Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
a fili. Me yasa ita ba'a mata haka? Idan kyaune tana dashi uwa ,uba ta fito cikin gata iyayenta attajiran masu kud'i ne gaba da baya, but still ta kasa samun attention da Bahiyya ke samu duk da cewa attention d'in was not in a good way, amma tasan deep down akwai dubbunnan mutane dake wishing ina ma sune Bahiyya suna kuma admiring nata from a far. Halin mahaifiyarta da irin gidan data taso yasa ake shakkar tunkararta. Tana da kyau, ilimi, hak'uri ga addini. Kwas-kwas shege k'aran takarmin Aisar ya cika cafeteria d'in kowa ya maida hankali kan k'ofar daidai Susu da Fadila na buɗewa Aisar ta wani sawo kai kaman wata sarauniya. Tunda labari ya baza gari Enzo ya yi having sex da ita jinkai da isan ta ya sake tsanani ji take babu wanda ya kaita sa'a musamman yanzu da mata da yawa suke son suga sun shiga jikinta saboda abunda ya faru, suna ganin ta gama cinyewa a rayuwa babu abunda ta rasa. Da wani murmushi ta shigo tana cilla hannu dayasha uban farce. Daga can gefe Nabila ta damke fork dake hannun ta tana bin Aisar da wani irin kallo ta k'asan ido. Shiru cafeteria d'in ta d'auka har ta isa tebir nata da sauran click nata suka zauna kowa ya fara buɗe abincin sa. Jakarta Aisar ta buɗe ta ciro d'an k'aramin mudubi tana sake gyara fuskarta kafin ta d'auko hadaddiyar wayarta ta ta lalubo number Enzo ta danna masa. Gaba d'aya tebir nasu ya yi shi kowa ya zuba mata yana son ji yanda alakar su take dashi yanzu kama yanda take tabi tana cewa suna dating. Har wayar ta gama ringing ba'a d'aga ba ta sake danna masa wani kiran amma shiru babu amsa. Saida tayi masa wajen kira biyar babu amsa jikinta duk ya yi sanyi ga borin kunya duk ya kamata ta gama cika baki gashi yana neman zuba mata k'asa a ido. Daga gefe Nabila tayi wani irin murmushi da ita kad'ai tasan ma'anan shi. Wani kiran ta sake danna masa gabanta n fad'uwa yanzu idan bai d'aga ba shikenan ya gama da ita. Tana gab da tsinkewa ya d'aga wannan murya tashi so deep yace "Who the f*ck is this?" Yanda tayi wani far da ido tare da sakin murmushi sai ka rantsa wata kalma ya gaya mata mai mugun dad'i. Murya ta sake d'agawa da yanga tace "Hi, Enzo ,Honeey." Shiru ya ratso daga b'angaren sa na y'an sakanni kafin yace da wani irin disgust "Listen you stupid b*tch. Am not your Honey and Don't, i mean don't ever call me again" Sai kit ya kashe wayar. Ranta in ya yi duba ya b'aci ta had'iye wani abu mai d'aci daya tukare mata makogaro. After the passionate moment nasu shine zai dinga zuba mata irin wannan zagi duk tabi ta yad'a gari yanzu shi saurayin tane?. To wlhi saidai ya yi duk abunda zaiyi amma wlhi soyayya da ita ya zama dole. Maimakon ta cire wayar daga kunne saita barta tana cigaba da murmushi kaman yana kan layi. D'an far ta sake da ido kafin tace "Ok i will see you later Babe" Ta janye wayar da kunnen tana murmushi amma ranta kaman zuciyar ta zatayi bindiga. Kowa kallont yake da admiration sai kuskus ake yi banda Nabila da idonta ya wani mugun rinewa tana cigaba da chaka fork d'in dake hannun ta cikin abinci. Kome ke ranta? Allah masani ➺➺➺➺➺➺➺➺ Sosai kid'a ke tashi don har waje kana ji samarin unguwa sai tashewa suke suna shewa. Manya da dattijai da suka mallaki hankalin kansu suna ta Allah wadai da irin wannan rayuwa. Babu wani abu da zasuyi domin sun gaza tashin ta daga unguwar saboda tarbiyar yaransu. An kai k'arar ta hukumar k'are hakkin d'an adam a banza, sun kaita hisba shima a banza ,sun kaita police station shima a banza. Da zarar sunzo kuma sai kaji shiru zancen ya mutu. Saboda haka suka zubawa sarautar Allah ido. Kwana biyu sosai tsegumi ya fara tashi na an daina ganin Bahiyya tana wucewa makaranta. Tun abun ba ana d'aukan sa sosai ya zama abun magana a unguwar duk inda ka wuce ana maganan an daina ganin Bahiyya. To kunsan malam Bahaushe da tsegumi da gulma da munafurci. Kowa da irin yanda yake bada labari. Wasu suce Maa ta siyar da ita. Wasu suce ta kasheta ta b'oye gawarta. Wasu suce aa ita Bahiyya ce ta gudu. Labari dai kala-kala ko ina kaje kowa da nashi labarin. Zakayi mamaki yanda duk inda ka shiga zakaji ana maganan Bahiyya. Da yawa zakaji suna jimantawa da kuma nuna tausayin su a kanta. Su sun sani yarinyar bata tab'a wani abu da zaisa a zarge taba amma kunsan malam bahaushe ,koda baka da wani hali wani naka yanayi kai ma sai anyi jefeka da wannan sunan musamman ma ita daya kasance uwa ce mai wannan halin. Bayan haka babu wani da suka tab'a gani matsayin uba ko d'an uwa tunda suka tare a unguwar. Shi yasa mafi aka sari sunfi tunanin ko shegiya ce babu kuma wanda yake so yaransa ya yi hulda da shege. Tana kwance kan kujera daga ita sai y'ar shirt da guntun sket daya kamata sosai wanda koya tayi wani kwakwkwaran motsi sai kaga pant d'in ta. Taba ce bakinta tana zuka tana fesar da hayakin da wani irin gwanancewa tana bin wakar lokaci zuwa lokaci sai gyada kai take. Kwana biyun nan jinta take kaman an yaye mata dukkanin wani damuwa da wani bara gurbi dake cikin rayuwar ta. She is so happy tana jinta a sama saboda babu wani burden a kanta. Tana raye ko ta mutu wannan sam ba damuwar ta bane tunda Allah ya rabata da alkakai. A firgice ya fad'o gidan kaman wanda aka wurgu Maa tayi saurin mik'ewa tana kallonsa cike da farin ciki. A guje ta nufeshi zata rungume ya buga mata uwar tsawa "Kar ki kuskura ki matso nan .ina Bahiyya? What happen to her da nake ji wasu labarai na banza tunda na shigo unguwar ?" Nan da nan annuri dake kan fuskarsa Maa ya b'ace ta zuba masa mugun kallo mai tattare da tsananin kishi. "Nima ban sani ba" Ta fad'a da tsawa. Kaman ya kifa mata mari yaji da ihu ya mayar "Baki sani ba kaman ya? How dare you zakice baki san inda y'ar ki take ba?" "Kaji abunda kace? Y'ata saboda haka menene damuwar nasan inda take ko ban sani ba? Wannan yarinyar y'ata ce nina d'auki cikin ta wata tara na haifa, na raineta ta girma har ta kai yanda take yanzu, saboda haka ina da iko nayi yanda naga dama da ita babu wanda ya isa ya tuhumeni ko ya tambayeni hujja a kanta tunda bashi ya haifamin ba. Duk abubuwan da ka ke ina sane dasu. Zamana ka ke bana Bahiyya. Nice matar da ka ke soyayya da ita kuma ni ka yiwa alkwarin aure, don me yasa zaka damu da rayuwar yata wacce zata zama tamkar y'ane a gareka?" Sosai take magana da ihu tana kumfar baki. Baki Lee ya cije da mugun k'arfi idansa tuni ya kad'a ya yi jazur saboda b'acin rai. Harta fuskarsa tayi ja abunka da farin mutum. "Listen and listen good you dumb old woman. Bahiyya itace nake so kuma zanyi komai in my power na nemota na bata rayuwa mai inganci. I will marry her and take her away from you evil witch. Da kasancewar ki uwa a wannan duniyar gwanda bakizo taba kuma sai Allah ya kamaki da amanar daya baki domin Bahiyya amana ce a gurinki. Duk wani tsanani da wahala da kunci da ki ka jefata kema InshaAllahu sai kin shiga wanda yafi nata tsanani tun daga duniya irin ku suke fara ganin hisabi. Just wish wani abu bai sameta ba duk inda take domin nayi alkawari sai na d'auki mummunan mataki a kanki. " Tana ihu kaman zata rufeshi da duka sai zuba huci take tace " ni ka ke ciwa mutunci haka Lee? Har ka kalli idona kace zaka auri y'ata? To billahillazi in har ina numfashi a doron k'asan nan bata isa ta samu farin ciki ba kaman yanda na rasa nawa saboda ita. Nayi tunanin ta fita daga rayuwata kenan amma zan nemota duk inda take a fad'in duniyar nan in har tana numfashi. Zan tabbatar maka baka isa ba kuma kayi kad'an Bahiyya y'ata ce dole ko ban nemeta ba ita zata nemoni I'm her mother after all bata da wata duk duniyar nan sama dani. She will come back to me and i promise you life nata sai yafi na baya zama miserable saboda itace sanadin komai daya shafi rayuwata. And again ta sake shiga rayuwata wajen rabani da kai. She will pay for this. Get out of my house" Ta k'arasa tana wani dukan k'irjinsa da turashi tana zuba huci kaman bijimi. Rai a tsananin b'ace ya juya fuu ya fice daga gidan. Dole ma ya fara nemo Bahiyya kafin wannan muguwar matar ta samota domin babu digon imani kona miskala zarratan tattare da ita. He wonder wane irin rayuwa Maa ta shiga haka da har yasa ta tsani y'ar data haifa ta d'ura mata alhakin abunda ya sameta. Tunda ya fice take ihu a falon kaman mahaukaciya tana jifa da kaya. Da k'arfi take kiran Bahiyya "BAHIYYA, BAHIYYA,BAHIYYA har yau dai kin sake rabani da farin ciki. Shegiyar yarinya mai taurin rai. Ahhhhhh" Ta d'auki shisha data ci karo da ita ta rotsata cikin yar plasma dake falon. A take kuwa ta fashe tare da yin spark. ➺➺➺➺➺➺➺➺ Sosai nake shek'a gudu cikin dokar dajin da bansan yanda akayi na tsinci kaina a cikin sa ba. Dajine mai tsananin duhu dako tafin hannun ka baka iya gani sai waini irin kukan tsuntsaye masu ban tsoro dake tashi cikin sa suna amsa kuwa ko ina. Duk tsananin duhun sa haka nake shek'a gudun gabana kaman ana haskamin inda zanbi. Daga nesa naji murya mai amo dake d'auke da wani irin sanyi ta kirani "Bahiyya " A firgice naci birki ina waige-waige daga inda naji sunan na ratsowa. Daga hannun dama naji muryar ta sake kira da taushi "Zo gareni Bahiyya. Gani nan" A firgice nayi inda naji muryar inda nake hango wani haske na bullowa ta bayan wasu bishiyu kaman yana dumfaru ni. Gudana na karawa kaimi ina so naga na cimma wannan haske dake kiran sunana, amma sai ya kasance duk taku d'aya idan nayi hasken namin nisa. Wata irin mahaukaciyar dariya naji mai ban tsoro daga bayana da gudun abu kaman iska na nufoni na juya a rude domin naga menene daidai na farka a firgice ina salati. Gaba d'aya na had'a zufa kace ruwa aka zubamin a jiki. Wane irin mafarki ne haka kaman gaske? Allah mai iko kenan bawai banyi addu'a ba da zan kwanta amma duk da haka nayi mafarki irin wannan dana kasa fahimta. A hankali na sauke numfashi na kai hannu na goge goshina dake digar gumi na yunƙura na sakko daga kan gadon saboda kiran sallah la'asar da naji anayi. Ina alwala Baba ta shigo da sallama kafin na amsa muryar Hassa'u ya biyo bayanta. Ras gabana ya yanke ya buga da mugun k'arfi na kasa k'arasa alwalar da nake. Baki har kunne ta k'araso inda nake kaman zata taka rawa. Walahi da naga anyi wajen sati banji wani motsi ba daga wajen sa na d'auka komai ya wuce ashe d'aurim talala yamin. "Ke y'ar albarka yarinya mai goshin arziki. K'arbi wannan ki fara rik'ewa a hannun ki" Envelope ta mik'omin. Ido na zuba mata kafin na kai hannu jiki a mace na k'arba. A hankali na buɗe kud'i ne a ciki y'an dubu-dubu bandir biyu sai wata y'ar takarda manne jikin kud'in. Wani irin shegen handwriting ne mai tsananin kyan gaske da akayi cikin tsari an rubuta kaman haka '𝐷𝑜𝑛'𝑡 𝑓𝑜𝑟𝑔𝑒𝑡 𝑜𝑢𝑟 𝑑𝑒𝑎𝑙 𝑀𝐴𝐼𝐷. 𝑦𝑜𝑢 𝑠𝑖𝑔𝑛 𝑡𝒉𝑒 𝑐𝑜𝑛𝑡𝑟𝑎𝑐𝑡. 𝑠𝑒𝑒 𝑦𝑜𝑢 𝑠𝑜𝑜𝑛 𝑦𝑜𝑢𝑟 𝑀𝑎𝑠𝑡𝑒𝑟😉. 𝑠𝑜𝑜𝑛!' Wayyo wata irin zuciya ta debeni a raina nace' naci Uban Master na bishi da gudu don ubanka kafirin banza da wofi' a zafafe na chukwuikwuye takarda zan tura a baki na taune shaf na manta dasu Baba da Hassa'u dake tsaye suna kallona saida naji muryar Baba ta jehomin tambaya "Me aka rubuta jikin takarda naga ranki ya b'aci?. Ai dama na gayawa Hassa'u idan har baki amince ba , ba d'an shugab k'asa ba ko d'an shugaban kasan duniya ne gaba d'aya baza kiyi masa aiki ba. Idan har kinga baki so a mayar musu da kud'in su wai allowance ne ya fara bayarwa saboda kiji dad'in fara aiki. Na gayawa Hassa'u ban kawoki nan don kiyi aikatau ba amma tana min naci har gidan aikina ta bini tana magiya saboda ance za'a k'ara mata albashi idan har kin yarda kinje" D'an murmushi nayi da akace yafi kuka ciwo. Allah ya sani ina san matar nan saboda Allah kuma zanyi komai a kanta koda bada rayuwa tane wanda naso ace mahaifiyata ce. A sanyaye nace "Zanje nayi aikin Baba muma ai karuwar mu ce" "Anya kuwa Bahiyya? Karfa ki takura kan ki wanda nake ma Allah ya amfana" Kai na sake girgiza da kulawa nace "Ya kamata yanzu Baba ki huta haka InshaAllahu ni zan d'ura daga inda ki ka tsaya koda ba gidan da ki ke aikin bane tunda wannan naga yafi inda ki ke yi alheri" "Ayyiriyiri kaga yarinyar yar zamani wadda tasan inda alheri yake. Kedai Allah ya miki albarka kin cika y'ar halak. Bari naje Baba yau ina ga ai sai nayi y'ar walima saboda zan zama attajira nan kusa" Kafin muce wani abu ta juya da sauri ta fice muka bita da kallo. D'an murmushi nayi na sauke kaina k'asa tare da zubawa takarda da kud'in ido. Su kansu kamshin sa suke. Alright Mrs bad boy. Let see what you get and i will gladly return the favour. Hmm chakwakiya mai zafi yanzu zamu fara zuba wuta a d'aure damara. Wai shin wane kangin rayuwa Maa ta fad'a ne da har yasa ta tsani abunda ta haifa? Tabbas ance son maso wani koshin wahala koya zata karke ga Bahiyya ga Enzo zasu zama karkashi inuwa d'aya? Wane kulabale ko nace me ku ke tunanin ya shirya mata? [09/07, 9:36 am] Ashantyluv: 𝐁𝐀𝐇𝐈𝐘𝐘𝐀 𝓓͟𝓮͟𝓼͟𝓽͟𝓲͟𝓷͟𝔂͟ 𝓸͟𝓻͟ 𝓯͟𝓪͟𝓽͟𝓮͟? Not edit! 【ch9】 ꋊꏂꉧ꓄ ꒯ꋬꌦ ✶⊶⊷⊶⊷❍ Washegari ya kama talata tunda nayi sallah asuba ban koma ba saida nayi tilawa ko zan samu sassauci damuwar dana kwanta da ita da fargaba. Saida gari ya yi haske na rufe na fito nayi abunda zanyi da d'ura mana abinci da Baba ta siyo bayan na bata kud'in don nace mata babu abunda zanyi dasu. Da kyar ta k'arba saida taga na cire wani abu na rike a hannuna wai saboda bukata ta yau da kullum. Haddedden tuwon semone da miyar ugu da yaji nama da kifi don takanas na bawa Baba sallaho na dumama naci na koshi harda k'ari ina gamawa na shiga wanka ban jima ba na fito. Baba har zuwa lokacin tana barci na buɗe kwaba na fito da doguwar riga da hijabi na saka ban shafa wani mai ba saboda zafi da ake. Sallama Hassa'u tsakar gida yasa na sauke ajiyar zuciya kafin na amsa ta d'aga labule ta shigo. Shigowar ta ya tashi Baba ta miƙe tana salati tare da kiran "Hassa'u har kin shigo?" "Eh wlhi Baba bakwai ai ta wuce nida nake sammako. " Bari nayi saida suka gama gaisawa sannan na gaishesu Hassa'u ta kalleni baki har kunne tace "Kai amma naji dad'i dana tarar har kin shirya naga alama baki da African time. Baba bari mu wuce lokaci na wucewa" "To Allah ya kiyaye hanya ya kuma tsare. Ki kula da kyau kinji Bahiyya don Allah ki kula kibi dokoki kinga gidan da zaki ba ko wane irin gida bane wannan dole akwai tsari" A hankali nace "InshaAllahu Baba. Ga abinci can na juye miki a flask kar ya yi sanyi" "To nagode Allah ya yi Allah sai kun dawo" Da haka muka fito zuciyata tayi nauyi amma addu'ar Baba ya d'an samin kwarin gwiwa. Bamu jima ba muka samu mota yauma ita Hassa'u ta biya bayan mun sauka. Kaman waccan ranan saida akayi checking namu yafi sau goma har muka shiga b'angaren first lady inda nan kowa yake taruwa wai sai tazo ta sallami mutane ta raba masu wajen aiki dakanta. Gaba d'aya duk suna sanye cikin kayansu kaman na waccan rana har Hassa'u itama ta chanza nata. Nida ina tsaye cikin haddedden falon katon gaske babu wani tarkace cikinsa amma an zuba masa dukiya komai na glass ne banda kujeru. Mun d'auki sama da minti ashirin kafin muji ana shelar ga first lady na fitowa falon ya cika da matakan tsaro tako kina. Hmm kud'i masu sawa mutum ya manta akwai Allah kenan ga wanda bashi da sa'a. Saida ta d'auki wajen minti biyar bayan shedar fitowar tata sannan ta bullo cikin wata arniyar gown kirar Dubai data sha tsones ko Daimons kaman anyi sarka dasu jikin rigar har zuwa k'irji. Kafin ma ta k'arasa sakkowa daga kan stairs d'in shi kansa saida ta d'auki sama da minti biyu tafiya take ka rantse da Allah bata kashi. Cikin raina naja dogon tsaki haka nan naji matar sam batayin ma tun had'uwar mu ta farko. Jinkanta da izzarta ya yi tsanani. Hadaddiyar 2 seater ta royal ta zauna masu tsaronta suka tsaya bayanta. Shiru falon ya sake dauka sai k'arar ac da fitar numfashin mutane kawai ka ke ji ga uban turaren ta daya cika falon dani sam bayamin dad'i. A hankali ta d'aga hannu kowa ya zube yana mata kirari kaman zasu ari baki na sake kwabe fuska cike da kyankyami abunda suke ina tsaye kyam ban motsa ba. Aikuwa idanta ya fad'a cikin nawa ta zubamin k'ananan idanuwanta kaman tana son gano wani abu kaman wancan ranan. Wajen sakan biyu tayi tana kallona sai kuma ta juya ta kalli d'aya daga ciki matakan tsaronta. Da girmamawa ta rankwafa kafin ta d'ago tayo inda nake da sauri fuskata a bugun had'e tace cikin tsawa "Ke kinfi k'arfin ki durkusa ne ki mika gaisuwa? " Duk da gabana ya fad'i amma na dake da dakiya nace "Ayi hakuri bansan haka al'adar take ba yau na fara zuwa" Ina jin Hassa'u najan zanina ta k'asa naki kallonta. A zafafe ta matso tana shirin kama hijabi yanda ta kawomin chakuma da alama waje zatayi dani. Kafin hannun ta ya sauka kaina First Lady tace da wata y'ar siririyar murya "Ki ka ce yau ki ka fara zuwa? Maganan ta yasa Bodyguard d'in nata ta fasa tab'ani amma tana tsaye gabana sai huci take gata aba tabarakalla akwai jiki ga uban tsayi kaman falwaya. Saida na d'an matsa don nasan wannan basamudiyar ta kareni na kalli first lady nace "Eh, nice sabuwar y'ar aikin da Enzo ya d'auka " Wani irin shiru falon ya dauka sai naga kowa ya juyo ya zubamin ido cike da mamaki matuƙa har ita basamudiyar dake gabana. Kallon da sukemin sai naji gabana ya fad'i inaji kaman na sake aikata wani gagarumin laifin. Da kyar naji tace "Wacece ke haka da har ki ke kiran sunan sa haka gatsal babu Sir? Banda haka harda karyar shiya d'auke ki aiki? Kin d'auka nan wajen wasa ne?" Wani gumi naji ya karyomin saboda yanda tayi maganan da tsananin b'acin rai na had'iye yawu daya tokare min a makoshi. To idan har basu san cewa shiyace nazo ba harya aikamin da allowance da kuma kashedi taya yake tunanin zanyi aiki a nan?. Yanda take kallona kaman zata saka a harbeni shima bai taimaka ba wajen sake jefani ciki rudu gashi Hassa'u ta kasa magana saboda tsoro sai zare ido take. Da alama itama baice mata komai ba bace bata umarni. Ni dama nasan akwai wani abu a k'asa. Ya had'amin sarkakkiya da bani da hanyar kunce kaina. A zafafe naji ta sake cewa "Bayan kin shigo kin nuna min disrespect ,kin kira sunan AIZAK gatsal saboda gaki ke ishashshiya hakan bai ishe kiba harda yi masa k'arya?, ke a wa da har zaije da kanshi ya nemoki kiyi masa aiki ba tare dani na sani ba. Duk wasu masu aiki da masu tsaro a gidannan nasa nike da ikon samosu duk inda suke idan har sunmin. Ke wacece kuma waye ubanki a nan?" Duk fad'an da take da yanda tension ya sake tsanani cikin falon bai hanani nanata suna da naji ta kiraba cikin raina. AIZAK? dama yana da wani sunan bayan wannan ko kuwa wani take magana a kai? "Ku kamata ku kaita cell ku horata sai ta gayamin ubanda ya aikota cikin gidannan da kuma mugun nufin data shigo yi" Me?ido waje nake kallonta tuni basamudiya ta fisgo hijabina sauran suka matso da sauri suma ban ankara ba naji an kwarfe ni na zube a k'asa an kama hannuna ta baya an dannamin ankwa. Tsananin mamaki da tu'ajjabi sai na kasa yin komai na zubawa First Lady idon kawai tunanin anya kuwa ba mafarki nake ba? Yo inba haka ba daga zuwa aiki sai kuma abun ya buge da sharri? To ni meya had'ani dashi da har zan shigo don aikata wani mugun nufi a kansa? Kaina gaba d'aya ya d'auki zafi na rasa wane tunani zanyi sama-sama naji Hassa'u na bada hak'uri naji kaman na kifa mata mari tunda ta kasa cewa komai ita kuma ta zoda sakon amma saboda shegen tsoro da san zuciya ta kasa fad'in gaskiya. Ban iya tashi ba suka jani kyee sukayi wajw kaman kayan wanki . K'asan kawai na zubawa ido Allah yasa ko ina grass kafet ne da duwawuna yaji jiki. Kaman ance na d'aga kai saboda ji da nayi kaman ana kallona. Waige-waige na fara har Allah ya sauke idona can b'angaren sa. Daga can wata hadaddiyar balcony mai shegen kyau da flowers suka kawata harda wasu tsuntsaye dake yawo a wajen na hango shi tsaye jikinta ta sanye da bak'ar jacket daya zugeta gaba d'aya k'irjinsa da cikin sa duk a waje da Ash jeans. Gashin kansa ya zubo goshinsa kaman a jike. Cup ne a hannun sa na dama d'ayan kuma yana cikin aljihun wandonsa. Muna had'a ido ya wani d'agomin cup d'in tare da kashemin ido d'aya ya kai cup d'in bakin sa da wani mugun smirk kan fuskarsa. Wayyo zuciyata ta d'auki wani irin zafi na yunƙura zan fisgi da wani irin k'arfi da naji yazomin naji ance "Ku saketa it's an other from Sir" Ko sakan d'aya basu sake ba suka sakeni da sauri na fesar da wani hucin numfashi mai zafi kafin na yunk'ura na mike k'irjina na suya. A zafafe na bangaje basamudiya ina karkade jiki na d'auki hanya zan fice. Itama Hassa'u ta sake taka k'afarta gida sai na wanke ido na zuba mata rashin mutunci. Ina ji ido ko nace idanuwa a kaina amma tsananin zafin da zuciyata yake baisa na juyaba na cigaba da tafiya kaman zan kifa.ya yi duk abunda zaiyi shi bai isa ya kassaramin rayuwa ba sai abunda Allah ya nufa zai sameni. "Where do you think your going?" Wani irin zabura nayi na juya tare da sakin y'ar kara jin yanda maganan tashi ta sauka kanya kaman saukan Aradu. Wata dankareriyar motace fake daga d'an bayana kad'an shi kuma ya jingina jikinta wani lazily ga matakan tsaro duk sun bazu a wajen. Wannan shegen smirk d'in ne kan fuskarsa da nake ji kaman na take da kafata. Saurin d'auke ido nayi daga kansa saboda yanda hasken rana ke haska k'irji sa da shafaffen fatan cikin sa dake d'auke da wasu shegun Abs kaman an zana. Astagfirullah. Allah ka mana tsari da irin wannan mutane. Da sauri na juya zan cigaba da tafiya na tsaya turus don wasu shegun Bodyguards ne turawa walahi harda makaman yak'i jikin su banda wasu shegun karnuka dake hannun su, duk yaushe suka zo kaman aljanu?Wani irin yawu na had'iye wani kafafuwana suka fara rawa na juya da kyar ina kallonsa k'irjina na harbawa. A hankali ya saki wata sexy dariya mai kaman smirk yana d'aga gira yace "What?. Go ,what are you waiting for?" Yawu na sake had'iyewa ina kallonsa da idona da nasan sunyi jaa saboda b'acin rai. Menene ribarsa ne wai a kaina? Tsananin b'acin rai yasa na cije lebena ina masa kallo mai cike da tsana da kiyayya. Ina ma ina da iko walahi yanzu

Chapter 7 of 11