Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
shi bata su yake ba abinda ya kawo shi kawai yake yi. Bayan ya gaji da nema har zuwa yamma rana ta tafi faxuwa a lokacin ya gaji tiqis da nema ya fita da ran samun wannan 27 DAN BAIWA baqar baiwa ya zo fita daga cikin kasuwar bayin ya ci karo da wani ayari na fatake sun shigo cikin kasuwar ga alama zuwansu kenan a cikin bayin daya gani suna cikin sarka hard a wata kyakkyawar baqar fata baiwa tana cikin sarqa hannu da qafa kanzu ya zuba mata idanu yana kallonta babu shakka ita ya zo nema. Cikin sauri ya sha gaban shugaban ayarin shugaban su yana ganinsa ya yi sauri zubewa a gabansa yana gaisuwa yace masa cikin nutsuwa “Ya shugabana me kake nema a wajena?” Kanzu yace mata. “Wacan baqar baiwa na gani nake so a wajenka zan saya” Cikin sauri ya juya yana kallon baqar baiwar da kuma firgici yace masa. “Ka yi min rai ya shugabana wanan baiwar da kake ganinta takanas na sayota saboda Jamru, shi ya bani umarnin siyo masa baqar baiwa akan dinare dubu, ban samo wannan baqar baiwar ba sai dana dangana zuwa ga qasar Habasha” Jin an ambaci Habasha ya saka ya samu yaqinin lallai ita ce ake magana akanta. Amman jin an ambaci Jamru shi ya bada saqon a siyo masa ita sai hankalinsa ya tashi ya yi imani wani sihiri zai aikata da wannan baqar baiwa don haka ba zai yi sake wajen mallakarta ba koda kuwa hakan yana nuni cewar sai ya nuna izza ta mulki da isa wannan dalilin yasa ya kalli shugaban fataken cikin izza yace masa. “To ni kuma ita na gani ina son siye kuma ko kana so ko baka so sai ka siyar min da ita, idan kuma ba haka ba lallai zan amshe ta da qarfin tsiya” Ya saurara yana duban shugaban fataken. “Ka yi min rai ya shugabana idan na je babu wannan macen jamru zai kashe ni’ Ya yi murmushin qarfin hali. “Nima idan baka ba ni ita ba kashe ka zan yi” Jin haka take ya soma karkarwa. ‘Ka zavi xaya da wanda zai kasheka anjima wanda kafin lokacin ka yi tunanin mafita da wanda zai kashe ka yanzu take” Nan take ya faxi gaban kanzu yana neman yafiya ya kuma bada umarnin a kwance macen a ba shi. Ya qare mata kallo mace mai kyawu cikar zati da anuri yana fita daga cikin fuskarta, wannan macen tasha bamban da duk 28 DAN BAIWA matan da ake kawo su a matsayin bayi. Nan take ya xauko darhami mai yawa ya bashi, ganin yawan su sai daya saka shi susucewa nan take ya zube yana godiya shi kuma bai bi ta kanshi ba ya yi gaba abinsa suka nufi gidan sarauta. Koda suka soma tafiya sai shugaban fataken ya yi murmushi ya soma tunanin qarya da zai yiwa jamru. Lokacin da kanzu suka qarasa gida sai ya shiga da wannan baqar baiwa ta varauniyar hanya babu wanda ya gansu har suka qarasa varinsa, wani qaton gida ne wanda aka qawata shi da kayan na’ikan kayan alatu ya kwance mta sarqa da take wuyanta. “Ga wani xa ki can acan za ki zauna, za ki samu duk abinda kike da buqata na rayuwa”. “Me yasa ka siyo ni ka kawo ni nan?” Bai faxa mata komai ba ya juya ya fita abinsa yana mai faxin “Yawan tambaya ba na ki bane, sanu a hankali za ki fahimci komai”. Al’amarin shugaban fatake kuma yan zuwa wajen jamru ya zube a gabansa yana rawar jiki da fargaba cikin fushi jamru ya daka masa tsawa “Ina baqar fatar dana baka umarnin ka siyo min?” Cikin rawar jiki yace masa. “Ka yi min rai ya shugabana na siyo wannan macen amman a hanya abokin gabarka kanzu ya tare mu ya amshe ta…” Ai baima bari ya qarasa magana ba ya yi saurin surar maqoshinsa ya cira shi sama nan take ya soma wutsil-wutsil a sama kamar an xaga xan tsako nan take idanunsa suka zazzaro. “Qarya shi tasha qarya”. “Ka yi min rai ya shugabana ba ni da ikon hana shi” Nan take ya sake shi tim! Ya faxo qasa. “Lallai kanzu ya xauko rikicin da duk duniya babu wanda ya isa kawo qarshensa” koda shugaban fataken ya samu da qyar ya tsira sai ya koma bayan Katanga ya rakave. Da tsakar dare jamru ya miqe ya haxa duk kayan tsatsubarsa ya yi wani sihiri take duk wasu jama’ar gidan sarauta suka shiga barci. Wannan barcin daya saka su ya yanke burin yau zai 29 DAN BAIWA yanko kan sarki laqamu kafin ya koma kan xansa ya karve wannan baqar fatar. Zai kuma kashe shi a bainar jama’a, bayan ya kammala duk abinda ya kamata ya nufi gidan sarauta cikin taqama kai tsaye ya shiga cikin turakar sarki laqama ya same shi yana barci bisa tafarkin sihirin daya saka shi, ya saka takobi ya yanke masa kai nan take jini ya soma gudana a qasa yana kwaranya. Ya xauko kan sarki laqamu ya xaga sama yana murmushin mugunta kafin ya juya cikin sauri ya nufi sashen gidan kanzu. A lokacin da jamru ya shiga sashen kanzu babu motsin komai yana tafiya takobinsa tana xigar jini, ya qarasa xakin kamzu ya same shi shima yana barcin sihirin yace masa. “Idan na so halakar da kai da yanzu na yanke kanka kamar yanda na yanke na mahaifinka,amman sai na tara jama’a na maka bayanin yadda na kashe mahaifinka sannan na kashe ka” Nan take ya xauko wani ruwa a cikin gora ya zuba masa nan take ya farka suka yi kallon-kallo shi da jamru sannan ya mayar da kallonsa zuwa ga hannunsa dake xauke da kan mahaifinsa. Ku min afuwa mu gamu a littafi na 2 domin jin ci gaban labarin. JARUMI XAN BAIWA 2 Idanun kanzu suka rufe ya rasa me yake masa daxi a duniya ya ji duk wani tsoro da fargaba ya fita daga cikin ransa, cikin qarfin zuciya ya taso a fusace da zumar surar Jamru su soma fafatawa amma ya makara saboda jamru ya gano manufarsa. Kafin ya qasara gareshi tuni ya yi zamiya kai tsaye Kanzu ya wuce ya gwaru da ganuwar ginin xakin ya yi wata faxuwa ya dawo daya ya yi zaman ‘yan bori. Jamru ya saka qafa ya daki gefen fuskarsa da takalmin da ke qafarsa take bakinsa ya fashe jinni ya soma kwaranya qarfin duka da ya yi masa sai daya sa ya yi tsalle gefe guda kamar an xauki karmamin itace an yi jifa da shi ya tafi can gefe guda ya faxi qasa. A hankali jamru ya taka 30 DAN BAIWA ya qarasa zuwa gareshi ya tsaya akansa yana kallonsa yana yi masa dariyar mugunta ya dube shi da duban wulaqanci yace masa. “Ka xauka cewar zan manta bashing aba da kuka ci nawa? Don haka kayi sani cewar wannan kan da kake gani a hannuna na mahaifinka ne sarki laqamu wanda mutuwa ta xauke shi kuma ni xinnan da kake gani da hannuna na yanka shi na kawo maka kan saboda ya zama abokin mutuwarka kafin zuwa washe gari” Ya bushe da dariya yana kallonsa ya ci gaba da Magana. “Kayi sani cewar babu gudu babu ja da baya tabbas washe gari zan kasha ka da mutuwa mafi muni da wani xan adam bai tava irinta ba a cikin qasarnan” Yana kammala faxar haka ya juya cikin isa da taqama ya xauko wani qaramin qaho daga cikin qugunsa ya soma busawa a hankali. Ai kuwa faruwar hakan ke da wuya sai gashi jama’ar qasar da suka shiga wannan bacci na sihiri suna farkawa xaya bayan xaya. Kowa ya farka sai ya cika da mamakin dalilin daya sashi yin bacci a lokacin da bai shirya ba. Jamru yana gama busa qahon sai ya yi wajen gidan kan sarki laqamu a hannunsa ai kuwa duk bafaden daya ci karo da shi yana ganin kan sarki laqamu a hannun jamru sai ya zube qasa yana mubaya’a ga jamru. Kai tsaye fada ya wuce yana zuwa ya samu waje akan kujera sarki laqamu ya zauna kafin wani lokaci fada ta cika maqil da jama’a ko wanne ya yi shiru yana jiran yaji abinda jamru zaice. Bayan ya qare musu kallo na tsawon wani lokaci sannan ya saukar da ajiyar zuciya cikin izza ta mulki ya soma Magana. “Yauce rana ta farko da burina ya cika na zama sarkin qasar shamara bayan na halaka da ruhin tsohon sarki laqamu kuma kuyi sani cewar washe gari babu shakka zan yiwa babban abokin gabata kanzu kisan gilla” Ya dubi jama’ar qasar gabaki xaya. “Da wannan kalamin nawa nake cewa daku kowa ya halarci bakin fada gobe da safe don ganin kisan da zan yiwa kanzu” Yana kammala faxar haka ya miqe kai tsaye ya nufi hanyar shiga cikin gidan saeki laqamu vangaren da matan sarki suke da bayani da kuyangi. Yana qarasawa ya saka sarkin gida ya fito masa da su dukansu suka tsaya carko-carko ya soma bi yana kallonsu xaya bayan xaya yana neman baqar kuyanga da kanzu ya amsa. 31 DAN BAIWA Har ya kammala dubansa bai ga mai kama da it aba yaja tsaki cikin fushi ya xauko madubin tsafi ya soma dubawa yaga ai tana vangaren kanzu daya baro. Ya yi murmushi ya kalli kuyangi da matan sarki laqamu yace musu. “Ku daga yau na maisheku matana kamar yadda tsohon sarki ya zauna daku a matsayin mata haka kuma kuyangi” Ya yi shiru yana kallonsu ya xan soma takawa a hankali har zuwa wajen jakadiya ya tsaya a wajen yana kallonta sai ya saka hannu ya fizgota kusa da shi yace mata. “Ke munafukace kece jakadiyar kakana don haka babu shakka kin tsufa da yawa mutuwa ce ta kamata da shekarunki” Ta zube gabanshi ta soma neman tuba amma ina ta makara don kafin ta kuma yin Magana ya saka kaifin takobi ya sare mata kai kan ya faxi qasa yana cizon rairayi. “Wannann izina gare ku sauran matan gidan sai kuma naga wacce zata kuma kawo min cikas akan abinda ya shafi sha’anin mulkina duk wacce tayi gardama hakace zata kasance da ita” Nan take jikinsu yayi sanyi jikinsu ya soma karkarwa don ganin baqin zallunci daya taya same su. Ya kaxa kai ya juya wannan karon cikin sauri da zafin nama da zumar isa vangaren kanzu daya baro yasan wannan dukan dayayi wa kanzu na jarumtaka babu abinda zai sashi moruwa daga yanzu har zuwa washe gari. Yana qarasawa ya samu kanzu yana kwance shame-shame kamar yadda ya fita ya barshi a wajen ya sunkuya ya cakumo shi ya soma jijjiga shi a hankali ya buxe ido da qyar yana kallonshi. “Ina baqar baiwar nan daka amsa a hannun shugaban fatake?” Kanzu yayi murmushi a hankali yace masa “Ai ko kasheni zaka yi sai dai ka kashe ni amma ba zaka tava sanin wajen da take ba” Jamru ya yi murmushin mugunta. “Kamar wani jarumin kirki har kake dagewa cewar ba zaka faxi wajen da take ba, ai ragwaye masu zuciyar mata basu da wani tasiri a rayuwa haka kuma babu abinda za su iya da hakan yafi maka kwanciyar hankali ka faxan wajen da take kafin mutuwa ta riskeka” Kanzu ya yi murmushi. “Ai wanda mutuwa take gaf da shi babu tsoron da zata ba shi amma kuma ko banza nasan cewar idan ka kasheni zaka riqa tunawa da ni a matsayin abokin gabarka kuma haka zaka riqa tunawa da ni a duk lokacin daka tuna har bayan mutuwata baka samu damar mallakar baqar baiwa ba” Maganar da Kanzu ya faxa mas aba qaramin ci masa rai ta yi 32 DAN BAIWA ba hakan yasa cikin fushi ya zare takobi da zumar sare maswa kai ayita ta qare. Amma abin mamaki koda ya kai sara da zumar sare masa kai sai yaji an tare saran daya kai masa jamru ya juya cikin fushi don ganin wanne ya masa wannan aika-aikan ai kuwa sai suka haxa idonu da baqar baiwar nan da yake nema. “Ai koda ka tsawaita bincike baka isa ka gano inda nake ba, ubangijin musulunci ya bani kariya ya tsareni daga duk wani tsafi naka kuma ka yi sani cewar tunda ka zama azzalumi babu shakka ba z aka yi tasiri wajen aiwatar da zallunci ba yanzu nan kaima zan kawo qarshen burinka na son zama sarki” Cikin tsananin vacin rai yace mata. “Ke shashashar banza kada ki xauka kowa soko ne kamarki ki kalli jarumi kamata kuma sarki mai girman daraja kina jin za ki iya xaukar wani mataki akaina to ki sani ‘yan maza ma sunyi sun kasa bare ke” Baqar baiwa ta gyara riqon takobinta tace masa. “Ai kaine ragon maza da ka maida zallunci ado tabbas yanzu za ka yi dana sanin yin haka” Ai kuwa sai takaiwa jamru sara da takobin dake hannunta ya yi saurin karewa amma duk da haka sai data yi nasa yi masa bile a fuska. Wannan abun data yi masa shi ya kuma harzuqa shi ya qona masa rai cikin tsananin fushi ya mayar mata da martanin sara data kawo masa, itama ta kare suka soma musayar kai sara da suka kafin wani lokaci duk wani abu da yake cikin xakin sun tarwatsa shi. Saboda duk wajen da suka kai sara basu samu juna ba sai dai kaga sun tashi wani abu sama nan danan suka hargitsa komai suka fito wajen gidan suna musayar sara da suka cikin gwaninta da nuna jariya ta yaqi. Kana ganin yadda wannan baqar baiwa take kare saran da jamru yake kawo mata kasan cewar ta gwanance wajen iya yaqi kuma jarumace ta gaske. Furuwar haka ya baiwa jamru mamaki kuma ya samu tabbacin idan bai zage damtse ba babu shakka wankin hula zai kaisa dare, don haka ya soma sauya salo-salo na yaqi da zumar samun nasara akanta amma duk salon daya sauya si ya samu tasanshi. Nan fa suka ci gaba da farauta ran junansu a haka gari ya waye jama’a suka taru suna kallon wannan fafatawar da suke yi kowa yana faxin 33 DAN BAIWA albarkacin bakinsa akan wannan faxan da ake yi wanda aka rasa wanda zai raba shi hakan nan kuma an rasa wanda zai samu nasara a cikinsu. Zuwa takewar rana sai jamru ya soma gajiya kuma duk wani salo na faxansa ya qare sai maimaici yake na wanda yayi na farko amma ita kuma kamar yanzu take kuma samun qwarin gwiwa da kuma wata hazaqa ta na shiga jikinta. Ai kuwa nan da nan jamru ya soma sarewa qarfinsa ya qare ya zama baya iya kai sara sai dai karewa ai kuwa yana ganin haka sai ya yarda takobin hannunsa suka tsaya carko-carko kamar zakaru yana kallon baqar baiwa cikin maida numfashi yace mata. “Babu shakka kin samu nasara wannan karon akaina wanda a tarihin babu wani jarumi daya tava tsayawa a gabana yayi tsawon sa’a guda ba tare dana halakar da shi ba amma ke gashi mun xauki tsawon sa’o’i kusan goma muna fafatawa amma babu wanda ya yi nasara saboda haka kiyi sani cewar idan hagu ta qiya sai a koma dama yanzu zan halakar dake ta hanyar tsafi” Ai kuwa yana faxar haka sai baqar baiwa ta yi murmushi sannan itama tace masa. “Ai kuwa ka zo wajen da zan nuna maka cewar tsafi harka qarya ce da kuma son zuciya da son vatar da jama’a babu shakka yau Addinin gaskiya zai dane na qarya”. Jamru yana jin haka sai ya soma karanto xalasiman tsafi ya yi nunu da baqar baiwa da zumar iska ta xauketa ta karkaryata. Nan take wata baqar guguwa ta tashi me qarfi ta nufi wajen baqar baiwa take duk abinda taci karo da shi kafin ta qarasa sai dai kaga ta sureshi tayi sama da shi tana rugurguza shi, amma ita tana tsaye qam bata motsa ko nan da can ba, a cikin zuciyarta ta soma neman taimakon Ubangijin musulunci tana neman xauki gareshi. Ai kuwa guguwar tana zuwa wajenta sai ta tsaya waje xaya tana juyi zuwa wani lokaci kuma sai ta lafa ta koma kamar ba guguwa ba. Ganin haka yasa yaa kuma wani sihirin ya aiko mata da wuta tana turuqo tana cinye duk abinda taci karo shi ta tunkari baqar baiwa amma tana zuwa kusa da ita sai ta zama hayaqi ta tashi sama. “Ke da me kike taqama wane irin sihiri kike yi?” Ta yi murmushi. “Ai bana yin tsafi kawai na dogara da izinin Allah, ubangijin musulunci wanda ya aiko da manzon Allah da gaskiya kuma yake kira da izinin Allah ga mutane da su zama suna bautawa Allah shi kaxai. A cikin addinin aka sanar damu cewar tsafi shirka ne kuma duk wanda ya yi 34 DAN BAIWA Imani da Allah to babu shakka Allah zai kare shi kamar yadda ka gani da idonka yanzu ka aikata wannan sihirin bai yi tasiri akaina ba. Yanzu ina kira gareka daka zama mai tsoron Allah ka yi Imani da shi ka sani cewar wannan aikin da kake aikatawa zallunci ne da kuma shirka idan hark a tuba ga Allah zai amshi tubanka” Jamru ya yi murmushi. “Kina cikin ma’abota musulunci kema?” Ta gyaxa masa kai. “Tabbas hake kuma ina kira gareka daka zama kaima ma’abocinsa” Ya yi murmushi. “Ai kuma an faxa mun duk ranar daa gamu da ma’abocin musulunci to rana ita ce rana mutuwa ta babu shakka ko wane lokaci idan na duba madubin tsafina sai naga namiji ne ya kashe ni amma kuma yanzu ya zan ga savanin haka mace ce zata halakar da mashahurin jarumi kamata. Bana jin zanyi wannan faxuwar baqar tasa tabbas ba zai tava faruwa ba, har abada ba zan amshi amshi wannan Addinin da kike min tayinsa ba kamar yadda na sani cewar ba zan samu nasara akan ki ba don haka zan xauki matakin da boka zalzabu ya xauka a lokacin da ma’abota addinin musulunci suka ci qasar shi da yaqi ya kasha kansa saboda baqin ciki nima ki sani yanzu nan zan kashe kaina, amma ki sani cewar da zarar na halaka kaina sirrin tsafina zai koma jikin wata birinya da nake kiwonta a wannan biranya zata hana duk wani mai shirin zuwa qasar sin koyon tsafi kuma zata adabi duk wasu fatake da aljanu da dabbobi da suka wanzu suna rayuwa a waje ba zata halaka ba har tsawon zamani” Ai kuwa koda gama wannan maganar sai ya suri wuqar dake qasa ya sokata a qirjinsa take ya faxi qasa yana shure-shuren mutuwa. Baqar baiwa ta qarasa kanshi ta tsaya tana kallonsa yanda yake fama da magagin mutuwa ta yi murmushi tace masa. “Maza sun faxi… amma ka yi sani cewar da izinin Allah yaro xan baiwa shi ne zai halakar da ita” Ta juya zata soma tafiya a cikin magagin mutuwa taji yace mata. “Wane kuma yaro xan baiwa?” Ta juyo tana murmushi tace masa. “Wani yaro ne da za a haife shi kuma Allah zai tsare shi ya kuma ba shi baiwa ta daban, duk tsafinka baka tava dubo wannan abun ba” Ta kaxa kai tayi gaba nan jamru ya yi mushe a wajen ugulaye suka sauka akan gawarsa suna tsatsagar namansa. 35 DAN BAIWA Kanzu ya fito yana yiwa baqar baiwa jinjina akan wannan aikin da ta yi kuma ya yi Imani da cewar duk wanda ya aikata alheri babu shakka zai samu sakayya me kyau. Nan ya amshi addinin musulunci kuma ya bada umarni ga jama’arsa da kowa ya amshi Addinin musulunci nan take jama’a suka yi ta shiga Addinin gaskiya. Daga ranar qasar shamara ta zama qasar da take zama cikin jin daxi da adalci da kwanciyar hankali haka ya yi Imani da cewar adalci shi ne yake zaunar da qasa lafiya. Ya dubeta cikin nutsuwa yace mata. “Wannan labarin ya tavani sosai kuma ya haska mun gabana akan cewar yiwa jama’ar qasa adalci shi ne yake sakawa sarki ya samu xaukaka, amma kuma kina ganin maganar da baqar baiwa ta faxa na cewar xan baiwa zai kashe birinya zai tabbata kuwa?” Macen sihiri ta yi murmushi. “Ai babu makawa shi kaxai zai iya halakar da ita zai kuma samu nasara akan sauran abokan gabansa wannan yaron duk yadda kake tunaninsa ya wuce nan kuma zaka sha mamaki lokacin da zai zo qasarka yana neman taimakonka” Ta juya tana kallon sham. “Nayi Imani da sham yana da iko daya taimaki wannan yaron sama da yadda yake taimakona” Sham ya yi murmushi. “Ai kuwa yanda kika bani labarinsa abin tausayi ne kuma abin a taimaka masa a bashi qwarin gwiwa ya samu damar halaka azzalumin sarki mazwan” Ta miqe tana qare musu kallo su duka sannan tace musu. “Yanzu aiki xaya zan maka shi ne idan na samar da dawakai guda biyu wanda yaro xan baiwa zai yi amfani da su wajen guduwa a lokacin da sarki mazwan zai so halakar da shi to zan kuma naxe nisan tafiya ta hanyar amfani da alqaluman sihiri wanda hakan zai bada gudumaewa wajen su sawa su gujewa mayaqan sarki mazwan. Babu shakka wannan zai taimaka masa matuqa wajen tsera da shi daga halaka amma idan bah aka ba sai sun samu nasara akansa” Sarki hamhas ya saukar da numfashi. “Amma kuma ta yaya kike ganin za mu tserar daa shi bayan mun zama bama ga maciji da sarki mazwa? Ta yi murmushi. “Kada ka damu da wannan abun yanzu zan sana’anta sirrin tsafi na aikawa da boka marmasi a cikin ilimin tsafi zai gane cewar ya zama dole idan suna son samun xaukaka to sai sun qula sulhu da ku sun 36 DAN BAIWA zauna lafiya da ku sun daina gaba da ku, ba zai tava ganin cewar sihirin qarya bane don haka idan yaga haka zai samu sarki mazwan ya faxa masa shi kuma yana bin duk maganar da boka marmasi ya je masa da ita. Idan haka ta kasance za su aiko da wasiqa neman sulhu ku kuma sai ku amince da haka amma babu shakka wannan gabar zata dawo bayan tsawon zamani yanda zai zama kun zama abokan gaba sama da yadda kuka kasance a yanzu zaai zama kuna neman farauta rayukan juna sama da wannan lokacin” Koda jin haka sai sarki jamhas ya yi murmushi. “Ai kuwa idan haka ta kasance zanji daxi na kuma yi farin ciki sosai saboda babu makawa nasan lokacin jama’ata sun samu ci gaba sama da na yanzu haka kuma dakaruna sun qara yawa ga faxin qasa da zamu qara haka kuma jama’a ta sun qaru idan hakae lokacin ba zamu yi shakkar tunkara sarki mazwan ba” Macen sihiri ta koma ta zauna. “Haka maganarka take ni yanzu zan zauna anan qasar taku zuwa wasu ‘yan kwanaki har sai sham ya warke sannan mu ci gaba da tafiya zuwa wajen da muka nufa” Ta tashi ta koma kusa da sham ta zauna. Sarki jamhas shi kuma ya tashi ya fita daga fada. Duk wannan abun ya faru ne kafin a haifi Yaro xan baiwa. ** Lokacin da yaro salhim ya cika shekara shida a lokacin tsufa ya rake almajira harsu ya zamana cewar ko fita bata iya yi don haka dole tasa ta koma zama da kuma kwana a cikin wata tsohuwar buka dake gefen kasuwa wanda sau tari idan ruwan sama ya zo sharkaf suke jiqewa saboda rufin bukar duk ya lalace kuma basu da kuxin da za su iya biya a gyara musu. A kullum sai salhim ya je ya yi bara sannan yake samo abinda za su sayo abinci da za su ci su kuma sha shi da ‘yar tsohuwa. Ana cikin haka ciwon ajali ya kama ‘yar tsohuwa Harsum shekara tana cika tace ga garin ku a wannan ranar salhim ya yi matsanancin kuka da bai tava irinsa ba. A kuma bisa al’adar idan mamaci bashi da ‘yan uwa ko kuma wasu da za su masa gata to baza’a yi bikin qona shi ba sai dai kawai a xauki gawarsa akaita teku a jefar. Itama gawar sai anga zata yi wari, ta damu mutane da suke wajen bisa wannan dalilin yasa lokacin da tsohuwa ta mutu aka rasa waxanda za su 37 DAN BAIWA kaita har sia datai yi kwanan keso, kafin safiya ta soma kumbura tana wari nan fa salhim ya fashe da kuka ya dunga bin mutanen kasuwa yana roqonsu akan su taimaka masa akai gawar. A qarshe dai a wulaqance aka xaurawa gawar igiya aka jata a qasa har zuwa bakin teku aka jefata cikin ruwa, tun daga wannan lokacin baqin cikin abinda ya faru yasa Salhim ya xaukar wa kansa alqawarin idan ya yi tsawon rai sai ya kawar da zallunci gami da jahilci da mutanen birnin Hindu suke cikinsa. Haka ya taso a cikin rayuwarsa cikin qunci da takura na rashin gata da samun kulawa a cikin rayuwa a haka ya kai shekara goma. Rana ya yini yana bara bai samu komai ba kuma yana jin yunwa ta isheshi kamar zai mutu adaidai wannan lokacin ya zo giftawa ta qofar gidan sarki muzwan yaga ana rabawa bayi gurasa don haka ya kutsa kai ya saci xaya domin ya samu ya ceci rayuwarsa. Wannan shi ne asalin dalilin daya saka wanan badakaren ya biyoshi da gudu har suka shiga cikin kasuwa domin samun damar halaka shi bisa umarnin sarki. Lokacin da yarinya ‘yar indiyan daji ta kama hannun salhim suka ruga da gudu daga cikin kasuwa har zuwa cikin dajin dakarun sarki mazwan suna biye da su a guje amma sun kasa cin masu a haka suka vace musu da gani. Nan fa hankalin dakaru ya tashi ainun, don sun san halin sarki muzwan idan har basu kai masa sassan jikin wannan yaron ya ciyar da kadojinsa ba to akansu zai huce fushinsa. Nan fa suka rarrabu a cikin dajin kuma kuma suka rarrabu sashe-sashe da zumar su samu damar kama yaron salhim amma ko xoriyarsa basu jib a al’amarin daya kuma dugunzuma musu hankali suka tsaya suna shawarwarin abinda ya kamata su yi wanda za su ceci kansu daga hannun sarki mazwan. Nan kuwa wata dabara ta faxo musu suka dawo cikin kasuwa wajen da wata mahaukaciya take kwana tare da ‘ya ‘yanta guda uku suna zuwa suka tarar da ‘ya ‘yanta suna kwance a cikin rufar kasuwa suna ta sharar baccinsu kawai sai suka lallava suka sace babba wanda girmansa zai yi daidai da salhim suka toshe masa baki yana wutsi-wutsin da qafaffunsa suka kai shi can bayan gari suka sare

Chapter 3 of 7