Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
hakuri, gida suka koma dashi, mutane sai magana ake wai rahama ce tayi sanadin mutuwan baba, mama tace "rahama karki kuskura ki taɓa babanki kece sanadin wannan mutuwan ki tashi kije rahama nima na yafeki duniya da lahira" tana kuka zatayi magana sabida bakin ciki mama ta fara dukanta kamar ranta ze fita ga bakin cikin mutuwan baba ga dukan da ake mata, da kyar nana ta janyeta ta rungumeta tace "unty rahama ba zan iya jure ganin ana wulaƙanta ki ba" tana haƙi cikin wahala tace "nana anya mama ce ta haifeni?" nana tana kuka tace "tabbas itace ta haifeki kawai ɓacin rai ne" tashi tayi tace "babu komai..." kayanta da aka watsa mata a kanta yasa ta ɗago kai ta kalli mama data nuna mata hanya tace "ki kwashe kayanki ki bar gidannan rahama koda wasa kika kara taka kofan gidannan ban yafe ba, rahama idan na kara ganinki zan tsine miki kuma na rantse" rahama ta kalli nana ta kalli mama cikin ruɗewa ta zube kan gwiwanta ta rike kafafun mama tace "mama ki gafarceni wallahi bada sona hakan ya faru ba" mama tana hawaye ta juya baya tace "kinja min magana a wajen mutane kinsa babanki ya mutu me zan kara yi dake? kinyi cikin shege a kauye? kinsa ina tafiya ana nuna ni, kinsa babu me zuwa ya auri kanwarki nana sabida kin aje mana tabo rahama, na yafeki wa duniya na tsani wannan cikin naki, na tsani wannan cikin na jikinki, cikinshi masifa ne a garemu idan kika haifeshi ze zame mana bala'i, ze kawo mana matsala sabida kinada cikin ma mun samu matsala bale ki haifeshi rahama kije duk lokacin da kika haihu kika rabu da wannan yaron na cikin naki kika wurgar dashi na yadda ki dawo inda nake, amma matukar kika dawomin dashi gidannan a ciki ko a waje ban yafe ba" bata kara magana ba ta durkusa ta kwashe kayan sannan ta kalli nana tace "nana, yaseer zan tafi sabida ba zan jure ganin mama tana kuka dalilina ba" rungume yaseer tayi tace "ka kulamin da nana kasan ina sonku sosai" ta sakeshi yana kuka ta juya ta rungume nana tace "Nana kiyi karatu kada ki yadda ki bar karatun da kike inada tabbacin zaki samu rayuwa me kyau, Nana kada ki aikata kuskuren dana aikata a rayuwa ki kula da kanki" sakinta tayi Nana tana kuka ta kwashe kayan ta fita, kuka take yi, mutane suna nunata suna mata tofin Allah ya tsine, yara ta gani sun fara harbinta da duwatsu suna mata ihun wai babanta ya mutu saboda ita, tana nuna ustazanci na munafurci, gudu ta fara sabida zasu illatata, da kyar ta samu ta fita daga kauyen, dare ya fara yi gashi daji take riska, haka dai ta daure tana tafiya ga yunwa ga ishin ruwa, har dare yayi nisa tana cikin dajin, rasa yadda zatayi yasa ta kwanta a kasa tana sadaukar da rayuwa, cikinta ta rike wanda take ji yana motsi, babu abinda ta tsana kamar wannan cikin dake jikinta, ko kallon cikinta batason tayi, har garin Allah ya waye tana wajen, tashi tayi taci gaba da tafiya, tayi kwana uku tana tafiya saide taci mangoro da ruwa har ta samu ta ganta a cikin gari, zama tayi a gefen titi tana kallon masu tafiya, me shayin dake ankare da ita yazo inda take yace "baiwar Allah tun ɗazu nake ganinki anan lafiya?" ta kalleshi tayi baƙi ta rame tace "lafiya ƙalau amma ina cikin wani hali, dan Allah ka taimakamin koda shayi ne" yace "to ina zuwa" shayi yaje ya kawo mata ta karɓa har jikinta yana rawa ta kafa a baki tana yagan biredi kamar zata cinye da hanunta, har ta shanye tace "na gode bawan Allah" yace "amma daga ina kike?" tace "babu amfanin sanin hakan bawan Allah wajen kwana nake nema" ya kalleta sannan yace "taimakon da zan iya miki shine na baki kudi kije ki kama ɗaki, sannan ki nemi aikin yi" ta durkusa kasa tace "na gode bawan Allah" kuɗi ya bata ta karɓa tana godiya ta tafi domin neman wajen zama, tafiya kawai take batasan ina zataje ba, wasu ƴammata biyu ta gani sunyi wanka sunci ado suna kallonta sukace "baiwar Allah me kike nema?" tace "ni baƙuwa ce ban san inda zanje ba ɗakin haya nake nema" kallon juna sukayi sannan suka ce "to gaskiya zaki jima baki samu ɗakin haya ba amma idan zaki iya zama damu kuɗin gidan da muke biya babu yawa" cikin jiri da zazzaɓin da take ji burinta kawai ta ganta a daki ta kwanta tace "na yadda zan zauna" sukace "muje" binsu ta fara har zuwa wani gida ta bada kuɗin wa mutumin data gani kamar baida mutunci bayan ta biya kuɗin suka tafi, wani gidan da tun a bakin kofa ta fara ganin masu shaye shaye da masu caca taga sun shiga da ita, bin ko ina take da kallo ƴammatan gidan duk karuwai ne domin kowacce da samarinta ga kuma caca da sukeyi da kalangu da ake bugawa, shiru tayi tana kallonsu suka nuna mata ɗakin da zata zauna, daga nan basu kara bi ta kanta ba, ɗakin ta shiga a tsorace take bin ko ina da kallo, babu ko katifa ga sanyin kasa na siminti, shiru ta zauna kasa tayi tagumi, turo kofan akayi taga ɗayar ce ta bata wani ƙaramin katifa da tabarma marar kyau da abinci a kwano, tace "gashi sai kici ki fita ki nemi ruwa, sannan zan faɗa miki wani abu, gidannan idan baki buɗe ido ba zakisha wahala" tace "na gode ya sunanki?" tace "sunana Abida" tace "to na gode" tafiya tayi ta kalli abincin sannan ta janyo ta fara ci, badan ta koshi ba ta kwanta ta fara rama bacci, har ta tashi tayi salla babu wanda ya kara shigo mata, sai dare kafin ta leƙo da sauri ta koma ganin tulin mazan dake gidan kowa da mace suna baɗala, dafa kirji tayi tace "Innalillahi ya Allah kasan bada sona nazo nan ba" zama ta fara a gidan duk da rayuwarta tana cikin tsoro amma tana daurewa, rashin kuɗi ke mata barazana yanzu batada kudi batada abinci kuma babu me kulata. kama kanta tayi sosai a gidan bata bari ta saba da kowa domin babu abin kirki da akeyi a gidan banda caca da zinace zinace, Allah yasa ta samu aiki gidan wata mata tana biyanta kuɗi anan take samun kudin siyan abinci, cikinta ya fara girma tana kula dashi, yauma kamar kullum ta dawo daga aikin ta zauna a bakin kofa tayi tagumi tana kallon mutanen dake harkokinsu, idan da sabo ta saba dasu, kowa ya shaida fuskanta a gidan kamar yadda ta shaida fuskan kowa, wata dake jin kanta a gidan taja tsaki bayan ta kalleta tace "sai sunkuyar da kai na munafurci da nuna bata bin maza gashi ita har ciki ta kwaso, tanada tsaraban bariki, gara mu ba muyi cikin shege ba" wannan maganan ya taɓa mata zuciya taji zafi sosai, idan akace cikin shege sai taji komai na duniya ya fita mata a rai, tashi tayi ta shiga cikin ɗakin ta zauna tayi shiru tana tuna rayuwar da wannan ɗan cikin nata zaiyi, tana jiye mishi zafi tun kafin ta haifeshi, tana jin ciwon kalman da za'a kirashi dashi na shege, mutane musamman na wannan zamanin basu san ƙaddara ba, ɗan da zata haifa koda shege ne to ai SHIMA ƊA NE haka Allah ya ƙaddara mishi. hanu ta ɗaga sama tana kallon sama tace "ya Allah ni kaskantacciyar baiwa ce, ya Allah banida komai sai abinda ka bani, ya rabbi kace mu roka zaka bamu, ya Allah a cikin hadisi kace koda mutanen duniya zasu taru su so mutum idan kai baka soshi ba to duk son banza ne, sannan kace da mutanen duniya zasu taru suki wani daga cikinmu idan ka soshi to ya tsira kuma zaka kareshi" dafa cikinta tayi cikin tsananin kuka da tausayin kanta da abinda zata haifa tace "Allah wannan abinda yake cikin cikina ina roka mishi soyayyanka, ya Allah ka soshi koda mutanen duniya baki ɗaya zasu kishi, Allah wannan addu'an uwa ce akan ɗanta ɗan da zan haifeshi a gidan karuwai, ɗan da zan haifeshi babu uba, ɗan da aka kyamaceni sabida shi, Allah ka zama gatanshi" kuka take yi sosai tana rokon Allah kuma tasan addu'an uwa karɓaɓɓe ne a wajen Ubangiji. Tana cigaba da rainon ciminta badan taso ba saidan karɓan ƙaddara a duk yadda yazo maka, zaune take cikin dare ita kaɗai a ɗakin tana jin bayanta yana sarawa, kirjinta kwankwasonta duk suna mata azababben ciwo, addu'a take yi a cikin ruwan dake kofi tana tofawa, bayan ta gama ta shanye ruwan, ciwon ya kara karuwa ihu ta fara tana juyi a kasa, tana kuka tana neman taimako amma babu wanda yasan da zamanta babu wanda ya ko leƙo ta, tana birgima jin azaban naƙuda tana zufa duk sanyin da akeyi tana cewa "ya rabbi ka ɗauki rayuwata a wannan halin" da haka har taji kan yaro ya fito, nan ta fara sabon ihu har ta haihu a ɗakin bata san inda kanta yake ba, abinda take iya ji shine kukan jariri janyoshi tayi jikinta ta rikeshi gam, sai yanzu taga an turo kofan an shigo, idonta dake rufuwa ta zubawa kofan, wani ta gani sanye da bakin kaya ya rufe fuska, yana shiga ya amsa wayarshi, sama sama taji yana cewa "eh an haifi jariri yanzu a gidan kuma zamu kawoshi" gani tayi yazo ze kwace yaron, cikin wahala da gajiya ta rike yaron gam, kwace shi ya fara nan take ta fara kokawa dashi tana kare jaririnta da iya karfin da Allah ya bata, cizo ta gantsara mishi a hanu taki sakin fatar duk ihun da yake yi bata damu ba burinta yaji zafi ya bar mata jaririn, ruwan sama ne ya sauko me karfi da iska me tsoratar wa, ganin haka ya zame ya gudu, da rarrafe taje ta kulle kofan sannan ta dawo, kasa rufe ido tayi sabida gani take kamar zai dawo ya ɗauke mata yaron da har yanzu be daina kuka ba, da kanta ta yankewa yaron cibi, sannan ta goge duk wani jini ta kintsa ɗakin a daren, kwanciya tayi akan katifan sannan ta janyoshi jikinta ta kanƙameshi gam tasa mishi nono a baki, rufe ido tayi tana hawaye, ganin yana jin sanyi ta ɗauko zani ta sashi a ciki, rufe ido tayi bacci ya ɗauketa da jaririnta a jikinta. washe gari ta tashi cikin azaban ciwon ciki ta kalli jaririn dake bacci, murmushi tayi ganin haske ya haska mata fuskanshi, shafa suman kanshi me tsantsi tayi, gashinshi kamar bana jariri ba, fari ne sol kamar ɗan larabawa, a hankali ta tashi ta zauna ta ɗagashi tana kallonshi, buɗe ido yayi, murmushi tayi ganin wasu kyawawan idanu da Allah ya bashi, mannashi tayi da kirjinta tace "barka da zuwa duniya jaririna" hawaye ta fara, da kyar ta lallashi kanta ta kwantar dashi ta fita daga ɗakin ta nemo ruwan zafi tayi mishi wanka sannan itama tayi wanka, ragowan abincin taci sannan ta dawo ta kwanta, ji take soyayyan yaron yana cika mata zuciya musamman idan ya buɗe idanunshi suka haɗa ido sai taji jikinta yana sanyi. haka ta fara rainon jaririnta wanda ko suna bata sa mishi ba, saida ta samu sauki sannan ta fara zuwa aiki, yauma kamar koda yaushe gidan da take aiki ta shiga, matar tana ganinta tace "sai yanzu kika zo?" tace "ayi hakuri ɗana ne babu lafiya" tsaki taja tace "ɗan da ko suna baki sa mishi ba sabida rashin gaskiya, da ɗan halak ne ai da kin jima dasa mishi suna har rawan jiki zakiyi" shiru tayi amma fa ranta ya sosu, matar tace "koda shike wacce ta zauna gidan karuwai me ba zatayi ba? je kimin aiki nikam ban san amfanin surutuna ba" shiru tayi taje ta fara wanke wanken, badan anan take samun kuɗi ta siya abinci ta kula da ɗanta ba da bazata kara aiki anan gidan ba tunda ta faɗi waɗannan maganganun, har ta gama aikin sannan ta karɓi kuɗinta ta tafi, tana komawa gida ta saukeshi ta kwantar dashi sannan ta fito tana haɗa abinci, abida ce ta shigo tace "idan akwai abinda bani mana yunwa nake ji" abincin data dafa wanda zataci shi ta bawa Abida, karɓa tayi batasan shine iyaka ba tace "na gode" har ta fita sai kuma ga dawo, tace "ki kula da ɗanki sosai saboda wannan gidan ana sace yara, matar data buɗe wannan gidan zata iya ɗaukanshi a yadda yake jariri taje ta girmar dashi ta fara lalata dashi, bama wannan ba koda yana yaro karami zata iya koya mishi yadda zaiyi lalata da ita hakan ya faru akan idona idan so samu ne a ki ɓoye ɗanki kada ki bari tasan kinada yaro, sabida zata lalata rayuwarshi sannan tana zuwa kowane karshen wata, abinda yasa baki ganta ba shine taje kasar waje jiya ta dawo" a firgice ta kalleta, taɓe baki abida tayi tace "kwarai abinda yasa na faɗa miki sabida naga kinada hankali abincin da zakici kika ɗauka kika bani shiyasa na faɗa miki ki kare ɗanki" tafiya tayi, ido ta zubawa yaron tana kara juya maganganun a ranta, yaron da take jinshi kamar rayuwarta ba zata yadda wani mugun abu ya sameshi ba, tun yana karami yake da wannan masifaffen kyawun ya zama dole ta kareshi ba daga matar gidan ba har mutanen waje, buɗe ido yayi ya kalleta, dariya taga yayi mata, hawaye ya cika mata ido itama ta mishi dariya tace "yau zansa maka suna ɗana, karka damu da rashin uba da kuma haifanka da nayi bata hanyan aure ba, Inaso ka sani kaima ɗa ne kamar kowa" share hawaye tayi tace "kai kyauta ne Allah ya bani hakan yasa zansa maka suna NAWAL ma'ana KYAUTA" kafin ta karasa rufe baki ruwan sama ya sauko da karfi, kallon sama tayi ta fito dashi zuwa waje cikin farin ciki ta tsaya a tsakar gidan ruwan sama yana wankeshi, murmushi tayi tace "Allah ya amsa wannan sunan naka na kyauta shiyasa ya kara saukar da ruwan sama na kyauta a lokacin dana raɗa maka suna" ɗagashi tayi sama ruwan yana wankeshi tace "Allah ka wankemin ɗana, kasa ya zamo kyauta a cikin al'umma, kasa ya kare rayuwa daga sharri, kasa ya zamo garkuwa a rayuwar bayinka" saukeshi tayi taga yana dariya, murmushi tayi tace "yara idan ruwan sama ya dukesu kuka suke amma shi nawal dariya yake ina fatan ruwan sama ya zame mishi kariya a rayuwarshi, ina fatan ya samu duk abinda yake so a rayuwa a cikin ruwan sama" *Shima ɗa ne is 400 via 8144818849 Hauwa shuaibu mapi moniepoint, evidence via 08144818849* _Jiddah Ce....✍️_ [17/08, 11:03 pm] +234 814 481 8849: 🌸🌸🌸🌸🌸 *SHIMA ƊA NE* 🌸🌸🌸🌸🌸 Na *Jiddah S Mapi* *Chapter 4* ~Tun daga ranan bata kara fita dashi ba duk inda zataje a ɗaki take barinshi sabida so take ta kareshi daga kowane sharri, yau tun safe take bacci sabida gajiya yau babu zuwa aiki shiyasa take hutawa, hayaniya taji a gidan da sauri ta buɗe ido ta tashi, lekawa tayi taga faɗa ake akan mace harda wuka, rufe ido tayi ganin yanke yanke da suke ta koma ta kwanta shiru tayi kamar bata ɗakin. haka take rayuwa da ɗanta wanda har ya fara girma sannan yana kara kyau fiyeda yadda ta haifeshi, hakan yana daga cikin dalilin da yasa bata fita dashi sabida bakin mutane ita kanta tasan kyau shine dalilin shiganta wannan halin, a ɗaki take barinshi duk inda zataje, tasan da batada kyau da yanzu tana tare da iyayenta da kannenta, share hawayen tayi tace "tabbas KYAWUNA JARABTA TA bana fatan kyawun ɗana ya zama mishi jarabtarshi" haka har yaron ya fara wayo a gidan, matsalanta dashi yawan tambaya duk inda taje ta dawo sai ya sata a gaba yana tambaya ina taje, idan ta faɗa kuma ya fara mata tambayoyi, shiru tayi mishi tana cin abinci, yace "Ammi?" tace "na'am nawal" yace "meyasa kullum ina ɗaki?" tace "sabida banaso ka mutu" ze kara wani tambayan tace "shiru" shiru yayi har ta gama cin abincin sannan tayi salla ta kwanta yana gefe yana wasa tunani ta rinƙa yi har bacci ya ɗauketa. washe gari zata fita aiki tace "na tafi nawal" yace "ammi yau zan biki" girgiza kai tayi tace "a,a nawal sai wani lokaci" zaiyi magana kawai ta fita, yana zaune a ɗakin tun safe har yamma, ji yayi muryan mutane dayawa a waje, buɗe kofan yayi yadda yaga tana buɗewa idan zata fita, ya leka sabida ta hanashi fita, caraf idonshi ya haɗu dana hajiya bilkisu wacce take sanye da bakin glasses, sauke glasses ɗin tayi tana kallonshi, tace "wow wannan ɗan waye?" duk sukayi shiru sabida sun san ana ɓoyeshi hakan yasa bata sanshi ba batama taɓa ganinshi ba duk zuwanta gidan, da hanu tayi mishi alaman yazo, make kafaɗa yayi yana kallonta da idanunshi farare masu hasken blue a ciki, tamkar ɗan turawa musamman gashinshi data gani a harɗe, ze rufe kofan tasa hanu ta rike, yace "ammi ta hanani zuwa" hanunshi zata rike ya fizge, murmushi tayi tace "tunda nake da wannan gidan ban taɓa ganin kyakkyawan halitta irin wannan ba, zanso ganin wacece mahaifiyarshi" kuka ya fara ganin taki sakin hanunshi, kira tayi wasu maza suka shigo suka ɗaukeshi tana biye dasu suka fita, a wani jeep baki suka sashi sannan itama ta shiga suka bar wajen, ihu yake mata a motan yana kiran Amminshi, maida glasses nata tayi tana kallonshi. saida ta biya kasuwa kafin ta dawo gida a gajiye, ganin kofan a bude yasa tace "ya akayi nawal ya buɗe kofan?" shiga tayi, ledan hanunta ne ya faɗi ganin babu shi a ɗakin, dudduba ko ina ta fara a haukace take tambayan ina nawal? duk cikinsu babu wanda ya amsa mata, kuka ta fara tana neman nawal tana bi kowane ɗaki tana ɗaga musu labule tana kiran nawal nata, zama tayi daram a cikin gidan ta ɗaura hanu aka tace "na shiga uku nawal ina ka shiga? nawal meyasa zaka tafi ka bar Amminka?" Abida ce ta shigo gidan tana sanye da riga da wando, kallonta tayi tace "meya sameki?" tana kuka tace "banga nawal ba na tambaya kowa babu wanda ya amsa min banga nawal ba abida" fashewa tayi da kuka, abida tace "hajiya bilkisu tazo ne?" da shike suna tsoronta suka amsa mata da eh, kallon rahama tayi tace "dama na faɗa miki ki kare ɗanki daga sharrin wannan matan amma baki jini ba, Allah ya bawa ɗanki kyau da hajiya bilkisu ba zata iya kyafta ido a kanshi bataji tana sanshi ba gashi tazo ta tafi dashi, taimako ɗaya da zan baki shine kada kije inda take ki hakura domin zata iya sa a ɓatar dake" shiru rahama tayi tana kallonta har ta gama maganan, zata tafi tace "abida" tsayawa tayi, tace "ki taimaka min koda shine karshen taimakon da zakimin dan Allah ki faɗamin ina gidan hajiya bilkisu yake" shiru tayi tana kallonta, sai kuma ta kalli gefe da gefenta taga babu me kallonsu, cikin kasa da murya ta faɗa mata inda gidan yake, godiya tayi ta tashi, duk kiran da take mata bata juyo ba tafiya kawai tayi, bata cikin hayyacinta har ta shiga mashin domin zuwa gidan. garin gombe yanada girma ba lalle ta gane inda zataje ba sabida bata fita. Nawal yayi kuka har ya gaji, babban gida ne me matukar kyau suka nufa aka buɗe musu gate suka shiga, buɗe mishi mota tayi ya fito yaki fita, hanunshi ta damko ta fito dashi, yana tirjewa har ta shiga dashi ɗakin dake da bala'in kyau, shiga ciki tayi bayan ta rufe kofan ta shiga bathroom tayi wanka ta fito da towel ɗaure a kirjinta, yana zaune a kasa ya takura kanshi ya ɗaura kanshi akan gwiwanshi yana kuka, a gefenshi ta zauna ta zuba mishi ido, yanada bala'in kyau ga wani kwantaccen gashinshi dake tafiya da imaninta, hanu tasa a kanshi zata shafa yayi baya yace "nikam karki taɓani" dariya tayi sannan tace "kyakkyawan yaro tunda aka haifeka a bariki a barikin ma a gidan karuwai ba zaka iya gujewa asalinka ba, ko bakayi yanzu ba zakayi a gaba, gara ka hakura na koya maka kaga zaka tashi da kwarewa" mannewa yayi da bango yana girgiza kai, duk da be fahimci me take cewa ba amma yasan abinda amminshi kullum take cewa ne babu kyau kada ya kuskura ayi mishi, ganin ta fara rabashi da kayanshi ya fara ihu, rufe bakinshi tayi saida ta rabashi da kayan sannan ta tashi cikin tafiyan da take girgiza jiki taje ta kashe wutan ɗakin, ganin duhu a ɗakin ya kara ihu yana birgima a kasa. rahama cikin tashin hankali ta fito daga mashin ɗin ko kuɗin bata bashi ba, yana tambayanta ma ko kallonshi batayi ba, gate ɗin da abida tace mata shine gate ɗin gidan hajiya bilkisu ta fara bubbugawa ganin baya buguwa mata da kyau ta ɗau dutse ta fara buga kofan da karfin da Allah ya bata, megadi ne ya buɗe yana mata kallon sama da kasa yace "me kike bukata?" tureshi tayi ta shiga a guje sabida tasan zasu hanata shiga, yana binta yana cewa "ki tsaya ki gaya mana wacece ke?" ganin ya rike mata gefen hijabi ta bangajeshi ta shiga ciki, kofan ɗakin ta tura ta shiga, jikinta ne yayi sanyi jin ihun da nawal yake yi har muryanshi yana dishewa, kasa karasawa tayi jikinta ya fara rawa, a hankali take takawa zuwa ciki, hajiya bilki taji tana wani irin nishin data kasa gane na menene, a hankali ta buɗe kofan bedroom ɗin ta rufe ido sabida batason ganin nawal a wani halin da zaisa ta samu bugun zuciya, juyowa hajiya bilki tayi domin ganin wani me karfin halin ne ya shigo mata ɗaki babu excuse, nawal ganin amminshi ya gantsara mata cizo ya tashi da gudu yazo inda Ammi take ya rungumeta, jikinta yana rawa tace "nawal me tayi maka?" yana kuka yace "ammi ki kaini gida tana min wani abu kuma ina jin zafi" jiri ta fara ji, ta rike hanunshi ta kasa magana kawai take janshi zuwa waje. hajiya bilki ta tashi da bargo a jikinta tazo ta rike hanunshi, rahama ranta yana tafasa tace "sakeshi" "bazan sakeshi ba, ubanwa ya baki daman shigowa gidannan har cikin ɗakina?" tace "ki sakeshi nace" tace "ba zan sakeshi ba saina gama abinda zanyi dashi" sakin hanun nawal tayi ta juya baya kamar zata tafi, nawal yace "ammi ki rikeni zata kasheni" flower ves dake kusa da bakin kofa ta ɗauka, cikin zafin nama ta juyo ta kwala mata akai, rike kanta tayi tana kallonsu ta fara silalewa kasa, faɗuwa tayi tim daga nan bata kara motsi ba, nawal yace "ammi ta mutu?" tace "mu gudu nawal nima ban sani ba" hanunshi ta rike suka fita a guje, saide abinda ta gani yasa ta tsaya turus, police ta gani sun kewaye gidan, jikinta yana rawa take kallon nawal, ta saki hanunshi ganin police ɗaya ya shiga ciki, tace "nawal ka gudu duk yadda za'ayi kada ka tsaya sai inda Allah ya tsayar da kai" shiru yayi domin ko zai mutu ba zai iya tafiya ya bar amminshi ba, koma meya sameta zasu zauna tare. police ya fito yace "tabbas ta kasheta domin bata raye ta mutu" jikin rahama ya fara rawa ganin sun sa mata ankwa sun fara janta, kuka ta fara tana cewa "wallahi cutar da ɗana tayi dan Allah kada ku tafi dani" nawal yana cewa "ku saketa karku tafi da ammi na" a mota suka sata, tace "nawal ka tafi karka bini ka gudu nawal" har suka fara tafiya da ita be tsaya ba binsu, ɗaukan hotonta aka fara da video aka fara yaɗawa a duniya tayi kisa, nawal binsu yake yana gudu motan yana gudu har suka isa prison, kayanta aka sata canjawa tasa uniform aka shiga da ita ciki nawal duk yadda yayi ya shiga sun hanashi, waje suka fitar dashi yana kallo ana dukan amminshi ana gana mata azaba na cewar tayi kisa, tana ihu yana jin ihun har cikin ranshi, a bakin kofa suka wurgar dashi, ya kwanta a kasa bai yadda ya tafi ba yasa a ranshi anan ze rinƙa kwana har sai amminshi ta fito. bacci yayi a wajen be tashi ba saida safe yunwa yana damunshi ya tashi ya zauna yana kallon masu shige da fice, hankalinshi akan ammi amma sunki bari ya shiga, a hankali ya tashi jin yunwa na damun cikinshi, bakin titi yaje ya tsaya

Chapter 2 of 17