ce ta faɗa musu kudirinsu na son auran fatima, babanta ne yace "to tunda yarinya tana so shima yaro yanaso ba zamu hana ba, to amma kin san maganan aure dole sai munga dangin mahaifinshi ina nufin koda mahaifinshi bai zo ba mu samu ko kaninshi ko yayanshi da zamuyi magana"
shiru sukayi, gaban nawal ya fara faɗiwa, Ammi kuma wani abu ne ya tsaya mata a wuya, ta kasa haɗiye miyau, babanta yace "shin ina mahaifinshi ya rasu ne? ko yana raye? idan baya raye ina kaninshi ko ɗan uwanshi na jini?"
shiru Ammi tayi ta kasa amsawa, kanin baban fatima yace "ya zama dole ku amsa mana wannan tambayan domin neman aure ba wasa bane, ina mahaifinshi?"
ammi ta nuna kanta tace "nice mahaifiyarshi kuma nice mahaifinshi"
da mamaki sukace "kamar yaya kina mace ki jagoranci aure?"
tace "nawal ba..."
nawal yace "banada uba"
kallonshi sukayi "bakada uba kuma?"
jijjiga kai yayi yace "eh babu aure aka haifeni"
babanta yace "ana wata ga wata ɗin kenan, kana nufin bata hanyan aure aka haifeka ba? kai ba ɗan sunna bane?"
Ammi ranta yana tafasa tace "kada ku kara ce mishi shiba ɗan sunna bane kawai dai tsautsayi ne yasa aka haifeshi bata hanyan aure ba"
"babu wani tsautsayi kina nema dai kawai ki kare kanki, ta yaya zamu ɗauki ƴa mu bawa wanda bayada asali? ta yaya zamu bawa wanda akayi zina aka haifeshi ƴarmu? so kuke a rama akan ƴaƴanta suma su haifi shegu? zuri'a ya taɓarɓare? ai bamu san kai mutumin banza bane...."
cikin tsawa Ammi tace "ya isheku haka, nawal ba shege bane nice shegiya domin baida laifin komai, baisan komai ba shi haifansa akayi babu wanda zan kyale matukar ya rinƙa faɗa mishi munanan maganganu, nawal ba shege bane rahama ce shegiya tunda ita tayi zina ta haifeshi...."
ganin har jikinta yana rawa nawal yazo ya riketa yace "Ammi please kiyi shiru"
fatima wacce ta ɓuya a bayan kofa tace "baba na yadda wallahi na yadda zan aureshi ko baida uba"
mamanta ne ta tashi tace "fatima kinyi hauka ne zaki haɗa zuri'a da shege? to wallahi matukar kikace zaki zaɓeshi saide ni ki rabu dani zan yafeki duniya da lahira fatima"
kuka ta fara, baba yace "barta yarinya ce ba zata gane matsalan yanzu ba saita haifi yara zata gane inda matsalan yake, kaida samun aure a gidan tarbiya waɗanda suka san darajan kansu zaiyi wuya, saide ka nemo daidai kai wacce itama ta hanyan zina aka haifeta kaga babu me yiwa wani gori cikinku amma ni gaskiya ku tashi ku fita ku barmin gida"
Ammi tace "ko baka faɗa ba zamu bar gidanka kuma insha Allah ɗana ba zai rasa mata ƴar gidan tarbiya ba aniyanka ya bika"
hanun nawal ta rike suka fita, kamal yana tsaye a gefe yayi shiru abin bai mishi daɗi ba sam, har suka tafi jikinshi a mace, Ammi banda kuka babu abinda take yi, tana ganin ta gama cutan rayuwan nawal domin tabbas zai samu matsala wajen neman aure, kamal har kofa ya ajesu sannan yace "kuyi hakuri Ammi bansan haka zai faru ba da bazan fara ba tun farko kuyi hakuri abokina"
yace "karka damu kamal duk a cikin rayuwa ne"
hanunshi rike dana Ammi suka shiga gidan, momy tana zaune a falo tana kallo suka shigo, da ido tabi Ammi sannan a ranta tace "wannan cikin ba dai ki haifeshi ba in shegen ne zan bari ya zauna amma banda ɗan halak ƴaƴana ne kaɗai ƴaƴan halak"
tagumi tayi a bakin gadon, ya durkusa a gabanta yace "ammi kada ki damu kinji? amma nasan za'a samu matsala a neman aurena me zai hana mu koma kauyenku nayi aure acan?"
tace "nawal babu abinda zai kara kaini kauyenmu, nawal mutanen kauyenmu sunfi kowa sanin kamun kan dana tashi dashi, a lokacin da ƙaddara bata hau kaina ba kowa yanason ƴarshi tayi ƙawance dani, nawal saida ƙaddara ya hau kaina suka manta duk kyawawan halina, suka ɗauki sharri ɗaya daya afku min suka rinƙa ƙyarata da hantara ta, ciki harda mahaifiyata wacce ta kasa karɓan ƙaddara wacce ta manta da wacece rahama a baya, nawal ko kallon mamana banason nayi sabida itace silan faɗawata cikin wannan bala'in, data jani a jiki da zan haifeka a kauyenmu duk zagin a zasumin zan daure na girmar da kai, zanyi sana'a kamar yadda na saba na ciyar da kai, amma ta koreni sabida maganan mutane wai batason abin kunya, batasan idan na tafi yunwa yana iya sa mace yin zina ba, batasan a gidan karuwai na haifi cikin data koreni sabida shi ba, batasan zan iya komawa ruwa ba idan wahala yamin yawa, a halin yanzu ko sunan kauyenmu tufan banason ji, mutane biyu nake tunawa sune kanwata nana da kanina yaseer su biyu ne kaɗai nake tuna ko wane hali suke ciki, ko tayi aure? ko tayi karatu kamar yadda nake faɗa mata kuma nake dagiya a kullum? ko ta samu miji me hankali kamar yadda nake mata addu'a, ko ta samu miji marar hankali, ko yasir yayi aure Allah ne kaɗai masani"
tace "nawal zaka samu mata me sonka wacce zata soka a kowane hali kake ciki, ba kuma zata iya gudunka ba ko wani hali ka shiga, nawal a lokacin dana haifeka nayi addu'a Allah ya baka matar da zata tsaya maka wacce batada tsoro zata iya fuskantar duk matsalanka, kuma zaka samu"
yace "na gode Ammi"
tashi yayi tunawa da wayan dady na jiya, da sauri yace "Ammi zan fita"
tace "ina zakaje?"
yace "zan dawo bada jimawa ba"
fita yayi da sauri, ɗakinshi ya shiga yasa bakaken kayanshi amma baisa mask ba, ya ɓoye bindiga sannan ya fita daga gidan.
_Jiddah Ce....✍️_
08144818849
[17/08, 11:13 pm] +234 814 481 8849: 🌸🌸🌸🌸🌸
*SHIMA ƊA NE*
🌸🌸🌸🌸🌸
Na
*Jiddah S Mapi*
*Chapter 18*
~Mashin ya hau me kafa biyu sannan ya tafi inda yaji dady yana faɗa jiya, babu kowa da alama basu fito ba, ya samu gefe ya zauna a bayan bishiya ta yadda ba zasu ganshi ba, har ya gaji da zaman ya tashi zai tafi yaga zazzafan mota yazo wajen, ɓuya yayi yana kallo yaga motan ya tsaya a daidai tsakiyan titi inda dady yace Ahlam ya tsaya, fitowa yayi kamar wanda zai duba mota, nawal ya kare mishi kallo sai yanzu yaga tsananin kama da sukeyi dasu naseer, yace "koda na girmi Ahlam ba lalle ya zama sosai ba, sabida zamuyi sa'a dashi, meyasa dady yake koya mishi cin amana da zamba cikin aminci? meyasa ya koya mishi yadda zai cuci wanda ya yadda dashi ya bashi amanan gidanshi da komai nashi, ya zama me bashi tsaro na musamman duk inda zaije koda wajen sirri ne tare suke tafiya"
gani yayi Ahlam ya juya baya ya ciro bindiga, waro ido yayi ganin ya ɓoye bindigan a baya yana knocking na glass ɗin motar alaman Abba ya fito, can saiga motar dady ta tsaya a gaban nasu, gani yayi dady ya fito Abba ya fito shima, da mamaki sosai akan fuskan Abba yace "Ahlam meyasa ka tsaya da mota?"
dariya yayi sosai sannan yace "mahaifina ne yasa"
yace "mahaifi kuma? Ahlam kai maraya ne iyayenka sun mutu tun kana yaro taya akayi ka samu mahaifinka?"
nuna dady yayi da bindigan sannan yaje ya rungume dady yace "kai wani irin wawa ne Alhaji usman makama? shin ka manta tsohon gaban dake tsakaninka da mahaifina Alhaji Alhasan medara? meyasa bakada kula baka kula da kamannin da nakeyi dashi ba? to ai mun jima muna shirya wannan ranan dama ta kan ƴaƴanka zamu fara wato ibtisam da janna amma munfi so mu gama da kai kafin mu koma kan ƴaƴanka sannan dady na ya aure matarka idan naga dama na auri ƴaƴanka"
Abba ranshi yana tafasa yace "Ahlam dama kai macuci ne? Ahlam dama..."
bindiga ya nunashi dashi yace "kwarai kuma yanzu zan kasheka domin na cika burin mahaifina nasan zai mutu yana alfahari dani"
nawal ganin sunyo kan Abba sun fara duka yaji ba zai iya tsayuwa yana kallon hakan ba, kallon wani da yake wucewa akan keke yayi tsoho ne ya tsayar dashi, ya durkusa kasa yace "dan girman Allah baba ka bani kayanka na sauya da nawa wancan mutumin zan taimaka"
kallon Abba da ake daka ga kuma bindiga dake hanunsu yayi, ya kalli nawal da babu alaman karya ko cutarwa a tare dashi, sauka yayi a keken yace "zan baka yaro Allah ya maka albarka Allah ya haɗaka da alheri duniya da lahira yasa kafi karfin makiyanka"
yace "ameen baba"
tsoffin kayanshi ya cire ya bashi shima nawal ya cire bakin kayan ya bashi sannan yace ya tafi sabida kada su ganshi suyi harbi, ya tafi shi kuma nawal ya ɗauko alebo (harami) da tsohon ya bashi ya ɗaure fuskanshi ta yadda babu wanda zai ganeshi, bindigan ya ciro sannan yabi ta bayansu, a lokacin Abba yana kwance a kasa suna mishi dukan mutuwa, bindigan ya harba kafan dady bullet ya sauka, waro ido yayi ganin ya harbi dady, Ahlam a razane yake kallon dady, ya kalli nawal daya zubawa bindigan ido shima da alama baisan harbin zai taɓa dady ba, Ahlam shima bindiga ya ciro zai harbi nawal ruwan sama ya sauko kamar da bakin kwarya ga wani iska me karfi, da gudu nawal yazo zai janye Abba daga wajen domin ya tseratar dashi Ahlam ya daga bindiga a cikin ruwan zai harbeshi, kwacewa yayi suka fara kokawa, Ahlam kokarin cire alebo yake shi kuma nawal kokarin ɓoye fuskanshi yake bayaso ko da wasa su ganshi, ruwan sama kara sauka yayi da karfi, yayi nasaran ture Ahlam sannan ya ɗaga Abba dake kwance rai a hanun Allah, ƙafan Abba yana jini ya sashi a mota, Ahlam jin ciwo da dady yake kira ga jinin dake zuba sabida hujin bullet yayi saurin komawa wajen dady yana duba ƙafan, a mota nawal yasa Abba, kamal ya koya mishi mota amma be kware ba.
sa Abba yayi ya shiga motan da gudu ya bar wajen Ahlam sai harbi yake amma iskan ruwan saman ya hana bullet samun su nawal.
har ya shiga cikin gari dashi yana lekawa yana cewa "sannu"
sai ɗaga kai Abba yake yi, asibiti ya wuce dashi na cikin gari, aka karɓeshi emergency sabida sun san matsayinshi, nawal yace "gara na tafi idan ya tashi kada ya sanni"
zai tafi dr yace "ga magungunan da za'a siyo"
ya karɓi takaddan sannan ya fita, da kafa ya tafi ruwa na dukanshi yaje ya siyo magani da ruwa sannan ya dawo, ɗaurawa Abba ruwa akayi sannan aka mishi allura duk ciwon da yaji sukayi dressing, yana kwance har yanzu be buɗe ido ba, fuskanshi ya kumbura sosai, nawal yace "ya rabbi kasa yanada rai bai mutu ba ameen"
kasa tafiya yayi ya zauna kusa dashi a bakin gadon, shiru yayi yana tuna harbin dady da yayi da hanunshi, ya tsani dady da family ɗinshi amma baiso ya harbi mahaifinshi ba, godiyan da yake yiwa Allah shine basuga fuskanshi ba kuma da wuya su ganeshi, yana wajen Abba har dare yayi bai farka ba, ya kira kamal yace yaje ya faɗawa Ammi ba zai samu dawowa ba akwai aikin da yaje, zama yayi a wajen Abba sabida bayada tabbacin Abba zai farka.
a wajen ya kwana akan kujera yayi bacci, Abba motsi ya fara da hanu a hankali yake buɗe baki yana cewa "ruwa..ku bani ruwa"
buɗe ido yayi yaga nawal kwance a kusa dashi ya rufe jikinshi da alebo yana bacci kamar zai faɗi akan kujeran kuma da alama a wajen ya kwana, yace "ruwa..ka bani ruwa"
firgigit nawal yayi ya yaye alebon sannan ya kalli Abba, wani murmushin da yayi na jin daɗin tashin Abba yace "ka tashi? na gode Allah"
muryanshi harya dashe sabida sanyin ruwan daya dakeshi kuma ya kwana da kayan a jikinshi ba tareda ya sauya ba, ruwa ya bashi, ya komar dashi ya kwanta, Abba yace "na gode"
shiru nawal yayi, rufe ido yayi ya kara komawa bacci, nawal yana wajen har yayi sallan azahar, koda ya shigo yaga Abba ya tashi ya zauna jikin da sauki, juyawa yayi zai koma Abba yace "zo mana"
a hankali ya koma, Abba ya nuna mishi wajen zama yace "zauna"
a gefenshi ya zauna, yayi shiru shima Abba shiru yayi yana kallon yaron, ji yake yaron yana shiga zuciyanshi, yaji kamar ɗanshi ne na cikinshi, bai taɓa samun wanda ya taimaka mishi gadan gadan ya sadaukar da ranshi ba sai wannan yaron, a hankali yace "ya sunanka?"
yace "nawal"
jinjina kai yayi sannan yace "nawal dan Allah ka faɗamin gaskiya kaga an cutar dani na yadda da mutum ya cutar dani wanene kai? kuma meyasa ka taimakeni?"
shiru yayi yana tsoron bashi amsa, ya riko hanun nawal yace "na rantse da mamana kuma na rantse da babana na rantse da kaina koda ka faɗamin kai wanene ba zan cutar da kai ba zan zauna da kai koda kai ɗin wanene koda ko kai ɗin makiyina ne"
ya kalleshi da mamakin irin rantsuwan da yayi, yace "haramun ne mutum yayi rantsuwa da wani wanda ba Allah ba, haramun ne kayi rantsuwa da mamanka ko babanka babu abinda zaka rantse dashi sai Allah sai kuma alkur'ani, rantsuwa da wani shirka ne"
shiru Abba yayi yana kallonshi, babu wanda ya taɓa mishi gyara koda ya aikata kuskure kowa yana tsoron gyarashi sabida yanada kuɗi yanada matsayi, yace "na gode"
nawal yayi murmushi sannan yace "sunana nawal rahama"
Abba yace "okay daga ina kake?"
yace "daga kauyen gombe"
"meya kawoka Abuja?"
yace "aikin gadi nakeyi a gidan Alhaji Alhasan medara"
shiru Abba yayi, kana yace "naji yana waya ne bai san ina jinshi ba naji duk plan ɗin da sukayi shiyasa naje wajen domin na taimakawa wanda suka shiryawa mugunta"
Abba yace "nawal na yadda da Ahlam harna faɗa mishi wasu sirrikana da suka shafi rayuwa ta, na bashi amanan yarana ya zama shine me kula dasu idan bana gida ashe shi ɗin yaron makiyina ne, nawal babu wanda ya tsaneni nima na tsaneshi kamar Alhaji Alhasan ko ganin juna bama son yi, ashe Ahlam dana yadda dashi Ahlam da yake shiga duk inda yaga dama a gidana ɗanshi ne"
sukayi shiru babu wanda ya kara magana, dr ne ya shigo ya duba Abba ya kara mishi allura, saida ya fita Abba yace "nawal"
a nitse yace "na'am"
"zaka iya aiki dani? ina nufin zaka iya zama personal bodyguard ɗina? zaka rinƙa bawa ƴaƴana mata guda biyu da ɗana namiji ɗaya kariya ka rinƙa kaisu makaranta da kuma duk inda ya kama zasu je? Idan ka yadda zan baka matsayin p.b a gidana wato personal bodyguard"
shiru yayi yana nazari Amminshi kaɗai yake tunawa amma ai yanada bukatan aiki sabida baya taɓa kuɗin daba nashi ba yaci, duk wani kuɗin da yasan ba haƙƙinshi bane baya ci saide ya tara idan bukatanshi ya tashi wa marasa karfi ya biya musu"
abba ya kara cewa "ba zan takura maka ba amma zanso hakan sabida naji ina sanka kamar ɗan dana haifa, ba kowane yaro bane zaiyi abinda kayi koda ko ɗan cikinka ne shiyasa ka kara samun matsayi a wajena"
a hankali yace "na yadda zanyi duk abinda kace"
murmushi yayi yace "na gode nawal daga yau kaine driver ɗina kuma kaine bodyguard na yarana da matata, zan rinƙa biyanka albashin dubu ɗari uku a kowane wata"
sunkuyar da kai yayi yana murmushi a ranshi yace "na godewa Allah na samu aiki hakan zai kara nesantani da cin kuɗin haram, zan fara yiwa Ammi siyayya na rinƙa kula da ita da aikin da nayi da karfina halal ɗina zan fara ci kamar yadda Ammi take cewa"
Abba sai kallonshi yake yadda yake maganan zuci yana murmushi ya nuna mishi yaji daɗin aikin, Abba yace "zaka iya dawowa gidana da zama domin aikinmu na iya kaiwa har dare"
a hankali yace "to zan dawo amma mahaifiyata tana gidan Alhaji Alhasan kuma da wuya ta yadda ta bar gidan sabida itama aiki take yi"
yace "babu damuwa zaka iya zuwa kullum ka dubata"
yace "na gode"
yaci gaba da kula da Abba, wayar Abba ya faɗi shiyasa basu kira gida suka sanar musu ba, yace kawai saiya samu sauki zasu tafi, yau kwanansu huɗu a asibitin
janna ce zaune akan sofa ta ɗaura kafa ɗaya akan ɗaya, wandon jinx blue ne a jikinta da riga shimi sky blue, kanta yasha gyara tasa mayafi siriri glasses na rashin mutunci data saba sawa baƙi tasa a idonta, gabanta kwalaben wine ne da kofunan glass, takalmin kafarta me tsini ne sosai shima sky blue sauti ke tashi a cikin falon gefe kuma kawayenta ne duk sunsa kaya sky blue sunyi bala'in kyau kowacce da glasses a idonta suna danna tsadaddun wayoyinsu, janna ta zuba wine a cup ɗin ta mikawa kowa sannan suka haɗa sukayi cheers, shanyewa sukayi tana rufe ido sabida gas ɗin ciki tace "lokacin yanka cake yayi"
duk suka tsaya kusa da ita itama ta tashi ta rike iphone16 zata yanka cake dashi, har zata fara yankawa tace "wait banga unty ibtee ba ya zama dole mu jirata"
tsayawa akayi saida ibtisam wacce ta shiga damuwa sabida rashin jin labarin Abba ta fito sanye da black abaya tayi kyau sosai amma fuskanta babu walwala tunani ya taru ya mata yawa ga tunanin Abba ga kuma tunanin wannan ɓarawon daya kasa gushewa a ranta, janna tana ganinta tazo da sauri taja hanunta tace "ke muke jira"
murmushin dole tayi sabida kawayen janna suna wajen, fara yanka cake sukayi kawayen suna tafi suna mata "happy birthday to you, happy birthday to you, happy birthday classy janna happy birthday to you"
tafi sukeyi ta fara sawa ibtee a baki sannan tasa musu suma suka sa mata, celebrating suka fara janna sai rawa take tana jin daɗi a ranta, tunda Abba yayi tafiya a cewarta, ta samu freedom sai yawonta take yadda taga dama, duk wani party da kawayenta da abokanta suka haɗa sai taje, yau birthday ɗinta ma zasuje da dare suyi celebrating a wani hotel hall ɗin data kama da makudan kuɗaɗen Abba data sace dalolin da suka jima da naira ɗin data sace babu jimawa, duk wani kuɗin da janna take wasa dasu na Abba take sata, Ibtee tazo kunnenta tace "janna ki daina wannan rawan karki manta fa yau kwana huɗu ba'asan inda Abba yake ba, p.b Ahlam numbernshi baya tafiya shima Abba wayarshi a kashe kuma kin san basu taɓa yin tafiya irin haka ba"
kallon ibteen tayi sannan taja hanunta zuwa tsakiyan falon ta fara rawa da ita, ibtee zatayi magana ta juyata ta yadda dole saita fara rawa, kawayen janna suka fara musu spray babu yadda ibtee ta iya dole ta biye mata suna rawan.
an sallami su Abba yau kuma Alhmdllh jikinshi yayi sauki ya samu kulawa sosai daga likitoci sannan nawal ma yana bada gudunmawa sosai wajen kula dashi, tare dashi suka shiga motan Abba yana gidan baya shi kuma nawal yana mazaunin driver, fita sukayi a asibitin, Abba yace "baka driving da gudu meyasa?"
cikin sanyin muryanshi yace "ban kware a driving ba abokina ne yake koyamin"
yace "okay zaka kware a hankali kuma zaka rinƙa zuwa wajen koyan mota sosai zaka kware tunda ka iya"
yace "to"
Abba ya lura yaron kamar wanda ya taso a takure baya sakin jiki duk shaƙuwan da zakayi dashi, baya yawan magana saide ya bada amsa, wani ma yanaji zaiyi shiru ba dan raini ba sai dan rashin sabo da cikin mutane da kuma takura daya girma a ciki, yi yayi kamar bai san gidan ba abba ne yake nuna mishi hanya har suka isa, hon yayi ba'a buɗe ba, yayi ta hon babu wanda ya buɗe, Abba zai fita nawal yace "bari na buɗe"
zuwa yayi ya tura gate ɗin sannan ya dawo yaja motan zuwa ciki, Abba yayi mamaki da babu megadi "ina yaje?"
tsaki yaja har nawal yayi parking a compound ya buɗe mishi marfin motan ya fito, bin cikin gidan yayi da kallo, fulawa sunyi tsayi sosai sun wuce misali a cikin kwana huɗu da yayi gidan yayi ƙura kamar ba'a wanke ba, saɓanin idan yana gida kullum sai a wanke, hasalima masu aikin baccinsu suke yi a karkashin bishiya kan grass carpet ɗin da yake bada iska me daɗi, a fusace Abba ya karasa wajen cikin tsawa yace "ubanme kuke yi a kwance?"
duk suka tashi a firgice suna kallonshi, kowa yayi zaton ɓata yayi kamar yadda sukaji a rediyo, cikin rawan jiki kowa ya fara neman hanyan kama aikinshi, yace "ku dakata dukanku"
tsayawa sukayi, cikin rawan murya tsaban ɓacin rai wato mutane idan kana wajensu sunada amana idan baka nan suci amanarta su kasa kula da abinka? yace "duk na koreku babu me kara aiki a gidana na sallameku"
zubewa kasa sukayi suka fara bada hakuri, yace "na baku minti goma ku kwashe komai naku ku bar gidannan idan kuma kun kara koda minti ɗaya akan minti goman dana baku kunfi kowa sanin me zai biyo baya lokacinku ya fara 1..2..3..4.."
da gudu kowa ya fara tattara abinda yasan nashi ne suka bar gidan dan sunfi kowa sanin waye shi, ya kalli nawal dake tsaye a gefe yace "muje"
binshi nawal yayi suka shiga ciki, tun daga nesa yake jin sautin waka yana tashi a falon, da farko ya zaci kunnenshi ke mishi gizo saida ya kusa sosai da falon yaji tabbas sautin waka ne yau yake tashi a cikin gidanshi, wakan ma bana masu hankali ba, jikinshi har yana rawa tsaban ɓacin rai, wato basu damu da ɓatanshi ba waka ma suke ji babu wanda ya damu?
tura kofan yayi, ibtisam wacce idonta akan kofa ko zataga mamee wacce ta fita zuwa police station domin sanar da ɓatan mijinta tareda jaad suka tafi, taga abba ya shigo, zaro ido tayi tana kallonshi, murza idon tayi domin tabbatar da shi ɗinne ko kuɗinta ne, tabbas Abba ne, janna ta juya baya tana karya waist nata cikin rawan take kaiwa kasa tana tashi sama, juya mazaunanta take yadda taga dama tana bin wakan kamar a club take, Abba ya kasa magana ji yayi idonshi na rufewa tsaban tsananin ɓacin rai, ibtee ce tace "ja...ja...ja..janna ga Abba"
bata jita ba sabida sautin yayi yawa, Abba jijiyan kanshi sun tashi telephone na gefenshi yasa hanu yaja sannan ya kira wasu numbobi yayi magana, yana huci yaje ya kashe wakan, janna cikin masifa tace "wani ɗan isk..."
ido huɗu sukayi da Abba wanda idanunshi suka rikiɗe suka koma jajur, kawayenta suna ganin haka kowa ya fara ɗaukan jakanshi zasu gudu, rufe kofan Abba yayi yana kallonsu baice komai ba, janna da jikinta ya fara rawa tace "dan girman Allah ka yafeni"
baiyi magana ba kuma bai matsa a bakin kofan ba, saida yaji karan mota sannan akayi knocking ya buɗe kofan, ibtee idanunta suka kara girma ganin police ne Abba ya kira, yace musu "bismilla ku shigo"
shigowa sukayi, janna ta fara ihu tana rokon Abba, a lokacin nawal ya shigo da kayan Abba daya bari a mota, ganin yaran tsaye cirko cirko da wancan fitsararriyar daya gani a wajen party ranan, da kuma wacce ta taimaka mishi a ranan daya shigo ga kuma police, ibtisam da mugun mamaki take kallon nawal wanda shima ya zuba mata ido suna kallon juna, kawar da kai yayi kamar baya kallonta, Abba yace "duk ku kamasu da laifin mayar min da gida club"
ya nuna harda janna, shirin kamasu aka fara, janna ta fara kuka, Abba yace "kafinnan bari na gabatar musu da wani"
ya riko hanun nawal yace "wannan shine sabon p.b ɗina shine zai rinƙa driving ɗinku sannan shine zai rinka kula da shiga da fitanku wannan da kuke gani a tsaye anan yafi min ke muhimmanci"
ya nuna janna dake tsaye ansa mata handcuffs, yace "yafi min ke sabida ya ceci rayuwata kuma ya hana idonshi bacci na tsawon kwana huɗu yana kula da wanda bai san daga ina yake ba baisan waye shi ba, amma keda kike ƴata baki damu ba janna kinzo kin haɗa birthday party ɗinki a gidana kina rawa baki damu da inda nake ba, kinsan na haramta shagalin birthday amma shine kikayi a bayan idona baku sani ba ko na mutu ko ina raye shagalinku kawai kuke yi, wannan shine ya ceceni a lokacin da nake tsananin neman taimako"
yace "officer ku tafi dasu sannan kada a bada belin kowa saina bada umarni"
officer yace "an gama sir"
kuɗi me yawa ya basu, ƴammatan sai kuka suke suna rokon Abba ya taimakesu yasa a sakesu, ko kallonsu baiyi ba, ibtisam ma ansa mata ankwa zasu wuce
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 17