Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
baku ha'kuri ba idan bana nan dan Allah kar kuyi abinda nace ku 'ketare sharud'an dan saka muku Ina daidai daku" juyawa yai yana kallon Momy wacce ta girgiza tana murmushi yace "Momy ki zama witness na riga na fad'a musu komai kar tsautsayi yasa su aikata min zan hukunta su suce kuskure ne ko Abdul-Hamid ya shiga maganar please Momy dan Allah duk abinda sukai ba daidai ba idan na kiraki ki ri'ka fad'a min zan rubuta a littafi na aje sai ranar dana dawo idan laifi d'ari sukai saina hukunta su sau d'ari bazan gaji ba idan suna bukata harda 'kari zanyi musu". Kai Momy ta d'aga tana cewa "Karka damu Ahmad insha Allahu bazasu kuskure ba zan lura dasu kasan su waye 'kannan ka akwai tarbiyya da ladabi ko baka bada sa'kon a kula dasu ba bazasu aikata maka kuskure kamar yadda ka hanesu ba" Momy tana rufe baki ya mayar da hankalinsa kansu yana jinjina kai yace "ba kunji ta shedeku ba wallahi idan naga abu sa6anin fahimta sai naci uban ku" ya fad'a fuska a d'aure ba wasa kafin ya mi'ke yana kallon Momy da itama ta mi'ke tana cewa "muje nayi maka rakiya Allah ya kiyaye hanya Allah ya dawo min dakai lafiya" da sauri Maryam da taci wanka tad'au kwalliya itama ta taso tana taku tazo har gabansa da karairaya tana sauya murya ta ma'kaleta sosai tana cewa. "Nima fa Ahmad yau harda ni za'ai maka rakiya tunsa Allah yasa ina gidan yau sai munje har airport tare sai naga tashinka koda ace zan baro can" bai kalleta ba kuma baiyi magana ba sai hanyar fita daya nufa Momy kuma ta koma part d'inta zata d'auko hijab da kallo Maryam ta bishi tana cije lips ji take kamar ta sake kiran sunansa amma bakinta yayi nauyi kawai kwarjini taga yayi mata musamman yau data sake ganinsa cikin kakin soja sai ta sake jin wani irin bala'in sonsa da kaunarsa suna linkuwa suna shiga zuciyarta gashi jinin sarauta gashi soja ga kyau da kud'i da ilmi innalillahi wa inna ilaihi raji'un ya Allah ka duba al'amari na ka bani bawan nan naka matsayin miji a gareni" ta fad'a a ranta tana sake kallon kofar daya fita wayar Khairat ya kira yace su fito waje yana jiransu ganin sun fita yasa Maryam bin bayansu da sauri kamar zata kifa tana cewa "ji wani rainin hankali wato saboda ni banza ce ka shareni amma su saida ka fita ka kirasu a waya su bika to wallahi ko har Russia zasu rakaka nima sai naje babu wanda ya isa ya hanani" ta fad'a da gudu ta fita itama daga part d'in Mami ta ganshi ya fito tare da Mami itama tana yi masa kyakkyawar addu'a har gaban mota sukaje prince Hamid zai kaishi duk suna tsaye bayan ya shiga ya zauna kusa da prince Hamid ya kalli su Khairat da suke tsaye suna 6oyewa a bayan Momy yace ''kai me kuke jira ku shiga back seat ko baku gane bane"? Zaro ido sukai Ina yake nufin zasu rakashi har airport ko kuma ina yake cewa su shigo............. Katse musu tunani yayi da cewa "Dan ubanku baza kuyi min rakiya ba zan tafi shine kuka zuro min ido kuna kallona wato yauma farin ciki kuke zan koma na dad'e ko"? Dariya prince Hamid yai yana cewa "kai malam ba'a son mugunta ina zasu rakaka ka 'kyale yaran nan su sha'ki iska mai kyau dan Allah". "Wallahi bazan kyale suba sai sunje" ya fad'a yana sake kallonsu murya ba wasa yace "zaku shigo ko saina fito kanku"? Tun bai rufe baki ba suka bud'e suna shigo kowa salati take bud'ewa itama Maryam tai tana shiga ta zauna kusa da Baby harda sake turata tana matsar ta dan tai magana ita kuma ta share kamar batasan da wanzuwar Maryam d'in a gurin ba hakan kuwa yasa ciwo a ran Maryam badan da Ahmad a motar nan ba wallahi yau saita faffalwa Baby maruka da zuciyarta tai sanyi................. Jin mota ta tsaya yasa ta d'ago daga tunanin da take tana kallon gurin a ranta tana cewa "to ina ne nan kuma dama ba airport zaije ba"? Ganin sun fito suna shiga yasa itama ta fito tana bin bayansu batasan gurin kakaninsu suka zo ba saida ta shigo ta gansu kan bala'i dama kakaninsu suna nan a raye bata sani ba anan suke a cikin masarautar kodan suna 6angaren su daban ne shiyasa basa zuwa kuma da nisa humm aiko taga gurin zuwa dole ta ri'ka kawo musu ziyara saboda su saba zata ri'ka nuna musu tana son Ahmad ko Allah zaisa ta dace tunda taga acan bata samu kar6uwa a gurin Momy ba. Iya su kadai suke zancen su banda ita saboda batasan me zatace ba kusan awarsu guda anan sannan suka mi'ke suna yi musu sallama suka fita su Baby kam sunyi tunanin iya nan zasu rakoshi shiyasa da suka fito iya Maryam ce ta shiga motar sukam daba marmarin tafiya tare dashi suke ba babu wacce tai motsi saida suka ji yace "ba iya nan zaku tsaya ba har airport zamuje mun fito kun wani 'kame a gu d'aya kamar dogarai ku shigo man kuna 6ata min lokaci" ya fad'a harda zare musu ido ba shiri sukai kowa tai 'kasa dakai saboda tsoron karma su had'a ido yace wani abu ko yace sun masa laifi tunda sun fahimci so yake yad'an ta'ba lafiyar jikinsu Kuma badama domin babu wanda yai masa laifin dazai dake sun shiyasa yake jansu kafin aje airport d'in ko zasuyi masa laifin.......... "Baby da Khairat baku ji abinda nace bane"? Kai Baby ta girgiza tana cewa "kayi hakuri Yaya ni kaina ke ciwo" ta karasa maganar har lokacin kanta yana 'kasa taki d'agowa gudun karya gane karya take son zuwa airport din ne batai...... "Ko duk jikinki ne yake ciwo yau sai kinje airport d'in nan wallahi tunda na rantse ba kaffara shigo" wata iriyar harara Maryam ta sakarwa Baby tana gyara zama ta babbake gurin dan karsu shigo tana kallon Ahmad ta mirron mota tace "kaima Ahmad kamar dole saida su mezasu baka daka damu saitaje tunda tace kanta ke ciwo ka kyaleta man su koma tare da Khairat ni zanyi maka rakiyar har airport d'in ma dawo tare da Abdul-Hamid" bai kula maganar da Maryam ke masa ba sai kallonsu dayai yana cewa "wai uwar me kuka tsaya kallo na fito kenan"? Ya fad'a yana shirin bud'e murfin motar ya fito ganin da gaske yake yasa da sauri kowa ta bud'a ta shiga kaiya jinjina yana had'e fuska daidai prince Hamid ya tada mota ya kalleshi da murmushi yana cewa "Allah ya shirye ka kai dasu kamar wasu Tom and Jerry kaine Tom d'in su kuma Jerry's ace ba dama ku kasance guri d'aya bakinka bazai shiru ba ka d'an ri'ka d'auke kai mana". "Wallahi basu isa ba indai suka samu damata kamar yadda suka samu taka humm wadannan yaran" ya fad'a yana nunasu ta mirror yana cigaba "da babu wanda zai fad'a musu suji kana gani fa wancan lokacin ina barin gari suka d'aura balloons harda sayo cake wai sukai valentine na tafiya ta kodan harda kai aciki laifinka ne daka hanasu baza suyi ba" Ahmad na rufe baki prince Hamid ya girgiza kai yana cewa "a'a malam kada ka la'ka min laifin daba nawa ba ni bansan party zasuyi ba wallahi har suka gama shirinsu saida na shigo gurin Momy zan gaidar da ita da la'asar sannan naga suna had'awa na tsaya na kalla kaga kuwa mene laifina a cikin nan waye me laifi d'an kallo ko me aikin"? Baki Baby ta rufe tana kallon Khairat wacce itama ta zaro ido ganin prince Hamid yana neman ya tada mutuwa daga barci yasa Ahmad ya dawo da laifin sabo yadda suke a airport d'in nan ba kusa da Momy ba ya dagargaje su son ransa, sun d'auka Ahmad zaiyi magana da prince Hamid yace haka sai kuma sukaga baice komai ba babu wacce batace alhamdulillahi a zuciyarta ba sai Maryam da take cika da batsewa ita kad'ai ganin kamar duk sun manta da ita a cikin motar d'an karamin tsaki taja wanda bai fito fili ba daidai sun shiga airport d'in prince Hamid yayi parking suna fitowa yana cewa. "Ahmad wannan lokaci ma yaso fita fa"? Ya fad'a yana kallon agogon hannunsa tsaye Ahmad yai a gurin yana mi'kawa prince Hamid hannu sukai musabaha yace "please Abdul-Hamid dan Allah na baka amanar kula da yaran nan duk abinda sukai kuskure karka 6oye min ka kirani ka fad'a min dan Allah saboda tunda suka fara idan na tafi su had'a party bazasu daina ba sunyi d'aya kar suyi na biyu idan suka sake zasu had'u da fushina wanda sai sun gwammace dama basu zo duniya ba" ya fad'a da serious face yana kallon su ganin yadda duk suke a tsarake kamar masu shirin zubawa da gudu jinjina kai prince Hamid yai yana cewa. "Karka damu Ahmad insha Allahu ni nayi maka alkawari bazasu sake aikata hakan ba idan baka nan" ya fad'a yana jijjiga hannunsa da yake ri'ke dana Ahmad d'in "ok thank so much zanso hakan ya faru na tafi saina dawo" ya rufe baki Maryam har 'kwaruwa tai wajen cewa "please Ahmad dan Allah ka tsaya Abdul-Hamid yayi mana photo" kamar bazai amsa mata ba sai kuma ya juyo yana kallonta kamar me nazari kashe masa ido tana matsowa inda yake cike da iyayi ta mi'kawa prince Hamid waya fuskarta fal da murmushi kamar an biya mata hajji tace "yauwa dan Allah d'auke mu Abdul-Hamid d'auke mu" ta fad'a tana sake mannuwa a jikin Ahmad d'in ganin yau ta samu damar data dad'e tana so har kwantar da kanta a jikinsa take tana qara matsarsa duk yana jinta yana shan kallonta kawai ya shareta ne shima saboda ganin tafiya zaiyi bai kamata ace sunyi rabuwar wula'kanci ba kusan photo ashirin akai musu kafin Ahmad yace ya isa haka kar'bar wayarta Maryam tai daga hannun prince Hamid tana dubawa jikinta har rawa yake tsabar yanayin data tsinci kanta na jin dad'i da shau'kin yau tayi photo tare da Ahmad ta ta'ba jikinsa humm har lokacin ji take kamar tana jikin nasa basu rabu ba. "Kun tsaya kallo nane ku baza kuzo muyi photon ba saboda bakwa son gani na ko kun matsu na tafi ku daina ganina haka ne"? Da sauri suka girgiza kai a tare suna cewa "a'a Yaya kayi ha'kuri" dariya prince Hamid yai yana kallon su yace "wato harda had'a baki kukai a bada ha'kurin idan ma photon ne dashi bakwa so mene a ciki ana dolene". "Ok Kaine kake zugasu kenan"?. "Ni ba nine nake zugasu ba kar kayi wannan zargin kawai dai na fad'i hakan ne saboda Naga kana neman takura musu idan Kuma basu da ra'ayi fa saika 'kyale su". "Wallahi sai an d'auka harda wani had'a baki suna bani ha'kuri kamar wasu 'kadangaru suna girgiza min kawuna zaku zo muyi ne ko saina................. Tun basuji hukuncin dazai yanke musu da gudu suka karasa inda yake tsaye kallon Khairat yai yana cewa "ke tsaya anan" ya nuna mata 6angarensa na hagu sannan Baby 6angaren hannun dama ya baiwa prince Hamid wayarsa yayi musu kar'ba yai yana dubawa ganin babu me fara'a a fuskarta ya d'ago ya kallesu yana cewa "bakwa so mukai photon nan babu wacce fuskarta da murmushi kamar wanda kuka samu mummunan labari kuzo ya sake mana wani duk wacce batai murmushi ba tare zamu tafi muje can naci ubanta sannan na sakota a jirgi ta dawo gida idan na dawo kuma tai watering"😳 jin abinda yace yasa kowacce ta sake fuska a bisa dole sukai murmushin da basu shirya ba har saida suka saka prince Hamid dariyar dabai shirya ba ya kalli Ahmad yana cewa. "Ahmad ka zama mala'ikan yaran nan tsoronka da suke ya 6aci please ka rage wasu abubuwan kodan gaba Ina fad'a maka haka kullum ka'ki wallahi abun zai dameka fa" Ahmad baiyi magana ba sai wayarsa daya kar'ba yana kallon prince Hamid yai mai magana da ido kaiya jinjina suna shirin wucewa yace "ya kamata nima ace munyi photon nan kafin ka tafi Ähmäd" jin abinda ya fad'a yasa Ahmad dakatawa yana bashi wayar alarmar yayi musu kar'ba prince Hamid yai yana mi'kawa Maryam wacce da sauri ta kar'ba ganin wayar Ahmad ce to d'auka iya su biyun zata d'auka sai taga Ahmad yasa su Baby su shigo tuni ta tsuke fuska tana sau'ke wayar kasa ta kalli prince Hamid tana cewa. "Ya haka ba photo kace zanyi muku kai dashi ba"? Kaiya d'aga yana cewa "eh man d'auke mu sauri yake zai wuce lokaci ya cika" 'kara had'e rai tayi tana cewa "ok su fita gefe nayi muku zakufi kyau ku biyu". "Su waye zasu fita"?. "Su Khairat idan sun shiga zasu 6ata muku photo" ta fada kanta tsaye tana harare-harare da mamaki prince Hamid yace "akan me zasu fita taya zasu 6ata mana photo"?. "Ta yadda ake 6atawa kalli ma basu dace ku d'auka dasu ba nidai badasu zan d'auka ba kaine ka bu'kaci ayi muku photo kaga kuwa ai banda su ko"?. "No harda su wannan na family dukkan mu zamuyi saboda tunawa kin gane"? Jin abinda yace yasa Maryam tace "oh indai photon family ne saidai mu nemi wani yayi mana tunda nima ba bare bace bari naiwa wani magana" tana rufe baki Ahmad yace "give me my phone" ya fad'a yana mi'ka mata hannu bata bashi ba sai baya kad'an data matsa tana cewa "akan me zan baka ka bari man ga wani ya taho ya d'auke mu kodan nace haka shine zaka 'kwace gani nayi nima jininku ce akan me za'a wareni"? Jin abinda take cewa yasa Ahmad yai banza da ita ko karasa kallonta baiyi ba sai prince Hamid da yace. "kina jiko Maryam ki fahimta ba hakan yana nufin za'a wareki bane a'a photo ne zamuyi na family 6angaren gidan mu d'aya ba dangi ba shiyasa ba'a saka dake ba ke kina 6angaren Momy ne basu abbanmu ba amma idan mun 6ata miki ranki akan hakan kiyi mana afuw................. "Abdul-Hamid" Ahmad ya fad'a muryarsa da alamar fushi kallonsa prince Hamid yai ganin yadda ransa ya 6aci akan maganar da Maryan ta fad'a yasa ya mayar da hankalinsa kan Maryam d'in yana cewa "bani wayar lokacinsa yana neman fita" mi'ko masa tai shi kuma ya mi'kawa Ahmad kafin suka wuce saida ya rakashi har gaban matakalar jirgin ya shiga sannan ya juyo ya dawo gurin da suke tsaye sai iya Baby da Khairat ba Maryam a gurin. "Ina Maryam ta tafi kuma"? Ya tambaya yana kallonsu Khairat ce ta bashi amsa "tana cikin mota Kuna tafiya ta koma" ok muje" ya fad'a suna wucewa tana zaune a gidan gaba tana kallon photunan da prince Hamid yai musu yanzu ita da Ahmad sai status take dasu tana turawa a group din'ta tana fad'awa 'kawayen shine mijin da zata aura tajin sanda suka shigo motar bayan tafiyar ahmad babu wanda ta d'ago ta kalla har ya tada mota suka tafi iya su uku suke magana a motar amma banda ita har dariya prince Hamid yake ganin yadda suka ware suna hira dashi amma d'azu sakamakon da Ähmäd motar ko tari babu wacce take yi sai iya Maryam. Suna zuwa gida ko tsayawar minti d'aya Maryam bata sake yiba kai tsaye ta wuce bedroom ta d'auko jakarta tana fitowa Momy dake zaune tare dasu Khairat suna fad'a mata abinda ya faru da Ahmad yasa dole suyi masa rakiya kawai sai ganin Maryam sukai ta bud'o kofa ta fito zata tafi da mamaki duk suka bita da kallo Momy dake kallon yadda Maryam d'in take kumbure-kumbure tace. "Maryam ya haka ina zuwa kuma"? Murya 'kar-'kar alamar tana cikin fushi tace "gida zan tafi" da mamaki Momy tace "gida dai? Haba Maryam rana tsaka kice zaki tafi gida babu shiri ba komai dama haka ake zuwa ziyarar"? Shiru Maryam tai Momy taci gaba "babu inda zakije saikin dad'a yimin sati a gidan nan koma ki aje jakar nan yanzu ki dawo nan muyi hirar tare" jin abinda Momy tace yasa Maryam kamar zata fashe da kuka tace "dan Allah Momy ki barni na tafi wallahi zan sake dawo muku yanzun uzuri ne ya taso min". "Wanne irin uzuri kuma ko a school"? Kaita girgiza tana cewa "a'a ba'a school bane gida zanje gurin Mama" murmushi Momy tai tana kallonta kamar zata sake cewa wani abu sai kuma ta 'kyale tana cewa "ok ki gaishe min da ita nagode sosai da ziyara Allah yayi miki albarka" su Khairat ta kalla tana cewa "ku tashi ku d'an taka mata man" Momy ta rufe baki Maryam ta girgiza kai da sauri tace "a'a basai sun rakani ba suyi zamansu na tafi" ta fad'a fuuu tana nufar hanyar fita dakatar da ita Momy tai. "Amma ai kya tsaya Khairat ta taso taiwa driver magana ya kaiki ko"? Nan kaita girgiza a karo na biyu tace "a'a Momy nagode zan fita can waje bakin titi na tari d'an napep saina sake zuwa miki" tana fad'in haka ta bud'e kofa wuff ta fice murmushi me had'e da jinjina kai Momy tai tana mi'kewa ta shiga part d'inta ta d'auko kud'i tana baiwa Khairat tace "tashi maza yanzun nan ku kai Mata tahau napep d'in ko ta'ki kar'ba karku dawo min dashi kusan yadda zakuyi ku bata" kar'bar kud'in Khairat tai suka mi'ke tare Baby suka bi bayanta tsabar saurin da take harta fice daga masarautar sai acan wajen gate d'in karshe ma farkon shigowa suka sameta hakan ma sai kira Khairat ta 'kwalla mata tana ji tai banza har saida suka dad'a sauri suka tarota kud'in Khairat ta mi'ka mata tana cewa "gashi Momy tace kihau napep ya kaiki gida" baki Maryam ta ta'be tana girgiza kai tace. "No nagode ki maida mata kud'inta ina dashi kud'in da yake gurina ya isheni har yayi min yawa". Kallon yadda ranta yake a 6ace Khairat Tai tana cewa "Tace karna mayar mata matsayin naki dabam nata dabam please Maryam ki kar'ba". "Nace miki a'a ki mayar mata ina da kud'in zuwa gida ya ishe ni". "Amma a tunani na Maryam ko duniya ce a tare dake dan Momy ta baki kud'i ki hau abun hawa bai kamata kice a'a ba ra'ayi tai ta baki aitasan kina da kud'in ta baki ki kar'ba dan Allah". "Khairat kinsan halina fa idan na riga na furta abu na furta kenan bana canzawa nima yakamata ki fahimce ni nace miki na gode ki maida mata ko bakiji sosai bane"? Ta fad'a tana aikawa Baby harara da dogon tsaki wacce tunda suke maganar su ko tari batai ba sai yanzu Maryam take nemanta da fitina tace "ke kuma uwar zulai meye kika zuro min ido kina min kallon 'kurulla idan make me lashe-lashe ce toni nafi 'karfin ki saidai kici kanki gida da bedroom kuma gashi na bar miki ki dafa kici nima muna da arzikinsa ba fatara ce ta kawoni gidan naku ba balle kiyi min wani jakin kallon ki" jin abinda Maryam tace yasa Khairat tai mugun had'e rai tana cewa. "Wai Maryam wanne irin abune wannan kike yi yada girman yayi yawa dan masifa bata kulaki bama saikin takale ta kunyi fad'a dad'in abun ma ita wacce kikeyi dan ita ko kallo baki isheta ba kotanan ya kamata ki sallama kiyi Dana sani nadama da saranda akan abubuwan da kike ba daidai bane" zazzafar harara Maryam ta sakar wa Khairat tana cewa "Babu ruwanki ba dake nakeyi ba gada wacce nake maganata idan ta isa yau ta tanka min kamar yadda Tai min kwanan baya wallahi saina 6allata a gurin nan dama ina wuya da ita dan haka duk abinda zamuyi naki idone Khairat karki shiga abinda ba'a saka dake ba karki d'auka" ta fada tana mayar da kallonta kan Baby tace. "Ke kuma ina sauraron ki idan kin isa ke cikakkiyar fitsararriya ce kiyi min magana yanzu kiga aiki da cikawa" d'auke kai Baby tayi tai banza da ita kamar dai irin bada ita take ba takaici ne ya kama Maryam har batasan lokacin data ciji yatsa ba murmushi Khairat tai tana cewa ''nida nasani Baby bazata kulaki ba ko kanki zaki cinye saidai kici ke kad'ai gashi kuwa hakan ya tabbata kinga da zaki gane saiki daina wahalar da kanki a kanta dan indai ba rashin neman zaman lafiya ba banga abinda ta tare miki ba alhali kece kika zo kika sameta". "Ai dama bazaki ga abinda tai min ba saina fad'a amma ki sani bani da lokacin ku dukka biyun baku isheni kallo ba banzaye ku jira dawowa gidan sai nayi maganinku mtswww" taja tsaki a fusace tai gaba da kallo Khairat ta bita tana cewa "Allah ya yaye miki wannan abubuwan idan masifa ce ta sameki idan kuma zaki gyara Allah ya ganar dake da wuri muje Baby" juyawa sukai suna komawa Momy tana zaune a inda suka barta basu nuna bata kar'bi kud'in ba ko kuma ga abinda tai kawai Khairat tacewa Baby kar tace Maryam ta'ki kar'bar kud'in sun dawo dashi zata 6oye sai abun ya wuce yadda koda ta fito da kud'in nan tace mata bata kar'ba ba tasan sannan abun bazai mata ciwo kamar yanxu ba shiyasa ma fuskarsu wasai suka dawo mata suna d'ora hirarsu daga inda suka tsaya. Maryam kam me napep ta d'auka har kofar gate d'insu ta bashi kud'insa tana d'aukar kayanta ta shiga ciki Mama tana zaune a parlor sai ganinta Tai ta shigo mata kamar mafarki harda murje ido Tai ganin da gaske itance yasa zubur ta mi'ke tana tahowa gurinta da sauri tace "Maryam ya na ganki haka da rana tsaka meya faru dawowar me kikai ne kardai wani abu ne ya faru a tsakanin ku"? Zama Maryam tai tana sau'ke numfashi tace "a'a kwantar da hankalinki babu abinda ya faru kawai tahowar dad'i ne". "To kice yau da labari kenan mu bud'e kunnen mu dakyau"? Kai Maryam ta jinjina tana cewa "akwai Mama labari d'aya kenan saidai kice akwai labarai". "Tofa labarai humn a fad'a mana muji dan harna 'kagu sosai naji abinda yake faruwa" ta fad'a tana sake matsowa ta saito kunnenta dariya Maryam tai tana cewa "kai Mama akwai son jin labari dama ba wani abu bane ya sakani farin ciki sai photo da mukai da Ahmad d'azu" zabura Mama tai tana kallon ta tace "um um fa Maryam banda 'karya Ahmad d'in nan a yadda kike fad'a min baya ko kallonki shine zai yarda kuyi photo"? Murmushi Maryam tai tana d'auko wayarta a cikin handbag d'inta ta bud'e tana nunawa Mama wacce babu kunya ta mike tana rawa harda wa'ka a gaban maryam d'in saida ta gama ta tsaya ta kalli Maryam tana zama tace. "Yauwa Masha Allah sai mene ya faru"?. "Babu komai kawai sai rakiya da mukai masa zuwa airport ya koma Russia shiyasa na tattara kayana na dawo gida kinsan yanzu zan taho harna fito sosai wai sai sannan Momy ta turo Khairat wai ga kud'i nahau napep ni kuwa na'ki kar'ba nace ta mayar mata dan tasan naji haushi" harararta Mama tai tana cewa "ji banza kawai meye abun 'kin kar'ba raba arne da makami ibada ne kikasan nawa ta baki" shiru Maryam tai tana d'aga kai sama kamar me tunani tace"kuma fa da yawa kud'in nan Naga suna da tudu yakai kusan dubu............... "Ke rufe min baki bana son kayan haushi kawai fad'a min meya faru a gidan tun daga ranar da kika je har zuwa yau yanzun nan da muke magana yaya kukai da Ahmad shin kin samu shiga ne koko a'a"?. Kai Maryam ta girgiza tana cewa "humm wai babban aiki kenan gaskiya yanxu a gajiye nake zanje na huta idan na fito saina fad'a miki komai nidai kawai abinda zai Dade yana bani mamaki shine yarda da Ahmad yai ya tsaya mukai photo kawai hakan ne yake 'kayatar dani". "A ina kukai photon ne a gidansu"?. "A'a airport fa mukai masa rakiya". "Ok komawa yai kenan shiyasa kika taho"?. "Uhm ya tafi d'azu sai kuma ya dawo amma naga tunda nazo nace miki ya koma" gyara zama Mama tana d'aga kai alamar eh sannan ta kalli Maryam da fuskarta take fitar da annuri na annashuwar wannan maganar da suke tace "ke Maryam baki fad'a min ya kukai dashi

Chapter 17 of 22