Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
bashi da ikon busa mata rai ta tashi tayi motsi, a zaman daya yi a gefen kushewarta matarsa, yana cikin halwa ne na son gano yadda zai busawa wannan sunduqin rai amman har shekara ukun bai gano ba. Abinda ya gano a cikin halwarsa duk abinda yake so ba zai samu ba, mafita xaya ce idan yana son ta motsa, sai dai 13 DAN BAIWA ya samo wata budurwa macen aljanu ya sakata a cikin jikin robar mai sifar matarsa sai ta riqa motsawa. Wannan abin daya gani shi yasa ya zauna yin halwa tsafi har sai daya nemo budurwa Aljana mafi kyawu a cikin yankin aljanu ya kamota ya sata a cikin butar tsafi ya xauki butar tsafin ya saka a jikin wannan gangar jikin roba. Da wannan ya tashi gangar jikin ya zama tana iya motsi tana iya tafiya tana iya magana. Ganin wannan nasarar daya samu ya saka ya xauki sirrin tsafi dubu xari tara ya saka a cikin jikinta, ya kuma saka mata qarfin sadaukai dubu ya saka mata hikima da balaga ta magana, wannan ita ce irinta ta farko da wani boka a duniya ya qirqira kuma mafi hatsari a duniya. Duk lokacin daya so ita kaxai yake turawa wani gari taje ta yaqi duk girman daular daya ga dama, haka kuma idan ta saka dakaru a gaba bata gajiya tana iya yin shekara guda tana yaqi bata gajiya ba, tunda ita bata ci bata sha bata da wani aiki sai yin biyayya ga boka, idan aka koma fanin tsafi idan tana faxar kalaman tsafi sai ka yi tsamanin duk duniya babu kamarta, hatta a wannan zamanin banda ni babu wanda ya kaita sanin sirrin bokanci, wannan fafatawar da kuka yi don na baiwa qasar nan kariya na tsafi shi yasa bata yaqe ku kuma tayi galaba akan ku ba, amman ba don haka babu shakka da kaga azaba irin wacce baka tava ganin irinta ba” Ya yi shiru yana kallonsa. Sarki mazwan ya yi shiru yana kallonsa Boka marmasi ya saukar da ajiyar zuciya ya qara cewa da shi. “Yanzu ya kake ganin za a yi yadda za mu qara mallakar takobinmu data karva kuma ka sanar da ni cewar kar na sake takai birnin Nur saboda sarki Lambo zai iya mallakar 14 DAN BAIWA wannan takobin tawa” Boka marmasi ya bushe da wata dariya sannan ya dafa kafaxar sarki mazwan yace masa. “Naga hankalinka ya tashi ka kwantar da hankalinka bisa wannan buqatar da ka zo min da ita, don haka zan aika saqo gareta bisa tafarkin tsafi kuma zan dawo maka da takobin taka domin na faranta maka rai” jin wannan kalamin ba qaramin faranta ransa ya yi ban an take fuskarsa ta washe zuwa ga murmushi. Daga nan suka yi sallama Boka marmasi ya vace daga cikin gidan sarautar. ** Lokacin da su macen sirri suka nausa suka shiga cikin daji tana kan ingaraman dokin data hau ganin tafiyar bata yi musu sauri sai ta tsayar da dokin ta xauki sham ta sava akan kafaxa ta ruga da gudu, kamar wacce take gudu akan iska kafin wani lokaci ta yi nisa da birnin Hindu. Wannan karon kana ganin fuskarta kasan ranta a matuqar vace yake, saboda babu anuri ko farin ciki hakan ya faru ne saboda ganin irin raunin da sarki mazwan ya yi wa sham. Tasan sham sadauki ne wanda baya tsoro ko fargaba, amman sarki mazwan ya shamace shi ya kafta masa sara wanda tun sanda aka yi masa bai kuma motsawa ba. Hakan yana nuni cewar akwai sirrin tsafi a tattare da takobin, don haka ta qara azama ta shiga cikin dajin a lokacin ta qarasa wani waje mai yawan rairayi da kuma ruwa mai kyau yana gudana a wata qorama gefe guda kuma ga wasu ‘ya ‘yan itatuwa jere reres gwanin ban sha’awa. Tana qarasawa ta samu waje ta ajiye shi akan rairayi mai sanyi ta zauna tana kallonsa, har zuwa lokacin banda idanu babu abinda yake juyawa nan take tausayinsa ya kamata ta 15 DAN BAIWA miqe ta komo kansa ta tsaya tana kallonsa da idanunta masu haske fari qal. Zuwa wani lokaci ta soma karanto wasu xalasimai na tsafi kala-kala take abubuwa suka bayyana garai-garai gareta cikin gaggawa ta buxe idanunta daga rufewar data yi takai dubanta zuwa ga wajen da yake ga mamakinta babu shi sama ko qasa. Ta juya ya kuma juyawa ya duba ko zata ga wata alama da zata nuna mata sawun wani abu amma sam babu wata alama, wane wannan ya aikata wannan zunibin gareta? Tabbas ko wane sai ta azabtar da shi da irin azaba irin ta yaqi, nan take ta taqarqare ta kumarma ihu wanda sai daya saka duwatsun da suke cikin dajin amsawa. Tsuntsaye da suke bakin ruwan suka bazama suka tashi sama, igiyar ruwa ta soma ambaliya kafin kace kwabo tuni launin wajen ya sauya saboda wannan ihun da macen sirri ta kurma. Idanunta suka kaxa suka yi ja, saboda tsananin fusata da tayi kamanita suka sauya daga kyakkyawar mace zuwa wata kalar ta daban. Lokaci guda ta soma nazari akan abinda ya shafi babi na tsafinta kafin wani lokaci duk wani abu daya faru ya bayana a gareta. A gaba da wajen da yake nesa kaxan akwai wasu arnan daji da suka kasance suna bauta ga wani dodon gunki da suka sassaqa shi daga itace. Wannan abin bautar na su ya kasance suna yi masa hadaya duk qarshen wata da jinin baqon matafiyi wanda hanya ta biyo das hi, hakan ya saka suka kafa wajen wannan qorama a matsayin tarko da suke kama baqi. Hakan ya saka suka sace sham suka nufi birin nasu na arnan daji domin yau kwana uku kenan ba su samu wanda za su yi hadaya da shi ba, wannan birnin ya kasance shi ne kusa da birnin Hindu kuma shekara da shekaru babu basa ga 16 DAN BAIWA maciji da masarautar birnin Hindu, wannan gabar ya saka jama’ar birnin Hindu basa iya shiga cikin dajin yin farauta ko kuma yin itace domin gudun gamuwa da tarkon arnan daji. Sarki mazwan yana sha’awar fita farauta amman saboda baqar gabar dake tsakaninsu hakan ya saka ya haqura, ya aika qashen da suke kusa da su aka sayo masa duk wani na’ika na dabobin daji ya zuba a cikin wani faffaxan waje daya kilace ya kuma qaramin kogi a gidansa yana kiwon kadoji. Wannan birnin na arnan daji ya kasance yana da kyau da kuma tsari anyi gidajen daga duwatsu suna mulki a qarqashin sarkin su Jamhas wanda ya kasance gawurtacen jarumi mai juriya da kuma bajinta a fagen fama. Matsala xaya take damun sarki jamhas shi ne rashin samun haihuwa, ya yi maganin ya kuma bi bokaye da ‘yan tsubu ya yi tsatsuba amman haihuwar bata samu ba hakan ya saka ya haqura ya saka sha’anin sarautarsa a gaba. Haka suka ci gaba bauta ga wannan gunki suna yi masa hadaya da jinin duk wani baqo da suka kamo,kuma hasalin yiwa gunki hadaya ya samo asali ne daga gaqar gabar da suke yi da jama’ar Birnin Hindu wanda gunki ne yake basu sa’a a duk lokacin da suka tashi yin artabu da dakarun birnin Hindu. Ana kawo sham gaban sarki jamhas ya tashi yana dubansa cikin nutsuwa ya xaga kai yana kallon dakarunsa yace musu. ‘Ya naganshi a cikin wannan halin na galabaita kuma ga ciwo a jikinsa? Anya kuwa abin bautar mu zai amshi wannan a matsayin hadayar da za mu yi masa?” Ya ci gaba da kallon sham sannan ya tashi yana zagaya shi. “Wane irin ciwo ne ya samu wannan har ya kasance a kwance kamar matacce?” colom sauri ya shiga wani xakin da 17 DAN BAIWA yake kusa da fadar wanda anan kayan tsatsubarsa yake. Ya xauko madubin sihiri ya soma bincike akansa nan yaga artabun da ya yi da jama’ar qasar Hindu da yanda suka shigo cikin dajin tare da macen sirri. Amman abinda ya bashi mamaki ya kuma xaure masa kai yadda madubinsa ya kasa nuna masa macen sirrin. Ya yi iya yinsa domin ganin ya samu bayani akan macen sirri da kuma nemo daga wane jinsi ta fito ganin haka ya saka hankalin sarki jamhas ya tashi, cikin zafin nama ya ajiye madubin tsafin ya xauko kayan tsatsuba ya buxe kwatarniyar tsafi ya baza wuri ya soma duba bisa tafarkin tsafi. A lokacin da yake wannan binciken game da wacce ce macen sirri ita kuma a lokacin ta shigo cikin birnin arnan daji cikin fushi da fusatar zuciya. Macen sirrin ta kai tsaye ta shiga cikin fada ai kuwa dakarun fada suna ganinta suka yo kanta cikin halin fushi suna daka mata tsawa. “Ke yarinya wane ya baki izinin shigowa cikin garin nan babu shakka halaka ce ta kawo ki” Macen sirri ta xaga kai tana dubansa kafin tayi wani murmushi mai xauke da fushi tana kallon yadda suke kusanto kawunan su zuwa ga halaka tabbas yaro baisan wuta ba sai ya takata. “Kana kallona kasan ban yi kama da yarinya ba, domin yarinta tana bayan mahaifiyarta ahir! Xinka da kuma gangancin kuma faxar wannan Kalmar, maza ku miqo min abokin tafiyata cikin ruwan sanyi idan ba haka ba fushina ya sauka akan ku” Nan wani ma gigiwa ya yo kanta cikin fusata musamman domin ganin mace ce bata da wani jarumtaka. Rashin sani yafi dare duhu. Yana zuwa kusa da ita yakai hannu da zumar zungure mata hanci amman ga 18 DAN BAIWA mamakinsa sai ya ji hannunsa ya soma laqwashewa yana komawa zuwa cikin hancinsa, nan yaga lamarin bana wasa bane, ya soma qoqarin hana faruwar hakan amman ya kasa take ya soma kwaranya ihu take jini ya soma fita daga cikin hancinsa ta sake ke shi ya faxi yana burgima a qasa. Ganin wannan abin mamakin daya faru ya saka sauran dakarun suka sha jinin jikinsu, tabbas wanan macen tana taqama da sirrin tsafi idan kuma haka ne gidan shi ta zo, haka ya saka suka ja da baya wasu dakaru da aka horesu da tsafi suka dawo gaba nan suka soma tsatsuba sai kaga badakare ya zama zaki yayo kanta da gudu, kafin ya qaraso wajenta sai dai kaga ta kalle shi da ido sai kaga wata iska ta sure shi tayi watsi da shi can gefe guda. Sai kaga wasu a cikinsu sun zama wuta kafin su zo wajen sai wani ruwa ya baiyana ya haxiye su. Ai ko da ganin sirrinta yafi na su sai suka yi xauki kanta da takobi a zare, masu kibiya suka soma yi mata ruwan kibiya amman abin mamaki duk kibiyar data je jikinta sai kaga ta narke ta zama ruwa ta zube a qasa. Hakan bai hana su xauki kanta,ho abin kallo ya samu nan suka gauraya ta zare takobin sarki samzan data amsa nan fa kasuwar yaqi ta soma ci, mutuwa ta soma shawagi a tsakaninsu kawunan sadaukai na birnin arnan daji ya soma zuba a qasa kamar ana sassabe. Babu abinda zaka gani sai gilmawar makamin macen sirri yana ratsa tsakanin mazaje yana fasa qirjinsu zuciya tana faxowa qasa jini yana zuba shaaa! Kamar gulbin ruwa. Kalar jan jinin dakarun birnin Arnan daji su kansu suka san cewar yau wata shaixaniya ta sauka a qasar su yau kam sun tsokano tsuliyar dodo. 19 DAN BAIWA Suna cikin wannan xauki ba daxi suka ji an kwatsama musu wata tsawa cikin sauri suka ja da baya suka tsaya carko-carko kamar zakaru suna kallon junansu a lokacin sarki jamhas ya fito daga cikin xakin tsatsubar shi cikin fushi ya dubi ginin fadar yaga yadda ya rine da jinin jama’arsa ya dubi qasa yaga yanda kawuna suka wadata a zube babu jikuna take ya tsorata da shu’umanci macen sirri babu shakka yanzu ya gamsu ita ce. Ya yi saurin dakawa jama’arsa tsawa da cewar. ‘Maza ku zubar da makamanku kuma ku zube gabanta domin nemn afuwa akan zunubin da kuka aikata mata” Ai kuwa da jin wannan kalaman na sarki sai mamaki ya kama su suka zube a gaban macen sirri suna neman tuba. Sarki jamhas ya qarasa gabanta ya kalleta cikin girmamawa yace mata. ‘Muna neman afuwa bisa laifin da muka aikata cikin rashin sani. Tun sanda naga abokin tafiyarki na shiga cikin xakin bokancina domin gano wane shi, a bincikena ne komai na ki ya bayyana a gare ni don haka muna neman afuwa a gareki bisa wannan lamarin da muka aikata miki” Jin kalaminsa ya saka macen sirri ta maida makaminta ba tare data ce komai ba ta nufi wajen da sham yake tana zuwa ta sunkuya ta xauke shi cak kamar ta xauki karmami ta nufi wajen da karagar sarki jamhas take ta kwantar da shi ta tsaya tana kallonsa har lokacin numfashinsa yana fita. Sarki jamhas ya yo wajenta cikin sauri ya zo kanta yana kallon sham zuwa wani lokaci ya nisa yace mata. “Takobin sarki mazwan ce tana xauke da wani dafi, kuma wannan dafin yana halaka mutum. Badon sham yana da nisan kwana ba da tuni ya halaka. Don haka mu jama’ar daji za mu karya wanna sirrin da yake jikin takobin” Take ya buxa 20 DAN BAIWA gefen duga-diginsa ya xauko wata ‘yar buta ya xauko wani guntun xan itace ya karyo shi ya saka a baki ya taunashi ya soma marmasa masa a wajen daya ji ciwon. Ai kuwa mintina goma da yin haka sai ciwon ya soma wata irin kumfa wajen yana tafasa kamar an saka abu a cikin wuta, kafin wani lokaci wajen ya gama zavalvala a hankali ya soma kamewa yana komawa kamar babu abinda ya faru a wajen a lokacin sham ya buxe idonsa suka haxa ido da macen sirri suka yi murmushi. Ya miqe yana duban jama’ar Arnan daji sannan ya maida hankalinsa zuwa ga sarki jamhas. ‘Ina godiya bisa kuvutar da ni da ka yi, kuma ina yi maka jajen rashin jama’ar ka da ka yi wanda macen sirri ta yi maka, nasan idan za ku shekara kuna fafatawa ba zata tava saduda ba. Ita da kuke ganinta hata ni tsoron fushinta nake saboda bata san ayi haquri ba. Kune alqarya da kuka vata mata rai bata qarar da ku ba” Macen sirri ta yi murmushi jin abinda ya faxa ta dubi sarki jamhas tace masa. “Kar ka damu nima zan saka maka da alheri kamar yadda ka taimake ni, zan baka maganin matsalarka ta rashin samun haihuwa, matarka zata haifa maka ‘ya mace wacce zata zama jaruma mai bajinta, kuma zan kawo wannan baqar gabar da take tsakaninka da sarki mazwan wanda hakan zai bunqasa tattalin arziqin ku” Tayi shiru tana duban cikin birnin arnan daji ta kuma kallon sarki jamhas wannan karon babu walwala akan fuskarta. “Ina baqin cikin sanar da kai nan gaba za a haifi wani yaro da zai kawo qarshen wanan zaman lafiyan da zan samar a tsakaninka da sarki mazwan. Yaron zai zo birnin ku yana neman taimakon ka, saboda sarki mazwan yana son halaka yaron kai kuma ya zamar maka dole ka taimake shi ka 21 DAN BAIWA kuvutar da shi, zan mallaka maka wasu dawakai guda biyu baqi da fari kuma zan yi wata tsatsuba a bayan gidanka tanan zaka fitar da yaron kuma dole ka haxasu da ‘yarka shi ka bashi farin doki ita kuma ka bata baqi ka aika da su zuwa birnin sin anan za a koya musu horo na yaqi” Ta xan saurara kaxan taci gaba. “Ka sani yakai jamhas duk wanda bai taimaki wannan yaron ba babu shakka nan gaba zai kasance cikin qasqanci saboda jarumi ne xan baiwa. Yana da abin al’ajabi mai tarin yawa shi ne kuma zai kawo qarshen baqin zallunci sarki mazwan zai kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali, ka sani duk duniya babu wani wanda ya isa yin nasara akan sarki mazwan face wannan yaron, tabbas ya bayyana gare ni sai ya zo wannan birnin naku, kuma tsakanin kai da sarki qasar Nur xaya daga cikinku wani zai mallaki takobin sarki mazwan wacce ita ce sirrin mulkinsa. Amman abinda sarki mazwan da bokansa basu sani ba wannan takobin ba komai bace a tarihin mulkinsa, wannan lamarin ya voyewa boka marmasi a cikin sha’anin bokancinsa kuma ba zai tava gano hakan ba sai lokacin da yaro xan baiwa ya bayyana, za su fahimci sun aikata kuskure wanda ba za su tava gyara shi ba kasan shi zallunci baya tava xorewa” Waxannan kalaman ba qaramin xaurewa sarki jamhas kai ya yi ba. ‘Mene abin yi yanzu?” “Ka taimaka masa ka tura shi zuwa birnin sin” Cikin kaxu yace mata. “Birnin sin fa kika ce birnin da zuwan sa yafi komai tashin hankali da hatsari na tsafafiyar birinya da kuma mashahuran ‘yan fashi ga bala’i kala-kala a hanyar zuwa qasar ta sin, haka idan mutum ya isa birnin bai tsira ba saboda acan 22 DAN BAIWA cibiyar mashahuran bokaye ta duniya take kuma a can ake saye da sayarwa na tsafi akan hanya a ko ina zaka koyi sihiri na tsafi acan idan baka zama matsafi ba tabbas ba zaka iya zaman qasar ba” Jin wannan kalamin ya saka macen sirri ta yi murmushi har sai da haqoranta suka bayyana. ‘Wannan duk abinda kake gani lamari ne na sihiri domin a riqa wahalar da jama’a, wannan birinyar da take tsare fatake tana kashe su wani boka ne ya samar da ita domin ta adabi jama’ar da suke kai kawo a wannan dajin zuwa birnin sin. Anyi haka ne domin hana jama’ar da suke tureniyar zuwa birnin sin domin koyon tsatsuba da kuma kai bayi. Nasan baka da sanin qasar shamawa ta kasance babbar daula data shahara wajen sayen bayi da kuma sayar da su zuwa ga manya dauloli wannan damar ya saka ta qula yarjejeniya da qasashe masu yawa” Sarki jamhas ya yi shiru yana kallon macen sirri a hankali yace mata. ‘Ina jinki kina bayani game da samuwar birinyar tsafi wacce ta adabi aljanu da mutanen da suke ilahirin dajin” Macen sirri tayi murmushi a hankali tace masa. “Ku ‘yan adam kuna son jin labarai, bari ka ji labarin na su a taqaice, duk dana san tarihin ba zai zame maka mai amfani ba tunda nasan duk duniya babu mai halaka tsafafiyar birinya sai jarumi xan baiwa” Ta saurara tana kallonsa sannan ta ci gaba. Bayan wani dogon zamani sarakuna sun gabata a wani qarni aka yi babbar daula ta qasar sin, ita kuma qasar shamara tana can gefe da qasar judan qaramar qasa ce da take cikin tsuburi da sai ka ratsa kwazazzabai da dajujjuka sannan zaka qarasa zuwa qasar sin. 23 DAN BAIWA A wannan lokacin babu abinda yake ci sama da tsafi duk wanda ya iya tsafi shi ne mai dukiya mai kuma iko da kowa a garin. Wannan dalilin yasa jama’a da dama suka riqa bazama cikin duniya domin koyo tsafi. Qasar shamara suna bin tafarkin duk wanda yafi wani qarfin tsafi shi ne zai zama sarkin daular wannan dalilin ya saka sarakunan da suke qasar basa jimawa akan mulki, saboda duk lokacin da wanda ya fi ka qarfi ya zo zai kashe ka ya haye kan karagar. Wannan tsarin da suke kai yana matuqar damun jama’ar qasar da kuma wani shashashan xan sarki wanda duniya bata dame shi ba, a iya tarihin qasar ba a tava yin sokon xan sarki kamarsa ba. Mulkin babansa bai dame shi ba zaka same shi ko wane lokaci a qarqashin bishiyar mangwaro yana xan kallo iskar dake kaxa ruwan wani tabki da yake gaba kaxan da gidan sarki, wannan xabi’ar tasa tana damun mahaifinsa ganin cewar tsufa ya kama shi kuma gashi xansa ba zai gaje shi ba saboda bai san tsafi ba ko na sisin kwabo. Hakan ya saka ya kasance cikin fargaba da faxuwar gaba, wannan dalilin ya saka sha’anin mulki ya soma tangarxa yana samun koma baya. Saboda yasan tabbas idan ya faxi ya mutu abokin gabanshi xan boka duqum ne zai gaji sarautar. Kuma yasan halin jamru ba shi da tausayi bai qi idan aka zo fitar da gwani na magajin sarauta ba ya kashe xansa kamzu, saboda yana buqatar xaukar fansar abinda sarki ya yi wa kakansu ya amshe mulki a hannunsa. Yasan babu makawa sai jamru ya yi amfani da tsatsub kala-kala saboda ganin bayan kamzu, hakan yana nuna za a yi haihuwar guzuma xa kwance uwa kwance zai zama mutuwarsa data xansa taqin sa’a ne. Tunda ana gudanar da gasar zama sabon sarki ne sa a uku bayan mutuwar tsohon sarki duk mai sha’awar shiga zai zama ya iya tsatsuba gwani kuma wajen iya bokanci. 24 DAN BAIWA A safiyar yau ne sarki laqamu ya kirawo xansa cikin turakarsa yana kishingixe suka zauna yana kallonsa cikin nutsuwa fuskarsa sam babu walwala yace masa “Me ka tanada domin gadona bayan mutuwata?” Ya xago yana dubansa. “Ban tanadi komai ba, tunda kaga ni ba jarumi ne bane kuma ban iya tsafi ba. Haka kuma ban maida hankali domin koyon ko xaya ba” Jin wannan maganar ba qaramin qonawa sarki rai ta yi ba. “Kai tafi can soko sulutun banza gwara haihuwar mace da kai… kana zaton akwai wanda zai gaji sarauta cikin sauqi, ya zama dole ka tashi tsaye domin neman kariya idan bah aka ba tabbas jamru ba zai sassauta maka ba. Ni kuma da kake gani kaga dai tsufa ya riske ni babu wani taimako da zan iya baka sai dai wanda ba a rasa ba, saboda duk wanda zan baka zuwa yanzu jamru yasan shi, saboda ya zama gagarabadau a fagen sihirin tsafi” Waxannan kalaman sun xagawa kanzu hankali, shi a ra’ayinsa sam babu ruwansa da sarauta saboda baya fatan gadon mahaifinsa saboda ganin yadda ake fama da tsatsuba da amfani da jinin mutane ana yin bokanci. Wannan abun yana damunsa yasan zallunci ne da kuma neman duniya. Yana gani wani lokacin za a yanka jarirai a yi sihiri das hi ko kuma a bine mutum da ranshi a qasa sai ya yi kwana goma sanan a tono sassan jikinsa a yi sihiri da shi, ganin wannan zallunci ne yana xaga masa hankali yasa baya qaunar mulkin na mahaifinsa. Amman wannan kalamin na mahaifinsa sun tsuma masa zuciya, ya soma tunanin kalamin da zai faxawa mahaifinsa domin kwantar masa da hankali. “Kayi haquri ya mahaifina tabbas baya tava yiyuwa barewa tayi gudu xanta ya yi rarafe, kai ka zama maxaukaki shi yasa kowa yake tsoronka amma ni kuma ban xauki ko xaya daga cikin halinka ba, amman tabas ba zan baka kunya ba idan wannan ranar ta zo, zan so wannan ranar ta zo min a lokacin kana numfashi tabbas da ka sai ka yi alfahari da ni domin zan zama mashahuri, kuma zan kauda tsafi daga doron duniya domin ni sam 25 DAN BAIWA ban bada imani da su ba” Wannan maganar ba qaramin xagawa mahaifinsa hankali ta yi ba. “Kar ka zo min da irin wannan salon na maganar bana jin wanan maganar zata zama mai tasiri a gare ni, don haka na umarce ka daka tashi tsaye domin neman tsatsuba da sirrin tsafi domin kare kanka” Ya jinjina kai. “Zan nemi mafita wacce zata kare ni” Yana gama faxin haka ya tashi ya fita ya nufi can wajen daya saba zuwa yana zama, shi kam yasan jarumtaka ba zata kai shi tudun muntsira ba domin jamru ya kasance gawurtacen jarumi haka kuma mashahuri a fagen tsafi idan haka ne ta yaya rago kamarsa zai samu nasara akansa har ya xare kan karagar sarautar mahaifinsa? Sanin hakan ba mai yiwuwa bane shi yasa ya cire ransa daga kan lamarin yasan kuma duk lokacin da jamru ya zama sarkin qasar sai dai shi da iyayensa su idan kuma ba haka ba sai ya kashe su ko kuma ya riqa gana musu azaba har zuwa lokacin da za su halaka don haka ya zamar masa dole ya nemo mafita. Kanzu ya ji duk abin duniya ya yi masa yawa ya rasa ina zai saka kansa, yana zaune a wajen da yake har zuwa gefen faxuwar rana sai ya ji wani sanyi yana sirarowa sanyi da sai daya saka jikin kanzu ya soma karkarwa yana makyarkyatar sanyi. Zuwa wani lokaci sai iskar ta tsaya wata mace doguwa mai kyawun diri ta bayyana tunda yake bai tava ganin kamarta bay a ga kai tsaye ta nufo wajen da yake cikin tsananin tsoro ya miqe da zumar zurawa da gudu amman sai ya ji qafafunsa sun saki sun koma kamar jiqaqen lagwani yana wajen har farar macen ta qaraso wajensa zuwa wani xan taqin lokaci tace masa. “Ko kasan ni wacce?” Ya gyaxa kai. “A’a amman alamu sun suna ke sarauniyar aljanu ce” Tayi murmushi. “Ka saki jikinka ka daina jin tsorona domin da ina da nufin cutar da kai a duk lokacin daka zo bakin kogin nan ka zauna. Ka sa ni na kasance sarauniyar aljanun cikin ruwa kuma bani da wajen zama face wannan kogin na kasance ina bin addinin 26 DAN BAIWA musulunci, babu cutarwa a cikinsa yana kuma hani da aikata zallunci da mugunta da hani da aiwatar da kafirci” Ta saurara tana kallonsa sannan ta ci gaba da magana. “Ka yi sani cewar na zo ne domin na taimake ka, saboda xa zu ina jin yadda kuka yi da mahaifinka kuma gaskiya ya faxa maka saboda idan jamru ya zama sarki za ku kasance cikin qasqanci, haka kuma jama’ar qasar za su kasance cikin qasqanci da tagayara wanda babu ranar fita daga ciki. A wannan zamanin babu jarumi kamar Jamru haka kuma a fanin tsafi, don haka ina kiranka daka zamo ma’abocin musulunci addinin da bai aminta da tsafi ba” Ai koda ya ji wannan maganar cikin sauri ya saukar da numfashi yace mata. “Ni kamar mahaukaci ne da yake jin yunwa komai na samu ci zanyi haka kuma kamar wanda ruwa ne ya ci yo shi, don haka zan amshi wanna addinin da kika zo min da shi idan har zan tsira daga sharin jamru” Jin haka ya saka sarauniyar aljanun cikin aljanu tayi murmushi. “Babu shakka zaka kuvuta daga sharinsa yanzu abinda nake so dakai shi ne ka shiga cikin kasuwar bayi zaka samu an kawo wata baqar baiwa ka siyeta tana bin addinin musulunci, sai ka bata aminci da salama ka kuma nemi ta sanar da kai komai daya shafi addinin tsira hakan zai kuvutar dakai daga duk wani sharrin jamru” Tana kawo wanan sai ya ji iskar da take kaxawa ta xauke ta koma daidai kamar bata tava faruwa ba. Ganin haka yasa ya sauke ajiyar zuciya ya tashi cikin sauri da azama ya nufi cikin kasuwar bayi da zumar ya sayi wannan baqar baiwar yana shiga cikin kasuwar ya soma dube-dube yana waige-waige ko zai ga baqar baiwa amma ko kaxan bai samu damar hakan ba. Haka ya yi ta yawo duk wajen daya gifta sai jama’a su zube suna yin gaisuwa a gare shi wasu suna cewa gaisuwa ga sarki mai jiran gado, amman

Chapter 2 of 7