Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 7
sarki ya ajiye wanna xin, 60 DAN BAIWA idan har sarki ba xauko littafin ya yi ba ya buxe babu yadda za a yi ya gane cewa an xauke na gaskiyar” Koda kuyangar ta zo nan a zancenta sai sarkin yaqi Marhat ya yi doguwar ajiyar zuciya, sannan ya dubi kuyangar cikin alamun tsananin damuwa yace. “Yanzu saboda Gimbiya bata son rasa ni, shi ne tayi gangancin xauko wannan littafin na sarki?” Kuyangar ta gyaxa kai tace. “Qwarai kuwa kuma ina tabbatar maka da cewar idan har Gimbiya bata mallake ka ba, duk wanda ya yi qoqarin mallakarta sai dai ya sami gawarta, zan dawo nan da cikar kwana shida da tsakar dare na karvi wannan littafin daga hannunka domin a mayar da shi inda yake, kafin washe garin ranar da za ku cika sharuxan zama ‘yan uwan mu” Koda gama faxin haka sai kuyangar ta yiwa sarkin yaqi marhat sallama ta tafi. Shi kuma sai ya miqe da hanzari ya je ya voye wannan littafin a cikin jakarsa ya guzuri ya zauna yana tunani gami da nazarin abubuwan da ke gabansa. A daidai wannan lokacin Dakarun nasa suka sake dawowa suka zauna suna masu kewayeshi nan take babban cikin nasu ya dubi Marhat ya ce. “Ya shugabana waye ya aiko wannan kuyangar kuma wane abu ta kawo maka a cikin mayafinta a qunshe?” Koda jin wannan tambayar sai Marnat ya yi murtuke fuskarsa yace. “Baya daga cikin halina na bayyana sirrin wani,shin baka ji abinda kuyangar tace ba? Cewar ta zo ne da sirri a gareta” koda jin haka sai kunya ta kama shugaban Dakarun ya sunkuyar da kansa qasa ya yi shiru bai qara cewa uffanba. Kamar yadda marhat ya tsara haka al’amarin ya kasance wato dare na rabawa ya tashi gaba xayan Dakarun nasa suka tafi izuwa bayan garin da suke, nan take Marhat ya fara basu horon yaqi na musamman irin wanda sam basu tava gani ba a rayuwarsu mai tsananin wuyar gaske. Haka dai marhat ya yi ta basu wannan horon har izuwa gefen alfijir saboda tsananin wahalar da suka sha a wannan horon yaqin said a wasunsu suka rinqa zubar da qwallar wuya. 61 DAN BAIWA Lokacin da aka shafe kwana uku ana wannan horon sai ya zamana cewar kowa jikinsa ya saba suna iya jurewa koma a sannane kowannensu ya sami gagarumin qarfi da jarumtaka ta musamman wacce bai tava jin kamarta ba a cikin jikinsa. A ranar dare na uku ne bayan sun tashi daga karvar horon sun zauna suna hutawa sai shugaban Dakaru ya dubi sarkin yaqi marhat yace. “Ya shugabana wai shin me yasa ka zavi mu rinqa yin wannan horon na yaqi a sirrance a cikin tsakiyar dare?” Koda jin wannan tambayar sai sarkin yaqi marhat ya dubi badakaren yayi murmushi yace. “Abin da yasa nake baku wannan horon a tsakiyar dare shi ne bana son Dakarun da zamu fafata dasu su san cewa muna yin wani qoqari don tunkarar su, tunda sun san cewar sun fi mu qarfi da iya yaqi ba za su yi tunanin suyi wani tanadi ba za su saki jikinsu saboda suna ganin cewar farat xaya za su gama damu. Ina mai tammabat muku da cewar yanzu da wannan horon yaqin da muke dashi zamu iya samun nasara akan su ammafa zamu iya shanwuyar gaske” Koda sarkin yaqi marhat ya zo nan a jawabinsa sai murna ta kama gaba xayan Dakarun amma sai qaramin cikinsu mai suna Lazyan ya dubi marhat yace. “Ya shugabana yaya batun ka na koyon yaren mutanan garinnan da akace kayi? Har yanzu banga kana yin wani yunquri akan hakan ba” Koda jin wannan batun sai marhat ya yi murmushi yace. ‘Kabar wannan batun kawai” Koda gama faxin haka sai marhat ya miqe tsaye ya shige izuwa cikin qurya turakarsa ya kwanta ya kama barci. Da dare sarkin yaqi marhat yana zaune ya yi shiru yana tunani abinda zai iya faruwa washe gari a fada sai sarkin Dakaru ya shigo yace masa. “Ka yi baquwa wannan kuyangar nan ce data zo kwanaki” Ya xan yi jim kamar bai ji abinda yace ba, har zuwa wa su ‘yan daqiqai sannan yace masa. 62 DAN BAIWA “Kace mata ta shigo” Ya juya ya koma wajenta ba a fi mintina ba sai gata ta shigo ta faxi gabansa ta yi gaisuwa. “Shugabata tace na gaishe ka”. “Ina amsa wa” Ya faxa a taqaice sannan ya miqe zuwa wajen daya adana littafin data kawo masa ya xauko ya bata. “Bansa irin godiyar da zan yi ba, domin wannan littafin ba qaramin taimaka min ya yi ba yanzu ka mina da qarfin gwiwa xari bisa xari akan lallai zan samu nasara akan wannan lamarin”. Kuyangar ta xago da kai a hankali ta dube shi sannan cikin qwarin gwiwa itama tace masa. “Ina godiya ga abin bauta da yake shirin cikawa Gimbiya burinta na son mallakar abinda take so”. Ya dubeta. “Kina da tabbaci akan abinda kika faxa?” Ta gyara zama. “Kamar yadda kwanaki na faxa maka cewar duk wanda ya auri Gimbiya bayan kai to sai dai ya auri gawarta amman ba ita ba, domin ina da yaqini xari bisa xari akan irin qaunar da take yi maka”. Sarkin yaqi marhat ya yi murmushi cike da jin daxi. “Wannan kalaman naki suna qara bani qarfin gwiwa sosai game da samun nasarata” Ya xan xaga kai sama yana duban saman xakin sannan ya ci gaba da magana. “Yanzu a wane yanayi Gimbiya take?” Kuyangar ta kuma sunkuyawa a gabansa. “Tana cikin halin begenka, na barota cikin fargaba da tsoron shin bayan ka karance littafin ka iya yaren namu, na kuma ga alamar tsoro a tattare da ita don bata son rasa ka” Koda jin haka sai sarkin yaaqi marhat ya yi murmushi yace mata. “Ina son ki baiwa Gimbiya tabbacin lallai ni ne mai nasara a wannan lamarin, kuma babu wani wanda zai zama mijinta face ni, don haka idan kin damqa mata wannan littafin ki faxa mata cewar ina bata tabbacin nan da wasu ‘yan kwanaki muna tare da ita a matsayinta na mata a gare ni” Koda jin haka sai kuyangar tayi murmushi sannan a hankali ta miqe tare da kuma yi masa fatan samun nasara. Bayan fitarta sarkin yaqi Marhat ya yi shiru sai tunanin matarsa da kuma xansa suka kuma dawo masa a cikin zuciyarsa, ya 63 DAN BAIWA sunkuyar da kansa qasa kawai ga mamakinsa sai ya ji hawaye yana fita daga cikin idanunsa. ** Kwana bakwai na cika tun da sassafe fadar sarki jamhas ta cika ta batse da al’umma domin a ga yadda za a qure su sarkin yaqi marhat saboda kowa gani yake cewa basu isa su tsallake wannan sharaxin da aka gindaya musu ba. Sai da kowa ya hallara a fadar amma sarki bai zo ba har izuwa tsawon ‘yan sa’o’i al’amarin daya dugunzuma hankalin ‘yan majalisa kenan da sauran mutanen gari,bisa wannan dalilin fadawa suka tashi manzo ya tashi ya shiga cikin gidan sarautar domin gano ko lafiya. A jarumi Dan Baiwa 5 she acan gidan sarautar hankalin sarki jamhas ne ya dugunzuma ainun sakamakon wani mafarki da ya yi. A cikin mafarkin an nuna masa cewar sarkin yaqi Marhat sun tsallake dukkan sharuxxan da aka gindaya musu amma sun yi amfani da najikinsa wajen samun nasara. Nan take sarki ya xauko madubin tsafinsa ya shiga bincike domin ya gano ta hanyar da su marhat za su sami wannan nasarar amma sai abu ya gagara. Koda ganin haka sai sarki jamhas ya zauna ya rinqa tunani har izuwa lokaci mai tsawo. Yana cikin wannan tunanin ya tuno da wannan littafin mai fassarar yaren qabilarsu cikin hazari sarki jamhas ya miqe tsaye ya tafi izuwa xkin da yake adana kayan tarihin qasar, da shigarsa sai ya durfafi inda wata farar akwatin zinare take cikin hanzari sarki ya buxe akwatin ya yi arba da littafin yananan kamar yadda ya ajiyeshi ko qurar jiki ba a goge ba. Kai hatta yana dake cikin akwatin tananan alamar cewa an daxe ba a buxe ba. Duk da haka sai sarki jamhas ya kai hannu da nufin ya xauko littafin ya buxe sai kawai ya ji an kirawo sunansa cikin fushi sarki jamhas ya waigo ya dubi mai kiran sunansa. 64 DAN BAIWA Ba wata bace face mahaifiyar Gimbiya Hamrita cikin sairi ta qaraso gareshi tace. “Haba ya kai mijina kayi sani cewa fiye da sa’a uku fada ta cika ta batse,kai kaxai ake jira har fadawanka sun qosa sun aiko manzo” Koda jin haka sai sarki jamgas ya yi tsaki ya mayar da murfin akwatin ya kulle ya datse da kwaxo ya sanya makulin a jikin mazugin wandonsa ya zuge sannan ya fice daga cikin turakarsa ya nufi fada kai tsaye. Koda ganin haka sai mahaifiyar Hamrita tayi doguwar ajiyar zuciya tana mai dafe qirjinta a lokacin ne Gimbiya Hamrita ta fito daga bayan wata qofa data lave suka dubi junansu suka yi murmushin farin ciki bisa ganin cewa asirinsu bai tonuba. Lokacin da sarki jamhas ya iso filin fada sai mutane suka ruxe da shewa aka kama yi masa jinjina makaxa da mawaqa suka shiga yi masa kirari nan danan Dakaru suka buxe masa hanya ya isa har inda karagar mulkinsa take ya zauna. A wannan lokacin su sarkin yaqi na tsaye a tsakiyar filin fadar a gefe xaya su goma. A wani gefan guda kuma manyan zakwaquran mayaqan qasarne a tsaye cikin gagarumin shigar yaqi, sarkin yaqin birnin ne shugabansu, suma xin su goma ne kuma kowanne daga cikinsu girman surar jikinsa ta sadaukai da tsawonsa ta ninka tasu Marhat sau biyu. Ba tare da vata wani lokaci ba sarki jamhas ya miqe tsaye daga kan karagarsa ta mulki ya fuskanci jama’a ya farad a gaishesu gami da neman afuwa bisa rashin fitowarsa da wuri bisa wata larura. Bayannan sai yace “Yak u jama’ar wannan birnin namu mai albarka kuyi sani cewa rana bata qarya sai dai uwar xiya ta ji kunya, yau ce ranar da su sarkin yaqi marhat za su cika sharuxxan da muka gindaya musu domin mu karvesu a matsayin ‘yan uwanmu kuma na baiwa sarkin yaqi marhat auren ‘yarta Gimbiya Hamrita” A daidai wannan lokaci ne aka ji an buga tambura kuma an busa algaita sai ga Gimbiya Hamrita ta fito daga cikin gidan sarautar kuyangi kimanin guda xari na take mata baya. 65 DAN BAIWA A wannan lokacin Gimbiya Hamrita ta cava ado na gaban kwatance wato na qure adaka kuma fuskarta cike take da murmushi gami da annuri tamkar wacce aka biya mata dukkan buqatunta na duniya. Kai tsaye Gimbiya Hamrita ta nufi inda sarkin yake tsaye ta rungumeshi sannan ta sumbaci goshinsa, shima sai ya kama hannayenta ya sumbata sannan ya zaunar da ita bisa kujerar dake daf da karagarsa ta mulki sannan ya juyo ya sake fuskantar jama’ar sa ya ce. “Yanzu za mu fara ne da sauyawa baqin mu addininsu da al’adarsu” koda gama faxin hakan sai sarki jamhas ya tafa hannayensa sau biyu. Nan take waxansu hadimai goma suka shigo cikin filin fadar xauke da tufafi akan farantai goma. A gaban bainar taron suka kwave tufafin dake jikin su, sarkin yaqi marhat suka sanya musu irin nasu, sannan hadiman suka fice. Fitarsu ke da wuya sai sarki jamhas ya sake tafa hannayensa sau uku, nan take malaman addinin qasar su goma suka shigo cikin filin ruqe da farantai. Kowane faranti akansa akwai ruwan jini a cikin kuttu da kuma silin gashin tsuntsun alhuda-huda. Nan take aka shafawa su sarkin yaqi marhat zanen kibiya akan kumatunsu da wannan ruwan jinin kuma aka soka gashin alhuda-huda a cikin gashin kansu guda daidai. Koda aka gama yi musu wannan adon sai suka ga ashe irin shigar dakarun qasar aka yi musu,bambancinsu dasu kawai shi ne su Dakarun birnin na arnan daji kalar tufafin jikinsu ruwan xorawa ne su kuma su marhat nasu tufafin shuxine nan take aka biyawa su marhat sunan gunki da ake bautawa a garin har sau uku suna maimaitawa. Faruwar hakan ke da wuya sai filin ya ruxe da sowa gami da tafi saboda ganin cewa malaman addinin suka fice daga cikin fiin sannan sarki jamhas yace. “Yanzu baqin mu sun cika sharuxa na farko daga cikin sharuxan da muka gindaya musu don haka za mu tafi izuwa kan sharaxi na biyu wanda shi ne muna son a yi hira da sarkin yaqi Marhat da yarenmu izuwa tsawon sa’a xaya ba tare da yayi kuskure ko tuntuven harshe ba a cikin ambaton kalmomi” Koda jin wannan batu sai hankalin 66 DAN BAIWA kowa ya dugunzuma domin ba a ga ta yadda marhat zai iya tsallake wannan matakin ba. Nan take wani dattijon mutum masanin yarensu sosai wanda yafi shekara xari a duniya ya shigo cikin filin fadar ya iso har gaban sarkin yaqi marhat ya tsaya suka qurawa juna idanu. Nan take fadar tayi tsit! Tamkar mutuwa ta gifta,kowa ya kasa kunnuwansu domin ya ji yadda sarkin yaqi marhat zai yi magana sosai a cikin yaren arnan dajin. Da yawa daga cikin jama’ar dake fadar sun san cewa ko sarkin yaqi marhat aljanine bai isa ya iya wannan yaren a cikin sati xaya jal ba kuma dolene wannan dattijon ya qureshi saboda shi ne mutumin dayafi kowa iya yaren a birnin. Ba tare da vata wani lokaci ba kuma sai dattijon ya buxe bai ya fara yiwa marhat tambayoyi akan waxansu al’adu na qasar da yadda ake gabatar dasu. Wohoho! Abin mamaki baya qarewa akan doron qasa. Nan take jama’a suka ji marhat yana bayar da amsoshin dukkanin tambayoyin da ake yi masa harma yana qarin bayani fiye da wanda masana yaren da al’adar za su yi. Bawai jama’ar garinba hatta sarki jamhas da matarsa da kuma ‘yarsa Gimbiya Hamrita said a suka kamu da tsananin mamaki. Musamman Hamrita da mahaifiyarta sunfi kowa mamaki saboda Karin bayanin da marhat ke yi babu shi a rubuce a cikin wannan littafin da suka bashi. Shi kansa Dattijon da yake yiwa marhat waxannan tambayoyin said a ya jinjina masa kuma ya sallamasa yace. “A yaun jaji kalmomin da ni kaina na manta dasu a cikin yarenmu daga bakinka saboda haka ina neman alfarmar na zo gareka na xauki karatu”. Koda jin haka sai fadar ta ruxe da shewa mutane suka rinqa yiwa sarkin yqi marhat jinjina da tafi. Bayan su marhat su gama haye duk kan matakan ya zamana cewa sauran matakin gumurzu tsakaninsu da manyan mayaqan qasar sai fadar ta sake yin tsit fiye da karo na farko. Inda ace tsinke zai faxo qasa daga sama sai anji qarar dirarsa akan tsakiyar filin da su marhat ke tsaye saboda tsananin shirun da aka yi. 67 DAN BAIWA Nan take sarkin jamhas ya dubi jaruman qasarsa gami da su sarki marhat yace. “Yanzu na za ku fafata muga iyakar qoqarin bakinmu, ku sani cewa babu sani ko sabo a cikin wannan faxan,kowa zai iya rasa rayuwarsa a wannan gumurzun amma duk wanda ya ji tsoro ya faxi qasa za a qyaleshi ammafa ya faxi gasar” Koda gama faxin hakan sai sarki jamhas ya xaga hannunsa guda sama, yana ajiye hannunsa sa qas sai aka buga gangar fara gumurzu ai kuwa sai zaqwaquran Dakarun birnin arnan dajin suka zare takubbansu suka rugo da gudu izuwa kan su sarkin yaqi marhat suna kururuwa mai ban tsoro. Qarfin gudun sawayensu ya haddasa tashin qura a filin, koda su sarkin yaqi marhat suka ga waxannan dakarun sun taso musu sai suma suka zare nasu takubban suka ruga suka taresu aka ruguntsume da masifaffan yaqi. Wahoho!, tabbas tashin hankali bashi da daxi kuma ita masifa ba a sa mata rana. Lokacin da aka runguntsume da masifaffan yaqi tsakanin rundunar biyu sai hankalin kowa ya dugunzuma a filin fadar saboda tsananin qarar haxuwar takubba gami da ihun mazaje da kuma qarar dudufniyarsu akan qasa. Ganin yadda rundunar biyu ke kaiwa junansu sara da suka cikin tsananin zafin nama, juriya da bajinta ne yasa kowa ya ximauce domin ba a tava ganin gumurzu irinsaba saboda karamin alhakin ya zama abin tsoro. Duk irin qarfin saran dakarun birnin ainan sai gashi su marhat na iya karewa gami da maida martani,kowa sai daya cika da xumbin al’ajabi saboda an zata cewa farat xaya za a gama dasu marhat. Abu dai kamar wasa said a aka shafe kusan rabin sa’a ana yin mugun artabu ba tare da an lakaci jikin koda mutum xayaba daga cikin rundunar biyu, kamar haxin baki sai rundunonin biyu suka ja da baya a tare lokaci guda suka yi carko-carko suna haki da kallon-kallo na juna kamar zakaru. Kai da gani kasan cewa kowane vangare na tunanin hanyar da zai bi ya sami nasara. A lokacinne sarki yaqin arnan dajin ya yiwa sauran ‘yan uwansa Dakarun raxa a kunne,kawai sai gani aka yi sun yunqura cikin zafin nama sun sake afkawa su sarkin yaqi marhat kuma wannan karon 68 DAN BAIWA sun sauya salon yaqin domin kowannensu ya zavi abokin gwafzawarsa ya afka masa da dukkan qarfinsa kuma ya haxa da kai masa sara da suka cikin tsananin zafin nama da mugun nufi. Ai kuwa nan take labari yasha bamban domin a cikin daqiqu basu fi arba’in bay a zamana cewa gaba xaya Dakarun sarkin yaqi Marhat an yi musu rauni babu wanda ba a sare shi ba ko yankarsa kamar sau uku ba. Sai gashi jini na zuba a jikinsu amma saboda baqin naci da tsananin juriya sun qi yarda su faxi qasa. Koda sarkin yaqi marhat yaga yadda aka yiwa yaransa wannan mummunar varna sai ransa ya vaci kuma zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata qone. Cikin tsananin fushi ya shammaci sarkin yaqin arnan daji ya daka tsalle sama ya doki qirjinsa da qafarsa guda, saboda qarfin dukan sai da sarkin yaqin ya yi taga-taga da baya yana neman faxuwa qasa. Ba zato ba tsammani sai aka gay a xago sama ya yi wuf cikin baqin zafin nama ya damqi maqoshin marhat kawai sai ganin marhat aka yi yana wutsil-wutsil qafafunsa yana qoqarin cire hannun sarkin yaqin arnan daga kan wuyansa a lokacin da idanunsa suka kaxa suka yi jawur yana qoqari har sarkin yaqin arnan daji ya yunqura zai maka marhat a qasa sai kawai ya kasa. Ba komai ne ya janyo haka ba face jin sukuwar dubunnan dawakai sun durfafo fadar cikin ximauta mutane suka waiga sai akaga ashe Dakarun yaqin birnin Hindune wanda yawan adadinsu ya kai mutum dubu suka kawo harin bazato. Sarki mazwan ne da kansa ke jagorantar wannan rundunar ya xaga takobinsa sama yana ruri da kururuwa. *** Su jarumi xan baiwa suka ci gaba da tafiya a cikin qungurmin daji duk a cikin niyarsu ta son qarasawa zuwa birnin sin bayan sun yi doguwar tafiya kamar yadda suka saba suka qaraso wajen wata qorama mai xauke da ‘ya ‘yan itatuwa da kuma sanyi yana tashi a wajen, suna zuwa wajen cikin azama da salhim ya soma cire ‘ya ‘yan itatuwa yana Tarawa ita kuma Gimbiya zasmin da azama ta saki dokinta ta nufi wajen da ruwan qoramar nan yake gudana. 69 DAN BAIWA Tana zuwa ta tsuguna ta kai hannunta ta xebo ruwan ta kai bakinta zata sha sai ta ji an yi mata magana cikin xaga murya, ta xago a hankali suka xaha idanu da Raiyan yana tsaye daga can gefe guda. “Kar ki sake ki sha ruwan nan” Ya nufo wajen da take a lokacin salhim shima ya qaraso wajen cike da gajiya ga kuma tsananin qishir ruwa daya kama shi. “Saboda me, ina ganin ruwa gwanin kyau za ka hanani sha?” Raiyan ya qarasa wajen yana xan yin murmushi. “Wannan ruwan da kike ganinsa tarko ne na wata shu’umar bokanya da take xanawa domin fatake masu tafiya, tana amfani da shi ne kuma domin kama duk wani wanda ya shiga hannunta sai ta mayar da su bayi tana bautar da su, duk wanda yasa wannan ruwan bashi da ikon savawa umarninta” Salhim da Gimbiya Zasmin suka saki baki kawai suna kallonsa cike da mamaki. “Amman gaskiya ba mu ga wata alama da zata nuna mana haka ba, don haka ni dai yadda nake jin qishin ruwa kuma ga ruwan ina gani babu abinda zai hanani sha” Salhim ya faxa yana mai sunkuyawa ya xebo ruwan. Kafin Zaiyan ya yi wani yunquri tuni har salhim ya soma shan wannan ruwan, bayan ya sha ya qoshi sai ya koma gefe guda ya zauna ya xauko ‘ya ‘yan itatuwan daya tsinko ya soma ci. Zaiyan ya yi shiru kawai yana kallonsa, ganin haka sai Gimbiya Zasmin ta kalli Salhim na wani xan lokaci sannan ta dubi Zaiyan. “Kace idan muka sha wani abu zai faru amman kuma ga salhim yasha babu abinda ya same shi” Zaiyan ya yi murmushi kawai. Koda ganin haka sai itama Gimbiya Zasmin ta sunkuya ta xebi ruwan ta sha, ta koma can kusa da salhim suka zauna suna cin ‘ya ‘yan itatuwan abin su. Ai kuwa Gimbiya Zasmin bata jima da zama ba sai suka ji wata qara mai tsananin firgitarwa ta karaxe wajen, bayan wani xan taqin lokaci sai wata baqar guguwa ta turniqe ilahirin wajen, nan fa su Gimbiya Zasmin da Salhim suka miqe cike da tsananin tsoro suna kallon wannan baqar guguwar da ta turnuqe tana toroqo sama. 70 DAN BAIWA Can bayan wani lokaci sai ta soma lafawa a hankali a hankali har zuwa wani xan taqin lokaci kafin daga bisani ta sarara a lokacin kuma suka ga wata sharveviyar macijiya ta bayyana ta tunkaro wajen da suke, lokaci guda ta buxe wangamemen bakinta tana haxiye duk abinda tayi karo da shi. Koda ganin haka sai su salhim suka ruga da gudu domin tsirar da ransu daga hakala. Duk gudun da suke yi da zarar sun juya domin ganin ko sun yiwa wannan macijiyar nisa sai suka tana qara kusanto su. Hakan ne ya qara xaga musu hankali sosai domin ganin lallai halaka tana qara kusanto su, a haka sai daya zama bai fi taku xaya wannan shu’umar macijiyar ta qaraso wajen su Gimbiya Zasmin sai suka yanke jiki suka faxi, ganin haka ya saka macijiyar ta tsaya da binsu suka tsaya suna kallon-kallo tsakaninta da su Salhim. Nan fa ido ya raina fata, ya juya yana kallon Gimbiya Zasmin a hankali yace mata. “Kinga abinda kika jawo mana” Ta buga masa harara. “Ni na jawo mana? Ka dai jawo mana ai daman sai da Zaiyan ya hana ka amman ka yi taurin kai yanzu gashi babu makawa halaka za mu yi” Salhim ya sunkuyar da kai cike da takaici yace mata. “Ni fa bana son mutuwa yanzu, domin kinga ban samu na cika burina ba na xaukar fansa akan sarki Mazwan” Gimbiya Zasmin ta dube shi cikin tsananin damuwa. “Yanzu dai bamu ga tsuntsu bamu ga tarko, yanzu dai ka gwada baiwar ka kamar yadda ka saba kuvutar da mu a baya” Ya buga mata harara. “Da hakan zata yiwu ai bama zan bari mu sha wannan wahalar da muka sha ba” Yana rufe bakinsa sai suka ga wannan macijiyar tayo kansu gadan-gadan bakinta a buxe da zumar cinye su, amman kafin ta qaraso zuwa wajensu sai suka ga taja ta tsaya, cikin tsananin mamaki suka juya bayansu domin ganin abinda yake tsaye a bayansu. Nan suka yi arba da Zaiyan a tsaye cikin shiri na yaqi, a hannunsa riqe da wata sharveviyar takobi, nan fa wannan macijiyar ta doko tsalle ta nufi Zaiyan da nufin haxiye shi, shima nan ya doka wani tsalle sama ya tunkareta. 71 DAN BAIWA Wohoho! Nan fa kallo ya koma sama,wai shaho ya xauki giwa domin wannan macijiyar tana kawowa zaiyan sara yana gocewa shima yana kai mata sara da tashi takobin, amman sai yaga ta goce cikin tsananin zafin nama, ta kawo masa duka da sharveviyar jelarta shima ya goce cikin zafin nama. Nan suka cure suna wannan gumurzun mai ban mamaki, sai da suka shuxe sa’ani bakwai suna fafatawa ba tare da wani ya samu nasara akan wani ba, ganin haka sai zaiyan ya qara azama da qarfin kai saransa da zumar ganin ya halaka wannan macijiyar, yana cikin kai mata sara sai ya yi tuntuve da wani dutse ya yanke jiki ya faxi qasa. Koda macijiyar nan taga haka sai ta yo kansa gaba xaya baki buxe da zumar haxiye shi, tana zubawa ta kawo masa cafka da baki cikin wani tsananin zafin nama ya goce, amman bai qarasa barin wajen ba ta saka jelarta ta mako shi kafin ya yi wani yinquri sai ta nannaxe shi da jelarta. Ta matse shi, zaiyan ya ji numfashinsa ya soma xaukewa saboda tsananin matsar data yi masa. Koda ganin haka sai hankalin su salhim da Gimbiya Zasmin ya yi tsananin tashi,domin suna da tabbacin lallai wannan kananaxewar da wannan macijiyar tayi wa zasmin babu makawa ya riga ya halaka. “Ka yi wani abu mana salhim” Gimbiya Zasmin tace masa. Shima ya dubeta a fusace “Da zan iya yin wani abu na faxa miki da tuni na yi” Ta kamo hannunsa cikin sauri. “Haba nawan kar ka bada ni mana, kaifa nawa ne nasan irin baiwar da kake da ita” Wannan maganar da Gimbiya Zasmin ta faxa sai salhim ya dubeta cike da mamaki suna haxa ido ta yi masa wani ni’imtaccen murmushi. Nan fa Salhim ya ji kamar alura ta yi masa, nan take ya zare takobinsa ya tunkari wannan qatuwar macijiyar yana zuwa wajen da take ya daka tsalle sama ya kai mata sara amman kafin saran yakai jikinta sai ta waiwayo ta cafke shi da bakinta ta soma qoqarin haxiye shi. Haba wa Gimbiya Zasmin tana ganin haka sai ta miqe cikin tsananin fusata ta rugo itama da gudu, hannunta zare da takobinta tana zuwa ta soma saka kaifin takobinta ta sari jelar wannan qatuwar 72 DAN BAIWA macijiyar nan take ta gutsire jelarta saboda qarfin saran data yi mata, nan fa macijiyar ta saki salhim dake bakinta saboda tsananin jin zafin wannan saran da Gimbiya Zasmin ta yi mata. Ta juyo kan Gimbiya Zasmin a fusace da zumar halakata, wannan karkatowar data yi kanta shi yasa zaiyan ya yunqura cikin sauri shima ya xauki takobinsa ya doka tsalle sama ya saka kaifin takobinsa ya sare kan macijiyar nan take kan ya faxo qasa, gangar jikinta ta faxi can gefe guda jini yana malala. Zaiyan ya sunkuya qasa yana sauke numfashin gajiya, ita kuwa Gimbiya Zasmin ta tashi cikin sauri ta ruga da gudu ta nufi wajen da Salhim yake kwance tana zuwa ta kamo kansa ta xora akan cinyarta ta zuba masa ido tana kallonsa, sam baya cikin hayyacinsa domin wannan macijiyar ta saka masa dafinta a cikin jikinsa. Ganin haka sai Gimbiya Zasmin ta yi tsamanin ya halaka nan take ta soma kuka tana faxin. “Kar ka tafi ka barni ni kaxai, kasan tun lokacin da muka haxu dakai na

Chapter 6 of 7