Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 9
fama meka ke shirin yi haka? Duka bashi bane, Addu'a ita ce makarin Mumini. Koma ka zauna" Ajiyar zuciya na sauke ina kallon Baffa daya sawo kai ciki gida. Duk gidan nan shi kaɗai yake sona. Baki ya Aliyu ya cije yana kallona kaman ya shaƙe kafin ya yi ƙwafa ya koma ya zauna kan tabarma. Da sauri Mamee ta miƙe ta karɓi kayan daya shigo dashi ta kai ɗaki ta dawo da dadduma ta shimfiɗa masa ya zauna yana aswaki. Ya Ƙhamis mai kunna wuta ya katse shirun "Ai Baffa da ka bari ya koya mata hankali tunda bata jin maganan kowa sai tashi " Murmushi Baffa ya yi ya kalleni "hamisu Duka ba shine maganin rashin jiba ko faɗa . Nasiha da Addu'a ita ce magani. ALLAH ya shirya min ku gaba ɗaya ya yiwa rayuwar ku Albarka. " Gaba ɗaya muka amsa da Amin. Baffa bai daɗe da shigowa ba aka fara kiraye-kirayen sallan Magriba don haka suka fice gaba ɗayan su mu kuma kowa ta tashi tayi alwala. Basu dawo ba saida suka yi sallan isha muka haɗu nan tsakar gida aka zubawa kowa tuwan masara da miyar zogale. Wannan al'adan muce tare muke cin abinci koda yaushe safiya,rana da kuma dare ana yi ana raha don Baffa badai barkwanci ba. 𝓉𝒽ℯ 𝒻𝒾𝓇𝓇ℯ & 𝒾𝒸ℯ. ༄ZUBAR HAWAYE༄ 𝒜ɱαȥιɳɠ ★'★ ɯɾιƚҽɾʂ ϝσɾυɱ ( 𝒜, ★ ʂƚαɾ'ʂ ,ɯ ★ ϝ) *ZINARIYAR MACE⚡* *Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.* Na gyaran nono. Na sanyi. Dilka tare da hadin sabulu. Duk Wani nau'in maganin mata. Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani. *08089965176* *07084653262* 𝗔𝘀𝗵𝗮𝗻𝘁𝘆 𝗹𝗼𝘃𝗲. " -- 𝐼 𝑛𝑒𝑣𝑒𝑟 𝑏𝑒𝑙𝑖𝑒𝑣𝑒 𝑖𝑛 𝑙𝑜𝑣𝑒 𝑎𝑡 𝑓𝑖𝑟𝑠𝑡 𝑠𝑖𝑔ℎ𝑡 𝑢𝑛𝑡𝑖𝑙𝑙 𝑖 𝑚𝑒𝑡 𝑌𝑂𝑈 " Vol/11-15. Washegari kaman yanda nayi niya na shirya da wuri cikin uniform namu na makarantar boko, na tura hutunan mu dana su Khadija don fara gudanar da aikina cikin jaka. Ina fitowa na samu ya Aliyu k'ofar d'akin Mamee daga shi sai dogon wando da shimi da alama magana suke mai humimmanci. Da sauri na k'arasa k'ofar d'akin na durkusa ina gaida Mamee da Ya Aliyu da suke kallo na cikin mamaki sunga abunda basu saba gani ba. "Ido na ne ko kuwa Sanaah ne yau ta riga Marwah shirin makarata?" Haushi ya kamani amma na d'aure banga laifin su ba a kuntace nace "Nice Mamee akwai abunda za muyi ne shi yasa zan tafi da wuri" "Yauwa nifa nace, to kin karya ne?, ki bari ki karya mana sai ku tafi da Marwah, ina take nema ?" Da sauri nace " ai ta shiga wanka Mamee in naje makarantar zan karya " "To shikenan Allah ya bada sa'a " Na amsa da Amin na miƙe da sauri zan tafi ya Aliyu ya kirani ya mik'o min naira 200. Wayyo a guje na karb'a bakina har kunne ina godiya na fice da sauri ina jin Marwah data fito daga banɗaki tana kirana ban saurareta ba nayi waje abuna. Ina fitowa naci karo da Baffa ya dawo daga masallaci shida ya Khamis. Har k'asa na durkusa na gaishe shi . Shima dai kaman Mamee tambayar da ya yimin kenan na bashi amsa k'afin ya shimin Albarka nayi saurin wucewa ina jin idon ya Khamis a kaina. Kaman yanda na tsara kai tsaye Shagon Talle mai hoto na nufa na kuwa ci sa'a buɗewar sa kenan. Yana ganina ya washe jajayen hak'oransa "A'a Sanaah ikon Allah yau kece nake gani haka da sassafen nan?" Baki na tab'e cike da kankyami nace "Wai kai talle anya kana brush kuwa? Ace mutum kullum hak'oran sa jajur dasu kaman mai cin goro?" Maimakon yaji haushin abunda nace sai ya k'ara washe baki. "Sanaah kenan duk abunda zakice bazan yi fushi ba. Masoyi baya fushi da rabin ransa. Yanzu gayamin mene ke tafe dake kiga aiki da cikawa" Baki na k'ara tab'ewa na tura hannun cikin jakata na d'auko hoton da nake son nuna masa na miƙa masa. "Yauwa kaga wannan hoton ?, wannan ta tsakiyar nake so ka cire ta ita kaɗai ka had'a hoton da wani dan saurayi wanda kasan d'an kwalisa ne" Wata irin dariya shakiyanci ya saki yana buga hannu a cinya yace "Kai gaskiya Sanaah ke Wuta ce. Ba'a tab'a ki a kwana lfy? Yanzu me tayi miki da ki ke neman b'ata mata suna?" "Kar ka damu da wannan kawai kayi abunda nace. " Fuska na k'ara tamkewa ina hura hanci karya kawomin raini nace "Nawa ne kuɗin? " Da sauri yace " Haba har kinsa raina ya b'aci na isa na karb'i kuɗin ki My labe. Kar ki damu zaki ga aiki da cikawa nan bada jimawa ba" Far nayi da ido na nace "yauwa to shikenan gobe zan dawo da yamma na karb'a " "An gama my labe" Fuska na yatsina saboda tsanan sunan da yake kirana dashi na juya na fice. Koda na fito tsayawa nayi ina tunanin inda zanyi don sam bana sha'awar zuwa makaranta. Sunan ZABINA ya fad'o min a rai. Wayata na d'auko ina labuben number nata da ya Khamis ya yi blocking. Zabina y'ar wani attarijin mutum ne da ake kira da ALHAJI TAHIR MAITURARE. Nan gaban layin mu hamshakin gidansu yake. Yarinya ce y'ar gayu y'ar kwalisa da bata rasa komai ba gurin iyayen ta. A wani shago dake tsakan kanin layukan namu muka had'u da ita an faka da ita a mota zata siyi kati. Dun daga nan ta karb'i number na muke zumunci. Ni dama Allah ya yi ni mutum mai son y'ay'an gayu da masu kuɗi. Wajen sau uku tana zuwa gidan mu ta wuni amma saboda bak'in ciki irin na ya Khamis saida yasan yanda ya yi ya rabani da ita . Baffa yasa takunkumi sosai a kaina koda wasa kar a k'ara ganina da ita. Bai tsaya daga nan ba saida ya karb'i wayata ya yi blocking number d'inta. Bansan yanda suka yi da ya Khamis ba don tun daga ranan bata k'ara zuwa gidanmu ba bata k'ara nema na ba a waya. Rab'awa nayi gefen kwata data hauro bakin layi saboda rashin tsabta na mutane ga ruwa da aka yi kwana biyu ya had'u gurin duk ya chab'e. D'an tsaki naja ina mitar rashin had'in kai na mutane duk gurin ya zaizaiye kaman rami da ace an had'a kai tunda hanyace babba da kowa ke bi ko yashi ai an d'an zuba. Banyi aune ba duk taka tsantsan da nake kar ruwan nan ya tab'ani sai ji nayi shaa kaman an deb'o shi da bokiti an watsamin shi da gayya. Tunda daga fuskata har zuwa kafata. Wani iri sandarewa nayi da hannun duka biyun a buɗe baki a sake nabi dankareriyar bak'ar motar data yimin wannan aika- aika da kallo. D'an gaba dani kad'an motar ta tsaya amma koma wake ciki bai fito ba yana jira na k'arasa saboda iko? .A fusace na sunkuya na rarimo dutse mai dan girma cikin chab'alin nan ban jira komai ba na saita motar da iya k'arfina na jefa. Shegiyar motar glass din ko motsin kirki bayi ba sai d'an tsagewa da ya yi. B'arin zaman direba aka bude wani gabjejen mutum ya fito sanye da kaki na soja. Yanda na tsani soja sai banji tsoron sa ba na nufeshi a zafafe kaman iska yana tsaye wajen motar sai zuba huci yake fuskarnan kaman gobara. Hannuna na d'aga ina nunashi a tsiwace nace "Kai wani irin mutum ne da zaka shigo layi a guje kaman kana kan titin gidan ku?, kuma kayi min laifi ka kasa fitowa ka bani hak'uri? Ko kana tunanin dan kai sojane zanji tsoron ka?" Da b'acin rai yace "ke baki da tarbiya ko?, bakisan na gaba dake ba" Aikuwa na k'ara harzuk'a " ba'a koyamin ba kai nake jira tukun .kuma Allah ya isa b'atamin kaya da kayi ban yafe ba" A fusace naga ya d'aga hannu zai kifamin mari na riƙe kugu ina jira ido na kyam kan hannun nasa ya tab'ani yaga bala'i yanzun nan. Bai kaiga sauke hannun nasa ba wata irin murya mai tsananin dad'i da gard'in gata so deep tayi magana cikin wani irin authorative voice da gaba d'aya gabb'an jikina suka yi sanyi kalau kaman an zubamin k'ank'ara. "Adam, leave it" Wanda aka kira da Adam ya fasa dukan nawa ya dunkule hannu kaman mai shirin kai naushi. Baki ya cije yana kallona a fusace irin baiso hakan nan ba na watsa masa harara. Juyawa ya yi ya shige motar na d'an ja baya kad'an ganin glass d'in bayan motar na sauka a hankali wani irin kamshi ya daki fuskata har saida na lumshe ido. Dana buɗe kuwa ban sauke su kan komai ba sai kan wata kyakkyawar fuska dake kwance bayan motar. Wani irin juyo da kansa ya yi b'arin da nake muka had'a ido. Numfashi na ya d'auke gaba d'aya na kara ware ido sosai ina kallon wannan kyakkyawan mutum da kyan sa hatsari ne babba ga Al'umma. Piercing Silver eyes nashi da suke a lumshe ya watsamin yana kallona tun daga sama har k'asa kafin naga ya d'ago rafar kuɗi ya ciro bandir d'aya ya wullomin ta daki k'irjina ta fad'i k'asa. Da wani irin voice naji yace "Take it go wash your clothes, and and learn some manners yeah?, ko kinsan muhimmanci na gaba dake. Adam, drive" Kafi nace wani abu Adam ya fisgi motar a guje suka barni nan tsaye da budad'd'en baki? Saida naga b'acewar motar sannan na dawo nutsuwa ta na tuna da kuɗin daya jefeni dashi kaman wata almajira. Durkusawa nayi na d'auko zuciyata na zafi amma kasan ta kuma wani irin yanayi ne na tsinci kaina a ciki dana rasa gane masa. Jiki babu kuzari nayi gidan su Zabina saida naje k'ofar gidan na kirata a waya. Bugu uku ta d'auka cike da matsanancin mamaki ta amsa wayar "Sanaah, da gaske kece ke kirana?, dama rai kanga rai?" Yak'e nayi muryata a d'an sanyeye nace mata "Ina k'ofar gidan ku?" "Ikon Allah yanzu da safiyar nan?Allah yasa ba wani abune ya faru ba ? Bawa mai gadi wayar" Matsawa nayi kusa da maigadin gidan na mik'a masa waya .da to Hajiya ya bata amsa ya buɗe min k'aramin gate na shige .ina shiga na hangota tana fitowa daga falo daga ita sai wani mini sket da half vest kan nan yasha gashin doki da akayi mata kalba dashi har kugun ta. A guje ta nufoni tana murmushi sai kuma ta tsaya turus tana kallona. "Meya sameki naga kayan ki haka?" Numfashi naja na fesar na kwashe duk abunda ya faru na gaya mata. Kai ta girgiza ta kama hannuna muka shiga cikin falon. Had'adden falon muka shiga dake d'auke da kayan more rayuwa. Wasu y'an mata ne guda biyu na gani a falon d'aya kwance kan doguwar kujera d'aya kwance a k'asa ko wacce ta dukufa wajen danna waya. Manyon woyoyin dake hannun su na kalla sai naji duk na muzanta. Allah nima ya nunamin ranan da zan riƙe waya irin wannan. Gaba d'aya suka d'ago jin shigowar mu. Kallon juna sukayi suka saki murmushi duk suka miƙe daga kwancen da suke suka zauna sosai. Yanayin kayan dake jikinsu duk sai naji kunya ta kamani saboda tsiraicin su dake waje. Wanda ke kance a k'asa daga ita sai wata y'ar yaleluwar rigar barci da ko cinya bata kai ba koya ta motsa sai kaga pant nata ga k'irjina ta dake nunawa ta saman rigar muraran dashi. D'ayar kuma dan mini wando ne a jikin ta da breziya kawai. Kasa shiga nayi Zabina ta jani da sauri tana cewa "Babies meet Sanaah da nake baku labari" Wani kallo naga sun jefamin da naji duk na tsargo. Mai shimin tayi saurin tasowa ta rungume ni kam kaman zata mayar ciki. Dariya Zabina tayi tana tureta. "Beela, saketa mana baki ga kayanta a b'ace suke ba" Janyewa tayi tana min wani kallo "ohh sorry ban lura ba, sunana Nabeela, Beela inshort. Nayi farin cikin had'uwa dake Sanaah. Da fatan zamu zama kwaye na amana " Kai kawai na d'aga mata ina binta da kallo. Dayar itama ta matso inda muke ta miƙo min hannu. "Sunana Blessings. Nice to meet you" Kai na jinjina kaman wadda aka d'aurewa baki na miƙa hannu ina d'an murmushi. Juyawa nayi kan Zabina dake kallonmu tana murmushi nace "Mom naki bata nan ne" "Yeah, suna England ita da Dad. Naji dad'in zuwan ki kuwa dan Next week Birthday d'ina dole kuma ki zo" Ido na d'an zaro ina naga hanyar zuwa Birthday ya Aliyu na gari. "Karma kice baza kizo ba dole kizo saboda ke yanzu zan kancile Hall da muka dauƙa a gida zamuyi don haka baki da wani excuse" Numfashi kawai naja tunda tace a gida ne dole nasan yanda zanyi kuwa. Zama muka yi muna hira tasa aka kawomin abinci naci nayi nak. Taso na ciri kayana chanza nace ta barshi kawai idan na cire nasa wasu za'a tambaya a gida ina naje. Bani na bar gidan ba saida na daidaici lokacin tashi nayi mata sallama na tafi ina tunanin yanda zanyi da kuɗi da wannan hurul'ain ya bani nevertheless dana kasa gane cewa Shine sanadin ZUBAR HAWAYE na and my destiny. 𝓉𝒽ℯ 𝒻𝒾𝓇𝓇ℯ & 𝒾𝒸ℯ. ༄ZUBAR H𓂀WAYE༄ 𝒜ɱαȥιɳɠ ★'★ ɯɾιƚҽɾʂ ϝσɾυɱ ( 𝒜, ★ ʂƚαɾ'ʂ ,ɯ ★ ϝ) *ZINARIYAR MACE⚡* *Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.* Na gyaran nono. Na sanyi. Dilka tare da hadin sabulu. Duk Wani nau'in maganin mata. Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani. *08089965176* *07084653262* 𝗔𝘀𝗵𝗮𝗻𝘁𝘆 𝗹𝗼𝘃𝗲. " 👋𝐇𝑖𝑖, 𝑤𝑒𝑙𝑐𝑜𝑚𝑒 𝑏𝑎𝑐𝑘 𝑡𝑜 𝑚𝑦 𝑔𝑟𝑒𝑎𝑡𝑒𝑠𝑡 𝑎𝑑𝑣𝑒𝑛𝑡𝑢𝑟𝑒 𝑜𝑓 𝑝𝑢𝑟𝑒 𝑙𝑜𝑣𝑒. -- ℎ𝑒𝑎𝑟𝑡𝑏𝑟𝑒𝑎𝑘𝑠, ℎ𝑎𝑡𝑒𝑠, 𝑏𝑒𝑡𝑟𝑎𝑦𝑎𝑙, 𝑡𝑒𝑎𝑟𝑠. -- 𝑊ℎ𝑒𝑛 𝑖 𝑠𝑎𝑖𝑑 𝑡𝑒𝑎𝑟𝑠, 𝑖 𝑚𝑒𝑎𝑛 𝑙𝑜𝑡𝑠 ,𝑎𝑛𝑑 𝑙𝑜𝑡𝑠 𝑜𝑓 𝑡𝑒𝑎𝑟𝑠. 𝑆𝑜 𝑔𝑟𝑎𝑏 𝑦𝑜𝑢𝑟 𝑡𝑜𝑖𝑙𝑒𝑡 𝑝𝑎𝑝𝑒𝑟𝑠 𝑎𝑛𝑑 𝑝𝑟𝑒𝑓𝑎𝑖𝑟 𝑓𝑜𝑟 𝑡ℎ𝑒 𝑤𝑜𝑟𝑠𝑡.... " Vol/16-20. Gida nayi kai tsaye don nasan yanzu dai an tashi . Da sallama na shiga ina tunanin ko Marwah ta dawo ko tana hanya. Turus na tsaya ina kallonta zaune bakin fanfo tana wanke-wanke babu alamun ma taje makaranta. Kwanukan da take wankewa nake kallo sai naga kaman sunfi na koda yaushe yawa. Don yau har sababbin flask da kofuna da Mamee ta siyo saboda Baffa gasunan duk abace tana wankewa. A iya sanina Baffa bai cika san tana zuba masa abinci cikinsu ba don yafi so yaci cikin iyalen sa. Idan kaga haka to bak'ine za'ayi. Tunani na ne ya katse sakamakon muryar Marwah data d'ago tana kallona "Subhanallahi Sanaah meya samu uniform naki?" Maimakon na bata amsa na jefeta da wata tambayar "Ya ban ganki a makaranta ba?" Wanke-wanke ta cigaba tana cewa " wlh har na shirya zan tafi sai abokin Ya Aliyu ya yi waya gashi nan a hanya zaizo shine Mamee tace na hak'ura da zuwa na taya ta aiki kafin ya k'araso" Kai kawai na jinjina ina k'ok'arin shigewa d'aki Mamee ta fito daga d'akin Baffa sanye cikin riga da sket da sukayi mata kyau sosai. Wato Mamee na ko budurwar Albarka wajen ado. A koda yaushe zaka ganta cikin gayu babu ruwanta da wai ta ajiye manyan yara a gida. Kullum cikin kwalliya take. Murmushi ne sosai kan fuskar ta dake nuna farin cikin dake tattare da ita "A'a Sanaah har kin dawo?" Rabon danaga fara'a haka kan fuskar Mamee tana min magana harna manta. Na kuwa tabe baki a shagwaɓe nace "Mamee shine ni baki ce na zauna ba gashi na fita wani ya b'ata min uniform haka nayi ta yawo da ruwan kwata a jiki " "Subhanallahi garin ya?,maza kije ki cire kayan kiyi wanka kici abinci " Wani irin dad'i ne ya kamani na shige d'aki da sauri na cire uniform dina na d'auro zani a k'irji na fito na iske Marwah harta gama wanke-wanke ta fara kwashe kayan tana kaiwa kitchen. A gurguje nayi wanka na d'auro alwala na fito. Sanda na fito babu kowa tsakar gidan dan haka nayi d'akin mu ina goge gashin kaina dana wanke. Bakin gadon na iske Marwah da waya a kunne tana magana cikin sanyi a mugun hankali kaman batason aji me take cewa. Kallo d'aya nayi mata na wuce kwabarmu na ciro doguwar riga na saka na shafa turaren humra da Mamee ta siyo mana kwanaki. Sallah na farayi babu wata Addu'a na miƙe da sauri saboda yunwa dake cina nayi k'ofa muryar Marwah naji da d'an k'arfi tana cewa "Sanaah kinsan ance ba'a so mutum daya idar da sallah ya miƙe, an fiso ka zauna kayi Addu'a. Ance duk wanda ya zauna bayan ya idar da Sallah mala'iku na nema masa gafara wajen Allah kuma kinsani" A zafafe nace " ai Malamai ma sunce ba'a cika son mutum ya yi sallah yana tare da yunwa ba saboda gudun wasi-wasi. Anfiso ka yita cikin nutsuwa don kana gaban ubangijin ka ,Amma duk da haka nayi saboda kar lokaci ya wuce bake ce ke karb'an sallan ba". Shiru tayi batace komai ba na lura kuma har lokacin wayar na k'are a kunnen ta. Idonta dake cike da hawaye na kalla naja tsaki ita a komai sai ta nuna ta fini sani da iyawa. Yanzu wannan ai tozarci ne takemin wajen koma waye take wayan dashi . Mtswww naja mugun tsaki na fice zuciya ta na zafi nayi kitchen. Flask na buɗe naci karo da had'addiyar fried rice data ji kayan lambu . D'aya flask d'in kuma ferfesun hanta ne yaji albasa sai kamshi yake. Ga had'adden lemo da aka zuba masa k'ank'ara. Lallai koma waye bak'on nan ba k'arami bane. Jiki na rawa na zuba abinci na koma d'aki har zuwa lokacin tana waya na tab'e baki fuska a had'e na samu guri na zauna na kwashi abinci na na koshi kafin na koma na kwanta banjin zuwa islamiya yau. Tunanin wannan mutumin ne ya fad'omin na juya rigingine ina kallon silin daddadar murya sa na yawo cikin kwanyar kaina. Wani irin unique silver eyes ne dashi dake sa ruhun ka ya bar gangar jikin ka. Tsintar kaina nayi ina Addu'ar Allah ya k'ara had'ani dashi ko a hanya ne na k'ara ganin kyakkyawar fuskarsa. Hannu nakai na dafe gefen kirjina da naji zuciyata tayi nauyi kaman an d'oramin katan dutse. "Sanaah kinyi barci?" Muryar Marwah ya katsemin tunanin da nake. Numfashi naja mai k'arfi ban bata amsa ba nayi banza da ita. A sanyaye naji ta k'ara cewa "Kiyi hak'uri bansan ranki zai b'aci ba" A yanzu kam ban iya yin shiru ba na yunƙura na miƙe zaune na juyo ina fuskantar ta tana sharar hawaye. Numfashi naja a hankali na fesar (sigh) wai nikam a duniya akwai mace mai sanyi kaman Marwah? "Shikenan ya wuce banji dad'in yanda kina waya kina min maganan sallah ba ,sai kisa wanda ku ke wayar dashi ya yi tunanin ina wasa da ibada ne" "Kiyi hak'uri " ta k'ara cewa hawaye shar na bin kuncin ta. Kai na girgiza na kawar da zancen ta hanyar jefo mata wani maganan "Wai su waye bak'in da aka yi" Ido ta zubamin kafin tayi d'an murmushi "Babban abokin Ya Aliyu ne kuma shine shugaban su na sojoji " Bata k'ara cewa komai ta koma ta kwanta haushi ya kamani nace "Bashi da sunane shi abokin Ya Aliyun" Shiru bata bani amsa har wajen minti d'aya na d'auka ma tayi barci. Tsaki naja mai k'arfi na koma na kwanta sai naji muryar ta a mugun hankali tace "DEEN. Sunan sa DEEN" Wani irin abu naji ya daki k'irjina kaman an harba mashi ya wuce da gudu. Komawa nayi na kwanta ina maimaita sunan cikin raina. Ban dad'e da kwanciya ba barci ya yi awon gaba dani. ♡︎♡︎♡︎ Numfashi Baffa yaja mai k'arfi ya fesar yana sauraran Aliyu dake masa bayani. Mamee dake zaune gefe tayi murmushi. "Shi Kamalun ne yace yana neman auren Marwah?" K'eye Aliyu ya sosa a d'an kunyace ya cigaba da cewa "Eh Baffa kasan shi babu harkar wasa gurin sa don da cewa ma ya yi inhar an amince masa nan da sati biyu ma a d'aura auren saboda yanayin aikin mu bare shida ke babba yana so ya wuce da Ita KUWAIT . " Ajiyar zuciya Baffa ya k'ara ja. Anya kuwa anyi haka. Bawai auren ne baya so ba Amma ina Kamalu

Chapter 2 of 9