabbatar muku zaku ji daɗin muamala da ita.
Ga masu bukatar a tallata musu hajarsu kofa a bude take cikin farashi mai sauki.
#09037093702/08082007142
#BR
[10/19, 21:18] RASHUNA: BEBEE'ARTH
Wattpad@Rashuna
KA NA NAKA
(Allah na nasa )
25
Ina shiga ɗaki na jingina da ƙofa ina mayar da numfashin da bansan ina riƙe da shi ba haɗe da danne saitin da zuciyata take da har lokacin take harbawa.
Rintse idanuwana nayi na buɗe kafin na furta .
"Ya Allah."
Cikin ƙasa-ƙasa da murya,kafin na ji ringing ɗin wayata ya karaɗe ɗakin,idanuwana na wurga ina neman in da Zuwaire ta ajiyen jakata dan nasan wayar na ciki,aikuwa na hangota kan mirro na ƙarasa da sas sar fa dan kar wayar ta katse.
Ina ganin me kiran na saki murmushi kana nayi peaking da sallama a bakina ya amsa mini da sanyayyar muryar nan tasa kafin yace.
"An dawo daga makarantar?"
"Ban jima da shigowa ba a gajiye,so samu na yi wanka na gasa jikina amman ƙanin nan naka ya tsayar da ni,sai yanzu na shigo,ina shigowa kana kira."
"Ayya,amman Bro bai kyauta ba da ya tsayar mun da ke, yanzu kije ki yi wankan kafin a kira sallah, ko kuma ki bari ayi sallar tun da magaribar ta kawo kai,idan an idar da sallar sai ki wankan, bayan sallar isha zan kira in sha Allah yau mu kwana akan waya."
"Ok tom Allah ya bamu iko."
"Amin cwty."
Daga haka ya kashe wayar ina mamakin ko tambayata abin da ƙanin nasa ya tsayar da ni yi bai yi ba, mutane kala kala a rayuwa, yadda na fuskanci Yaa Sulaiman yana da matuƙar sauƙin kai,rayuwarsa yake me sauƙi,duk da baiwar wakin da Allah yayi masa hakan ba ya damunsa,duniyar sam ba ta dame shi ba,ba shi da tsauri da jin kai irin na ƙaninsa ko kaɗan,halinsu ma ba su zo ɗaya ba,a kyahun sura ma Yaa Sulaiman zai iya ɗara Mu'azz sai dai Mu'azz ya nuna masa gogewar fata da gayu, da kuma buɗewar jiki, dan da ganin Mu'azz siffar sa irin ta ƙarfaffun mazan nan ne ka na ganinsa kasan ya na ɗaga ƙarfe. Amman fa ba ina nufin Yaa Sulaiman ba ya gayu ba,shima yana zuba nasa gayun amman kana ganin Mu'azz kasan ba ajinsu ɗaya gurin gaye ba.
Sai da nayi sallar magariba kana na shiga wanka na gasa jikina da ruwan zafi sosai kana na fito na mutstsika mai na saka khumra na fesa turare, na ɗauko doguwar rigar baccina na saka na saka hula na fito daga ɗakin, dan na fara jiyo rigingimun su Neehal.
Suna falo da Nasreen ta barbaza musu Kay an wasa a gabansu,wannan ya cafo wancan wannan ya cafo wancan suna ta zuba gwarancinsu.
"Exxam ta saka Nasreen ta ƙwace mini rainon twince ɗina."
Murmushi Nasreen tayi kafin tace.
"Kina gama Exxam ɗin kuma ki tattara ki tafi ki barmu tare ba."
"Wa ya gaya miki?ai ƙafata ƙafarsu."
Na kai ƙarshen maganar ina ɗaukar Nimra dan itace kusa da ni aikwa ta hau washen baki.
"Ai wallahi Momy baza ta iya kyautar twince ba,tuni fa suka ƙwacen fadata,yadda kika san a kansu ta fara haihuwa."
"Ta fara haihuwa ko suka fara haihuwa? Ai kin cire Abban,dan ni tuni na sallama musu tawa fadar."
"Au Najjwa har da ke kema?"
Mu ka ji muryar Momy tana nufowa gurin.
"A'a Momy suɓutar baki na yi."
Na faɗa ina dariya.
"Shi kenan kinwa kanki na fasa baki ya yen nasu ."
Sigina Nasrin ta yi mun haɗe da alamun cewar dama na gaya miki baza ta iya baki ba, sai ji mukai Momy tace.
"To munafuka, ko dan ke ai na bawa Najjwa ya yen twince."
Murmushi nayi yayin da Nassren ta turo baki gaba tana.
"Kai Momy nice munafukar?"
Momyy ba ta saurareta ba sai Zuwaire da ta ƙwalowa kira yayin da Zuwairen ta fito daga kicin da sauri ta nufo in da Momy ke zauna ta duƙa haɗe da faɗin.
"Gani Momy."
"Ba'a gama abincin ba ne?"
"An kusa saura ƙiris."
"Ok to maza a hanzarta."
Sai da na jira Zuwaire ta ƙarasa girkin, dambun couse-couse ne da ya ji vegetables da hanta,aka ɗora soyeyyen kifi da coleslow a kai ga ginger drink a gefe,sai da na cika cikina kana na gudu sashen Gwaggo dan na ƙudirci bazan haɗa masa coffe ba shiyasa na gudu kar ma yazo ya same ni a nan dan sam wallahi bana son haɗuwarmu dan ni kaɗai na san abin da nake ji a jikina."
A falo na zauna ina danna wayata, tv na ta zubar gadonta, nasan Gwaggo tana ɗaki tana lazimi sai kuma anyi sallar isha ta gabatar da ita kana zata fito, shi kwa Baffa yana masallaci dan in ya fita sallar magariba dama sai bayan isha yake shigowa wani zubin ma sai ya kai goman dare bai shigo ba idan sun zauna da dattijan unguwar.
Ina nan zaune aka kira sallar isha na tashi na shiga ɗaki na ɗauro auwala na gabatar da tawa sallar na daɗe ina addu'a da nemawa mahaifiyata da kakata rahama gurin Ubangiji tare da dukkan wan da suka rigamu gidanmu na gaskiya kafin na shafa.
Takwas daidai kiran wayar Yaa Sulaiman ya shigo wayata.
Video call yace mini zai kirani ya kashe, jin hakan yasa ni barin hijabin jikina, na hau kan gado haɗe da ɗaukar remort na ƙara ƙarfin Acn.
MU'AZZ
Tun kunun madarar nan babu abin da ya yadda ya sakawa cikinsa,saboda yau yasan yana da coffee ɗin da zai saukar masa da nutsuwa, dan sai ya fanshe na kwanakin da bai sha ba.
Tara da rabi daidai tayi masa cikin harabar gidan Momyn,yayi parking ya fito cikin ta kun nan nasa na ƙasaita ya nufi cikin gidan,knocking biyu yayi Zuwaire tazo ta buɗe cikin yanayin baccin da ya fara fusgarta, tana ganin shine ta bashi hanya haɗe da risinawa tana gaishe shi duk da ta san ba lallai ya amsa ta ba,a tsakiyar falon ya tsaya yana ƙare masa kallo,yayin da Zuwaire ta risina a gabansa tace.
" Momy tun bayan sallar isha tayi mana sallama ta shige, Nasrin kuma ba ta da ɗe da shiga ɗaki ba,wa za'a yiwa magana?"
"Ɗayar "
Ya bata amsa yana mayar da bakinsa kamar ba shi yayi maganar ba kafin idonsa ya sauka akan tangameman hotonta da ke manne a bangon falon.
Zuwaire kuwa ya barta cikin tunanin wa yake nufi,kamar kuma ance ta kalli saitin da yake kalla sai idonta ya faɗa kan hoton Najjwa, lalle gayen nan ɗan rainin wayo ne Najjwan ce bai san sunanta ba ko ya,ko kuma kawai rainin sens ne?
"Najjwa za'a kira?"
Jinjina mata kai yayi, yayin da tace.
"Aikam ina to ta riga kowa bacci a gidan nan,dan tun ɗazu ta yiwa kowa sallama ta tafi sashen Gwaggo yau can zata kwana."
Ranta cike da mamakin me zai yiwa Najjwan yake nemanta da wannan daren.
Juyawa yayi ya fice daga falon yayin da Zuwaire ta mayar da ƙofa ta rufe.
Kansa tsaye ya nufi sashen Gwaggo babu tunanin komai a kansa sai kawai Najjwa ta bashi coffe ɗinsa.
Murɗa handle ɗin ƙofar yayi ga tsammaninsa kuma sai ta buɗe yasa kai cikin falon, tsit falon yake an kashe komai ban da fitilu, tsayawa yayi cak yana ƙarewa falon kallo ba tare da yasan me zai yi da ya kawo ƙafafuwansa nan ɗin ba.
Najjwa
Ba'a je ko ina da fara vidio call ɗin ba na gaji da zama,kwanciya kawai nake biɗa nace ya kashe vidio call ɗin ya kira ni voice call kawai,yace shi sam bai gaji da ganina ba shiyasa ma in sha Allah sai ya yakice wannan weak end ɗin yazo ganina, nace.
"Ni dai kam har ga Allah na gaji da zaman."
Dan ni dai kam idan har an gan ni a zaune aiki nake,ko a makaranta ko kuma in naci abinci ina son ya tsirgan bayan hakan nikam ko da yaushe a kwance nake, Gwaggo ta kan ce mini me karyayyan ƙugu."
"Ya zan yi da ke Gimbiyata? Ai dole na bi umarninki."
Yana kawo ƙarshen maganarsa ya kashe vidio call ɗin kana ya kira muka ɗora daga in da muka tsaya bayan na kwanta kan tausassan gadona ina mimmiƙewa, muna cikin wayar na ji ƙishirwa ta kama ni sai lokacin na tuna ma da na ci abinci ban sha ruwa ba lemo nai ta ɗaɗɗaka, miƙewa nayi na fito muna cigaba da wayarmu.
Duk da na ji bugawar ƙirjina ban kawo cewar shine a gurin ba tun da nasan me zai kawo shi nan a wannan daren?
Tafiya nake hankalina ba ya kan hanya yana kan wayar da muke da Yaa Sulaiman sai kawai na ji nayi karo da mutum, a razane na ɗago dan ganin waye idona ya sauka a kansa,baki na buɗe zan saki ihu cike da mugun tsoron da yayi sanadiyar fitowar idanuwana dan ni tunanin da ƙwaƙwalwata ta bani aljani ne yayi suffarsa ya zo mini, hannu yasa ya riƙo ni ganin ina yin baya kafin ya saka tattausan hannunsa ya toshe mini bakina dan hana sautin ihun da nayi niyar kurmawa fita, yana jin kamar ya saukewa idanuwana kiss sabo da yadda sukai matuƙar yi masa kyau,tun ba yau ba yasan idan na tsorata idanuwana na yin mugun kyahun da ke ƙayatar da shi.
"Ina coffe ɗin nawa."
Ya faɗa yana sakina dan ya san tun da yayi magana na dawo cikin nutsuwata, sai lokacin na bi wayata da kallo in da tayi gefe ta kife, ƙarasawa na yi in da ta kife dan dukkan alamu Yaa Sulaiman bai yanke kiran ba, ɗagota nayi scring ɗin yayi raga-raga.
"Cwtyyy me ya faru,shirun yayi yawa."
Kara wayar nayi a kunne kafin nace.
"Bani mintina ashirin zan kira ka."
"Na baki hamsin ma ranki ya da ɗe."
"Tom godiya nake." Daga haka na katse kiran duk da ban yi tunanin wayar zata dannu ba.
Kallonsa na yi,yana nan tsaye ƙiƙam kamar an dasa shi fuskar nan a tamke,na ce.
"Ka je sa shen Momy ka jira ni,yanzu zan kawo maka."
Dan na tabbata Baffa yana gab da shigowa kuma bani da amsar da zan ba shi idan ya tarar da mu a haka,ba ma ni da ita bare na ba shin."
"Zan jira ki a nan."
Ya faɗa yana ƙarasawa kan cussion ya zauna.
Kicin kawai na nufa,dan idan na tsaya magiyar yaje ya jira nin ba lallai ya tafin ba kuma na ƙara ɓatawa kaina lokaci.
Sai da na fara buɗe fridge na ɗauki ruwa me sanyi na sha, ina jin yadda wani abu me ɗumi da ke tsirgawa ta marata,wani irin filing nake ji akan Mu'azz da ban san ina da shi ba, wannan wata iriyar masifa ce? Dole na gujewa haɗuwata da shi idan ina son kaina da lafiya amman ta ya ya?.......
"Ku kallla."Fatma tace da 'yan tawagarta, gaba ɗayansu kuwa suka juya idanuwansu ya sauka akan Sajda,tana taku ɗaiɗai cike da yauƙi da yanga wan da ya zame mata jiki domin kuwa duk in da gayu yake Sajda tasan gayu ta kuma san ta kansa. Abin da ya bawa su Fatma mamaki ba komai ba ne sai yadda Sajda ta samo mayafin da ya mugun shiga da leshin da ke jikinsu gaba ɗaya,anko ne na class mate ɗinsu, sun zaga kasuwanni da dama haɗe da super market suma da dama amma basu samu mayafin da ya mugun shiga da leshin ba kamar yadda na Sajda ya shiga, abin da suke gudu ya faru (Sajda ta fisu ɗaukan wanka) Har ta gifta su ta ankara da yadda suka zuba mata ido kamar su cinyeta ɗanya, basa shiri shiyasa bata shiga shirginsu, su kullum burinsu su fita ɗaukar gayu amman hakan ya gagara saboda ta fisu sanin takan gayun.
"Lafiya dai ko na ci muku bashi?"
" Muna mamakin yadda akai kika samu mayafin da muka gama karaɗe kasuwanni da dama ba mu samu ba."
"Hmm shine matsalarku?"
"Eh"
"To matsalarku tazo ƙarshe in sha Allah zan haɗa ku da NEEHAL COLECTION daga yanzu wahalar neman mayafai ƙare muku da yardar Allah, dan nima tun da aka haɗa ni da ita na huta, duk mayafan da ake so ana samu a gurinta ko wani irin kala ne, kuma masu kyau da ɗaukar ido cikin farashi mai sauƙi."
"Au wai kina nufin mayafin na gida ne ?"
"Eh mana ɗan hannu ne."
Amma ta iya mayafai maza maza haɗa mu da ita dan baza mu shiga gurin bikin nan ba sai da irin mayafin ki muma mu ƙure gayu.
https://wa.me/message/AD4MDTQJLXIRD1
Ku bi wannan link ɗin zai kaiku in da zakui magana da NEEHAL COLECTION daga yau matsalar mayafai ta ƙare muku zaku samu duk kalar mayafan da kuke so cikin farashi mai sauƙi ina mai tabbatar muku zaku ji daɗin muamala da ita.
Ga masu bukatar a tallata musu hajarsu kofa a bude take cikin farashi mai sauki.
#Najjwa
#Sulaiman
#Mu'azz
#BR
#09037093702/08082007142
[11/4, 13:30] RASHUNA: BEBEE'ARTH
Wattpad@Rashuna
KA NA NAKA
(Allah na nasa )
26
Tun da dai ga shinan in da nake ganin na samu mafaka ya biyo ni har nan,dama ban fito shan ruwan ba ƙarƙari in ya gaji da tsaiwar ya juya ya fita,ƙishirwar nan dai ba ta kyauta mini ba da ta addabe ni ta saka ni fitowa.
To ko dai Momy ko Yaa Sulaiman zan gayawa? To kuma nace musu me? Tun da dai ba wani abu yayi mini wan da bai dace ba,ko ya gaya mini maganar da ba ta kamata ba,ƙarƙari yasa ni nayi masa girki,kuma wannan ma Momy na saka ni nayi masa.
Magana a taƙaice yake mini ita,ban taɓa kama shi yana kallona ba sai dai ni na saci kallonsa ni kaɗai kenan nake karɓar sabon yanayi a kansa,zuciyata kawai ke doka masa? To idan hakane me zan ce da Momyn ko Yaa Sulaiman ɗin?
Hakan yana nufin,haka zan ci gaba da jure abin da nake ji game da shi har zuwa lokacin bikinmu,tun da bikinma 'yan satittika ya rage na samu su koma in da suka fito,na huta da wannan jarabar,koma ba su koma ba duk tsaurin idonsa yana ganina a matsayin matar wansa bazai cigaba da takura mini kamar yanzu ba.
Ina ta wannan tuna ninnikan har na samu na gama haɗa masa coffee ɗin na ɗauko sabon tea flask mai matuƙar kyau na zuba masa a ciki,ina tunkaro in da yake zaune ƙirjina na mun bugu, yau ɗin yayi masifar kyau cikin wata arniyar blue ɗin jallabiya ta karɓi fatarsa fiye da yadda kuke zato,kwantacciyar sumar kansa da sajensa sai ƙyalli suke gwanin sha'awa, ya saya idanuwansa da siririn glass shima blue da ya ƙara ƙawata fuskarsa, ga ƙamshin turaransa da ya kama falon gaba ɗaya.
Ina gab da ƙarasawa in da yake zaune naga ya miƙe, ashe kenan yana ankare da ni yayi kamar bai ga fitowata ba,miƙa masa flask ɗin nayi yasa hannu ya ansa haɗe da sanya mini wata kyakkyawar waya a hannu kana ya taka ya huce,wayar na ɗago ina kallo haɗe da bin bayansa da kallo,kana na taka da 'yar sassarfa na bi bayansa lokacin har ya kai gab da ƙofa nace.
"Ka ga."
Juyowa yayi idanuwansa ba su sauka a ko ina ba sai cikin nawa wan da hakan yasa zuciyata dokawa tayi tsalle kamar zata rabu da ƙirjina,cikin rawar murya saboda yadda nake jin idanuwansa a ko wata gaɓa ta jikina nace.
"Me za'a yi da wayar?"
"Wullarwa za'ayi."
Amsar da ya bani kenan ya buɗe ƙofar ya fice,tsintar kaina nayi da sakin murmushi sabo da yadda ya daƙuna fuska da zai bani amsa ba ƙaramin ƙarawa fuskarsa kyau yayi ba.
Kan kujera na zube na tafi tunanin da bazan ce ga na meye ne ba, kawai dai jin jikina nake a mugun mace,nayi nisa cikin tunanin na ji muryar Baffa yana.
"Ke Najjwaa wani irin bacci kike ido biyu haka?"
Tashi nayi ina miƙa cikin macewar jiki nace.
"Nima ban sani ba Baffa."
"To Allah ya kyauta, maza je ki ki kwanta."
"To Baffa sai da safe." Na faɗa ina rufe bakina sabo da hammar da ta kubfce mini.
"Allah ya tashe mu lafiya,ki tabbatar kin yi addu'a kafin ki kwanta."
"In sha Allah Baffa."
Sai da yaga shigewata ɗaki kana ya kashe fitilun falon ya nufi ɗan kwaridon da zai Sada shi da nasa ɗakin.
Ina shiga ɗakin zubewa nayi akan gado na ja bargo na rufe har kaina,na rasa wani irin yanayi nake ji a jikina, wannan masifa da me ta yi kama? Ko yaa Sulaiman ɗin ji nayi bana son jin muryarsa duk da nace zan kirasa, so samu dai Mu'azz ya kira ni mu raba dare muna waya ina ji a jikina kamar bazan gaji da hakan ba,wayar da ya bani na ɗago ina dubata naga ba sim a ciki, amman tayi kyau sosai, hancina na kaita na shaƙi ƙamshin jikinsa da ya shafa mata.
Washe gari da safe haka na tashi sukuku da ni, dan ko karyawa ban yi ba na baro gidan, dan son samu na zuciyata na ganshi,ina jin kamar hakan zai rage raɗaɗin
ƙuncin da na shiga jiya cikin dare.
Driver na saka ya sauke ni a makaranta dan tuƙin ma ji nayi sam bazan iya shi ba,Allah yasa ma na iya rubuta abin kirki a jarabawar.
Da yake paper ɗaya ranar zamu zana ba mu wani jima ba muka fito na bi Nauwwa gidanta a can na samu na ci abinci, ai ina jin Najib ba ya nan yayi tafiya nace bazan koma gida ba,ba sai na ganshi shegiyar zuciyar ke zillo kamar zata fito ba, to na guje masa sai inga yadda za tayi.
Ba musu ko jaa in ja kamar yad da muka saba idan Najib ba ya nan tace na taya ta kwana wannan karan na amince, sabo da ni kaina so nake na bawa gidan space ko na samu sauƙin abin da nake ji, waya na yiwa Momy dan gidan ma sam ji nayi ban son komawa nace Nasrin ta haɗo mini kayana driver ya kawota gidan Nauwa ta kawo min, wayar Momy ta bawa Nasrin ɗin na gaggaya mata abubuwan da za ta ɗauko mini kana ta bawa Momy wayar nace.
"To Momy alhakin gayawa Baffa da Gwaggo yana wuyanki, dan kashe wayata zan yi wallahi."
Ban jira cewarta ba na kashe wayar ina dariya dan na jiyo sautin dariyarta itama, kashe wayar tawa nayi da gaske dan nasan halin Baffa yana iya kirana yace na dawo, ni bansan ya zaiyi idan nayi aure ba, ba ya ƙaunar yaga naje wani guri na kwana,ko ɓangaren Momy idan na kwana acan to ba da saninsa ba ne da bazai barni ba,dan akwai ranar da har bacci na fara yasa aka taso ni.
'Yan kwanakin da nayi gidan Nauwwa na samu sakewa sosai tun da ba ganinsa nake ba, wayar da ya bani ma a can gida na baro ta saboda kar ta dinga tuna mini da shi,na bada tawa aka gyara mini naci gaba da amfani da aba ta tun da ina son kayata.
Ranar friday Yaa Sulaiman yace mini zai zo da yamma ranar Sunday da yamma sai ya koma,dama tuni na sanar masa ina gidan Nauwwa duk da ya so na koma gida yadda zamu fi jin daɗin sakewa nace bazai yuhu ba, dan Baffa ma da ya matsan na dawo gida plane muka haɗa da Nauwwa na bata wayar ta roƙe shi akan ya barni ba ta da lafiya ne anman tana jin sauƙi in sha Allah zan taho shine muka samu lafiya.
Yau ta kama Friday ɗin kuma aka ci sa'a ranar bamu da paiper,ranar monday zamu zana paiper mu ta karshe,dan haka da wuri na gama yi masa komai na tarɓarsa.
SULAIMAN
Jirginsu na gab da tashi ya kira Mu'azz ya gaya masa.
Kamar ko da yaushe kuwa jirgin nasu na sauka a filin jirgi ya samu Mu'azz ɗin.
"Idan na tafi naga wan da zai zama driver
ɗinka."
"Matata mana,yau dinma kawai dan ban son wahalar da ita ne tun da kana nan."
Kasan ransa kuwa ba wannan dalilin ne ya hana shi cewa tazo daukarsa ba illa yad da yake jin tsananin kewarta zai iya rungumeta abin da sam ba dabi'arsa ba ce shiyasa yake kaucewa hakan,ji yake kamar ya janyo satika biyun da suka rage na bikinsu ayi kowa ya huta.
Matata ɗin da ya faɗa ya tuna masa da ita, yau kusan kwana biyar bai ganta ba,dan ya jajje nemanta ba ya ganinta,coffee ɗin da tayi masa ranar nan ya matuƙar jin daɗinsa abin da yasa kenan yake so tayi masa dan yana masa ɗanɗano da ƙamshi ɗaya da wan da ya saba sha a saudiyya,amman yayi zarya a gidan kusan sau nawa ba ya ganinta,kuma bai tambayi kowa ba haka ya dinga maleji da na Nasrin dan ya zamar masa jiki shan coffee zai iya yini yana sha ba tare da ya nemi wani abinci ba,kunun madara kuwa tun da yasa Nasrin tayi masa sau ɗaya ya kusa amai daga kurɓa sau ɗaya ya haƙura da sha,amman da zai samu irin natan zai so hakan.
Sulaiman ɗin ne ya an shi tuƙin ya cewa Mu'azz.
"Na ajiyeka gida ko mu wuce tare?"
Sauke masa idanuwansa yayi alamun tambayar ina yake nufin zasu je ɗin.
"Zan fara tsayawa gurin Najjwa ne."
Jinjina masa kai yayi alamun su je ɗin.
Ya na karyo kwanar layin gidan Nauwwa ya kira ni a waya akan ga shinan ƙarasowa dan haka na tashi na ƙara gyaggyarawa,ya na daidaita parking ya kuma kirana na fito, bai kai ga fitowa daga cikin motar ba na fito haɗe da ƙwanƙwasa glass ɗin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 17