Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 7
afka cikin qaunarka, ba zan iya rayuwa ba idan na rasaka” Tana faxar maganganun tana zubar da hawaye na takaici da tsananin baqin ciki. Jin wannan kalaman nata su ne suka saka zaiyan ya nufi wajen cikin gaggawa yana zuwa ya miqa hannu ya kamo hannun salhim ya riqe wata jijiyar hannunsa, zuwa wani xan lokaci ya sauke ajiyar zuciya ganin haka sai Gimbiya Zasmin tace masa. “Kai taimake ni zaiyan kar salhim ya halaka, ka ceci rayuwar mutum biyu domin tabbas idan ya halaka ni ma sai na halaka” Zasmin ya buxe wata ‘yar qaramar jaka dake gefen damtsensa ya xauko wani xan guntun garin magani, ya xebo shi ya na mai amnaton sunan Allah sannan ya zuba a wajen da macijiyar ta yiwa salhim rauni. Bai daxe da zubawa ba sai salhim ya soma motsawa, bayan kamar wasu ‘yan mintina kuma sai ya miqe yana mai kwarara wani baqin amai, duk sai daya amayar da dafin macijiyar sannan ya xago kai yana duban Gimbiya Zasmin da Zaiyan. “Ku bani ruwa na sha” Ya faxa cikin galabaita, zaiyan ya xauko wani jalo na shi dake cike da ruwa ya bashi yasha, ya dube shi yace masa. 73 DAN BAIWA “Na gode da taimakona da ka yi wajen ceton rayuwat” Zaiyan ya yi murmushi. “Ba ni za ka yiwa godiya ba, Gimbiya Zasmin za ka yiwa domin daga ni har kai ita ta ceci rayuwar mu” Salhim ya juya yana kallonta ga mamakinsa sai yaga ta sunkuyar da kanta cike da jin kunya, sannan lokaci xaya kuma hawayen farin ciki suna fita daga cikin idanunta. “Mene ne ya saka ki zubar hawaye? Ai gani ban halaka ba” Gimbiya Zasmin ta xan xago idanu ta kalle shi sannan tace masa. “Na godewa abin bautar zaiyan daya kuvutar min da kai” Koda jin haka sai zaiyan ya dubeta cike da mamaki. ‘Me yasa kika yi godiya da abin bautata alhalin baku yi imani da shi ba” Gimbiya Zasmin tayi murmushi. “Ai kuwa yanzu ne na samu yaqini akansa, domin a lokacin da naga wannan macijiyar ta kama salhim tana shirin halaka sai na ji ina mai neman taimakon abin bautarka, kuma lokacin dana xaga takobi zan sari macijiyar taimakon abin bautarka na nema don haka ka yi sani ni kam na yi imani da shi, na kuma aminta lallai shi ne abin bauta na gaskiya” Su duka suka yi shiru suna kallon Zaiyan can salhim shima ya ce. “Nima yanzu na yi yaqini da abinda Gimbiya Zasmin ta faxa, kuma na bada gaskiya da abin bautarka ka faxa mana yadda za mu shiga cikin wannan addinin naka” Koda zaiyan ya ji haka sai farin ciki ya lulluve shi, nan take ya faxa musu yadda za su zama musulmai suka nanata suka zama ma’abota bin addinin musulunci. Nan take zaiyan ya rungume salhim cikin tsananin farin ciki yana faxin. “Daga yanzu kun zama ‘yan uwana na musulunci...” bai qarasa magana ba sakamakon wata iska da suka ji tana busawa, bayan wani xan lokaci sai suka ga wani jibgegen aljani ya sauka a gabansu yana sauka sai Gimbiya Lazma ta bayyana cikin shiga ta bokanci, tana sauka sai ta yi nuni gasu zaiyan da salhim da Gimbiya zasmin tana ambaton wasu kalamai na sihiri nan take suka ji kamar an saka sarqa an xaxxaure su duk kuzarin jikinsu ya qare, suka yanke jiki suka faxi. 74 DAN BAIWA Gimbiya Lazma ta yi murmushi a hankali cikin taqama ta qarasa wajen da su zaiyan suke kwance ta sunkuya a gabansu tace musu. “Ai baku isa ku tserewa mahaifina boka marmasi ba, lallai yanzu nan zan miqa ku hannun sarki mazwan ya cika qudurinsa akan ku”. Tana gama faxin haka ta miqe nan take zaiyan ya yunqura ya miqe,yana kallonta sannan cikin qwarin gwiwa yace mata “Haba kyakkyawa me ya ribaci zuciyarki kika bi ra’ayin mahaifinki kika zama bokanya tun da quruciyarki?” Koda jin sautin murya zaiyan sai Gimbiya Lazma ta qura masa ido tana kallonsa nan take gabanta ya yanke ya faxi. “Zaiyan?” Ta faxa cike da mamaki, shima ya qura mata idanu suna kallon-kallo nan take ya tuno wajen daya tava ganin Gimbiya Lazma, sun tava haxuwa a kasuwar bayi ta qasar sham ta shiga tare da kuyanginta suna sayen bayi sai kawai wani zaki da sarki yake kiwo ya kwace daga kejinsa ya shigo kasuwa yana banke mutane yana kashewa, nan fa aka shiga guje-guje nan take kuyangin Gimbiya Lazma suka tsere suka barta a lokacin wannan zakin ya ritsarta ita kuma saboda tsananin firgita ta kasa aiwatar da komai. Lokacin daya yo kanta da zumar halakata sai zaiyan ya dako tsalle ya rungumi wannan zakin suka soma kokawa, sun jima suna fafatawa kafin ya samu ya halaka shi, tun daga wannan lokacin Gimbiya Lazma ta faxa cikin tafkin qaunar zaiyan amman abinda ya yi mata shamaki da shi data gano shi ma’abocin addinin musulunci ne. Ta xauka gano hakan zai cire mata qaunarsa, domin duk duniya babu wanda taqi ji sama da ma’aboncin musulunci amma kuma sai ya zamana kullum zaiyan yana cikin zuciyarta, ta kasa samun ikon cire son shi daga cikin zuciyarta. Tun daga lokacin take nemansa amman ta kasa samun sa domin iya bincikenta na tsafi ya qi nuna mata wajen da yake. Sai yanzu data gano su jarumi xan baiwa, shima bata gano shi ba, kawai taga wani ma’abocin musulunci yana taimaka musu shi yasa tsawon lokaci ita da babanta suka kasa gano su. ”Gimbiya Lazmin?” Shima ya faxa cikin tsananin mamaki. 75 DAN BAIWA “Daman kunsa juna?” Salhim da Gimbiya Zasmin suka haxa baki wajen tambayar su. Nan take cikin sanyin jiki ta yi nuni garesu nan take suka ji wannan xaurin da aka yiwa jijiyoyin jikinsu ya yayye, suka zubawa juna idanu suna kallon-kallon ‘Daman kai ne kake taimakon su Salhim?” Ya gyaxa kai. “Kwarai ma kuwa, na kuma san mahaifinki Boka Marmasi da sarki mazwan suna qoqarin ganin an kamo salhim da Gimbiya zasmin an kai masa domin ya halaka su” Ta dube shi cikin tsananin mamaki tace masa. “Ya aka yi kasan haka?” Ya yi murmushi. “Wanda sarki jamhas ya aika su salhim da Gimbiya zasmin wajensu a qasar sin ki sani ba kowa bane face mahaifina, kamar yadda kema mahaifinki ya kasance boka haka nima mahaifina ya kasance mashahurin boka amman da shiriya ta zo masa sai ya amshi addinin musulunci ya kuma daina yin sha’anin bokanci, a lokacin da aka aiko su salhim shi ne ya kirawo ni ya bani umarnin na kawo musu xauki domin mahaifinki da sarki mazwan suna qoqarin halaka su, wannan dalilin ne yasa na zo nake taimakon su”. Cike da mamaki Gimbiya Lazmin ta dube su, har ta buxa baki zata kuma yin wata maganar sai suka ji wata qara haxi da rugugin aradu, nan take kuma wata walqiya ta bayyana kafin su zaiyan su yi wani yinquri sai suka ji an suresu anyi sama dasu. Nan take suka vace vat daga wajen. ** Sarki mazwan ya qarasa shiga har cikin tsakiyar fadar takobinsa a sama suka yi kallon-kallon tsakaninsa da sarki jamhas cikin tsananin fushi ya miqe daga kan karagarsa. Har ya buxe baki zai yi magana sai suka ji wata qara gami da walqiya da rugugi bayan wucewar wasu ‘yan sakani sai boka marmasi ya bayyana, ya watso da su salhim da Gimbiya zasmin da zaiyan da Gimbiya Lazma a gaban sarki jamhas ya bushe da dariya. “Ai basu isa su gujewa halakar sarki mazwan ba, na kawo su ne domin sarki mazwan ya halaka su akan idonka kafin kaima ya sare kan ka” Yana gama faxin haka sai ya juya gaban sarki mazwan dake tsaye takobi zare a hannunsa ya ce masa. 76 DAN BAIWA “Ya shugabana ga abokan gabarka daka daxe kana neman su, na kawo maka su ka yi duk yadda ka yi niya da su” Koda ganin su salhim da Gimbiya Zasmin sai daxi ya cikawa sarki mazwan rai amman ganin ‘yar boka marmasi sai ya xaure masa kai yace masa. “Ya naga Gimbiya Lazma?” Boka marmasi ya sunkuya yace masa. “Cin amana ta tayi, na gargaxeta akan afkawa cikin soyayyar ma’abota musulunci amman taqi don haka gwara itama ta halaka” Koda jin haka sai sarki mazwan ya jinjina wa boka marmasi nan take kuma ya baiwa dakarunsa damar su afkawa abokan gabarsa. Nan fa suma sauran tsirarun dakarun arnan daji da su sarkin yaqi marhat suka yo xauki akan dakarun qasar Hindu nan fa aka yi wata qazamar haxuwa aka soma fafatawa, nan take kasuwar yaqi ta soma ci, shima sarki mazwan ya zaburo kan su salhim da Gimbiya zasmin da zumar sare kawunansu. Yana qarasawa ya kai musu wani wawan sara, amman kafin ya qarasa sai zaiyan ya saka takobinsa ya kare saran, nan take ya juyo kan zaiyan da nufin kawo qarshen numfashinsa, nan fa kallo ya koma sama, suka soma wani baqin gumurzu banda qarar takubansu babu abinda kake ji. Haka suma sarkin yaqi marhat da sarkin yaqin qasar arnan daji suka kasance, duk wajen da suka tunkara sai dai kaga kawuna suna tashi sama,nan fa jini ya riqa gudana a qasan fadar. Faxa ya rincave babu abinda kake ji sai qarar haxuwar takuba, nan fa aka riqa wannan baqin gumurzun, yadda sarki marwan ya yi tsamani sai yaga wanki hula yana neman kai shi dare domin dakarun arnan daji sun tirje sun kuma jajirce. Haka shima da suka ci gaba da fafatawa da zaiyan ya xauka cewar zai samu nasara akan shi cikin ‘yan lokuta amman sai haqarshi taqi cima ruwa domin kuwa ya same shi ne sadauki ne shima mai tsananin jarumtaka. Koda ganin yadda waje ya rincave da yaqi sai boka marmasi ya yi gaggawar matsawa wajen da ‘yarsa take ya kamo hannunta cikin tsananin fushi yace mata. 77 DAN BAIWA “Maza ki nemi hanyar guduwa tun kafin sarki mazwan ya kashe saurayin naki ya dawo kanki” Ta bugawa mahaifinta harara tace masa. “Har kana tunanin wannan tsohon azzalumin zai samu nasara akan zaiyan, to idan baka san wane zaiyan ba ka tashi daga magagin baccin daka ke yi domin kuwa shi xan boka sambul ne mashahurin bokan nan na birnin sin wanda ya tumbatsa a duniyar bokaye” Ai kuwa boka marmasi yana jin haka sai ya taqarqare ya qwala wata qara domin kuma tun tsawon zamani abinda tsafinsa yake nuna masa kenan cewar ba ma’abota musulunci ne za su samu nasara akan sarki mazwan ba, wanda zai samu nasara akan shi yaro ne kuma da tsafi zai kashe sarki mazwan, amman yanzu daya ji zaiyan xan boka sambul ne sai ya samu yaqinin lallai shi ne wanda zai samu nasara akan sarki mazwan kuma ya mulki qasar Hindu. Ai kuwa kafin boka marmasi ya gama rufe bakinsa sai ya hangi hannun sarki mazwan dake riqe da takobi an yanke shi ya yi sama, shi kuma sarki mazwan ya qwala wata qara cikin razana, yana riqe da gundulmin hannun da zaiyan ya yanke yana faman tsartuwar jini. Zaiyan ya xaga takobinsa zai sare masa kai nan fa ya zube akan gwiyoyinsa yana neman afuwar zaiyan akan ya yi masa rai, zai ba shi duk abinda yake buqata, ganin haka yasa duk Dakarun qasar Hindu suka zubar da makamansu ganin sarki mazwan a cikin halin qasqanci. Zaiyan ya juya ya dubi salhim da Gimbiya Zasmin a hankali yace masa. “Ya kai yaro xan baiwa salhim ka yi sani cewar yau ga ranar daka daxe kana jira don haka sai ka zo ka cika burinka” Ai koda xan baiwa ya ji haka sai ya zaburo cikin gaggawa takobi riqe a hannunsa ya qaraso har gaban sarki mazwan. “Kar ka kashe ni” Salhim ya girgiza kai. “Ashe akwai ranar da zaka ji tsoron mutuwa? Har ka manta kisan da ka yiwa mahaifiyata ka manta yaron daka kashe ka baiwa kadojinka namansa? Ai ba a san gwarzon namiji da kururuwa ba idan mutuwa ta zo masa” Yana gama rufe bakinsa ya kafta masa sara a dokin wuya take kan shi ya tashi sama gangar jikin ta faxi qasa a gefe. 78 DAN BAIWA Koda boka marmasi yaga haka sai ya zube gaban zaiyan yana tuba, yana faxin. “Ka yi min rai, na aminta zan bar bokanci na komo addininka na musulunci” Koda jin haka sai ya xago idanunsa ya kalli Gimbiya Lazma koda suka haxa ido da ita sai yaga ta sunkuyar da kanta qasa, hakan ne yasa ya taka a hankali ya matsa zuwa wajen da take a cikin kwantar da murya yace mata. “Ba zan zarta da hukunci komai akan mahaifinki ba, amman ke kina da ikon yin duk abinda kika ga ya dace akansa” Yana gama faxin haka sai ya nufi wajen da karagar sarki jamhas take yana zuwa suna haxa ido sai aka ga sarki jamhas ya sauka daga kan karagarsa ya kamo hannun zaiyan ya xora shi akan karagar mulkin hakan shi ya baiwa kowa mamaki. Bayan zaiyan ya zauna akan karaga sannan ya soma magana cikin xaga sauti. “Ya ku jama’ar qasar Hindu da qasar arnan daji ku yi sani cewar ni ne Yarima zaiyan xan sarkin qasar sin, kuma xa ga mashahurin boka sambul don haka kamar yadda labari ya riski sarkin ku mahaifina ya zama ma’aboncin addinin musulunci, to ya aiko ni domin na zo wajen amininsa sarki jamhas na yi kira gare shi zuwa ga addinin gaskiya wato addinin musulunci, don haka ina kira gare ku domin shiga cikin wannan addinin na tsira” Bayan ya kammala maganar sai aka ga sarki jamhas ya miqe yaje gabansa ya tsuguna sannan ya ce masa. “Tabbas tunda aminina yabar addinin gargajiya ya shiga wannan addinin to wannan hanyace mai kai mu tudun mun tsira don haka maza ka faxa min yadda zan kasance daga cikin wannan addinin” Nan take zaiyan ya faxa musa. Nan take jama’ar qasar dana qasar Hindu suka amshi Kalmar shahada suka zama ma’abota musulunci. Daga nan aka shiga sha’anin rayuwa cikin kwanciyar hankali, jama’ar qasar Hindu dana qasar arnar daji suka zama kamar ‘yan uwan juna. Bayan komai ya nutsa aka xunguma aka koma can qasar Hindu inda za a sha shagalin bikin zaiyan da Gimbiya lazma da kuma sarkin yaqi marhat da Gimbiya Hamrita. 79 DAN BAIWA Yanzu kam sarki yaqi marhat ya daina fargaba domin yana da yaqinin addinin musulunci ya bashi ‘yanci auren mata huxu bama biyu ba. Haka rayuwa ta ci gaba da gudana cikin ‘yanci da haxa zuri’a tsakanin qasahen biyu. MASHA ALLAHU QARSHE 80 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 7 of 7