Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 7
kansa kuma suka daddatsa sassan 38 DAN BAIWA jikinsa suka kaiwa sarki muzwan ya saka aka watsawa kadojinsa sassan jikin wannn yaron suka kama ci har suna faxa a junansu. Kadojin da sarki mazwan yake kiwatawa sun kai guda arba’in da uku kuma ko wacce a cikinsu takai girman bil’adama saboda zallunci sarki muzwan ko wani qaramin laifi mutum ya aikata sai ya saka a kawo shi da ransa ya saka a cila shi cikin kadojin su kuma su hau watanda da sassan jikinsa. Baya kadojin sun gama cinye sassan jikin wannan yaron xan mahaukaciya sai sarki mazwan ya salami waxannan dakarun da suka yi aikin, tafiyarsu ke da wuya sai boka marmarsi ya bayyana tsulum a gabansa ya kalleshi fuskarshi a murtuke yace masa. “Babu shakka ya kai wannan babban sarki ka yi sani cewar ka tafka babban kuskure sama da irin wand aka aikata akan macen sirri ka yi sani cewar waxannan dakarun naka daka aika akan su kawo maka sassan jikin yaron ha’intarka suka yi don yaron daka ce su kasha ba shi suka kashe ba tuni wannan yaron ya gudu bisa xauki na ‘yar arna daji. Kuma idan baka tura an nemo maka shi ba duk inda yake ba to ina mai tabbatar maka wannan karon wannan yaron shi zai kawo qarshen mulkinka ya kuma kawo qarshen rayuwarka kamar yadda macen sirri ta faxa maka. Kuma babu shakka bayan ya kashe ka zai hau kan karagar mulkinka zai sauya rayuwar mutanen birnin hindu ya kawar da tsoro a zukatan duk mutanen da suke rayuwa a cikin birnin. Kuma zai kawo qarshen fatara da talauci daya adabi jama’a duk tsoro da talaka suke masa zai fifitasu akan sarakai da attajirai da bokaye lallai wannan yaron zai zama gawurtaccen jarumi kuma xan baiwa da zai gagari kowa zai zama alaqaqai a nahiyar nan gaba xaya a rasa wanda zai iya cin nasara da qarfin damtse ko na sihiri akansa” Lokacin daya zo nan wajen sai sarki mazwan ya taqarqare ya qwala ihu cikin tsananin takaici da baqin ciki gami da dugunzumar hankali nan take ya tura aka kirawo masa sarkin yaqinsa sadauki marhat ya bashi umarni akan aje a kamo dakarun da suka kawo sassan jikin xan mahaukaciya. Kafin ya gama Magana tuni an gabato da su gaba xayansu su arba’in nan aka yi musu kisan gilla nan take. Bayan nan sai sarki muzwan ya yi wa sadauki marhat bayanin yaro salhim da bayanin cewar ‘yar sarki arnan daji ta xauke shi don 39 DAN BAIWA haka ya xauki dakaru dubu xari biyar ya tafi da su birnin arnan daji ya buqaci su bashi wannan yaron salhim. Idan suka qi ba shi ya kashe kowa kuma ya zo da kan yaron salhim ta ko wanne hali, nan take sadauki marhat ya risina ga sarki muzwan yace masa. “An gama ya shugabana” Kawai sai ya juya ya fice daga cikin gidan sarauta da zumar yaje y haxo wannan runduna da aka ba shi umarnin haxawa kuma ya yi shirin tafiya. Sarkin yaqi marhat ya kasance gwarzon mayaqi mai tarwatsa maza wanda kowa yake shakunsa a gaba xaya mayaqan da suke nahiyar saboda tsananin qarfin damtsensa da iya yaqinsa da kuma qarfin sihirinsa na tsafi. Sadauki marhat yana da xa guda xaya a duniya mai suna shamzan tare da matarsa itama guda xaya tak wato mahaifiyar shamzan ana kiranta da suna larufa a duniya babu abinda sadauki marhat yake so sama da wannan xan nasa wanda sun shaqu ainun da shi ko kaxan baya son ganin abinda zai rabasu dai-dai da rana xaya. Lokacin daya shiga gidansa cikin sauri ya soma haxa kayan yaqi ganin haka sai hankalin xansa dana matarsa ya dugunzuma cikin alamun firgici xansa shamzan ya ruga da gudu izuwa jikinsa ya qanqame hannayen shi guda biyu ya fashe da kuka. Ko da ganin haka shima sai hankalinsa ya tashi ya shiga lallashin shmzan yana mai tambayarsa. “Ya kai xana meye ya vata maka rai haka?” Shima ya dubi mahaifinsa yace masa. “Abba ina amfanin wannan shirin na gaggawa haka, shin yaqi zaka fita ko kuma wani abune ya faru mara daxi?” Koda jin wannan tambayar sai jikin sarkin yaqi marhat ya yi sanyi ya tsuguna a gaban shamzan ya riqe kafaxunsa da hannunsa guda biyu ya kalle shi cikin nutsuwa yace masa. “Ya kai xana kayi sani cewar sarki ne ya bani umarni akan na tafi can birni arna indiyawan daji na xauko wani yaro wanda idan ba akawo shi an kashe shi ba to nan gaba zai rushe mulkin sarki ya kuma halakashi sannan ya haye kan karagar sa kuma ya kawo sauyi a cikin qasar” Sa’ar da marhat ya zo nan a maganarsa sai zuciyar shamzan ta buga da qarfi ya kalli mahaifinsa yace masa. “Wanne yaro ne haka har zai firgita sarki ya xaga masa hankali kamar haka?” Ya kalli xansa yace masa. 40 DAN BAIWA “Sunan shi salhim kuma ya kansace xan wata almajira marigayya da ta rasu” Koda jin wannan maganar sai shamzan ya yanke jiki ya daxi qasa sumamme cikin ximuwa da gigita mahaifinsa ya ruga da gudu ya samo ruwa ya yayyafa masa ya farfaxo da qyar. Koda ya buxe idonansa ya kalli mahaifinsa nan take sai qwalla ta cika masa idanu ya soma Magana cikin murya kuka. “Ya kai Abbana kayi sani cewar wannan yaron da kake shirin zuwa ka kamo shi ka saka akashe shi abokina ne kuma aminina saboda akwai ranar daya ceci rayuwata daga faxawa rijiyar nan ta bayan kasuwa muna cikin wasa, muna cikin wasa sai kwatsam mukaga wannan macijiyar ta cikin rijiya ta fasa kai a daidai wajen da nake zaune ta yo kaina tana shirin sarana ko da ganin haka sai salhim ya dako tsale daga wajen da yake ya rungumi macijiyar. Ai kuwa sai ta kananaxeshi da nufin ta karya sassan jikinsa amma sai naga ya zaro wani xan siririn itace daga jikinsa ya cakawa macijiyar a cikin idonta guda xaya take idon ya tsiyaye ta saki salhim ta faxi qasa tana birgima anan take ta mutu tun daga wannan rana muka zama abokai ni da shi. Don haka yanzu wanda ya ceci rayuwata shi zaka kashe?” Koda jin wannan tambayar sai jikin mahaifinsa ya yi sanyi kuma hankalinsa ya dugunzuma ainun ya sake duban shamzan cikin alamun tsananin damuwa yace. “Kayi sani idan banje na kamo salhim na kawo shi gaban sarki ba to babu shakka rayuwarka data mahaifiyarka tana cikin hatsari a hannun sarki kuma kafi kowa sanin baqin halinsa don haka sai ka zava da rayuwarka data salhim wacce kafi qauna?” Hawaye ya soma zuba shar…shar daga cikin idanunsa yacewa mahaifinsa. “Idan har rayuwata zata fanshi tasa to na sadaukar da rayuwata akan ta shi” Kafin shamzan ya gama rufe bakinsa tuni mahaifinsa ya daka masa tsawa cikin vacin rai yace da shi. “Baka da hankali ne? wane hali kake tunanin zamu shiga ni da mahaifiyarka idan muka rasaka bayan mun fitar da ran samunka sannan muka samu haihuwa. Shekara goma muna son haihuwa bamu samu ba sai akan ka” Koda jin wannan maganar sai shamzan ya yi wuf zai ruga da gudu zuwa waje amma sai mahaifinsa ya yi zafin nama ya kama shi ya soma jansa da qarfin tsiya yana ta faman daddagewa. Tare da kukan 41 DAN BAIWA baqin ciki a haka ya jefa shi cikin xakinsa ya janyo xakin ya dates da makuli daga waje, cikin hanzari ya juya ya ci gaba da yin shirinsa ya xauki takobinsa da garkuwa ya nufi qofar fita daga cikin gidan amma sai matarshi Larufa tasha gabansa a lokacin da hawaye suke suvucewa daga cikin idanunta sannan tace masa. “Ni alfarma guda xaya nake nema a wajenka idan har kayi nasara kama yaro salhim kada ka bari ai masa kisan gilla lallai ai masa kisa na farat xaya wanda ba zai sha azaba ba” Ya kalleta ba tare daya bari sun haxa idanu da ita ba yace mata. “Ba komai lallai zan yi iyakacin qoqarina naga hakan bai faru ba” Ya miqa hannu ya dafa kafaxarta yayi gaba abinsa kafin ya fita tace masa. “Babu matsala” Ya qarasa fita daga cikin gidan ya nufi wajen da barga dawakansa take bawan da yake kula da barga yayi saurin jawo masa dokinsa wanda dama tuni ya kammala xaura masa sirdi take sadauki marhat ya kama dokinsa ya haye sannan ya zabureshi da gudu ya fice daga cikin gidan. Marhat yana zuwa qofar fada ya iske dakarun da za su yi masa rakiya izuwa birnin arnan daji suna bisa dawakai xauke da muggan makamai sarki muzwan na tsaye a gefe guda ya fuskance su fuskarshi a murtuke babu sassauci koda sarkin yaqi marhat ya qaraso sai sarki ya kalle shi yace masa. “Kayi sani kai da wannan dakarun ba za ku iya yaqar mutanen birnin arnan daji ba, amma ina son ka isar da saqona ga sarkin su cewar idan har wannan yaro yana hannunsa to ya bani shi cikin ruwan sanyi idan kuma ba haka ba zaman lafiyar da yake a tsakanin mu ka isar masa da wannan saqon a matsayin saqon dana baku kwa iya tafiya na sallame ku” Koda sarki muzwan ya zo nan a zancensa sai sarkin yaqi marhat ya nisa bisa girmamawa yace. “Za muyi komai kamar yadda ka umarta” Nan take sarkin yaqi ya kaxa linzamin dokinsa ya nufi hanyar fita daga cikin gidan sarauta da gudu cikin hanzari ragowar dakarun suka rufa masa baya. Shi kuma sarki muzwan ya bisu da kallo yana yin wani guntun murmushi mugunta. A daidai lokacin wani hadiminsa mai kula da komai nasa mai qaton ciki 42 DAN BAIWA kamar an kifa masa qwarya da wani murtukeken gashin bakinsa ya ruga da gudu zuwa wajen sarki muzwan yana qyalqyala dariya yace masa. “Ya shugabana ka tura musu dodon maza kuma sa gudu maganin qi gudu, ina mai tabbatar maka marhat sai ya zo maka da wannan yaron salhim ko a mace ko a raye saboda baka tava tura shi aikin daya gagareshi ba” Koda jin haka sai sarki muzwaan ya kwaxawa shambur mari kuma ya qyalqyale da dariya shima shambur sai shima ya qyalqyale da dariya yana sosa kuncinsa. A kullum ta Allah sarki muzwan yakan mari shambur sau ashirin ko sau goma sha a duk lokaci da ya yi abinda ya bashi dariya ko kuma ya bashi haushi ko kuma ya burgeshi. Duk da cewar shambur yana shan wannan marin amma ya nacewa sarki muzwan ko yaushe suna tare saboda kaf qasar Hindu babu wani mutum da yake samun kuxi a jikin sarki sai shambur saboda duk mari xaya a matsayin dinare dubu yake. Shambur ya tara dukiya mai yawa a jikin sarki muzwan har takai kaf birnin Hindu babu gidan manomi kamarsa amma kasancewar shi da sarki hakan baya hana shi biyan haraji da kuma raba noman shi ya baiwa sarki kaso biyu a cikin uku na duk abinda ya noma. Koda sarki yaga shambur ya soma sosa kuncinsa daga marin daya yi masa na farko a ranar sai ya qara qyalqyalewa da dariya yace masa. “Idan ka yi wasa yau ba zaka samu kuxi ma su yawa ba, saboda bana son kowa ya zo wajena har sai sarkin yaqi ya dawo gareni da kyakkyawan labari” Koda gama faxin haka sai sarki muzwan ya juya ya kama hanyar da zata kais a cikin turakarsa. A ko wanne lokaci idan ya shiga cikin turakar tashi akwai kuyangi da suke binsa suna masa fifita suna kuma yi masa tausa har sai ya yi bacci amma yau sai ya koresu ya kuma hana kowa zuwa gareshi kai tsaye ya shiga cikin turakarsa. Shi kuma shambur ya bi sarki da kallo cikin tsananin takaici bai san lokacin da zancen shi ya fito fili ba yace. “Haqqiqa wannan sarki ka cika azzalumi idan banda zallunci ka gawurta amma qananan yaran ma baka qyale ba” Koda shambur ya fahimta a waje ya yi Magana sai ya yi saurin marin bakinsa. “Kai xan banza kar ka jawo mun hukunci kisa a banza” Yana gama faxin haka sai ya juya da gudu ya nufi varin da gidansa yake a cikin masarautar. * 43 DAN BAIWA Al’amarin su yaro salhim kuwa tun daga lokacin da wannan yarinya ‘yar qabilar arna daji ta jashi da gudu sai su ka yi ta gudu babu sassautawa abinda ya xaurewa salhim kai wani irin gudu suke na ban al’ajabi. Harma qafaffunsa suna rabuwa da qasa tamkar za su tashi sama kuma gudun da suke yi abin ya wuce qima saboda suna wuce komai na dajin kamar wucewar tauraruwa mai wutsiya. Nan take salhim ya fahimci wannan yarinya tana da qarfin sihiri na tsafi saboda tun lokacin data kama hannunsa suna wannan gudu ko kaxan bai ji wata gajiya ba kuma gashi har kusan sa’a biyu suna wannan gudun. Abu guda ne yake kai kawo a cikin zuciyarsa me yasa wannan yarinya ta ceci rayuwarsa? Kuma yanzu ina zata kai shi? Amsar da salhim ya kasa baiwa kanshi kenan. Sai da suka kuma shafe rabin sa’a suna wannan azababen gudun sannan suka iso birnin arna daji. Tun daga nesa mamaki ya cika salhim don ganin gidajen arna daji birjik a wajen wanda aka yisu da baqin dutse na wuta. Girman wannan gari ya ninka cikin ainahin birnin hindu da kuma faxi sau goma. Kuma a tsakiyar birnin aka gina fadar sarkinsu da isowar su qofar shiga birni tare da wannan yarinya sai dakarun da suke tsare qofar wasu qarfi majiya qarfi kimanin su xari uku suka soma risinawa suna gaida yarinya. Su dai waxannan dakarun sun kasance babu komai a jikinsu sai wani warki kuma sun kasance ma su tarin qwanji da murxewa jiki kuma sun kasance ko wanne su yana rataye da takobi, kwari da baka da kuma wuqaqe masu yawa a jikinsu. Koda salhim yaga waxannan masu gadin sun rusuna suna gaishe da wannan yarinya sai jikinsa ya bashi cewar ta kasance ‘yar wani babban mutum xaya daga cikin jama’ar birnin. Babban abinda yake damun salhim babu damar ya yi hira da wannan yarinya ko kuma ya ji daga gareta amma banda haka yana da tambayoyi masu yawa da yake da buqatar yi mata amma kuma bai iya yarensu ba haka itama bata iya nasa ba. Hakan yasa tun da suka baro birnin Hindu babu wanda yace da xan uwansa qala sai dai duk lokacin da suka haxa idanu sai dai kawai yaga ta yi masa murmushi. Da shigar su salhim cikin wannan birnin arna daji sai ya zama wani xan qauye ya soma kalle-kalle yanda yanayin rayuwarsu ya burgeshi matuqa, suma matan garin babu wata sutura ta 44 DAN BAIWA kirki a jikinsu domin qirjinsu da qasansu ne kawai a kare da wani yadi mai kauri wanda sune suka saqa shi da tasu hikimar ta sarafa auduga. Su kuma maza da qananun yaran qasansu kawai suke suturcewa da wani qaramin zani iya cinya babu abinda ya kuma qara burge shi sai yanda mata su ka yi ado da sarqoqi a wuyansu da kuma qafafunsu wanda aka yi su da ‘ya ‘yan wuri. Babban mutum a cikinsu wanda ya zama basarake ko kuma attajiri shi ne yake yafe da mayafi bayan haka kuma matan cikinsu masu daraja suna yin ado da sarqa lu’u lu’u ko zinare gaba xaya jama’ar birnin suna gabatar da sabgoginsu kuma ga kasuwa tana ci ana ta cinikayar kayayyaki iri-iri na amfanin yau da kullum kayan abinci kala-kala da kuma kayan ado iri-iri. Koda shigar su salhim cikin garin tare da wannan yarinya sai kallo ya koma kansu kowa ya zuba musu idanu aka tsaya cak da gabatar da komai amma kuma duk wajen da suka ratsa sai salhim yaga ana gaida wannan yarinya cikin biyayya da girmama kuma sai jama’a suka riqa binsu a baya xu tamkar jama’ar gari ba su tava ganin mutum mai sutura irin na salhim ba har zuwa wannan lokacin wannan yarinya tana riqe da hannun salhim bata sake shi ba. Nan suka durfafi wajen da fadar sarki take kai tsaye ba tare da shayin komai ba kafin su isa qofar fadar tuni labari ya riski sarki jamhas cewar Gimbiya zasmin ta shigo gari da wani irin mutanen hindu. Koda jin haka sai hankalin sarki jamhas ya tashi ainun ya tashi tsaye cikin sauri ya hau kan wani gini mai tudu inda aka girke wani tebur xauke da tarkacen kayan tsafi da sihiri na tsubacetsubace cikin sauri ya xauki madubin tsafinsa ya shafe shi. Nan take yaga hoton komai daya faru a birnin hindu daga lokacin da salhim ya yi yana yawo yana bara bai samu abinci ba zuwa lokaci daya shiga gidan sarki muzwan ya saci gurasa guda xaya da kuma umarnin da sarki ya bayar akan cewar a bishi a saro kanshi amma kuma sai gimbiya zasmin ta ceci rayuwarsa ta gudo da shi zuwa wannan birnin na su. Bayan da sarki jamhas ya gama ganin wannan abinda ya faru nan take ya ji ya kamu da tsananin tausayin yaro salhim abinda ya saka kenan ya kuma bincike akan yaron salhim yaga irin zallunci da sarki muzwan ya yi wa iyayensa bayan an kwashe dukiyar su kuma aka qona iyayen 45 DAN BAIWA nashi a cikin gidansu bisa sa’a da kuma nisan kwana yaro salhim ya tsira da rayuwarsa. Koda sarki jamhas yaga wannan abubuwan sai ya ji ya kamu da tsananin son shi gami da tausayinsa har sai da qwala ta zubo masa ya ci gaba da bincike a cikin bincikensa nasa gano lallai wannan yaron xan baiwa ne nan gaba sai ya gawurta ya shafe duk wani tarihi da wani jarumi ya kafa a yanki kuma zai kafa tarihin da wani bai tava kafawa ba a duniyar ba. Koda ganin wannan lamari sai hankalin sarki jamhas ya kuma dugunzuma ya miqe zumbur daga kan turakar shi ya nufi can wajen da babbar fada take yana isa ya iske fadar ta cika maqil da kusa gaba xaya jama’ar da suke qasar wanda suna tsaye suna jiran bayani daga bakinsa. Su kuma salhim da Gimbiya Zasmin suna tsaye a tsakiyar fadar suna fuskantar wajen da sarki jamhas zai fito zuwa wani lokaci sai taga ya fito fuskarsa a murtuke ganin haka ya saka zuciyarta bugawa da qarfi kuma tsoro ya kamata lokaci guda fadar ta yi tsit. Kwatsam babu zato babu tsamani sai salhim yaga sarki ya kalle shi cikin murmushi da yaren mutanen Himdu yace masa ‘Marhaba da salhim xan baiwa ni ne sarki jamhas mahaifin Gimbiya Zasmin yarinya dake riqe da hannunka” Koda ya zo nan a maganarsa sai ya juya ya kalli Gimbiya Zasmin cikin mamaki sannan cikin sauri ya cire hannunsa daga nata ya duqar da kansa qasa gareta cikin alamun girmawa don yasan a matsayinsa na talaka bai kamata ya haxa hannu da ‘yar sarki ba bare har hannunsa ya tava nata. A daidai wannan lokacin ne kuma sarki jamhas ya kalli Gimbiya zasmin wannan karon fuskarshi ta sauya zuwa vacin rai kamar ba shi bane ya yi murmushi ba yanzu yace mata. ‘Me yasa kika ceci rayuwar wannan yaron shin kinsa irin bala’in da za mu shiga a dalilin wannan laifin da kika aikata?” Koda jin wannan tambayar sai jikin Gimbiya Zasmin ya kuma yin sanyi ta sunkuyar da kanta qasa ta buxe baki cikin murya mai xauke da sautin tsoro tace. “Ka gafarce ni ya Abbana ka sani ba komai ne yasa na ceci rayuwarsa ba face yau kimanin sati biyu kenan ina bincike akan madubin tsafina naga komai akan tarihinsa kuma taurarin sa’a da xaukaka suna kan rayuwarsa anan take tausayinsa ya kamani kuma na Aiyana hakan cewar sai na taimaka masa a rayuwata na ceci rayuwarsa. Sanin kanka 46 DAN BAIWA ne idan ban ceci rayuwarsa ba to babu shakka macen sirri za ta zo ta kuvutar da shi wane irin hukunci kake ganin cewar za ta yi mana idan ya zama ita ta aikata hakan? Kafi kowa sanin ta dalilinta muka samu ‘yanci muka samu xaukaka qasar wajen mu take noma har muka samu damar da mazajenmu sue iya tsayawa a fagen fama su yi yaqi da dakarun qasar Himdu wanda a baya basa iya yin haka. Akan wannan dalilin yasa na shiga cikin birninsu a yau saboda tuni naga abinda zai faru da shi a bisa satar gurasa don haka ina mai roqonka alfarma daka tsare rayuwar salhim ta ko wacce hanya saboda nasan zaka iya yin haka” Sa’ar da Gimbiya Zasmin ta zo nan a maganarta sai sarki jamhas yaja dogon numfashi gami da ajiyar zuciya yace. “Yake ‘ya ta haqiqa kin tsokano tsuliyar dodo domin karo da sarki mazwan haqiqa ba qaramin bala’i bane banda ni da shi xin kar tasa kar da abinda yanzu kika aikata zai iya zama sanadin rushewar birnin mu da kuma asara rayukan jama’armu. Fiye da shekara arba’in bay muna zaman lafiya da juna bamu da wata matsala da masarauta qasar Hindu bisa waxansu qa’idoji da aka yi su a rubuce daga lokacin yaqi bai kuma varkewa a tsakaninmu ba amma sai gashi yanzu kike neman kawo qarshen wannan alaqar daga tsakanin mu ki kawo qarshen kwanciyar hankali a garemu. Yanzu dai hanya xaya zanbi na tserar da rayuwar wannan yaron kema kuma na tsera dake daga shiga halaka bisa wannan laifin da kika aikata yanzu mafiya guda xaya ce ya zama dole dake da shi ku bar wannan nahiyar gaba xaya ku koma can birnin sin wajen aminina Boka sambul inda za ku ci gaba da rayuwa har zuwa matakin matasa inda anan za ku ci gaba da karva horo na yaqi kuma a tsumaku a cikin kwatarniyar tsafi idan har baku nesanta daga wannan nahiyar ba babu yanda za a yi na iya kareku daga farmakin sarki muzwan. Amma idan kuka yi nisa da wannan nahiyar har zuwa lokacin da sarki muzwan zai daina farautar ku. Kuma nasan ma zai wahala ya daina farauta ku tunda Boka marmasi ya yi masa bayani akan shi saboda haka har abada hankalin sarki muzwan ba zai tava kwanciya ba don haka dole ne kuyi yanda za ku iya kare kanku a can birnin sin kafin sarki muzwan ya gano cewar kuma can ya aika da dakaru da za su yi farautar ku. 47 DAN BAIWA Kuma yanzu haka baifi sa’a uku ba sarki mazwan ya aiko sarkin yaqinsa marhat akan umarnin ya zo nan garin da zaqaquran sadaukai majiya qarfi akan ya zo ya farauce ku saboda haka ku zo yanzu mu je na shirya ku cikin sauri kubar wannan nahiyar tamu” Ko da kammala faxar wannan Magana sai sarki jamhas ya nufi wata qofa ta daban cikin sauri su salhim da gimbiya zasmin suka bishi a baya kai tsaye barga dawakai ya shiga ya zavo wasu qosasun dawakai guda biyu fari da baqi ya miqa musu yace musu. “Maza ku hau waxannan dawakai kubi wannan hanyar kuyi maza ku fita daga cikin wannan qasar kuma kuyi sani cewar waxannan dawakai sune za su yi musu jagora har zuwa gidan aminina boka sabir na birnin sin kuma tafiya ce ta kwanaki xari da sitin amma dawakan na ku za su gajarceta su yi muku ita a kwanaki arba’in da xaya. Duk wani guzuri da kuke buqata ko abinci ku samarwa kanku a cikin daji ko kuma duk garin da kuka ratsa akan hanyarku ta tafiya kuma duk wani mutum daya kawo muku hari walau mutum ko aljan ko wata muguwar da bar ku kare kanku” Koda sarki jamhas ya zo nan a maganarsa sai salhim ya kalleshi cikin alamun tsananin tsoro da fargaba yace masa. “Ya shugabana nifa ban tava hawa doki ba bare na sarafa shi sannan kuma ban iya riqe koda takobi ba bare na iya kare kaina daga harin wani mugun abu, kuma ya yaya zan iya rayuwa a cikin daji har tsawon kwana arba’in alhalin yauce rana farko dana soma shiga cikin daji a rayuwata. Nifa babu abinda na iya face bara a cikin kasuwar garinmu ina neman abinci da zan saka a cikin bakina” Koda salhim ya zo nan a maganarsa sai sarki jamhas ya dube shi yaxan yi murmushi ya dafa kafaxarsa yace masa. “Kada ka damu ya kai jarumin gobe ka yi sani cewar babu wani bala’i da z aka shiga ba tare da ka kuvuta ba saboda kai xan baiwa ne haka qaddaraka take” Ko da sarki jamhas y agama Magana sai ya xaga salhim sannan ya xora shi akan farin doki ya sashi ya riqe linzamin dokin ko da ganin haka sai gimbiya zasmin ta daka tsale sama ta haye kan baqin dokin sannan ta yiwa sarki jamhas kallon bankwana a lokacin da idanunta suka ciko da kwalla tace masa. “Ya kai abbana nasan cewar zamu xauki lokaci mai tsawo bamu haxu ba kai ba amma ina roqon a duk lokacin daka samu damar kai mana 48 DAN BAIWA ziyara ka kawo mana a birnin sin” Tana gama Magana sai ta juya ta zaburi dokinta da gudu ta nufi hanyar sa sarki jamhas yace su bi ai kuwa dokin nata yana motsawa sai na salhim ya bishi a baya. Salhim ya ji kamar zai faxo a lokacin da kuma xan jiri ya xauke shi sakamakon rashin sabo da hawa dokin amma sai ya qanqame jikinsa da qafafunsa a jikin dokin zuciyar shi tana bugawa da qarfi sakamakon tsoro daya kama shi. Koda gimbiya zasmin ta waigo taga halin da salhim yake ciki sai ta bushe da dariya tana dariya tace masa “Kada ka damu jarumin gobe da sannu zaka zama gwanin iya doki wanda zai zama gwarzo mai lashe gasar sukuwa da doki” Koda jin wannan sai mamaki ya cika zuciyar salhim yace ta yay azan zama gwarzon da zan lashe sukuwa alhalin tsoro garen kamar farar kura. Lokacin da gimbiya zasmin tabi hanyar da sarki jamhas ya nuna musu su bi suna binta sai suka cika da tsananin mamaki kawai tsintar kansu su ka yi a cikin wani qungurmin daji wanda basu tava ganin kamarsa ba wannan dajin ya fita daban da irin yanayi da dukan dazukan dake can nahiyarsu. Hakan ya nuna mata ta fahimci lallai tsafi gaskiyar mai shi tafiyar lokaci mai tsawo suka gajarce tafiyar haka dai gimbiya zasmin da salhim su ka ci gaba da tafiya a cikin dokar daji ba tare da sanin inda suka nufa ba. Dawakan na su ne suke tafiya akan hanyar ba tare da sun sani ba. Sai da suka yini suna tafiya

Chapter 4 of 7