Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya zuba musu, domin kwata kwata baijin auren a jikinsa, da za'afasa auren to dazai fi kowa murna, saboda Zahrah yakeso Zahrah ce muradinsa, amma kuma haryanzu yakasa samun wani gamsashshiyar amsa daga gareta. Ƙarfe 3 dai dai jirginsu ya sauƙa a babban airport ɗin dake cikin garin Abuja, motoci ne iri da kala har guda shida suka zo tarbansa, ciki kuwa hadda Dad ɗinsa, a hankali yake sauƙowa daga cikin matakalar jirgin sanyen yake da kayan sanyi hadda hula, yayinda fuskarsa ke ɗauƙe da wani haɗaɗɗen baƙin glass na maza, sosai yaƙara kyau da fari, kallo ɗaya zakai masa katabbatar da cewa yakai cikekke kuma gwarzon namiji, a gaskia yana da kyau da kuma kwarjini, uwa uba kuɗaɗe sun samu mazauni a jikinsa. Bakowacce mace bace zatayi tozali da haɗaɗɗen namiji kamar Zaid, kuma takau da idanunta ba, saboda Zaid yahaɗa duk wani abu da kowacce mace zata so awajen ɗa namiji, shidai matsalan sa ɗaya munanan halaiyansa. Yanda yake tafiya cike da izza shiyafi komai ɗaukar hankali, dakuma jan hankali zuwa garesa. Cike da farinciki Alhaji Ma'aruf yarungume ɗa'nnasa, duk da cewa babu wani shaƙuwa me ƙarfi a tsakaninsu amma yana matuƙar son Zaid. Mota ɗaya suka shiga shida Dad ɗinsa, yayinda guard ɗinsu suka mara musu baya a cikin sauran motocin. Kwanciya yayi lamo ajikin kujeran motar haɗe da lumshe idanunsa, wani irin sanyi yakeji acikin zuciyarsa, koda wasa baitaɓa tunanin haka zai kasance dashi ba, kamarshi Zaid ace tunanin mace yahanasa sukuni harsaida yabaro duka abun da yakeyi ya dawo zuwa gareta, amma zaiyi maganin abun a yau bawai sai gobe ba yake da buƙatar ganin sugar baby'nsa, sai dai kuma wannan lokacin bada wasa yazo ba... Zahrah ne keta kai kawo a tsakiyar ɗakinta, tabbas tayarda da duk wani shawara da zuciyarta ta bata, zuwa yanzu yakamata ace tayi abunda ya dace. Wayarta ne yasoma ƙara alamar shigowar ƙira, tana ɗaga wayar Dr Sadeeq yace "Gani na'iso ina ƙofar gida!" "To" tace haɗe da aje wayar, ajiyar zuciya ta sauƙe haɗi da cije lips ɗinta, dama ɗaya kawai take dashi kuma tabbas idan tarasa wannan daman to zaiyi mata wahala tasake samun wani daman. Hijib ɗinta ta sanya, koda tafito tsakar gida bata taradda Inna ba tana kuma da tabbacin cewa bama ta gidan. Zaune yake acikin motar tasa, dagani kasan cewa yana cikin damuwa, domin gaba ɗaya har rama tasoma bayyana a jikinsa. Murfin motar tabuɗe tashiga, bakinta ɗauke da sallama, amsa mata sallaman nata yayi haɗe da gyara zamansa yafuskance ta " Baki taɓa min irin wannan ƙiran ba, naƙosa naji wace maganace zaki faɗamin mai matuƙar mahimmanci haka" gaba ɗaya hankalinsa ya tattara zuwa gareta. "Dagaske kake Zaka aure ni?" Zahrah tajefo masa tambayar dabai taɓa zata ba balle tsammani. Kansa yashiga kaɗawa muryarsa har rawa take yace "Dagaske nake Zahrah, wallahi auren ki nakeso nayi, samunki a matsayin mata shine babban burina a yanzu." yafaɗi hakan da iya gaskiya'rsa "So na kakeyi kokuma tausayina?" Zahrah takuma jifansa da wata tambayar. "Sonki nake Zahrah, inamiki so mai tsanani, wlh inasonki da duka zuciyata!" Dr Sadeeq yabata amsa, cike da kulawa. "Nayarda na Amince Zan aureka, muyi zama na har abada!" Abun da yafito daga bakin Zahrah kenan bayan tagamajin amsar da take buƙata daga garesa, cikin tsananin mamaki Dr Sadeeq yashiga kallonta, jin sauƙar maganarta yayi tamkar daga sama, kodai kunnuwan sa basu jiye masa dakyau bane?.... (To fa readers Ga Baba Zaidu yashigo Gari, ga kuma Zahrah ta amince da auren Dr Sadeeq, gashi kuma ɓangaren gidansu Dr anatashirye shiryen bikin Dr da Salima, koya zata kaya 🤷‍♀, please kusani a addu'anku wlh cikina ke ciwo sosai😥 idan kunga typing eror kuyi haƙuri gaba ɗaya banda wata isashshen nutsuwa ne 😭) *10/December/2019* *Voted,Comment,and Share please.... Follow me on Wattpad @fatymasardauna* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *SHU'UMIN NAMIJI!!* *Written by* *Phatymasardauna* *Dedicated To My Brother KHABIER* *🌈Kainuwa Writers Association* '''{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & mitivate the mind of readers}''' *https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation* *WATTPAD* @fatymasardauna *Editing is not allowed📵* *(This page is Dedicated to you HAROUN UMAR (H Umar) admin of 📖✍️BENEFICIAL WRITERS ASSOCIATION, inajinjinamawa ƙoƙarinka ako da yaushe haroun, kuma inagodia a gareka marar iyaka.)* *CHAPTER 53 to 54* Kasa motsa koda laɓɓansa yayi balle har yakai ga furta wata kalman, "dagaske ne abun da kunnuwansa suka jiye masa kokuwa mafarki yake?" yafaɗi hakan a cikin zuciyarsa. "Kada kayi kokonto kokuma shakka, dagaske nake, na amince da aurenka, amma ina mai roƙon wata alfarma a gareka"...."Dan Allah kada ka wulaƙantani aduk yanda kasameni, kada kuma ka tozartani, nasan cewa tausayina yafi yawa acikin zuciyarka fiye da soyayya ta, saboda haka ina da tabbacin cewa ko gaba zaka iya sake samun wata mace,wacce itace zata kasance zaɓinka, kada haka yasa ka wulaƙantani dan Allah, kada kuma kacutar da rayuwata!" cikin sanyin murya ta ƙare maganarta ta, yayinda hawaye suka shiga fitowa daga cikin idanunta,suna sauƙa akan ƙuncinta. Jiyayi gaba ɗaya wani irin matsanancin farinciki ya lulluɓesa, gani yake tamkar wasa Zahrah take masa, amma kuma ba'abun mamaki bane, saboda babu abun da yagagari Allah. "Bansan ta'ina kokuma tayaya zan fara godemiki ba Zahrah, kin gusarmin da duk wata damuwa dake damuna, kinbani farinciki cikin ƴan mintuna ƙalilan, kiyarda dani Zahrah, inamiki Soyayyace ta gaskiya bawai, irin soyayyarnan tako oho ba, zan'iya sadaukar da duk wani abu nawa akanki Zahrah, soyayyar da nake miki, yasanya bana ganin laifi ko kuma aibun duk wani abun da kikamin, burina da fatana shine murayu tare dani dake amatsayin miji da mata, kuma aƙarƙashin inuwa ɗaya, Inasonki Zahrah, kuma namiki alƙawari komai wuya komai tsanani bazan taɓa gujemiki ba, ZANRAYU DAKE Zahrah!!" Dr Sadeeq yafaɗa cike da matsanancin farinciki, jiyake tamkar yajawo Zahrah jikinsa yabata kyakkyawan runguma. Kuka Zahrah ta fashe dashi, wanda batasan dalilin yinsaba, ita ta amincewa kanta cewa zata auri Dr Sadeeq amma saitakeji tamkar dole tayimawa kanta. Batayi zato ba saiji tayi Dr Sadeeq yajawota jikinsa haɗe da sanya hannayensa duka biyu ya rungumeta. "Inasonki Zahrah, kuma nayi maki alƙawarin bazantaɓa wulaƙanta ki ba har'abada, kidaina kuka kinji princess ɗina!" yaƙare maganar tasa cikin sigar lallashi. Daddaɗan ƙamshinsa shiyaso birkita mata tunani don haka tayi saurin janyewa daga jikinsa, tana mai yin ƙasa da kanta. Sam shikam ma yamanta da cewa hakan da yayi ba'abu bane mai kyau, gaba ɗaya murna yacika masa zuciya. "Uh sorry baby, gaba ɗaya kece kikamantar dani komai!!" Dr Sadeeq yafaɗi hakan yana mai dafe goshinsa. Ƙasa ƙasa Zahrah tayi murmushi haɗe da kawar da kanta gefe, hakanan taji wani irin nauyin Dr Sadeeq ɗin yaƙaru acikin zuciyarta, haka kuma yaƙara girma acikin idanunta. Wani irin kallo Dr Sadeeq yashiga yimawa Zahrah duk dacewa takau da kanta gefe, sai yanzu nema yake ƙara ganin haɗuwarta fiye da da, tabbas da Zahrah bata amince dashi ba to da ya tabka babban rashi, domin kuwa Zahrah tahaɗu, macece ita da kowanni Namiji zaiyi fatan mallaka. Sam batayi tunanin kallonta yake ba, don haka taɗan juyo dan itama ta saci kallonsa, aikuwa karab idanunsu suka sauƙa akan najuna, da sauri Zahrah tayi ƙasa da kanta haɗe da cusa fuskarta tsakan kanun cinyoyinta. Dariya Dr Sadeeq yayi cike da shauƙi haɗe da shafa sajen dake kwance akan fuskarsa. "Yaushe kika farajin kunyana? lallai zamu ɓata idan harkinajin kunyana!" ya faɗi hakan cike da zolaya. Ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba, haɗe da marairaice fuska cike da shagwaɓa tace "To bakaine kaketa kallo na ba, saikace baka sanni ba!" Lumshe idanunsa yayi haɗe da buɗesu a lokaci guda, irin wannan salon shagwaɓan ai saita sashi bacci batare da yashiryawa hakan ba,lol. "Ki faɗamin laifi ne don nakalli abar sona? saidai kiyi haƙuri amma kallonki yanzuma na fara, tunda kinamin kyau, kina kuma burgeni!" yanayin yanda yayi maganar abun burgewa ne, ga macen da tasan daɗin soyayya. "Nidai kada ka wani ce inada kyau, daɗin bakine kawai nasan kakemin!" still da yanayin shagwaɓa tayi maganan. Lumshe idanunsa yayi haɗe da fitar da iskan numfashi daga bakinsa, yanayin shagwaɓan Zahrah yafi komai burgesa a tattare da'ita, haka kuma sosai yake sauƙar masa da kasala. "Princess!!" yaƙira sunanta dawani irin murya mai taɓa zuciya. A hankali ta ɗago idanunta ta kallesa, batare da ta amsa masa ba, ganin idanunsa a rufe, yasanya taɗan tsaya ƙaremawa fuskarsa kallo. "Duk kallona ɗaya da zaki yi bazai tafi a banza ba, sai kin biya kuɗi, gwamma ma kisani!" Dr Sadeeq yafaɗi haka batare da ya buɗe idanunsa ba. Saurin ɗauke kanta tayi daga kallonsa haɗe da cewa "Niba kallonka nake ba" "Zaki iya rantsewa cewa bani kike kallo ba?" yaje fo mata tambayar da batayi zato ba. kanta tashiga girgizawa haɗe da cewa "Ai bankalleka sosai ba, kaɗan nakalleka!" Dariya Dr Sadeeq yasanya wanda harsaida dimple ɗinsa suka bayyana, yanzu yayarda cewa Zahrah yarinyace ƙarama, kuma zakayi saurin kamata idan tamaka laifi. Ƙoƙarin buɗe murfin motar Zahrah tasomayi, cikin mamaki Dr yace "ina zaki?" "Zankoma gida ne, dama magana zan faɗa ma, shiyasa na ƙiraka, kuma nafaɗa ma, inada karatu, gobe muna da test a makaranta" Zahrah tafaɗi hakan dai dai lokacin da ta gama sanya ƙafafunta waje. "Shikenan to My Princess kikulamin da kanki kinji, inasonki sosai!" Dr Sadeeq yafaɗa cike da kulawa. Wani irin muguwar kunyarsace takama Zahrah, bashiri ta wuce cikin gida tana mai rufe fuskanta da tafukan hanunta. Shima Dr ɗin murmushi yayi cike da jindaɗi, lallai idan ya auri Zahrah yakasance mutum mai sa'a, acikin satinnan insha Allah, zai sanarda ƙanin mahaifinsa azo a nemamasa auren Zahrah, a wajen Baffa. "Aurenka da Salima fa?" Wata zuciyar ta jefo masa wannan tambayar, wani irin bugawa yaji ƙirjinsa yayi, gaba ɗaya amincewa dashi da Zahrah tayi yasanyashi manta halin da yake ciki na batun auren sa da Salima. Jiyayi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, tabbas akwai ƙalubale a gabansa, domin kuwa yanada tabbacin cewa Hajiyarsa bazata taɓa sanja maganarta ba, gashi har ansoma shirye shiryen bikinsa da Salima, kuma shi a tsarinsa bai sha'awar auren mata biyu, Zahrah ita kaɗai ta'ishesa rayuwa, amma kuma tabbas yasan zai fuskanci matsaloli da yawa daga ƴan uwansa, matuƙar ya jajirce akan cewa Zahrah yakeso ba Salima ba, to amma dole zai jarraba sa'ansa, domin a gaskiya baijin cewa zai'iya haƙura da Zahrah. Cike da sanyin jiki yayimawa motar tasa key, haɗe da nausawa kan titi. Suna isa katafaren gidannasu, adai dai parking space motar tasu ta tsaya. Bawani jinkiri Zaid yabuɗe murfin motar yafito, batare da yatsaya sauraran Mahaifinnasa ba, yanufi ɓangarensa kai tsaye. Komai dake cikin ɓangaren nasa a gyare yake tsab, tamkar akwai wani wanda ke rayuwa a cikinsa, hakan kuma yasamo asaline da yawan gyara part ɗin da akeyi duk bayan kwana biyu, kasancewar Zaid mutum ne da bayason ƙazanta. Direct bedroom ɗinsa yanufa, yanashiga yasoma rage kayan dake jikinsa, rigan wanka irin na maza mai gashi gashi a jiki yasanya, haɗe da sanya badroom slippers a ƙafafunsa, kai tsaye wajen fridge ɗin dake aje cikin ɗakin yanufa, maltina can yaciro haɗe da ɓalle ɗan ƙarfen da aka rufe bakin can ɗin dashi, yakai bakinsa, tunda yakai maltina can ɗin nan bakinsa bai ɗauke ba harsaida yatabbatar da cewa bakomai ciki ya shanye, cikin dustbin ɗin dake aje a ɗakin ya jefa can ɗin. Bathroom ya wuce haɗe da sakarmawa kansa shower. Wanka yakeyi amma gaba ɗaya tunaninsa baya garesa, yanaga shugar baby'nsa, amatuƙar matse yake da sha'awarta, haryanajin bazai iya daurewa yakai zuwa wani ɗan lokaci mai tsawo batare da'ita ba. Bayan yafito a wanka yashiga shirya kansa cikin, haɗaɗɗun riga da wando masu kyau da tsadar gaske, gaskia komai na Zaid me kyau ne, domin kuwa kowani kaya yasanya saiya yi kyau, bakuma kayanne yake masa kyauba, shi ɗin kansa ne yake mawa kayan kyau,lol. Haɗaɗɗen takalminsa sau ciki ƙiran kamfanin Gucci yasanya, aƙafansa, bayan ya ɗaura tsadadden agogon nan na Rolex a hanunsa mai kyau da burgewa. Daddaɗan ƙamshi ne kawai ke fita daga jikin shi, ƙamshine mai wahalar mantawa. Black facing cap, yasanya akansa, domin kuwa yanayin garin ana ɗan busa sanyi, duk dakuwa cewa daga cikin sanyin yafito. Wayarsa yaɗauka haɗe da car key ɗinsa, kai tsaye yafice daga cikin ɗakinnasa. Ɓangaren Mom ɗinsa yanufa. Hajiya Safara'u ne tsaye a gaban ƙatoton teburin cin abinci, yayinda Alhaji Ma'aruf ke zaune tana serving ɗinsa, batasan da shigowarsa ba saiji tayi ya rungumeta ta baya haɗe da ɗaura kansa akan kafaɗarta, cike da soyayyar mahaifiyarta sa yace "Barka da gida Momy!" Cike da tsananin farinciki itama ta rungumesa haɗe da basa sumba a kan kumatunsa, "Barkanka da dawowa my son, ya gajiyar hanyar?" "Alhmdlh!" Zaid yafaɗa a taƙaice, bayan ya janye jikinsa daga na mahaifiyartasa. Ƙoƙarin juyawa yakeyi, Mom tace "Inakuma zaka my son ba abinci kazo ciba?" cike da kulawa ta tambayesa. Ɗan ɓata fuska Zaid yayi haɗe da cewa "Banajin yunwa Mom, idan nadawo zanci!" baijira jin maizasu ceba yasakai yafice daga cikin falon. Da kallo kawai Mom tabisa har yafice, fuskarta ɗauke da damuwa, itakam ta rasa wani irin haline da Zaid, sam ba'a iya gane gabansa da bayansa. "Miye abun shiga damuwa Hajiya Safara'u? zuwa yanzu yakamata ace duk wani hali na yaronnan Zaid kin gama saninsa!" Alhaji Ma'aruf yafaɗi hakan cike da nuna kulawa ga matar tasa. "Nasan halinsa Alhaji, amma kuma ace mutum shi baya taɓa sanjawa, ko da yaushe fa Zaid bayason zama a cikin mu, sannan kuma sam baya sakewa damu!" Mom tafaɗi hakan cike da damuwa. "Zauna muci abincin mu, aishi ba ƙaramin yaro bane, yasan me yakeyi!" Alhaji Ma'aruf yafaɗi hakan yana mai kama hanun Mom yazaunar da'ita a kusa dashi. Zaid kuwa yana fita daga ɓangaren mahaifiyartasa, kai tsaye wajen motarsa yanufa, koda driver yanemi da yabarsa ya tuƙasa, ɗaga masa hanu yayi alamar baya buƙata, shida kansa yayimawa motar key, ya harbata zuwa kan titi. Tafiya yake cikin nutsuwa yayinda airpiece ke saƙale a kunnuwansa, wayarsa ce tasoma ƙara alamar shigowar ƙira, ganin cewa babban manager'n company'nsa dake nan gida Nigeria ne ke ƙiransa yasanya shi ɗaga ƙiran. Banji mai Manager'n nasa yace masa ba, sai gani nayi ya'aje wayan, haɗe da buga dogon tsaki, lokaci ɗaya yakarkata akalar motar tasa zuwa wata hanya daban saɓanin hanayar daya nufa, wanda zai sadasa da unguwar su Zahrah. Dr Sadeeq kuwa yana barin unguwar su Zahrah kaitsaye gidansu yanufa, acewarsa gwamma yayi maganin matsalarsa tunkafun tayi nisa. Usaina mai aikin ɓangaren Hajiyarsa yasanya tane ma masa iso awajen Hajiyar tasa, domin kuwa bai isketa a falo ba. Da sallama yashiga cikin ɗakin Hajiyar tasa, fuskarta ɗauke da fari'a ta amsa masa sallaman da yakeyi. Zaune take akan gado, yayinda take duba wasu kayayyaki dake zube a gabanta. "Barka da huwatawa Hajiya!" yafaɗa cike da ladabi. "Yauwa barkanka, kamar kuwa kasan ina nemanka, wai me kake nufi da auren nan ne Sadeeq? har yanzufa banga kana wani cuku cuku ba, kayan lefe ma saini kabarmawa ɗawainiyar haɗasu, gashi kuma Salima tacemin tunda kaje sau ɗaya baka sake zuwa ba, mai ke damunka ne wai?" Hajiya tatambayesa cike da kulawa. Kansa yashiga sosawa haɗe da sake yin ƙasa da kansa, "Am...dama Am...." "Dakata banson wani kwana kwana, kafaɗi abunda zaka faɗa kai tsaye kawai" Hajiya ta katsesa daga kame kamen maganan dayake ƙoƙarin yi mata. "Hajiya kamar dai yanda na faɗamiki ne, wallahi Hajiya dagaske nake, yanzu nasamu wacce nakeso kuma idan harkin yarda aurenmu bazai wuce nan da Sati uku ba, kamar yanda kikeso!" yafaɗi hakan cike da ladabi. Sororo haka Hajiya ta tsaya tana kallonsa, "anya kuwa Sadeeq yana lafiya? " tatambayi kanta. "Inagadai bakasan mekake cewa ba Sadeeq, wato nikakeson watsamawa ƙasa a cikin idanu ko, ya yi maka kyau, to inaso kabuɗe kunnuwanka da kyau ka saurareni, wallahi ko da wasa kakuma zuwamin da irin wannan zancen saina ɓata maka rai, nagama baka duk wata dama dazan baka, bakuma zan sake baka wata daman ba, tashi kabani waje, tunda nalura kai baka da tunani!" Hajiya ta ƙare maganan cikin faɗa. Cikin rashin kuzari haɗe da sanyayewar guiwa Dr Sadeeq yamiƙe daga gaban mahaifiyartasa, haɗe da nufar ƙofar fita daga cikin ɗakin, Saida yakai ɓaƙin ƙofar fita ckafun yatsaya cak, haɗe da juyo da kallonsa ga Hajiyar tasa cikin murya mai rauni yace "Hajiya dan Allah.." "Fita kabani waje nace!!" Hajiya takuma faɗa cikin ɓacin rai tanamai yi masa nuni da ƙofar fita daga ɗakin... *(Readers nifa Hajiyannan tasoma ban haushi yasin🙄🤣)* *Kuyi manage da wannan ba lallai gobe nayi typing ba shiasa, namuku yau* *11/December/2019* *Voted, Comment, and Share please..... Follow me on Wattpad @fatymasardauna* *6:17 pm* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *SHU'UMIN NAMIJI !!* *Written By* *Phatymasardauna* *Dedicated To My Brother KHABIER* *🌈Kainuwa Writers Association* '''{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}''' *https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation* *WATTPAD* @fatymasardauna *Editing is not allowed📵* (Kuyi haƙuri shekaran jiya nayi mistake ɗin number 52 to 53 zansa, sainasaka 53 to 54🙏) *CHAPTER 55 to 56* Cikin sanyin jiki Dr Sadeeq yafita daga cikin ɗakin mahaifiyarta sa. Gaba ɗaya jiyayi zuciyarsa ta cika da ƙunci. Yana isa ɓangarensa ya zube akan ɗaya daga cikin kujerun falonnasa, "yanzu wazai je yasamu da wannan matsalar? tabbas yasan Hajiyarsa mutum ce mai kafiya, idan tace eh zai yi wuya ta dawo tace a'a" hanunsa yasanya cikin sumar dake kwance akansa haɗe da yamutsa ta, sunan Aunty Raliya ce yafaɗo masa arai, tabbas ita kaɗaice ƴar uwarsa da zai kai mata matsalansa har ma ta tayasa magancewa, sai dai kuma yanatunanin itama ra'ayinta ɗayane da Hajiya, amma yasan idan yayi mata kyakkyawan bayani zata fahimcesa, zumbur yamiƙe daga zaunen dayake. Ko bedroom baishiga ba yakuma ficewa daga cikin falon, mota ya koma, haɗe da kunnata, mai gadi ne ya wangale masa gate ɗin gidan yafice. Hajiya najin ƙarar ficewar motarsa daga cikin gidan ta sauƙe ajiyar zuciya. "Gaba ɗaya tunaninta ya kulle, batasan wani irin abu Sadeeq keshirin shigo mata dashi cikin gida ba, kusan sau uku kenan tana bashi dama, akan yafito da matar aure, amma dazaran lokacin da ta ibar masa yacika, sai ya farayi mata kame kame, yanzu da tagaji da sakarcinsa ta zaɓa masa mata, sai yake nema yawatsa mata ƙasa a idanu, bakuma zata lamunci hakanba. Direct Dr Sadeeq gidan Aunty Raliya yanufa, domin baida wata ƴar uwa da ta wuce ta a duniyar nan. Yanashiga gidan tunbai gama fitowa daga cikin motarsa ba, su Meenal da Affan ƴaƴan Aunty Raliya, suka rugo da gudu zuwa garesa, dama wasan ball suke a farfajiyan gidan nasu, hakan yasa duk wanda yashigo da kuma wanda zaifita zasu gansa. Rungumesu yayi a jikinsa, haɗe da shafa kawunansu, "Oyoyo babies ɗina, ashe girma yazo muku, har wasan ball kukeyi!" yafaɗi hakan cike da nishaɗi. "Eh Uncle ai harma nafita iyawa!" Affan yafaɗi haka cike da zumuɗi. "Ƙaryayake Uncle baifini iyawa ba" Meenal tafaɗi hakan tana mai kama ƙugu, alaman ƙarya Affan ɗin yakeyi. Murmushi kawai Dr yayi haɗe da sake shafa kansu, "kuyi wasa da kyau, idan nafito zan baku alewa!" yafaɗa yana mai nufar kofar da zata sadashi da babban falon gidan. Yayinda yabar su meenal sunata tsallen murna saboda yace zai basu alawa. Da sallama ɗauke a bakinsa yashiga cikin falon. Aunty Raliya dake zaune tana kallon tv, ta amsa amsa masa sallamar tasa, fuskarta ɗauke da fari'a, haɗe da yi masa iso. Ƙarasowa yayi yazauna akan kujera, haɗe da sauƙe ajiyar zuciya, gaba ɗaya a gajiye yakejinsa, domin tun safe yau baisamu nutsuwa ya huta ba. Aunty Raliya da kanta, ta jere masa kayan fruit da juice agabansa, cikin tsokana tace dashi "Ango kasha ƙamshi, duk gajiyar shirye shiryen bikinne haka?" Ɗan ɓata fuska yayi haɗe da ɗaukan apple ƙwaya ɗaya ya kai bakinsa. "Ango labari ya sauya salo" yafaɗi hakan bayan ya cinye gutsuren apple ɗin dake bakinsa. Cikin mamaki Aunty Raliya tace "bangane ba mekake nufi?" Ajiyar zuciya yasauƙe haɗe da gyara zamansa. "Akwai matsala Aunty!" yafaɗi hakan lokacin da gaba ɗaya yanayin fuskarsa ya sauya. "Matsala! wace irin matsala Uncle?" Aunty Raliya tatambaya cike da ɗaurewar kai. "Akwai wacce nakeso na aura, yarinyar tana matuƙar buƙatar taimakona, nayi ƙoƙarin na fahimtar da Hajiya hakan, amma taƙi saurarata, yanzu haka daga gida nake, nasoma yi mata bayani, tace natashi na bata waje, gaba ɗaya kaina yakulle bansan yazanyiba Aunty Raliya!" Ya faɗi haka cikin damuwa. Ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya Aunty Raliya ta sauƙe "Turƙashi, lallai kuwa kazo da babbar magana, amma maiyasa tunda baka bayyana wacce kake so ɗinba, sai yanzu da komai yariga da yayi nisa? kafasan Hajiya da kafiya balallai ne ta fahimce ka ba, shawarata a gareka shine, kamabar wannan zancen, domin balallai kasamu abun da kakeso ba!" Aunty Raliya tafaɗi hakan da'iyaka gaskiyarta. Cike da rauni Dr Sadeeq ya kalli Yayartasa. "Dan Allah taimakona zakiyi Aunty, kije kisameta kibata baki, wallahi inamatuƙar son Zahrah, sannan kuma yarinyar tana buƙatar kulawata, nikaɗai nasan matsalarta, please Aunty!!" yafaɗi haka yana me marairaice fuska, hadda haɗa hannuwansa biyu ga Aunty Raliya'n alamar roƙo. Kallon mamaki Aunty Raliya tashiga binsa dashi, "wai yaushe Sadeeq yazama bawan soyayya ne?" ta tambayi kanta. "Abune me matuƙar wuya amincewar Hajiya, amma zan jarraba, saidai kafun naje gareta, dole sainasan wacece yarinyar kuma su waye iyayenta, saboda kada aje Hajiya ta amince, akuma zo asamu wani mummunan labari akan ta" Wani irin bugawa ƙirjin Dr Sadeeq yayi, domin kuwa anzo wajen, lallai baizama dole kowa yafahimcesa ba domin sanin sirrin Zahrah, zai iya sanyawa kowama yaƙi amincewa da aurensa da'ita, wanda shi a wajensa baiga ta'inda aurensu zai zamanto rashin dacewa ba, amma ba'a ƴar ɓoye a harkan aure, domin koda anɓoye tofa sai ya bayyana. "Sunanta Zahrah, a unguwar Maraba take, sannan kuma marainiyace bata da uwa bata da uba, baffanta ne yake riƙonta, yarinyar tana da hankali sosai Aunty, sannan kuma tana da tarbiya, bata da wani aibu ko abun kushewa a tattare da'ita, saidai kuma..." kasa ƙarasa maganar yayi, domin kuwa baisan yanda yayartasa zata ɗauki maganar ba. "Umm inajinka saidai kuma me?" Aunty Raliya tatambayesa cike da zaƙuwa. "Ƙaddarace kuma tana kan kowa, haka kuma babu wanda ya'isa ya tsallake mata idan har tafaɗo kansa, akwai wani tsohon saurayinta da ya yaudareta yayi mata fyaɗe, watannin baya da suka wuce, wanda hakanne ma sanadin haɗuwata da'ita, amma ni banɗauki hakan amatsayin wani abu ba dazai hanani aurenta, kasancewar kowa da'irin tasa ƙaddaran a rayuwa!" Sororo haka Aunty Raliya ta hangame ido da baki tana kallon Dr Sadeeq har ya idar da zancensa mai kama da tatsuniya. Salati Aunty Raliya tasanya cike da tsantsar mamaki haɗi da al'ajabi, lallai Sadeeq baisan meyake faɗa ba. "Fyaɗe! fyaɗe fa kace Sadeeq, anya kuwa kansan mekake faɗa? yanzu kai saboda rashin hankali irin naka, karasa wacce zaka gani kace kanaso, sai yarinyar da taraba budurcinta wa ƙattin maza, yarinyar da wani yagama sanin sirrinta!" Aunty Raliya ta faɗi haka cike da ɓacin rai. Saurin rumtse idanunsa yayi domin jin magananganun Aunty Raliya'n yake tamkar sauƙan aradu, a kunnuwansa. Cigaba tayi da cewa " Lallai yanzu na tabbatar dacewa ba lafiyanka lau ba, taya kana cikekken namiji mai hankali da kuma kamala, karasa wacce zaka aminta da ta zamo uwar ƴaƴanka sai wacce wani ƙato ya haiƙemawa, yazama dole kasanja tunani Sadeeq, wannan ma ai zancen banzane, to gwarama kasani

Chapter 17 of 47