zuwa garesa..
Wani irin sanyin daɗi taji acikin zuciyarta lokacin da taji kalamansa, babu musu ta ƙarasa garesa haɗe faɗawa cikin ƙirjinsa.
Kansa yaɗaura akan wuyanta haɗe da sanya harshensa yasoma yawo dashi yana lashe fatar wuyanta. Hanunsa ya ɗaura adai dai kan hips ɗinta, cike da zolaya yace.
"Barin taɓa naji ko ciko akayi, anaso a yaudareni"
Dariya ne yakamata. Cewa tayi
"Allah ya sauwaƙe inyi cikon hips, taɓa da kyau kaji hips ɗina ne da Allah yaban bawai soso ba"
Shima dariya yayi haɗe da sake matseta acikin jikinsa.
"Nasani to ko kema kina ɗaya daga cikin mata masuyin cikon hips ɗin tunda ai naga mata sunayi sosai"
Da sauri ta ɗago ta kallesa lokaci guda ta ɓata fuska.
"Wato mata kake kallo sosai idan kafita ko? harkasan ana cikon hips, hmmm thank you" tafaɗi haka tana me ƙoƙarin zare jikinta daga nashi..
Da sauri yasake matseta ajikinsa haɗe da tausasa muryarsa.
"Tuba nake madam, amma nisam mata basa gabana, inadake mezanyi da wata kuma daban, ke kaɗai ce kinkuma isheni, amma kinsan ba abun mamaki bane dan nasan hakan, saboda yanzu hakan ya yawaita sosai, wasu mata basa haƙuri da surar da Allah yayi musu, dole wai sai sunyi ciko, inakaranta labarai, ina kuma gani a Instagram, amma kema kinsan baruwana da duk wata mace ina da me daɗina mezanyi da wata me ɗaci!" yafaɗi haka cike dason shagwaɓata.
Aikuwa take ta hau dariya sosai taji daɗin kalamansa, amma kalman me ɗacin nan yabata dariya sosai, ko wace macece me ɗaci oho.
(Please maza kuna faɗawa matayenku kalamai masu daɗi, koda ita ɗin bata da wani kyau, ka hure mata kunne kace ai ita kyakkyawace, wallahi zataji daɗi sosai, kai inda halima kadinga ƙiranta da sunan me daɗi🤣🙈wallahi yanzun sai gaka ranta yayi fari ƙal, kuma always zakaga tana cikin farinciki, wayyo wayaga anƙira su O'O da sunan me daɗi, ai nasan sai sunkusa sumewa saboda daɗi😂😂😂)
Zama sukayi akan kujera haɗe da jawota ya ɗaurata akan cinyarsa, kansa yacusa acikin ƙirjinta, bayan ya ɓalle aninayen dake jere agaban rigarta, sosai ƙamshin dake fitowa acikin ƙirjinta yake yi masa daɗi, yanason ƙamshinta, domin kuwa yana sa masa nutsuwa sosai.
Lumshe idanunta tayi, tana mejin daɗin kissing ɗinta da yakeyi a ƙirjinta, hanunta ta sanya acikin gashin kansa tana yamutsawa a hankali. Ƙaran wayarsane yakaraɗe musu kunnuwansu, akasalance Dr.Sadeeq ya jawo wayartasa batare daya duba wanda ke ƙirannasa ba ya kara wayar akan kunnensa. Waro manyan manyan idanunsa waje yayi haɗe da cewa
"Dagaske kake?"
Banji me wanda yaƙirasa a wayar ya faɗa masa ba saiji nayi kawai yace
"Okay ganinan fitowa."
Kallonsa Zahrah tayi, tanameson jin ƙarin bayani daga bakinsa.
"Lumshe mata idanunsa yayi haɗe da ɓuɗesu alokaci guda.
"Friends ɗinane sukamin surprise wai suna waje, banaje na shigo dasu, please mintina kisanja wannan kayan kinji, ina kishinki sosai banason kowa yakallemin ke!" yaƙare maganar yana wani lumshe idanu, domin kuwa cike yake da shauƙinta.
Murmushinta me kyau tayi masa haɗe da tashi daga kan cinyarsa tana cewa.
"Yanzu kuwa zan sanja kayan."
Ɗaki ta wuce shikuma yayi waje don shigo da abokansa.
Zama tayi akan gado bayan ta sanja shigarta zuwa riga da sket na material marar nauyi takuma yane jikinta da mayafi, tanajin hayaniyansu acikin falon.
"Maza kenan wai nan su fa taɗi suke, amma kuma yawancin zancen nasu kama yake da musu" tafaɗi haka acikin zuciyarta. Bata ida zancen zucin da take ba, Dr.Sadeeq ya shigo cikin ɗakin.
Hanunta yakamo haɗe da kai mata sumbata a goshinta.
"Ko wani irin kaya kika sanya sai sunyi miki kyau, kyau ajininki yake ƴan mata na!" yafaɗi haka yana me ƙare mata kallo.
"Ƴan mata kuma?" ta tambayeshi tana ɗan murmushi.
"Eh mana ƴan matace ke a wajena ae har gobe, kuma ke sabuwace a wajena, tunda har yanzu bangama lashe zuma na ba" yafaɗi haka yana me kashe mata idanunsa ɗaya.
Kunyansane ya kamata, amma babu yanda ta iya shidai duk irin kalamansa kenan.
"Ki kawowa baƙinmu drinks kinji"
"To" Kawai tacemai.
A tare suka fita ita tayi hanyar kitchine shikuma yayi cikin falon..
Hanunta ɗauke da wani ɗan madaidaicin trey wanda ke ɗauke da kayan drinks da kuma ƴan madaidaitan glass cups tafito daga cikin kitchine ɗin, kanta aƙasa tanufo cikin falon saida takawo cikin falon kafun ta ɗago kanta fuskarta ɗauke da ɗan murmushi, wani irin bugawa taji zuciyarta tayi, lokaci guda idanunsu ya sauƙa acikin na juna, take ta saki trey ɗin dake hanunta yafaɗi ƙasa, ƙaran faɗuwarsa yajawo hankalin gaba ɗaya waƴanda suke cikin falon......
*(😳Waye Zahrah tagani🙆♀ badai Zaid bane yabiyota har cikin gida? kai ina ai Dr.Sadeeq yasan Zaid bazai barshi yashigomasa cikin gida ba, to waye ne wai??? 😂 kutaimaka kufaɗamin waye, bazan iya jiran next page ba😂😂)*
*(Kuyi haƙuri dan Allah jiya banyi muku update ba🙏🏻)*
*Vote and Comment please my lovely fans🙏🏻*
*4/February/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 106*
Da sauri Dr.Sadeeq yataso ya taho gareta, durƙusawa yayi yashiga tayata tattare wajen, saboda har wasu daga cikin cups ɗin dake kan tray ɗin sun face. Bisa tsautsayi ta zo ɗaukan wani fasashshen cup kwalba ya caketa a ƴar yatsar hanunta, take ta saki wani ɗan ƙaramin ƙara, cike da kulawa Dr.Sadeeq yace.
"I'am sorry kibi a hankali, muga hanun yayi jini ne?" yaƙare maganar yana me kama hanunta wanda kwalban yasoketa.
Murmushin ƙarfin hali tayi haɗe da cewa
"Yayi jini amma baso sai ba" hanunta Dr.Sadeeq yakama yashiga hura mata iskan bakinsa ahankali, yama manta da cewa basu kaɗai bane a cikin falon.
"Sannu amaryarmu, munsa kin yanke da ƙwalba ko, i'am really sorry" wani daga cikin abokan Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana ɗan murmushi.
Murmushi itama ta ƙaƙalo haɗe
da girgiza kanta, alamar
"bakomai"
"Tashi ki gaishesu sama sama ae duk sune silar jin ciwonki" Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana me miƙar da ita tsaye.
Ɗan matsawa tayi wajen da suke zaune tashiga gaidasu cikin sassanyar murya, amma bata yarda ta kalli inda yake ba, shima kallo ɗaya yayi mata ya sadda kansa ƙasa, "Itaɗince dai duk da taƙara kyau hakan baihanasa ganeta ba" yafaɗi haka acikin zuciyarsa, zuciyarsa ne ke ingizasa daya ɗaga idanunsa ya kalleta, amma kuma yaƙi bin umarnin zuciyartasa saboda yasan hakan baidace ba.
Dr.Sadeeq dakansa yakawo musu wani drinks ɗin ita kuwa ta wuce ɗakinta..
Zama tayi akan gado haɗe da sauƙe wata irin ajiyar zuciya me ƙarfi, bazata taɓa manta wannan fuskarba, tabbas shine.
"To meya kawo JABEER gidanta kuma? kodai shima abokin doctor ɗin ne?"
tayi mawa kanta duka wa ƴannan tambayoyin, ganin da tayi cewa tunani bazai fishsheta bane, yasa ta miƙe ta ɗauko ɗan ƙaramin Al'Qur'ani'n ta tashiga karantawa a hankali...
Yanashigowa cikin ɗakin yajingina bayansa da jikin ƙofa haɗe da sauƙe ajiyar zuciya.
Kallonsa tayi haɗe da ɗan sakin murmushi.
"Yadai sai kace wanda yayi gudu?"
"laifine idan nayi gudu dan nazo naga matata?" shima yatambayeta yana me tsareta da idanunsa.
"A'a, amma ae abun bana gudu bane, tunda dai batashi sama zanyi ba inanan tare dakai" tafaɗi haka tana me gyara zamanta.
Takowa yayi yaƙaraso gareta, zama yayi gab da ita haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta.
"Ya hanun naki?" yatambaya yana me ƙoƙarin kamo hanun nata wanda taji ciwo dan ya duba.
"Da sauƙi bayama min zafi sosai"
Iskan bakinsa ya hura ahanun kafun yaɗago ya kalleta.
"Amma nayi mamaki ƙwarai da abun daya faru ɗazu, ko dai tuntuɓe kikaji ne?"
Da sauri ta shiga kaɗa kanta. "Bankula da gabana bane alokacin danake tafiya shine kawai na buge da kujera" batasan sanda ta mulmulo wannan ƙaryan ta rantaɓa masa ba.
Kansa ya jinjina haɗe da sanya hanunsa ya rungumota zuwa jikinsa.
"Nagodewa Allah ma dayasa bakece da kanki kika faɗi ba, tray ne kawai ya faɗi, da bansan inda zansa kaina ba" yafaɗi haka yana me shafa gashin kanta da hanunsa.
Ɗan shirune yashiga tsakaninsu kowannensu da abunda yake saƙawa acikin ransa, tabbas bazata iya haƙura ba sai ta tambayeshi waye Jabeer agareshi, to amma tace masa me? tace masa me ya haɗasa da Jabeer tsohon saurayinta ko kuma me? bari dai tayi masa wani wayon, tafaɗi haka acikin ranta...
Ɗan sake gyara zamanta tayi haɗe da cewa. "Amm wai duka waƴannan abokanka ne?"
Murmushi yayi batare daya ɗago ya kalleta ba yace "Eh"
Kanta ta jinjina haɗe da sake cewa "Dukansu fa nake nufi"
Murmushi yakumayi saidai a wannan karon ya ɗago idanunsa ya kalleta.
"Eh dukansu abokaina ne, meya faru?" yatambayeta yana me tsareta da idanunsa..
Murmushi ta ƙaƙalo haɗe da cewa
"Babu ko mai kawai dai naga sunyi yawa ne, kuma naga wasu daga cikinsu banga fuskokinsu a wajen bikinmu ba shiyasa"
"Ae mu maza ba irinku bane munfiku yawan jama'a, wasu daga cikinsu basu samu daman zuwa bikinmu ba shiyasa bakisansu ba, kamar Jabeer baisamu halattaba saboda baya Nigeria yana Polland yana karatu, kuma baijima da dawowa ba, sauran kuma wani uzururruka ne suka hanasu zuwa, kinsan maza da sabgogi" yafaɗi haka yana me sake kwanciya acikin jikinta.
Yanzu tasamu amsar da takesonji cikin sauƙi, kenan dama Jabeer baya Nigeria ne shiyasa bainemeta ba, da sauri ta yi watsi da tunaninsa haɗe da ƙoƙarin zame Jikinta daga cikin nasa jikin.
Ƙara rungumeta yayi batare daya bata daman tashi ba, kallon cikin ƙwayar idanun juna suka shigayi, kallon tsananin SO Dr.Sadeeq keyi mata, yayinda ita kuma nakasa fassara wani irin kallo takeyi masa, na ƙauna nane ko na SO oho, Lumshe idanunsa yayi haɗe da buɗesu alokaci guda, yanayin yanda taga idanun nasa sun mareraice shiyasanya taji tsikar jikinta ya tashi, aduk sanda ta kalli cikin idanunsa takanji wani abu na ratsa har cikin ɓargonta, hakanne ma yasa bata ɗaukan lokaci me tsawo tana iya kallon cikin idanunsa, sosai idanunsa keyi mata kyau.
"Baby bacci nakeji!"
yafaɗi haka cikin murya me sanyi, yana me sake lumshe idanunsa.
"Ɓacci a wannan lokacin? Yanzu fa lokacin sallan isha ne"
ta faɗi haka cike da mamakinsa, tasan dai shiba mutum ne dayake da saurin bacci ba.
Hanu yasa yaɗan murza idanunsa, kansa kawai ya kaɗa mata batare dayace da ita komaiba yakoma jikinta ya kwanta. Yana lumshe idanunsa ladanin masallacin kusa da gidansu yasoma kwaɗa ƙiran sallah'n Isha. Jiki babu ƙwari haka yayi alwala yawuce masallaci..
Koda ta idar da sallah batayi yunƙurin tashi akan sallayan ba, zama tayi tana me rero karatun Al'Qur'ani ahankali.
Yana shigowa ta rufe Al'Qur'ani'n domin dama takai ƙarshen suran da take karantawa.
Direct bathroom ya wuce, tanajin ƙaran ruwa tasan wanka ƴakeyi.. Bawani jimawa sosai yafito daga shi sai towel ɗaure aƙugunsa, kallo ɗaya tayi masa ta ɗauƙe kanta, har yau bata iya jure ganinsa a haka, tashi itama tayi ta wuce bathroom ɗin donyin wanka.
Dogon wandon jeans kawai ya sanya ajikinsa haɗe da feshe jikinsa da turarensa me daɗin ƙamshi.. Kwanciya yayi lamo agadon haɗe da lumshe kyawawan idanunsa.
daga ita sai wani ɗanƙaramin towel tafito ɗaure ajikinta, yanzu kam bata wani jin kunyarsa sosai, tana iya fitowa gabansa a haka, sai dai idan taga ya kafeta da idanu, sai taji gaba ɗaya tayi wani irin da ita. Kallonta yayi yakuma sake lumshe idanunsa, yayi imani idan yaci gaba da kallon wannan haɗaɗɗiyar surar tata zata iya zautar dashi.
Turare kawai ta shafa ajikinta, ko sleeping dress batasanya ba, yau kuma da towel takeson kwana, kashe musu wutan ɗakin tayi ta kunna musu na bacci, wanda bashida haske sosai.
A maimakon tanufi gefensa ta kwanta, sai ji yayi ta haye kansa.
"Wayyo mama lutiya zata karyani!" yafaɗi haka aɗan shagwaɓe.
Sake sakar masa duka nauyinta tayi akansa, haɗe da cusa kanta cikin wuyansa.
"Kai nauyinka baisa na karye ba sai nine zan karyaka, ko kamanta kafini nauyi" taƙare maganar tana me manna masa wani irin hot kiss akan wuyansa.
Lumshe idanunsa yayi sosai yaji kiss ɗinnata ya ratsa shi.
"Wai yaushe kika zama haka ne princess?" yatambayeta, don harga Allah kwana biyun nan yana mamakinta.
Cikin rashin fahimtar maganan nasa tace "Bangane ba"
"Naga ne kindaina jin kunyana, sannan kuma nima da nake da kunyan nema kike ki lalatani ki maidani marar kunya"
Cizo takaimasa akan ƙirjinsa, wanda yasanya sa sakin wata ƴar ƙara.
Yana dariya yace
"To ƙarya nayi ai gaskiya nafaɗa, yanzu bakyajin kunyana ko kaɗan, har kaya kike cirewa a gabana..."
Wani cizon takuma kaimasa batare da ta bari yaƙarisa abunda yakeson faɗa ba, da sauri yatureta takoma ƙasansa shikuma yazama yana samanta, yayi mata rumfa da kirjinsa, duka hannayenta yakama yariƙe acikin nasa.
Cikin dariya ta soma ƙoƙarin ƙwace kanta daga jikinsa don talura cizon da tamai yakeson rama wa.
"Dan Allah kayi haƙuri bazan ƙaraɓa!" tafaɗi haka aɗan tsorace dan ta lura dagaske cizonta zaiyi.
"Ae babu maganar haƙuri yarinya, aƙirji kika cijeni, nima kuma dan haka aƙirjinki zan cijeki" yafaɗi haka yana me warware towel ɗin dake jikinta.
Cikin dariyan data kasa hanashi fitowa tashiga yi masa magiya amma yace sam shi sai ya rama.
Yana ɗaura bakinsa akan ƙirjinta, tayi shiru lokaci guda ta shiga sauƙe ajiyar zuciya akai akai, harwani lumshe idanunta take tsabar daɗin abun da yakeyi mata da takeji, shikuwa dagangan yayi mata haka so yake ya tsokalota sai yayi mata wayo yayi baccinsa, hanunta tasanya ta ɗago kansa, wani irin kallon tayi masa wanda ya rikirkitasa, bakinsu ta haɗe waje ɗaya, atare suka soma sucking lips ɗin juna, shida yake shirin mata wayo sai gashi ya susuce alokaci ɗaya, har yazo yafita ɓuƙata..... Bargo yaja ya rufe musu duka jikinsu, yana kwance akanta bacci me daɗi ya ɗaukesu.....
*****
*_ZAID_*
Tunda aka sallamosu daga asibiti baice da kowa ƙala ba, haushin kowa yakeji, tuƙuƙin baƙin ciki zuciyarsa keyi masa, ji yake yatsani kowa, bayamaso wani yashigo cikin lamarinsa..
Zaune yake a cikin falonsa, dagashi sai 3 guater jeans ko riga baidashi duk da kuwa irin sanyin da ake busawa a gari amma shi haka yake zaune a tuɓe, bawai kuma don bayajin sanyinba taurin kai dana zuciya ne kawai irin nasa ya hanasa suturta jikinsa.
Ƙafansa nakan rug yayinda kansa ke kalllon sama ya lumshe duka idanunsa, sake muskutawa yayi akaro na barkatai, haɗe kuma da ƙara ƙanƙame idanunsa da suke a lumshe, waishi adole so yake yayakice tunanin Zahrah acikin zuciyarsa, amma duk yanda yaso cire tunanin nata acikin ransa ya kasa, hanu yasa ya ɗan bugi kansa da ƙarfi, dai dai lokacin Afrah tafito daga cikin ɗaki daga ita sai wata ƴar ƙaramar riga dake sanye ajikinta, ko guiwarta rigan bata wuce ba.
Wani irin ƙamshin turaren dayaji acikin hancinsa ne yasanya sa buɗe idanunsa, ya watsa su akanta, kallonta yashigayi daga sama har ƙasa. "gatanan dai kamar wata ƴar kaza amma shegiya sai fitinan tsiya" yafaɗi haka acikin zuciyarsa, saboda ya lura kanta yana rawa, nema take ta shigarmai rayuwa taƙarfin tsiya, kuma zaiyi maganinta ne.
Afrah kuwa zuciyartane tashiga dukan uku uku, tsoronsa ne yasake shiganta bama kamar yanda taga idanunsa sun juye sunyi jajur dasu, harta juya zata koma ɗaki, saikuma ta tuno da shawarar da ƙawarta Asma ta bata, Asma tace mata " Zaid ɗan duniya ne yanason mata sosai, saboda haka tayi duk yanda zatayi ta shawo kansa ta hanyar nuna masa surarta a fili, idan ta nuna masa bata da kunya zasu dai dai ta" tunowa da waƴannan kalaman na Asma yasa Afra taji tasamu ƙwarin guiwa.. Sanja takunta tayi zuwa wani salo da ban, direct wajen dayake kishingiɗe ta nufa tana me motsa kowani gaɓa dake jikinta.
Bai taɓa yin zato ba saiji yayi Afra tafaɗo cikin jikinsa kamar wacce aka jefo, baikai ga buɗe idanunsa ba yaji ta saki wani irin munafukin ƙara..
"Wayyo Allah ƙafa ta honey kataimakeni na karya ƙafa ta" abun da Afrah ke faɗa kenan cikin iyayi.
Wani irin kallon takaici Zaid keyi mata, waishi zata gwadawa bariki, tafaɗo kansa da gangan sannan kuma tana yi masa ihun banza wai yataimaketa.
Da sauri yasake maida kallonsa gareta alokacin da zuciyarsa ta ƙitsa masa wani abu akanta.
"Tabbas hakanne ma, sai yanzu yasake lura da ita, amma ba ya gwadata ya gani" yafaɗi haka acikin zuciyarsa..
Da ƙyar ya iya buɗe bakinsa yaƙira sunanta "Afrah"
Dasauri Afrah dake yashe aƙasa tana kukan ƙarya ta ɗago kanta tana kallonsa jin da tayi yaƙira sunanta. "Kodai Target ɗina yafara aiki ne?" ta tambayi kanta .
"Ba ƙiranki nake ba da bazaki amsa minba!" yafaɗa murya aɗan kausashe.
"Kayi haƙuri honey ƙafa ta ce kemin zafi shiyasa" tafaɗi haka cikin yanayi na shagwaɓa tana wani yayyarfe hannu, ita adole so take ya faɗa cikin tarkonta.
Cike da tsananin takaicin ƙiransa da sunan honey da takeyi yasanyasa rumtse idanunsa da ƙarfi, ji yake kamar yaje ya shaƙeta bazai saketaba harsai yaga bata numfashi, amma akwai abun da yakeson ganowa a tattare da ita dolensa saiya daure.
"Zo muga me yasamu ƙafartaki"
Jiki na rawa Afrah ta matso garesa dama haka takeso yace, tana matuƙar so taganta akusa dashi, haɗa jiki dashi kuma shine burinta batun yau ba.
Hanu yasa ya kama ƙafarta ta, a hankali yashiga shafawa cike da wani irin salo, wayyo Allah Afrah dama haka takeso, ita kanta batasan sanda ta lumshe idanunta ba, wani irin daɗi takeji acikin jikinta, "Gaskiya shawarar Asma tayi aiki" tafaɗi haka acikin zuciyarta, cigaba yayi da shafa ƙafannata ahankali harzuwa wajen cinyoyinta, tuni ta narkemasa ajiki taƙara kusanto da kanta garesa, hanu tasanya akan faffaɗan ƙirjinsa tashiga shafawa ahankali, duk iskanci irin na Zaid saida ya tsaya yana kallonta, tabbas yanzu ya gano abun dayakeson ganowa atattare da ita, wani irin baƙinciki da ɓacin raine suka tokare masa maƙoshinsa.
"Hakan da Afrah keyi masa alamace dake nuna ita babaƙuwa bace a harkan tasan namiji kenan kome?" tambayar da yake tayiwa kansa kenan, shiba ƙaramin ɗan iska bane, yanda Afrah keyi masa alama ne dake nuna cewa tasaba irin haka da wasu mazan. "Kenan ita ƴar iska ce?" still yakuma tambayar kansa. Hanunsa yasanya ya damƙi gashinta haɗe da miƙar da ita tsaye, da fari ta ɗan tsorita amma ganin irin kallon dayakeyi mata yasa taɗanji sanyi acikin ranta, ganin sunnufi hanyar ɗakinsa yasa ta shiga sakin murmushi, daɗi taƙeji yau Allah zai cika mata burinta..
Suna shiga cikin ɗakin yasanya hanunsa da ƙarfi ya yaga ƴar fingilan rigar dake jikinta, take komai nata ya bayyana, hankaɗata yayi kan gado haɗe da soma yunƙurin zare belt ɗin dake jikin wandonsa,, idanu Afrah ta zaro waje amatuƙar tsorace, bata taɓa tsammanin haka daga garesaba ta ɗauka kasheta zaiyi da soyayya amma meyake shirin yi matane haka "Dukanta zaiyi ne ko kuma turmusheta zaiyi batare dayatsaya sunɗanyin romancing juna ba?" waƴannan tambayoyin sune suka cika zuciyarta fal...
(Me Zaid yakeyi hakane🤔 hahhhh da'alama dai yau amarci za'aci agidan Baba Zaid, team Zaid karkuyi nisa saboda nan gaba kaɗan Zaid zai buƙaci taimakonku, yayinda komai ya wakana tsakaninsa da amarya, inaga dole saikun shigo cikin lamarin😂)
*(Thank you my wattpadfans💋 Comment da vote ɗinku suna ƙaramin ƙarfin guiwa sosai, SON SO nake muku)*
*Vote and Comment please😘*
*6/February/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motive the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 107*
Tana ganin yagama zare belt ɗin jikinshi, tasoma ƙyaf ƙyaf ta idanu, kamar wacce aka kamata tana sata, tsoronsa ne ƙarara, ya bayyana akan fuskarta, ganin sa a haka tun farko, ya isa ruɗata, amma kuma dayake bariki ne a gabanta, ya sanya bata fuskanci hakan ba, sai yanzune taga, gaba ɗaya yacika mata idanu.
Cike da tsantsar rashin mutumci irin nasa, yasanya hanunsa ya jawo ƙafarta, zama yayi akan gadon, haɗe da sanya hanunsa akan fuskarta, ya matse mata baki, idanunsa yaɗaura akan ƙirjinta, wani irin murmushi yasake, haɗe da cije laɓɓansa, wai wannan tatsitsiyar yarinyarne, takeson ɗaukar hankalinsa, yaga waƴanda suka fita komai, bai kuma ji wani abu akan su ba, balle kuma ita ƙaramar alhaki, yanaji ajikinsa cewa. "A yanzu ba ayi wata mace wacce zata ɗau hankalinsa sama da Zahrah ba"
Hanunsa yakai kan wuyanta, yashiga shafawa a hankali, tsuru Afrah tayi tana kalllonsa, karo na farko a rayuwarta, da taji wani irin mugun fargaba ya daki zuciyarta, akan abun da ta aikata, "Me zata ce masa yanzu idan har yanemi haƙƙinsa awajenta?" take idanunta suka kawo ruwa taɗago ta kallesa.
Ko kallonta baiyi ba, ya ci gaba da shafa wuyanta, lumshe idanunta tayi, a zahirin gaskiya tana amsar saƙonsa, amma kuma acikin zuciyarta, tsoro ne yayi tasiri.
Ɗayan hanunsa yasanya ya yakice duk wani abu na sutura dayayi saura ajikinta.
Kamar wata mutum mutumi haka Afrah ta tsaya tana kallonsa.
"Tashiga ukunta idan wannan ingarman namijin ya haiƙe mata, batare da ya tsaya yayi romancing ɗinta ba"
ta faɗi haka acikin zuciyarta, bata ida tunanin nata ba, taga yayi off na wutan ɗakin..
Kwanciya yayi akanta, haɗe da sake mata gaba ɗaya nauyinsa, da ƙyar take iya fidda numfashi, sosai yayi mata nauyi, idan ba mugunta bama, taya zai kwanta akanta haka, aiko katifa ce saita lotse balle kuma ita.
Cikin zafi zafi yashiga kissing lips ɗinta. Yi yake kamar zai cijeta, dagani kai kasan muguntane ke cinsa, baƙaramin zafi kuwa hakan keyi mata ba, gaba ɗaya ya taune mata baki, lokacin daya ɗaura hanunsa akan breast ɗinta kuwa, saida tasaki kukan wahala, komai bayayi mata shi cikin nutsuwa, duk wani abu da ƙarfi yake yi mata, abu yake kamar me huce haushi.
Ganin da yayi zata cika masa kunne da kuka ne, yasanyasa sanya hanunsa ya matse mata baki. Yunƙurin ƙwace kanta takeyi amma ina bazata iya ba riƙon Zaid ba wasa ba.
*****
Wani juyawa kansa keyi masa lokaci ɗaya ya firgice, idanunsa ne suka kaɗa sukayi jajur dasu, yayinda jikinsa ke ɓari kamar wani mazari, iya ƙololuwar ɓacin rai a yau Zaid yashigesa, da ƙyar ya iya laluɓawa, ya sauƙa akan gadon, jefa ƙafafunsa kawai yake batare daya koda kalli gabansa bane, yana shiga cikin bathroom ya banko ƙofar da ƙarfin gaske.
Jikin Afrah ne ya ɗauki tsuma, take ta fashe da wani irin kuka me taɓa zuciya.
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 38 Chapter of 47