suke zama sabida SHIMA ƊA NE kamar sauran yara, sannan wannan auren babu saki saida kwakkwaran dalili saɓanin haka kotu zata ɗau mataki a kanka"
silalewa matarshi tayi kasa ta faɗi a sume jin an fara ɗaura auren, alkali be tsaya ba saida ya tabbatar aure ya ɗauru kafin ya bada umarnin a dubata, Alhaji sai zufa yake mutane kowa yana tofa albarkacin bakinshi, nawal shiru yayi yana kallon yadda Alhaji ya ruɗe akan matarshi yana tashinta tareda kiran sunanta NAJA'ATU sai zufa yake sharewa, taimakon gaggawa aka bata akan gadon asibiti aka kwantar da ita, Alkali yace a kai nawal da amminshi gidan Alhaji alhasan sannan a basu masauki kamar yadda matarshi da ƴaƴanshi suke zama, jikin nawal a mace yake bin tafkeken makeken tsararren gidan da aka kawosu wanda cikinshi kamar aljannan duniya, wannan gidan ya wuce tunanin me tunani, wani ɗaki da aka kaisu kamar ɗakin gomna acan aka musu masauki, banda kallon gidan babu abinda suke yi, daga shi har ammi a tsorace suke domin basu saba zama a irin wajennan ba sunfi zama a bola da datti.
dan kyar hajiya naja ta dawo hayyacinta, Alhaji banda hakuri babu abinda yake bata daga karshe ya fashe mata da kuka, a duniya babu wanda yake jin magananta kamar matarshi bayaso ko kaɗan ranta ya ɓaci tamkar aikin asiri, yaransu biyu maza nawal ya girmesu ɗaya sunanshi naseer ɗaya kuma nabil tanada karamin ciki kuma yanzu suma sun girma kuma sunada wayo nasir shine babba nabil kuma karami, suna tsadadden makarantan da yaran wane da wane ne a nigeria suke ciki, basajin hausa sosai sunfi gane turanci amma suna fahimtan hausa, duk duniya babu abinda Alhaji Alhasan yake so kamar matarshi da wannan ƴaƴan nashi da cikin dake jikinta bayason ko kuda ya taɓasu, koda yaushe suna cikin shaƙatawa, yana neman gomna kuma ya ɗau hanyan samu saide wannan abin daya faru yasa jikinshi yayi sanyi, yaji babu abinda ya tsana a duniya kamar wannan yaron da aka kawoshi rana tsaka akace wai ɗanshi ne, wannan yaron ze taɓa kujeran da yake nema idan beyi sa'a bama ba zai samu ba, har suka koma gida taki mishi magana yaran ma sunki mishi magana sabida sunga komai a social media sannan hoton da Alkali yasa aka ɗauka na nawal da Abbansu sun gani.
kwance Abba yake akan makeken gadonshi na alfarma ya ɗaga kai sama yana kallon saman ɗakin, ya kasa amsa kiran kowa duk yawan kiran da yake shigo mishi ya kasa ɗauka, sakonni sunata shigowa ya kasa ko kallon wayan, nasir ne ya shigo, kyakkyawa ne sosai sabida Abba yanada kyau ya tsaya a bakin kofa sanye yake da armless fari da gajeren wando, jikinshi na ƴan hutu ne sosai yake glowing, yace "dady wai da gaske ne bamu kaɗai bane yaranka an haɗamu da wani?"
shiru yayi yana kallon yaron, hawaye yaron ya fara yace "dady i can't wallahi i can't share you, nida nabil kawai nakeso ka zama dadynmu banda wancan kazamin da yazo yau, Abba i hate him I hate him so much Abba, please I want him to leave this house banason ko ganin fuskanshi dashi da wannan kazamar gurguwan matar, dady nasan sharri sukayi maka sabida sunga zaka samu kujeran gomna, they want to ruined you, dady kasa security su koresu please, kaga momy ma tun ɗazu sai kuka take yi she's not feeling good"
a hankali ya sauka akan gadon, zuwa yayi ya janyo yaron jikinshi sannan ya fara shafa bayanshi cikin lallashi yace "calm down my boy wannan umarnin alkali ne amma ni ɗan siyasa ne nasan duk wani hanyan da zanbi na samu duk abinda nakeso, i will never compare you with anyone, ku kaɗai ne yarana he will just be with us for some times amma shi ba ɗana bane bazan taɓa karɓanshi a matsayin ɗana ba"
yace "dady i hate him ka koreshi kawai momy ma batason ganinsu she hate them with all her heart"
shiru yayi, turo kofan akayi momy ce ta shigo ɗakin babu ko sallama, hanun nasir ta rike ta fizgeshi daga jikin dady sannan tace "bance kada ka kara zuwa wajenshi ba har sai ya fitar da waɗannan dattin daya kawo mana gida? why are you stubborn ne nasir? can't you see your brother ya kama kansa baizo wajen wanda ya haɗaku da wani a matsayin ɗa ba? your father cheat you, he cheat"
dady ya rike hanun nasir sannan yazo gabanta ya durkusa ya haɗa hanu biyu yace "please and please my love kada kimin haka, da wanne zanji? da wannan bala'in daya sameni ko da wannan abinda kuke min, an tabbatar ɗana ne amma ai kuskure ne, kuma nima banji ina sanshi ba ko kaɗan a cikin raina, kinfi kowa sanin ni ɗan siyasa ne yanzu takaran gomna nake yi kuma zan samu, abu kaɗan ne zai iya sa na rasa wannan kujeran kuma kinsan zan iya yin komai domin na samu wannan kujeran sannan zan iya yin komai idan na rasa wannan kujeran...."
wayarshi ce ta fara ringing da sauri ya saki hanun nasir ya tashi yaje ya ɗauka sabida wannan ringtone ɗin na kiran majalisa ne, ɗauka yayi yace "your highness barka da warhaka"
cikin tsawa da masifa yace "abinda nake ji da gani a social media gaskiya ne?"
shiru yayi, ya kara cewa "gaskiya ne?"
jikinshi yana rawa yace "eh"
cikin ɓacin rai yace "yanzu haka munyi meeting na gaggawa kuma mun zartar da hukunci mun saukeka daga neman kujeran gomna mun ɗaura abokinka Alhaji sammani, an koreka a party daga yau kai ba ɗan DCD bane"
wayan ne ya faɗi a hanunshi ya rike kirji yana ciza baki, yace "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un..."
kafin ya karasa ya faɗi kasa, da gudu momy da nasir sukazo suna jijigashi idonshi ya rufe.
*Shima ɗa ne complete is ₦400 via 8144818849 hauwa shuaibu mapi moniepoint, evidence via 08144818849*
_jiddah Ce...✍️_
[17/08, 11:03 pm] +234 814 481 8849: 🌸🌸🌸🌸🌸
*SHIMA ƊA NE*
🌸🌸🌸🌸🌸
Na
*Jiddah S Mapi*
*Chapter 7*
~Jikinta ya fara ci da wuta, nawal ya shiga tashin hankali fiyeda ɗazu, janta yake yana cewa "ammi mu gudu, ammi banaso ki mutu"
sai yanzu ta saki hanunshi da gudu ya fita yana kiran mutane su taimakeshi, hajiya da gudu ta hauro jin ihun nawal, yanzu yaran suka dawo daga shopping, ganin wutan da yake ci suka fara neman hanyan tseratar da mutanen ciki, ammi tana kwace a cikin wutan itace kaɗai suka ceta shi kuma Alhaji umar already ya kone harma ba zaka iya ganeshi ba, asibiti aka tafi da ammi domin akwai rai a jikinta, saide idonta a rufe domin kafafunta sun kone fatan ƙafan ya ɗaye sosai yayi jajur, nawal a tsirara ya bisu asibitin, da kyar aka kashe wutan, ammi kuma aka bata taimakon gaggawa, likitoci sun dubata amma sun tabbatar kafafunta ba zasu kara tafiya ba domin dole sai an yanke sabida wutan yaci har kashin kafarta, yaran Alhaji umar sun tafi sun barshi shi kaɗai a asibitin sabida suma ta babansu suke ba tashi ba, yana zaune tsirara babu kaya ya haɗa kai da gwiwa yayi shiru a bakin kofan ɗakin da ammi take kwance suna aikin yanke mata kafafu sabida ƙafan ba zai kara aiki ba"
duk masu wucewa sai sun kalleshi be damu ba burinshi ya tabbatar ammi tana raye, take aka fara yaɗawa a gari Alhaji Umar ya mutu sakamakon gobaran daya faru a gidanshi, sai dare kafin suka bari ya shiga, ammi tana kwance ansa mata oxygen kafafunta kuma duk biyu aka yanke, gata dai a kwance kamar mara rai, kanshi ya ɗaura a cikinta yayi shiru ya kasa kuka, yadda yaga rana haka yaga dare, da kyar bacci ya saceshi baima san yayi ba, har washe gari yana bacci saida dr ya tasheshi, a firgice ya buɗe ido yana kallon dr, yace "tashi mana nan wajen bacci ne?"
yace "a,a kayi hakuri"
cikin sanyin muryanshi yayi maganan, dr yace "ina ƴan uwanka?"
yace "banada ƴan uwa daga ni sai Ammi"
cikin tsawa yace "me kake nufi da bakada ƴan uwa? du waɗanda suka kawota su waye?"
yace "yaran mijinta ne"
yace "to kaje ka kirasu suzo su biya kuɗin aiki"
shiru yayi, dr yace "baka ji bane?"
a firgice yace "naji"
yace "me kake jira?"
tashi yayi ya fita jikinshi har yana rawa tsaban tsoro da yunwa, a tsirara yaje gidansu ya samu hajiya da yaran yace suje asibiti su biya kuɗin aiki koranshi sukayi sukace basu da komai a gidan kada ya kara taka kofan daga shi har Ammi ko kuma su sa police su kullesu, jin haka yaji tsoro da yaji police ya koma asibiti, Dr yace "ina suke?"
jikinshi yana rawa yace "sunce bamuda komai a gidan..."
wani tsawan daya daka mishi saida ya ɓuya a bayan kofa, ya kwala kira nurse suka shigo yace su ɗaurata akan keken marasa lafiya su fitar da ita daga asibitin, duk inda sukaga ya dace su wurgar da ita.
nawal ya durkusa ya fara bashi hakuri ball yayi dashi ya fita a ɗakin, suka ɗaurata saman keken suka fitar da ita, a kofan asibitin sukayi wurgar da ita, rasa yanda zeyi yasa ya tashi yana bin mutane yana neman taimako, kowa ya gani sai yace "ku taimaka ku ɗaukemin ammina daga can batada lafiya"
babu wanda ya kulashi kowa kallon mahaukaci yake mishi musamman da suka ganshi tsirara.
har dare babu wanda ya kulashi, a bakin kofan asibitin yaje ya sameta ya kwanta, bacci ya fara ga sauro ga sanyi, rungume da ita yake har yanzu bata buɗe ido ba, washe gari ya tashi yana kara neman taimako, da kyar ya samu wani riga me datti daya gani a kasa yasa a jikinshi, babu wando amma rigan ya sauka ya rufe gabanshi, kamar yadda suka saba bara shida ammi yauma haka yake bin titi yana bara, kwano ya samu yana zuwa neman abinci, Allah yasa ya samu abinda zeci ga kuma kudi ya samu kaɗan, komawa yayi ya janye ammi ya kaita bayan asibitin kan wani bola ya kwantar da ita sannan shima ya zauna a kusa da ita ya buɗe abincin ya fara bata, kallonshi take bata iya magana sabida zafin wutan ya bugata sosai shiyasa har yau bakinta be buɗe ba, datti yayi sosai gashinshi ya taru yayi kura yayi datti, duk da shi fari ne amma ya dishe yayi baki saide har yanzu da haskenshi, hawaye yana wanke mishi fuska, share mata hawayen ya fara sannan yace "ammi kici abinci karki zauna da yunwa"
kasa buɗe baki tayi, ya buɗe bakin a hankali yake sa mata, ci tayi sannan shima yaci yana farin ciki yau tashi abinci.
haka yake kula da ita idan yaje yayi bara ya kawo abinci suci, babu me kula dasu har ya fara girma ya fara zama saurayi a bola suke kuma bara yake yana samun na rufin asiri, yanzu ya kai 15year kuma a kullum rayuwa darasi take kara koya mishi, be taso cikin daɗi ba amminshi tana cikin wahala gashi babu kafafu, hadari aka haɗa sosai yau da alama ruwan ba mai sauki bane, ga iska da yake tashi sosai, yayi shiru yana kallon ammi yayi tagumi ya rasa ina ze kaita kada ruwan ya taɓata, ammi murmushi tayi mishi tace "nawal meyasa kayi shiru?"
bai amsa ba kawai ya rike hanunta yana murzawa idanunshi sunyi jajur har ruwan sama ya fara dukansu da ita, duk yawan ruwan a kansu ya kare daga karshe aka sauko da wani sanyi me ratsa jiki, ammi ta fara rashin lafiya ta fara rawan sanyi, yana rike da ita yana kallonta tana kakkare jikinta, tashi yayi domin zuwa siya mata magani, cikin asibitin ya shiga yana kare jikinshi sabida sanyi, ya samu dr wanda shine ya yiwa ammi aiki shekaru dayawa da suka wuce, yace "maganin zazzaɓi nake so"
Dr be ganeshi ba ya fara haɗa mishi magani saida ya gama sannan yace "gashi"
karɓa yayi ya ciro ɗari biyar shine iya kuɗinshi daya rage ya bashi yace "gashi"
wani kallon da yayi mishi kallon bakada hankali ne?
cikin tausayin ammi yace "ka taimaka min wallahi ammina ce babu lafiya"
cikin tsawa yace "ta mutu mana ina ruwana? matata ce? ka aje magani kafita kafin na kira maka police"
ajewa yayi yace "zata iya mutuwa Dr"
yace "ta mutu, ba zaka samu magani ba sai ka kawo dubu goma"
duk rokon da yayi mishi yaki yadda daga karshe ya ɗaga waya ya kira police, nan ne ya fita sabida beson a kamashi.
ya koma wajen ammi ya zauna yana kallonta har tayi rawan sanyin ta gaji, be samu kuɗin magani ba har washe gari, ya tashi da sassafe domin neman abinda zasuci, cikin rashin sa'a aka biyo ɓarawo mutane ne dayawa da sanduna, suna ganin nawal wani yace "shine wallahi shine ɓarawon"
nawal cikin rashin sanin me suke nufi yace "wallahi ni ba ɓarawo bane, banyi sata ba kuma ban taɓa sata ba...."
sanduna bulala duk suka fara dukanshi dashi, duka suke mishi na rashin imani, yace "bani bane"
wani yace "dama taya zaka yadda kaine? idan ba kai bane meya fito da kai da sassafe haka? mutane suna gidan ubansu kai kana layi? ko dai shege ne kai bakada uba mun san sune suke addaban mutane"
jikinshi yayi lankwas sabida ba karamin duka sukayi mishi ba, ɗayan yace "ku kawo fetur mu kona shi gobe ba zai kara sata ba"
fetur suka kawo suka zuba a kanshi tayoyi suka sa mishi sannan suka kara fetur ɗin, ashana zasu kyafta wani babban mutum yana wucewa yace "haba bayin Allah meyasa zaku kashe shi?"
wanda ya kyasta ashana yace "sata yayi kuma dole sai mun kashe shi"
wutan yasa, take jikin nawal ya fara ci da wuta, da gudu mutumin yazo yana kashe wutan daya fara ci a jikin nawal, yace "Allah be ce a kashe wanda yayi sata ba, yace a yanke hanunshi ɗaya idan ya kara a yanke ɗayan hanun idan kuma ya kara a yanke kafarshi idan ya kara a yanke ɗayan kafar, me yasa zaku ɗau hukuncin kisa aka ɓarawo?"
shiru sukayi, yace "bawan Allah tashi ka tafi"
tashi yayi zasu kara rufeshi da duka mutumin ya tareshi da kyar ya samu ya kuɓuce, jikinshi kamar babu jini haka yake tafiya ya gaji sosai kuma be samu komai ba.
ya koma wajen ammi wacce jikinta yayi zafi, yayi tagumi kawai yana kallonta, motan dr ya gani yana wucewa, a ranshi yaji babu wanda ya tsana kamar wannan dr ɗin, binshi yayi a baya be san me zaiyi ba amma ji yayi a ranshi yanaso ya hukunta wannan daya hana amminshi magani, har yayi nisa kafin ya tsaya siyan nama, saida yaga babu kowa ya buɗe boot na motar ya shiga rufewa yayi har dr yazo ya shiga motar yaja, a fili yace "ya naji yanzu motar ta ɗanyi nauyi?"
cigaba yayi da driving har zuwa gidanshi aka buɗe mishi gate nashi na alfarma ya shiga, fita yayi ya ɗauki manya manyan ledojin daya zo dashi, nawal saida yaga ya fita kafin shima ya fita, dare yayi hakan yasa babu wanda ya kula, yana ganinshi matarshi tazo ta karɓi ledojin, fakewa yayi har dare yayi nisa, wani kyalle daya gani a motar ya ɗauka ya ɗaure fuskanshi ta yadda babu me iya ganeshi, shiga ciki yayi cikin sanɗa yake bi ta jikin bango har ya shiga ciki, duk sunyi bacci harda Dr, wani irin zafi nawal yake ji a ranshi idan ya tuna duk abinda dr yayi mishi daga shekarun baya har zuwa yau, durkusawa yayi ya ɗaure bakin dr da ɗankwalin matarshi, janshi ya fara akan tile ya fita dashi, a motar ya sashi sannan ya shiga baisan yadda ake driving ba amma yana gani, hakan yasa yayi hon dr ya buɗe ya fita dashi a gidan, gudu yake bai san inda ze taɓa ya tsaya ba, da haka har dr ya tashi ya fara fizgewa, nawal cikin rashin magananshi yace "kayi shiru ko kuma na kifar damu a motar nan, iyalanka su zama marayu"
tsit yayi, nawal yayi yayi ya tsayar da motar taki tsayawa saida suka shiga wani daji suka bugu da bishiya kafin motar ta tsaya, ganin motar zata fara ci da wuta yayi gaggawan cire dr ya wurgar dashi a gefe, take motar ta kama da wuta, dr yana kallonshi ya rufe fuska ba zaka gane shi ba, wayan aljihun dr ya ciro sannan ya ɗaureshi a jikin bishiya bayan ya buga mishi itacen bishiya a kanshi ya suma, ya zauna a gefe yana jin kukan tsuntsaye, a wajen yayi bacci, washe gari da ruwan sama aka tashi, buɗe ido yayi a hankali yana bin dajin da kallo, sauke idonshi yayi akan dr wanda har yanzu a sume yake, wayan ya ɗaga ya amsa call ɗin daya shigo, cikin tashin hankali matarshi tace "mun nemeka na kiraka na kiraka baka ɗauka ba, nasan babu lafiya ina kake dr?"
murmushi yayi yace "yana nan yana raye amma dab yake da mutuwa a hanuna"
cikin tashin hankali tace "waye kai? me yayi maka? me kake so?"
yace "amsan karshe kawai zan iya baki shine me nake so"
tace "dan Allah kada ku cutar dashi ka fadi duk abinda kake so wallahi zamu baka"
murmushi ya kuma yi sannan yace "idan kika sake kika sa hukuma a wannan maganan zan kashe shi"
tace "wallahi na rantse maka da Allah babu wanda zan faɗawa ka faɗi duk abinda kake so"
yace "magani nake so"
da mamaki tace "magani kuma?"
yace "eh maganin zazzaɓi nake so"
shiru tayi, sai kuma tace "shikenan ka faɗi inda zan aje zan kai maka harma da naira miliyan ɗaya"
yace "magani kawai nake so ki aje a kofan asibiti sannan idan na ɗauka zan faɗa miki inda yake kije ki ɗaukeshi"
tace "yanzu zan aje"
da gudu ta fita ta kai, ta kirashi ta tabbatar ta kai sannan yaje ya ɗauka, ganin ba'a kamashi ba ya faɗa mata inda zata ɗaukeshi.
maganin ya kaiwa Ammi ya bata tasha kuma Allah yasa zazzaɓin ya fara sauka, hamdala yayi ya kara godewa Allah da bata mutu ba.
matsalan abinci da wajen zama ya fara damunshi duk hanyan da zebi ya samu kuɗi yabi be samu ba, Allah ya haɗashi da wani me gyaran gado yana zuwa suna gyara tare saide naira 500 yake bashi, duk gajiyan da zeyi ɗari biyar yake bashi, yana kallon irin makudan kuɗaɗen da mutumin yake samu kuma tare dashi suke aikin, yau yazo mishi da zancen baida lafiya ya bashi kuɗi ya siya magani, mutumin ya fara masifa da bala'i meyasa ze tambayeshi kuɗin magani kenan be gode da 500 ɗin da yake bashi ba?
shiru yayi kanshi a kasa har ya gama, cikin rashin magananshi da tsananin hakurinshi ya fara aiki.
har zazzaɓi yaci jikinshi babu magani babu kuɗin magani, shawara ya yanke ze sace uban gidanshi har sai ya samu kuɗin magani zai sakeshi, hakan kuwa akayi saida aka kusa tashi yasa mishi magani a ruwa, yana sha ya fara bacci a wajen har dare nawal yayi kamar be ganshi ba yana cigaba da aikinshi, saida dare yayi nisa kafin ya janyeshi a wajen ya kaishi inda babu wanda ze san yana wajen, kara haɗa maganin yayi yasa mishi a baki saida ya shanye ya kwantar dashi ya rufe bakinshi, nemanshi aka fara ciki da waje, iyalanshi sunfi kowa shiga tashin hankali, murmushi nawal yayi kuma tare dashi suke nemanshi, waya ya samu karami yasa sim ya kirasu kudi ya yanka musu miliyan ɗaya domin ko kaɗan baya jin tausayinshi.
sun aje kuɗin ya dauka kafin ya faɗa musu inda yake, bayan komai ya wuce tare suka kara cigaba da aiki.
hankalin nawal ya fara rabuwa kashi biyu, kuɗin daya samu beso ya rabu dashi, murmushi yayi shi kaɗai yana kallon ammi da take cin abinci me kyau daya siya mata, sauran kuɗin ya sadakar wa yara, sabida kullum nasihan ammi shine nawal kaji tsoron Allah.
*Shima ɗa ne complete is ₦400 via 8144818849 Hauwa shuaibu mapi moniepoint, evidence via 08144818849*
_Jiddah Ce...✍️_
[17/08, 11:03 pm] +234 814 481 8849: 🌸🌸🌸🌸🌸
*SHIMA ƊA NE*
🌸🌸🌸🌸🌸
Na
*Jiddah S Mapi*
*Chapter 9*
~Cikin tashin hankali hajiya naja ta kira layin Dr, nabil ne ya shigo shima yaro ne kyakkyawa yana kama da yayanshi nasir, saide yafi nasir kiba domin jikinshi irin na girman falo ne, ya kalli nasir da yake kuka yace "bro nas meya samu dady? kar dai sabida wannan useless ɗin ya faɗi?"
nasir yace "eh sabida su ne nabil banaso dady ya mutu ya barmu"
nabil yace "that's why I hate them, I don't even want to see there faces daga shi har wannan kazamar gurguwan matar, dama momy tace talakawa suna son yiwa me kuɗi sharri they want to have connection with us sabida kuɗin dady"
nasir ya janyoshi jiki ya rungumeshi yace "stop crying dady will not die insha Allah"
momy kam ta goya hannaye a baya banda safa da marwa babu abinda take yi, ta rasa me zata fara yi, dr ɗinsu wanda yake kula dasu ya shigo domin security tasa suka shigo dashi, fara dubashi yayi ya kalli momy dake kallonshi tana jiran amsa yace "yana bukatan gado emergency"
a ruɗe tace "to ka taimaka mana mu kaishi"
hijabi tasa suka rike dady harda su nasir suka fita dashi.
nawal dake zaune yayi tagumi sabida yadda yaga gidan yasan da wuya suji daɗin zama anan, Ammi tace "nawal"
a hankali yace "na'am"
gefenta ta nuna mishi tace "zauna anan"
zama yayi ya ɗaura kanshi akan keken guragu sannan tace "nawal ka saki jiki ka zauna a gidannan domin nan shine asalinka, wannan shine mahaifinka nawal banaso na mutu na barka bakada kowa, ka daure duk wani abinda za'ayi maka kamin alƙawari ba zakayi fushi ka bar asalinka ba"
a hankali yace "na miki alkwari"
tace "nawal ka ɗago ka kalleni kace nayi alkwari duk wahalan da zansha ba zan tafi na bar asalina ba"
da kyawawan idanunshi masu ɗaukan hankali ya kalleta, a hankali cikin nutsuwanshi ya motsa lips nashi wanda suke pink sosai har sun koma red kaɗan, yace "nayi alkwari duk wahalan da zansha ba zan bar asalina ba"
murmushi tayi tace "Allah ya maka albarka"
ya ɗaura kanshi a cinyarta a hankali yace "ameen"
hawaye ta share na tausayinshi, tasan akwai kalubale me yawa da zai fuskanta a gidannan sabida taga alamu tun a kotu, amma dole ya hakura sabida shine mahaifinsa, fitowa sukayi da dady wanda baya motsi, momy ihu ta fara tana cewa "na shiga uku ku taimakeni kar ya mutu"
nasir da nabil babu takalmi a kafarsu suke binsu a baya dr yana rike dashi, nawal da sauri ya tashi yana kallonsu, ganin dady a haka ya kalli ammi, lumshe ido tayi ta mishi alaman yaje, da sauri ya fita, babban compound na gidan wanda yake ɗauke da manyan motoci masu tsada da kyau suka nufa, wani katon jeep baƙi ƙirin suka buɗe, ɗaga dady yayi amma ya kasa sashi a motan, nawal ne yazo yasa hanu zai taimaka musu a sashi a mota, wani marin da momy ta bashi saida ya dafa kunci, ta rike hanunshi da karfi tayi wurgi dashi, faɗuwa kasa yayi ta nunashi da yatsa cikin masifa da tsananin tsanan da take mishi tace "don't dare touch my husband"
jikinta har yana rawa tace "idan ka kara taɓashi da wannan ƙazamin hanun naka sai na lahira ya fika jin daɗi, kaje ka samu wannan kazamar matar da kuka taho tare ka faɗa mata ni nafi karfin kishiya, sannan ka gaya mata babban goro sai magogin karfe, bamuda alaka da matsiyata daga zuriyar mahaifina har na mahaifiyata harma da zuri'ar mijina kaje ka nemi ubanka wannan uban ƴaƴana ne kuma ba zasu haɗa uba da kowa ba"
dr yace "hajiya muje kada wani abin ya samu Alhaji"
tana huci ta tufawa nawal yawun bakinta tace "kazami"
nasir da nabil kallon tsana suke mishi har suka shiga mota suka barshi a wajen, tashi yayi bayan sun fita ya koma ɗakin Ammi, duk abinda ya faru ta gani, suna haɗa ido taji hawaye a idanunta, murmushi yayi mata sannan yace "ammi banji ciwo ba fa kinga murmushi ma nake yi"
sunkuyar da kai tayi tace "ka yafemin nawal..."
da sauri yazo ya rufe mata baki yace "shii Ammi kada kice haka baki min komai ba kuma banji komai ba"
rungumeshi tayi yayi shiru yana tuna maganganun da hajiya naja ta faɗa mishi.
kwana biyu sukayi a asibiti
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 17