Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
ba tare da sun haxu da wani abu ba sai daya zamana rana ta faxi magariba ta shiga sannan ne gimbiya zasmin ta dubi salhim tace masa. “Abokina ina ganin ya kamata mu sauka anan mu huta zuwa washe gari muci gaba da tafiya saboda wannan daren babu hasken farin wata ko kaxan wanda zai zama fitila da dawakan mu za su ga gabansu har su iya gane hanya” Lokacin da salhim ya ji wannan shawara da gimbiya zasmin ta kawo sai ya kalleta cikin tsananin mamaki yace mata “Wai ke shin ya aka yi kike da basira haka gami da hangen nesa? Kuma bah aka ba ashe kin iya Magana da yarena amma har muka gudo daga birnin Hindu baki min Magana ba koma kallona kice dani qala baki yi ba?” 49 DAN BAIWA koda jin wannan maganar sai ta bushe da dariya sannan ta nutsu tace masa. “Ai naqi yin Magana da kai ne saboda naga yanda zaka karveni shin zaka amince ka bini ba tare da tava gani na ba kuma kasan wacece ni ba? Idan na kuskura na yi maka Magana da yarenaka zaka saki jiki dani ka bani amanar kanka amma nib a haka nake so ba nafi son na jaraba imaninka naga shin z aka iya tara abinda ya zo maka ba tare da shakkar komai ba” Koda jin wannan maganar sai salhim ya jinjina kai cikin alamun gamsuwa yace mata. “Tabbas kin cika ma’abociyar hikima” Gimbiya zasmin ta yi dariya tana jinjina kai tace masa. “Kai kuma ka cika xan baiwa da har ka samu damar tsalake duk wata masifa da take binka hark a kawo zuwa wannan lokacin” Gimbiya zasmin tana gama faxaar haka sai ta hango wani kogon dutse a gabasu tace masa. ‘Muje ga wani kogon dutse can gabanmu muje mu yada zango a cikinsa koma samu nutsuwa zuwa washe gari ko kuma akwai wani qorafi akan haka?” Salhim ya gyaxa kai yace. “Yaya zanyi qorafi ni da bansan komaoi ba kuma ban isa na iya kare kaina da komai ba” Ta yi murmushi ta juya ta ci gaba da tunkara wannan kogon dutse. Shima ya ci gaba da binta a baya suka tunkari wannan kogon dutse. Gaskiyar ma su iya Magana da suka ce rashin sani ya fi dare duhu. Tabbas inda Gimbiya zasmin sun san bala’in da za su riska a cikin wannan kogon dutsen da ba su yi gaggawar dosar shi ba bare har su kai ga sun shiga saboda abinda yake cikin kogon na halaka. 50 DAN BAIWA L JARUMI XAN BAIWA 4 okacin da Salhim yaga Gimbiya Zasmin ta sunkuyar da kanta qasa ta yi shiru bata ce komai ba sai ya kalleta yace. “Ranki ya daxe kinyi shiru baki ce komai ba, shin kema kin amince da duka sharuxan da jarumi Zaiyan ya gindaya mana?” Koda jin wannan sai Gimbiya Zasmin ta yi murmushi sannan ta dubi Jarumi Zaiyan tace masa. “Yakai wannan jarumi mai ban al’ajabi ka yi sani cewar ai tunda ka ceci rayuwar mu ga hannun wannan mugun aljanin wanda ya zo ya sace mu. Dole ne mu yadda da kai mu kuma karvi yarjejeniyar daka zo mana da ita tunda ko shakka bana yi ba za mu iya kare kanmu daga hannun wannan aljanin ba, ko da yake xan uwana yana da wata baiwa…” Kafin Gimbiya Zasmin ta kammala faxin wannan maganar dake bakinta sai Salhim ya yi sauri ya tari numfashinta yace. “Ni bani da komai dan haka maganar ki ta farko ita ce haqiqanin gaskiyar” Koda jin wannan sai Jarumi Zaiyan ya yi murmushi ya dubi Sahim yace. “Haba abokina ‘yar uwarka tana son sanar da ni cewar kana da wata baiwa ta musamman ko ba haka bane?” Koda jin wannan tambayar sai mamaki ya turnuqe Gimbiya Zasmin da Salhim ya kalle shi yace masa. “Abokina ya aka yi kasan haka?” Zaiyan ya yi murmushi yace “Tun farkon shigowar ku cikin dajin nan ina biye da ku a baya baku sani ba. Ina kallon duk abinda kuke yi ina jin duk abubuwan da kuke tattaunawa. Inda na fahimci cewar bakwa daga cikin mugaye, azzaluman mutane wanda hakan shi ya saka na taimake ku. Dana same ku kuna xaya daga cikin irin waxan nan mutanen da sam ba zan taimaka muku ba. Tabbas ko wane bil’adama Allah yana halittarsa da tasa baiwar. Ba mamaki abubuwan da kake yi na al’ajabi da ban mamaki sun baiwa ce irin ta sihirin tsafi da iyayenka da kakaninka suka sanya maka a jikinka tun kana jariri. Koma dai wacce baiwa ce lokaci zai bambance mana. Yanzu sai ku zo mu ci gaba da tafiya ko?” Koda jin 51 DAN BAIWA haka sai Gimbiya Zasmin ta dubi Jarumi Zaiyan cikin alamun damuwa tace masa. “To yanzu ta yaya tafiyar mu zata zamto xaya da taka alhalin mu akan dawakai muke kai kuma baka da abin hawa?” Koda jin haka sai Jarumi Zaiyan ya yi ‘yar guntuwar dariya yace. “Kada ku damu da yanayin tafiya ta kuyi gaba ni zan riske ku a yayin da rana ta faxi domin a sannan ne ya kamata mu yada zango” koda jin haka sai Gimbiya Zasmin ta kalli Salhim ta masa inkiyar su tafi. Nan take kuwa suka ta shi suka hau dawakan su suka bar Zaiyan a nan wajen suna waigensa. Kawai sai suka ga ya xauko butar ruwa ya yi alwala, sannan sai ya fuskanci alqibila ya tayar da sallah koda ganin haka sai Salhim ya kalli Gimbiya Zasmin cikin damuwa yace mata. “Wai shin anya kuwa Raiyan mutum ne? ki dubi fa yadda yake yin wata irin ibada kuma yace mu yi gaba zai same mu a gaba alhalin shi da qafafunsa yake tafiya mu kuma muna kana abun hawa. Ke kin sani kafin rana ta faxi mu yada zango sai munyi tafiyar sa’ani kusan bakwai” Zasmin ta gyaxa kai tace. “Ni kaina na soma zargin ba mutum bane saboda idan banda kai dana ga ka kashe muguwar birinyar nan ban tava ganin wanda ya yi wa aljani kisan galaba sai shi” Sahim ya gyaxa kai yace “Ai dole ne mu ci gaba da gyada shi sabida mu gano alnahin gaskiyar al’amarinsa shin kin san abubuwan da za mu lura da su mu gane shi mutum ne ba aljani ba?” Gimbiya Zasmin tace. “Kwarai kuwa abu na farko da za mu soma lura dashi shi ne yanayin cinsa da shansa, shin zai iya rayuwa ta tsawon kwanaki ba ci bas ha? Aljanu suna rayuwa tsawon kwanaki babu ci ba sha. Suna ma iya rayuwa tsawon shekara ba ci ba sha. Abu na biyu kuma shima aljani yana iya rayuwa a cikin akwatin da babu numfashi a cikinta da kuma qarqashin ruwa. Aljani na iya rikixa ya zama ko wace irin siffa. Batun shafe dogowar tafiya kuwa a cikin qanqanin lokaci kuwa ba komai bane a wajen aljani. Hatta wannan doguwar tafiyar dake gabanmu zuwa birnin sin wacce a qallah takai ta watanni uku aljani zai iya shafeta a cikin sa’a xaya. Yanzu abinda za mu yi shi ne mu sakarwa dawakan mu linzami mu yi gudu daga nan zuwa faxuwar rana, idan ya so sai muga lokacin 52 DAN BAIWA da Raiyan zai zo ya riskemu”. Koda jin haka sai salhim ya yi murna yace. “Tabbas kin zo mana da shawara mai kyau haka za mu yi” Nan take suka sakarwa dawakansu linzami suka yi ta gudu babu sassauci haka dai suka yi ta tsala gudu basa tsayawa face sun gaji sosai ko qishirwa ta kama su ko dawakan su. Sai da rana ta faxi,gari ya soma duhu sannan su Salhim suka yanke shawarar su tsaya su yada zango don haka sai suka ruke dawakansu suka fara tafiya a hankali suna kokarin su tsaya a bakin wata qorama. Kwatsam sai suka hango wani hayaqi yana tashi a can bayan wani dutse. Al’amarin dayai matuqar basu mamaki kenan. Salhim ya dubi Gimbiya Zasmin yace mata. “Nifa naga wani bil’adama ya shigo cikin wannan dajin ya kuna wuta yana jin xumi, alhalin wannan dajin hatta fatake tsoronsa suke ji” Koda taji wannan maganar sai ta xaga kai tace masa. “Ni kaina abinda ya bani mamaki kenan amman dai mu qarasa mu gani sai muga ko waye. Idan mutumin kirkine sai mu rabu da shi lafiya, idan kuma mugune sai mu yaqe shi” Ba tare da gardamar komai ba salhim ya bi zasmin a baya suka durfafi wannan dutsen inda suka hango hayaqin. Lokacin da salhim da zasmin suka iso gaban dutsen suka zagayo bayansa sai suka qame kamar gumaka tamkar an zare musu ruhinsu. Ba komai ne ya haddasa hakan ba face tsananin mamaki bisa ganin wanda ke zaune a wajen ya banqare wata barewa yana gasawa. Ashe hayaqin da suka hango na wutar da ake gasa barewar ne. ba wani bane ba ke gasa wannan barewa ba face Jarumi Raiyan. Koda Raiyan ya xago kai yaga zasmin da salhim sun iso sai ya miqe cikin murna ya tarbe su yace. “Har kun iso sannunku da zuwa. Na yi farin ciki da ganinku yanzu saboda dama lokacin yin ibadata ya yi. Ku zo kuci gaba da gasa wannan barewar kafin na hattama ibadar tawa sannan na zo mu ci” koda gama haka sai jarumi Zaiyan ya nufi wajen da wata qorama take ya tsuguna a gabanta ya fara yin alwala. A sannna ne zasmin da salhim suka sauko daga kan dawakansu suka xaure su a jikin bishiya sannan suka zo gaban wutar suka zauna. 53 DAN BAIWA Tsawon ‘yan daqiqu suna kallon junan su amman xayan su baice uffan ba. Daga can sai zasmin ta ja numfashi ta ce “Tabbas zaiyan aljani ne, idan kuwa bai kasance aljani ba to gagarumin matsafi ne. Ta yaya za’ace bayan mun baro shi a can baya kuma mun falfala wannan azababben gudun da dawakanmu amman duk da haka ga shi ya riga mu zuwa nan”. Salhim ya yi murmushin qarfin hali sannan yace. “Ni kuma abin ya xaure min kai, to amman dai za mu ci gaba da yin nazari akansa”. Zasmin ta numfasa tace “Abinda nake so da kai shi ne idan zaiyan zai dawo lokacin da za mu ci wannan naman barewar ina son ka qurawa idanunsa kallo sabida ka gano yadda akai ya riga mu zuwa nan tunda kana da baiwar hakan. Koda jin haka sai salhim ya yi murmushi yace. “Tabbas kin zo da babbar dabara hakan ya kamata na yi” haka dai Salhim da zasmin suka ci gaba da gasa naman barewa hart a gasu sosai, har maiqon jikinta na xiga qasa. A daidai wannan lokacin jarumi Raiyan y agama shafa addu’a sannan ya taso daga inda ya yi sallah ya dawo wajen su zasmin ya zauna. Ba tare da vata lokaci ba Zaiyan ya saka wuqa ya na yanko naman yana ajiyewa a gaban zasmin da salhim suna ci. Sannan shima ya yanko xan kaxan ya saka a bakinsa. A wannan lokacin salhim ya qurawa cikin idanun zaiyan idanunsa da nufin gano abinda ya yi xa zu kawai sai yaji kamar an watsa masa barkono a cikin idanunsa dan haka bai san lokacin daya yi sauri ya kauda idanunsa daga cikin nasa ba ya sunkuyar da kansa qasa yana mutsutsuke idanunsa a lokacin idanunsa suka soma zubar da hawaye. Sai daya sake jarraba kallon idanun zaiyan a karo na biyu amman ya kasa domin ji ya yi ma kamar idanun nasa za su doxe ya daina gani.babu shiri ya sunkuyar da kansa qasa. Har suka gama cin nama bai sake yarda ya qurawa qyayar idanunsa kallo ba. Abinda ya kuma xaure musu kai game da shi loma uku kawai ya ci ya yi hamdala ya daina cin abinci. Sai ya miqe ya nufi wajen da jakar guzurinsa take ya fito da tantuna guda biyu. Nan take ya soma aikin kafa tantuna, a cikin qanqanin lokaci ya hattama ya koma wajen da suke yace musu. “Ga tantuna can guda biyu na kafa muku sai kowa ne a cikin ku ya shiga cikin xaya ya kwanta” Da jin haka sai mamaki ya kama 54 DAN BAIWA salhim da zasmin suka dubi junansu sannan zasmin ta dube shi tace masa. “Saboda me ka rabamu kace kowa ya shiga tantinsa daban?” Dajin wannan tambayar sai Jarumi Zaiyan ya gyaxa kai yace. “A Addinina idan har yara sun kai shekara bakwai a duniya to lallai ana son a raba musu shimfixa. Ni kuwa ko qyaleni zan yi gadinku da izinin ubangijina kamar yadda na yi muku alqawari. Kusani cewa ni ban cika yin bacci ba da dare,domin lokacine da nake gabatar da ibadata. Koda gama faxin hakan sai Jarumi zaiyan ya koma can gefe xaya ya shimfixa buzu ya zauna a qasa ya kama yin addu’a yana jan carbi. A sannan ne salhim da zasmin suka sake duban junansu suka gyaxa kai Salhim yace. “Nifa na soma ji a jikina Salhim mutum ne kamar mu duk abinda yake yi na al’ajabi yana yi ne da taimakon ubangijinsa. Yanzu ne maganar daya faxa min a baya ta faxo min a rai cewar; ni baiwata tafi qarfin sihirin tsafi. Tabbas na yadda da haka sabida tsafi da sihirin tsafi basa haxuwa tunda gashi na kasa qura masa idanu naga gaskiyar al’amarinsa” Koda Salhim ya zo nan a zancen sa sai Gimbiya Zasmin ta vata rai ta dubeshi a fusace tace. “Yanzu kana nufin cewar har kayi imani da addininsa kenan? Ni har yanzu ban yadda cewar shi mutum bane kuma da sannu zan tabbatar maka da hakan kai dai kawai ka ci gaba da haquri gami da zuba idanu”. Wannan shi ne abinda ya faru tsakanin Gimbiya Zasmin da Jarumi Xan Baiwa Salhim akan hanyarsu ta zuwa birnin sin domin tsira da rayuwar su sai gashi sun haxu da wani sabon jarumi wanda ya fi Salhim Baiwa. A can birnin Arnan Daji kuwa lokacin da ‘yan majalisar birnin suka zauna domin su tattauna akan shawarar day a kamata su yanke akan sarkin yaqi Marnat sai kace nace ya yi yawa. Majalisar ta rabu gida biyu daidai. Vangare farko sukace su basu yarda da abaiwa marhat auren Gimbiya Hamrita ba. Kawai a kore shi ya koma garinsu sabida zaman shi a nan ma zai iya haifar da wani yaqi tsakaninsu da qasar Hindu kuma dole idan aka yi yaqin ayi asara rayuka da ba a san adadinsu ba kuma dole ayi asara dukiya mai xumbin yawa. Xaya 55 DAN BAIWA vangaren kuma sai suka ce su sun yadda a xaura auren Marnat da Hamrita kuma a karve su hannu biyu shi da sauran ‘yan uwansa tamkar ‘yan gari a kuma koyar da su duk irin al’adarsu da addininsu. A lokacin da aka ga anyi kunen doki babu vangaren daya yi rinjaye sai aka je aka sanar da sarki Jamhus abinda ya faru a majalisa. Lokacin da Sarki Jamhas ya ji wannan batu sai shima ya cika da mamaki yai shiru yana nazari. Daga baya sai bada umarnin cewar aje a yi shela ana son ganin kowa a fada. Nan take kuwa masu shela suka kama yawo a cikin birnin lungu-lungu saqo-saqo suna aikinsu al’amarin daya baiwa kowa mamaki sabida ba a san dalilin daya saka sarki ya shirya taro cikin gaggawa ba. Cikin qanqanin lokaci fada ta cika ta batse, duk inda mutum ya hanga babu abinda zai gani face kawunan bil’adama. Sai bayan kamar rabin sa’a da taruwar al’amma sannan aka ga fadawan sarki jamhas da dattawan garin suna shigowa fadar suna zama. A can gidan sarauta kuwa tuni sarki jamhas ya saka aka zo da sarkin yaqi marhat da abokan tafiyarsa suka gurfana a gabansa sannan ya sake turawa aka kirawo Gimbiya Hamrita. Bayan Hamrita tai so ta zauna a kusa da sarki, tana hada idanu da Marhat sai ta yi masa murmushi mai taushi amman kuma idanunta sunyi jawur alamun cewar tasha kuka ta more. Al’amarin daya dugunzuma zuciyarsa tausayinta ya malala cikin zuciyarsa ya kuma ji wani sonta ya kuma shiga cikin ransa. Kawai sai sarki ya yi gyaran murya ya kalli Marhat yace masa. “Yakai sarkin yaqin qasar Hindu kayi sani cewa yanzu ‘yan majalisa sun zauna a kanka saboda su yanke hukunci da yafi dacewa akan ka amman sai duka vangarorin biyu suka yi kunen doki, bisa haka na saka aka shirya taron gaggawa a nan fada na saka a gayato dattawa sabida a yanke hukunci na qarshe akan ku sabida ci gaba da zamanku a cikin birnin nan ba tare da sanin matsayin ku ba ka sani abu ne mai hatsari ‘yarta Hamrita ta kamu da tsananin sonka kuma kai baka san cewar jiya kwana tayi tana kuka tana roqona na barta ta aureka. Ka sani ba zan jefa rayuwar jama’ata a cikin hatsari ba kawai na kyautatawa ‘yarta na samar muku da farin ciki wasu kuma su shiga cikin qunci. Dan haka yanzu nan zamu fita fada gaba xayan mu. 56 DAN BAIWA Ni kaina ban san hukuncin da dattawa za su yanke akan wannan al’amarin ba” Yana gama faxin haka sai Sarki Jamhas ya miqe tsaye ya nufi hanyar fada yana riqe da hannun Gimbiya Hamrita dakaru suna take masa baya, inda aka tasa qeyar su sarkin yaqi Marnat a baya inda Hamrita ta yi ta waigensa domin tana ganin cewa ba zata tava mallakarsa ba a matsayin abokin rayuwarta. Lokacin da su sarkin jamhas suka iso fada sai jama’a suka ruxe da yi masa jinjina har said a yaje ya zauna akan kujerar sannan fadar tayi tsit aka yi shiru ana sauraro don jin dalilin day a saka sarki ya kirawo wannan taro. Ba tare da vata lokaci ba kowai sai Jamhas ya miqe tsaye ya fuskanci jama’a yai gaisuwa sannan yace. “Yaku jama’ar wannan birnin na mu mai albarka gaba xayanku kowa yasan abinda ya faru lokacin da muka gabatar da gasar neman auren ‘yarta Gimbiya Hamrita wanda ya zamana ba kowa bane ya lashe wannan gasar face baqon mu Sarkin yaqin qasar Hindu wato sadauki Marhat. Dukan su kunsan abinda ya kawo su birnin mu domin su cika umarnin azzalumin sarkin su na su kamo wasu yara guda biyu. Tabbas yanzu sarkinsa yana cikin mugun fushi da mu kuma zai iya kawo mana tayin yaqi sabida mun ba shi masauki shi da abokan tafiyarsa. Bisa wannan dalilin ya saka na kira kowa da kowa sabida a yanke hukunci yanzu take sabida ‘yan majilisu sun kasa. A halin yanzu na miqa wuqa da nama ga dattawanmu saboda sune suke warware mana wata matsala data gagaremu tsawon shekaru tun daga kafuwar wannan birnin namu mai albarka” Gama faxin haka ke da wuya sai sarki jamhas ya dubi wajen da dattawan suke zaune yace. “Muna sauraren ku” Nan take Dattawa suka shiga yin qusqus suna tattauna Magana yadda babu mai jin abinda suke faxa sai su isu. A wannan lokacin cikin Gimbiya Hamrita dana Sadauki Marnat ya xuri ruwa, hankalinsu ya dugunzuma ainun suka fara tunanin cewar abu ne mai wuya dattawa su amince da aurensu. Sai da Dattawa suka shafe kusan sa’a guda suna wannan tattaunawa sannan suka gama yanke hukunci, kawai sai babban cikin su wani mutum tsoho tukuf mai farin gashi ya miqe ya tunkari jama’a yace “Bisa la’akari da sanin hakkin xan adam da kuma sanin darajar soyayya da kuma ceto rayuwar waxanda ake zalunta mu Dattawa mun amince 57 DAN BAIWA Sadauki Marhat ya auri Gimbiya Hamrita” Kafin tsoho ya gama rufe bakinsa tuni fada ta ruxe da ihu da shewa. Ita kuma Hamrita miqewa ta yi zumbur daga kan kujera da take kusa da Sarki Jamhas ta ruga da gudu tsakiyar fada wajen da Sadauki Marhat yake tsaye ta rungume shi cikin matuqar farin ciki suka soma qyalqyala dariya murna. Kwatsam sai aka ji Sarki Jamhas ya daka tsawa. Take fadar tayi tsit, Gimbiya Hamrita ta firgita ta janye jikinta daga cikin na Marhat a wannan lokacin kuma tsohon nan ya ci gaba da bayani. “Mun yadda da wannan abun bisa sharaxin dole ne Sadauki Marhat da abokan shi su yi yaqi da mayaqan mu waxanda babu kamar su a filin yaqi su kai su qas. Sharaxi na biyu dole ne su yi rantsuwa cewar za su zauna da mu da gaskiya da amana kuma za su kare qasar mu kamar yadda za ku kare wacan da kuka baro taku ta haihuwa. Sharaxi na uku dole ne ku ajiye waccan naku addinin na qasar Hindu ku amshi na mu. Sharaxi na huxu wanda shi ne na qarshe dole ne Sadauki Marhat ya iya yaren mu a cikin sati guda kuma dole shi da yaransa su ajiye na su yaren su riqe na mu” Lokacin da Tsoho ya zo nan a jawabinsa sai hankalin kowa ya tashi a cikin fadar saboda an san cewa ba abu ne mai yiwuwa ace su Marhat sun tsallake duka waxan nan sharuxan.Nan fa aka sake yin tsit a lokacin da jikin kowa ya yi sanyi tamkar ana zaman makoki. Abokan tafiyar Marhat kuwa durqushewa qasa suka yi suka dafe kawunan su cikin alamun baqin ciki kamar su fashe da kuka. Ita kuma Gimbiya Hamrita sake rungume Marhat ta yi ta fashe da matsananci kuka mai tattare da baqin ciki. Sautin kukan nata kawai ake ji a fadar yayin da kowa ya yi jigum-jigum. Kawai sai aka ga Sadauki Marhat ya janye jikinsa daga cikin nata ya dubeta cikin murmushi a lokacin da ya sanya hannunsa ya share mata hawaye sannan yace. “Abar qaunata idan har qaunata a gare ki ta gaskiya ce na miki alqawarin ni da abokan tafiyata duk za mu tsalake wannan sharuxxa da aka gindaya mana” Da jin haka sai farin ciki ya lulluve Gimbiya Hamrita ta sumbaci goshin Marhat tace. “Zan zuba ido na gani idan soyayyarka a gare ni ta gaske ce babu algus a cikinta” Dajin haka sai Marhat ya taka ya zo gaban karagar Sarki Jamhas ya risina a gabanshi sannan yace “Ya shugabana yaushene 58 DAN BAIWA za mu fafata mu da manya dakarun naku abin dogaronku?” Sarki Jamhas ya yi murmushi cikin jin izza gami gami da yadda da kai yace masa. “Nan da cikar kwanaki bakwai kuma a wannan ranar ne za ku iya yaren mu kuma ku cika sauran sharuxan da muka saka muku” koda gama wannan maganar sai sarki jamhas ya miqe tsaye ya yafito Gimbiya Hamrita ta taho gare shi ya kama hannunta ya jata suka fice daga cikin fadar. Nan dai fatar ta waste kowa ya kama gabansa. Lokacin da sadauki Marhat tare da abokan tafiyarsa suka dawo masaukinsu sai suka zauna sukayi tagumi cikin sanyi jiki gami da tsananin damuwa tsawon ‘yan daqiqa xayansu bai ce qala ba. Daga can sai mafi girma da iya yaqi daga cikin dakarun ya dubi Marhat yace “Ya shugabana ta yaya kake ganin za mu iya haye waxan nan sharuxan da aka gindaya mana? Na yarda cewar zamu iya karva ad’adunsu da addininsu amman ta yaya zamu iya samun nasara akan zakwakuran dakarunsu? Ta kuma yaya zaka iya koyon yaren su a cikin sati xaya? Kuma mu ina batun iyalin mu da muka baro a can qasar Hindu? Shin baka tunanin cewar a yanzu haka sarki ya saka an halaka su? ” Koda jin waxan nan tambayoyyin sai sarkin yaqi ya ja gwauron numfashi ya yi shiru kamar ba zai ce wani abu ba can ya miqe ya yi tafiya taku uku yana mai juya musu baya yace. “Nasan halin sarkinmu bazai kashe iyalinmu ba face ya kamomu a raye domin ya yi musu kisan gilla a gabansu. Sannan muma ya yi mana kisan wulaqanci. Ina son ku saka a cikin ranku cewar babu wani abu da ba zai yuwu ba a wannan duniyar face ba’a jarraba shi ba. Bisa wannan dalilin nake son mu zage matse muyi qoqari wajen ganin mun tsallake duk waxan nan sharuxan da Sarki Jamhas ya shimfixa mana kada ku damu da nawa sharaxin kudai ku yi naku daga yau zamu soma baiwa kanmu horon yaqi har zuwa cikar kwana ki bakwai da za mu yi wannan gumurzun. Ku sani akwai sababin hanyoyi danayi tunani akai wajen tunkara waxan nan zaqaquran mayaqan na birnin nan ina mai tabbatar muku idan har kuka dage kuka karvi horon da zan baku tabbas za mu samu nasara akan su dan haka ina son ko wanen ku ya zauna cikin shirin fara karva horo a yau idan dare ya raba” koda ya zo 59 DAN BAIWA nan a cikin zancen sa sai shugaban dakarun ya kalli sauran su takwas xin sannan ya dubi Marhat yace. “Ya shugabana komai tsanani da irin wahalar da zaka bamu zamu jure koda kuwa za mu rasa rayukan mu sabida wannan ne kaxai abinda za mu yi mu ceto iyalinmu daga sarki mazwan kuma mu kwato ‘yancin talakawan qasar tamu daga hannun azzalumin sarki. Amman ni abinda nake shakka kai ta yaya zaka iya yaren su a cikin kwana bakwai alhalin yaren nasu yana da wahala? Su kuma gashi sun iya namu yaren”. Sa’adda sarkin yaqi marhat ya ji wannan batun sai ya buxe baki da nufin bashi amsa amma sai ga wata kuyanga ta shigo cikin masaukin nasu xauke da wani abu a qunshe a cikin mayafi, kuyangar ta zube qasa a gaban marhat ta kwashi gaisuwa sannan tace. “Ya kai sarkin yaqin birnin Hindu ina son na yi magana da kai a sirance” Cikin mamaki marhat ya dubi kuyangar yace. “Wacece ke kuma wane ya aiko ki zuwa gare ni?” Kuyangar tace. “Duk bazan iya baka wannan amsar ba face mun kaxaita” Kawai sai marhat ya dubi gaba xaya dakarun nasa kawai sai suka miqe tsaye suka fice daga cikin xakin fitarsu ked a wuya sai kuyangar ta miqawa marhat wannan abun dake hannunta ta ce, “Gimbiya Hamrita ce ta aikota ni na kawo maka wannan saqon,littafi ne wanda babu komai a cikinsa face dukkan kalmomin yarenmu waxanda aka fassara su cikin yaren ku na Hindu, wannan littafin na sarki ne kuma a sirrance Gimbiya tasa aka sato mata shi aka kawo maka domin ka sami damar iya yarenmu a cikin kwanakin nan bakwai. Gimbiya tace na gaya maka cewa kada ka kuskura ka bari wani yaga wannan littafin a hannunka” Koda jin wannan batun sai Marhat ya dubi kuyangar cikin alamun tsoro yace. “To yanzu idan sarki ya duba baiga littafin nasa ba fa?” Kuyangar tayi murmushi tace. ‘Kada ka damu ya shugabana tuni Gimbiya ta xauki tsatstsauran mataki aka hakan domin tasa Bokanta ya qirqiri wani littafin irin wannan sak an ajiye shi a inda

Chapter 5 of 7