Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ɗakin sirri da kwanon abinci. yayi mamaki, domin wannan ɗakin ba a yawan amfani da shi sai da wani sirri mai girma. "Waye a ɗakin?" ya tambayi bawansa. “mai martaba ne ya hana kowa magana akai, ranka ya daɗe,” bawan ya ce da kansa yana rawa Tarhim ya gyara tsayuwarsa, ya ce cikin natsuwa: “Na isa in sani. gobe da asuba, zan je kaina.” Washegari da safe, Prince Tarhim ya leƙa ɗakin sirri. kafin ya buɗe, ya tsaya yana sauraron wani motsi. daga ciki, ya ji murya mai rauni tana karanta addu’a cikin sanyin murya. ya bude ƙofar da hankali... idanuwansa suka sauka a kan Rahila, wacce ta zauna cikin tabarma, tana daure da farin zani, gashinta ya bazu kan kafadarta. Lokaci ya tsaya. Rahila ta dago ido lkacin da ta kalli Tarhim, zuciyarta ta ɗan tsinke – ba domin tsoro ba, amma domin tunanin irrin halarci da ya mata na ceto rayuwar ta duk taye sanyi tasha tambaya kanta cewa me yasa har yanzu bai dawo garita ba har sarki Mujse ya gano inda take ya rufe ta yana azabtar da ita bisa laifin mahaifinnta duk gaba da faɗa da take tunkaho dashi tun da Prince Tarhim ya ceto ranta ta rasa dalilin faɗan da zataye akansa tabbas tana da. burin kashe su dukkan su to amma akan wani dalili tabbas mahaifin ta mugun sarki ne akan bayin sa ya aikata zunubi daban daban amman hakan ba wai ya na nufin a ɗauke fansa akan ta ba ita ma bawai tayi ta faɗa har tsawon rayuwar ta ba Amman rashin ganin Prince Tarhim ya tabbatar mata da tazama losser !.. Bai ce mata komai ba ya juya zuwa fada kai tsaye domin ganawar sa. da mahaifinsa Sarki Mujse ya tsaya gaban sa da ƙarfi da girmamawa " Ya kai baba na nasan rashin ɗa akwai cutarwa musamman idan ya kasance maƙiyanka ne sukaye galaba akanka" yakai Baba na Sarki Numan mutum ne azzalumi da duniyar mu ta sanshi akan mulkin sa baya barin kowa cikin sallama a haka muka samu nasarar shiga har fadar sa mukaye galaba akan sa shin Baba kasan dalili !? Saboda karshen zalunci sa a hannun mu yake kuma karshen mulkin sa ya ƙare a dalilin mu mun raunata sa mun kashe sa har abada bazai dawo ba mun ɗauke fansar kashe mana namu da yayi ,to shine me laifin me yasa muma yanzu muka dawo azzalumai irinsa ka tuna mulkin da kakiye cikin aminci da adalci ya za'a yi mu azabtar da Rahila bisa laifin uban ta ?, shin ta kashe mu ko ta dauke fansa ko ta cutar damu a'a Baba to me yasa ka rufe ta kake azabtar da ita tsawon wanan lokacin "?. Rungumar juna sukaye nan Sarki ya share hawayen sa da cewa " tabbas na aika ta kuskure mai girma na azabtar da wanda bashi da laifi kuma nasan cewa soyayya mai girma ce a zuciya ka daga lokacin da kaganta shiyasa na fara gaba da ita don inason ka kasance da Afra matsayin mijin ta Amman nayi laife ka gafarta min yaro na ka zaɓi muradin ka a rayuwar nan sanan sanyi murabus zaka kuma kan sarauta nan da wata ukku za'a yi wanan bukin ... BAYAN WATA UKKU Jama’a suka ɗaga kai cikin mamaki. Dukka yankunan sun taro an tabbatar da Prince Tarhim a matsayin sarautar sa “Ban tursasa masa ba, ya aikata haka bisa adalci da tausayi kuma yanzu na yarda da zaɓinsa. Idan zuciyarsa ta karɓi Rahila, to hakan na nufin akwai wani ƙuduri na sama.” Sanan Princeces Rahilat ta dawo daga muƙamin ta na asali yankunan mu na ƙarƙashin ta sarauta ɗaya ne kuma itace asalin jinin yankin Buga Afrika Rahila ta ci gaba da zama ginshiƙi a masarauta, yayin da ake yawan kawo mata mata da yara don karɓar yaƙi da shawara ta zama cikakkiyar Princess nata a inda ta rungume jarumin ta Tarhim domin a duniya idan akwai wanda take muradun to mijin ta ne shine asalin jarumin da take buƙatar kasance wa dashi tsawon rayuwar ta...... --- BACK TO STORY BAYAN WATA AJIYAR ZUCIYA Ajiyar zuciya mai nauyi Ihsan ta sauke, yayin da ta buɗe idonta a hankali, idon ta kai ga duk sansanin da suka taru a kusa da wutar da suke zaune, idanun mutane sun cika da kewa, da kuma ƙaunar jin ci gaban labarin da ta kawo musu suna kallonta da nutsuwa, kamar sun manta da gajiyar hanya, yunwa da ɓacin rai tayi shiru na ɗan lokaci, sannan ta sake numfasa. “Wannan shi ne labarin Princess Rahilat,” ta faɗa cikin natsuwa. “Ina fatan ya ɗan ɗauke muku kewa a cikin wannan mawuyacin yanayi.” duk suka jinjina kai sai Maryam ta ɗaga hannu cikin annashuwa. “A gaskiya labarin ya kayatar, Ihsan. Amma ina da tambaya,” ta ce tana kallon ta kai tsaye. “Meyasa kike mana labari da Hausa da Turanci a haɗe?” Ihsan ta murmusa, ta gyara zama kafin ta amsa. “Hakika tambayar ki ta da muhimmanci Maryam domin shekaru fiye da dubu biyu da suka wuce, kafin turawa su shigo nahiyarmu, sukan ɗauki baƙaƙen fata tamkar bayi ne sun raina mu, sun mulke mu , amma akwai wani sarki mai suna Numan, wanda ya ƙwato yanki biyar daga hannun turawa, ya mayar da su 'yan ƙasa masu cikakken 'yanci.” Ta dan yi shiru, tana kallon yadda idanu suka cika da sha'awa. “Shi ya sa ya zama sarki na musamman a zamaninsa duk da kuwa mahaifin Rahilat azzalumi ne, amma saboda bajintarsa da yaki da turawa, aka ba diyarsa Rahilat sarauta – don ta ci gaba da kare mutuncin mutane kamar ku da ni. Wannan ne dalilin da ya sa nake haɗa Turanci da Hausa – domin har yanzu muna da ragowar tasirin turawan, amma da karatun irin wannan ne za mu dawo da mutuncinmu da fahimtar tarihinmu.” Hannu suka sa, suka rungume ta duka daga gefe kuma Yazid ya ce da dariya: “Wallahi, Ihsan, wannan tafiya tazo da darussa labarin Rahilat ya ɗaga min zuciya!” John ya ɗora: “It’s like traveling into history and coming back with strength.” Ado ya jinjina kai yana murmushi, “toh yanzu fa dai na tabbata, Ihsan ke ce jigo a cikin wannan tafiya, bari mu ci gaba da tafiya gobe, amma yau... yau dare ne na tunani.” Suka kalli juna da murmushi, suka miƙe suna shirin kwana. Daga can gefen zuciyar Ihsan, sai ta ɗan lumshe ido tana tunani: "Bayan wata... akwai haske kuma wannan shi ne farkon komai." continued by narnah ƙanwar soja ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON🌕 BY NARNAH KANWAR SOJA MARUBUCIYAR MIJIN MAGE FARASHIN SO BIYAYYA GA UWA DUHU CIKIN HASKE RUHI BIYU HANYAR RUWA MAI CIKI CE MADOBIN IDO AHLIN LASHKAR PRINCESSS RAHILAT RAYUWAR UMMAH BAYAN WATA SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 13/ 14 04 / 05 / 2025 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Maryam ta shafa gumi a goshinta, hannunta na rawa sai yanzu zafin jikin da ya ɗauke ta tun safe ya fara raguwa duk da haka, Idanunta sun ƙi buɗewa sosai, sai ihun zuciya da tafasar hawayen da take riƙe. "Ihsan..." ta kira da rauni, "zan iya tafiya." Ihsan ta rungume ta, hawaye na gangarowa daga idanunta. “kin ƙarfafa zuciyata fiye da yadda na zata,” ta ce cikin sanyi Su Yazid, John da Ado sun zuba ido, zuciyoyinsu cike da yanke shawara basu da ƙarfi sosai, amma lokaci yana guje musu. “Yanzu ko ba yanzu ba ne idan yanzu muka tsaya nan wata rana, za a cafke mu.” Yazid ya ce da ƙarfi, yana gyara jakar sa a bayansa. sukai shiru har sai da aka ji murya kamar ƙarar iska daga can nesa sai suka lumshe ido, suka lumshe zuciya. Su biyar suka tattara kayan su da ƙarancin haske suka ratsa cikin duhu, gaban su cike da fargaba, amma babu wanda ya waigo baya, Gabar boda na ƙasar Libiya ba kasafai ake iya shige ta da sauƙi ba. Rana ba ta faɗuwa sosai a hamada. Gashi da ke fesowa daga ƙasa kamar harshen wuta, yana fitar da zafi da ƙamshi irin na ƙasa mai mutuwa babu bishiya, babu ruwa, sai yashi mai girma kamar kogon wuta. Tsakanin dare da kwana biyu, sun ratsa titin ƙasa da ƙafa, su na bin jagorar wani tsoho wanda suka biya sauka-ka-tafi tsohon yana da hannu biyu kawai, amma gwaninta da sanin hanya sun fi soja da komfuta. “Yanzu nan,” ya ce da ƙasƙantar murya yayin da suka isa ƙaramin rami da aka lulluɓe da dausayi. “Nan ne na ƙarshe kafin ku tsallaka Libiya. bayan nan, ba ruwa, babu tsaro kawai da zuciyar ku kuke tafiya.” “Shikenan,” Yazid ya ce, yana gyara rigarsa. “za mu fuskanta.” Maryam ta kama hannun Ihsan. “In muka tsallaka, to Allah ya bamu mafita.” John ya lumshe ido. “I’ve never seen darkness this wide... but I feel hope.” Suka shiga cikin hamadar da babu ƙyalli, suna tafiya suna shan iska mai zafi kamar wuta tana hura musu cikin hanci, cikin dare, rana tana walƙiya, ba saboda haske ba – sai saboda yashi yana motsi kamar ruwan teku. Ado ya ce da jinjina kai, “wannan garin ba na mutane bane...” “amma mu fa mutane ne da mafarki,” Ihsan ta ce, murya kamar zuma “mu ma muna da hakkin tsira". Zuwa wannan lokaci, tafiyarsu daga bodar Libiya ta ɗauki kwanaki, daga na farko zuwa na biyu, ƙarfinsu yana ragewa. Na uku sun fara kwana da cikinsu babu ruwa, babu abinci rana ta huɗu, numfashinsu ya zama kamar na dabbobi, idanu sun ɗebe, fata ta bushe ta fara fashewa. Hamadar Sahara ba fili bane na yashi kawai wani lokaci dutse ke cikinta, wani lokaci gami da koguna da suka bushe shekaru da suka wuce amma duk inda suka kalli yanzu, sun haɗu da komai: rairayi masu santsi, ƙasa mai zafi, iska mai ƙarfi da tsintsiya da ke ɗagawa daga ƙasa har sama kamar baƙin hayaki. Maryam ta fara jan ƙafarta a jikin yashi. takalminta ya dade da karyewa, yanzu ƙafarta bare – jajaye sun yi, cike da toka, ƙyalli daga rana. “Ihsan... ruwa... just one sip,” ta furta kamar mafarki. Ihsan na bin ta da ido, kanta yana juyawa. Idanunta sun canza launi, sun zama kamar ƙwai, ba su da ƙyalli gashinta ya manne da gumi da ƙura, har ta daina jin sauyin iska. “Ba ruwa, ba komai amma ki tsaya Maryam... ki tsaya.” Yazid yana gaba, yana rarrafe, yana fitar da numfashi kamar wanda aka sakar daga ƙarƙashin ruwa. John yana masa baya, amma yazo ƙasa. “I can’t feel my tongue...” ya ce da harshen da ya fara murɗewa. Ado, wanda shi ke riƙe da jakar kowa, ya durƙusa. “I’m seeing mirages I saw my mother – she was standing in water, calling me.” Yashi ke rawa, rana ke ƙuna. Iska ta taso – iska mai nauyi, ƙamshi kamar zafi duka suka durƙusa, suka lulluɓe kansu da tsintsiya da kaya, amma iska ta kwashe su kamar hayakin gobara sun yi ta birgima kamar jakunkuna, har aka jefar da su zuwa wani ƙaramar rami – wani tsibiri a cikin sahara, tamkar tafkin dutse da ya bayyana daga ƙasa, cikin haka suka faɗi su ka suma. Wani lokaci daga baya... Cikin ɓangararren inuwa da aka samu daga wata harsashen dutse, suka farka jikinsu a sanyi, amma cikin yashi babu ganye, babu ruwa, babu abinci. sai ga jikinsu ya fara nuna alamar rushewa – la'bbansu sun fashe, hancinsu ya bushe, idanunsu ba sa kallon juna, fatar hannu da ƙafa sun fara murɗewa, ta rikiɗe tamkar kaho “Zan mutu,” John ya furta, yana kallon sama, “Ba ruwa na sha fitsari na jiya ba zai isheni yau ba.” Yazid ya kalli jikin sa, ya ji kamar naman jikinsa yana motsi. ya taɓa fatarsa – ta cire. “Wallahi mun gama.” ya fashe da kuka, amma ba kukan da kake ji ba ƙara, sai hawaye masu zafi kamar gawayi. Ihsan ta lumshe ido, ta kai bakinta ga wani ƙaho da ke ƙunshe da ragowar fitsari. ta sha kadan gaban Allah, ya fi komai wannan ba lokacin kunya bane, ko tsoron mutuwa. wannan yanayi ne da rayuwa take ƙi barin jikinsu , Maryam na jingine da dutse, tana kallon jikin ta kamar ba nata bane. “I’ve become sand,” ta ce. “Even my voice sounds like wind.” Daga nesa... Ado, wanda ya fi ƙarfinsu kaɗan saboda tsawon jikinsa da kwazon zuciyarsa, ya fara bin duwatsu da sandar da ya kakkarya bayan lokaci – sai ya hango wani abu wani rami mai zurfi da ke wani rami kamar tukunyar wuta. Yayi tsalle, ya kalla – ƙananan ragowar ruwa! Yayi ihu kamar kura mai murna: “Ruwa! Wallahi, ruwa!” ya dawo da gudu yana faɗuwa, yana hura numfashi kamar za a sa wuta a jikinsa. “gashi chan ! gashi chan!” Suna ta matsowa da karfin halin da ba su san inda ya fito ba. kowa da dabara, suka tsinke leda, suka tattara ƙwanƙwaso daga jikin su, suka kai bakin su... dan kadan, amma ceto. sannu a hankali zuciyarsu ta dawo ba da kyau ba, amma da rayuwa suka kwanta, suka kalli sama, tsibirin da suke kai tsaye ne a tsakiyar Sahara, ba ruwa sosai, amma nan ne Allah ya basu mafaka. Yazid ya ce da karamin dariya, “Idan muka tsira daga nan sai na ce duniya ba baƙi bane. duniya rana ce da yashi, amma ina da mafarki.” Ihsan ta ce, “Na fi son mutuwa da mafarki fiye da rayuwa babu buri.” Maryam ta rufe idanunta " ya Allah mun gode maka da kyautar ruwa lallai ruwa zai rayu inda ba halitta amman mutum bazai rayu ba ruwa ba ".. Ruwan da suka tsinci ya zama tamkar aljanna. kowa ya samu ɗan kaɗan ya ji cikinsa ya huta. bayan kwanaki biyu a cikin wannan tsibirin – inda babu ciyawa, babu dabbobi, amma akwai inuwa da ƙaramin ramin ruwa – sai zuciyarsu ta ɗan dawo. Ihsan ta janye rigarta mai sheƙi, ta taka da ƙafarta mai jini zuwa ga sauran su, ta ce cikin sanyin murya: “Ku ji ni mana...” “Mu ne matafiya, Wanda ba su da gida, amma zuciyarmu da rai, suna cikin mafita...” Maryam ta kama hannunta, suka fara juya da kasala, suna dariya da hawaye. Yazid da Ado suka buga ƙafa a yashi, John ya murɗa murya kamar yana wake, sai suka kama da karfi. “Ruwan nan, ka ceci mu, yashi da rana sun cinye mu, amma muna raye, muna tafe – cikin fata!” Sai suka rungume juna – gaba ɗaya biyar – suna sharar hawaye, suna murza fatar jikinsu da suka rasa. Wannan rana ce da suka yi murmushi cikin azaba. " Bayan wata akwai haske Bayan wuya akwai daɗi "... Bayan sati biyu a wannan wuri, ruwa ya kusa ƙarewa sai suka yanke shawarar ci gaba da tafiya, domin sun san idan sun zauna za su mutu da yunwa da ƙishirwa. sun ɗaura jakarsu da fata, suka fito daga tsibirin suna zamewa a yashi. Kwana biyu sun yi suna tafiya cikin rana da yamma. rana na dafa ƙafarsu, yashi na kai musu zafi daga ƙasa. idanuwansu sun fara ganin abu biyu, zuciyarsu ta fara shakku da juna. Maryam ta fara rikicewa, ta yi ihu tana zagin Yazid tana cewa: “Ka ce zaka kawo mu Dubai! ka ce za mu ci kuɗi! Ashe ba haka bane?!” John ya zube a ƙasa yana dariya da kukan hauka. “We’re already in Dubai – in hell's part!” Ihsan da Ado suka kama su, suka kwantar da su kamar yara. Bayan wata guda cikin tafiya da yunwa, sai suka hango wani gari daga nesa – amma ana shigarsu kusa da shi sai suka ji hayaniya. mutane masu bindiga da dabbobi ke yawo a kusa – mafarauta ne amma ba na noma ba – ‘yan fasa-ƙwauri ne da ke farautar masu tsallaka haddi don su sayar da su ga masu aikatau ko masu fatauci. Sun kamasu a dare sun ɗaure su da igiya, suka ajiye su a cikin wani daki tamkar kurkuku da yashi a ƙasa. Maryam ta fara kuka, John ya yi shiru yana kallon su kamar wanda ya hakura da rayuwa. Yazid ya yi ƙoƙarin fita, aka yi masa dukan tsiya, aka zubar da jininsa. Ihsan da Ado sun tsaya suna kallon juna da hawaye. Ado ya ce: “Na rantse, idan muka tsira daga nan, ko ruwa ne, ko wuta, zan kawo ki gida da hannuna.” Ihsan ta runtse ido. “Zan riƙe ka da zuciya har ƙarshe.” Continued ............. by narnah ƙanwar soja ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/BsQ0CkOCA83FgwnQ177z9y 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON🌕 BY NARNAH KANWAR SOJA MARUBUCIYAR MIJIN MAGE FARASHIN SO BIYAYYA GA UWA DUHU CIKIN HASKE RUHI BIYU HANYAR RUWA MAI CIKI CE MADOBIN IDO AHLIN LASHKAR PRINCESSS RAHILAT RAYUWAR UMMAH BAYAN WATA SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star 15 / 16 08 / 5/ 2025 Kamar yadda aka saba duk shekara, Alhaji Saminu bai taɓa yin ƙasa a guiwa ba wajen nuna ɗimbin darajarsa a idon mutanen ƙauyen Gembò amma wannan karon daban ne. wannan karon ba kawai don shanaye ya zo ba ya zo ɗaukar amana. A gaban Moddibbo da wasu dattawan gari guda biyu, Alhaji Saminu ya fito da sadakin Halima. kudi ne masu yawan da fulani ba su fiye gani ba a lokaci guda baya ga hakan, ya kawo 'yan dabbobi da kayan gyaran amarya, tare da alkawarin dawowa bayan Sallah da sati biyu—kai tsaye daga birnin Tarayya Abuja inda matarsa ke zaune. Moddibbo ya karɓi sadakin cikin nutsuwa da girma ya san me hakan ke nufi: yanzu Halima zata koma karkashin Alhaji Saminu amma ko da yake zuciyarsa na cike da nauyin amana, bai nuna ba, saboda a rayuwa irin tasu, alƙawari tamkar doka ne da ba za a karya ba. Halima kuwa... ta zauna a gefen mahaifinta da cike da kunya, fuska a kasa kamar yadda aka koya mata, duk da cewa an ba ta labarin cewa rayuwar birni ce zata zame mata gaba, kuma Alhaji Saminu mutum ne mai arziki da daraja—amma a zuciyarta babu motsin soyayya ko ɗokin aure. Zuciyarta tamkar fili ne, babu shuka, babu furanni kawai akwai wata siririyar lafazi da take maimaitawa a ranta: "Na yarda da mahaifina na amince da kaddara. kuma zan bi Alhaji Saminu, ko da zuciyata ba ta motsa ba." Irin wannan biyayya ce da ta sa ta karɓi sadakin da lafazi guda biyu: “Na yarda.” Moddibbo kuwa kamar kowa yana ganin yana murna amma shi da zuciyarsa sun san gaskiya , ya san Halima ba ta kai matsayin aure ba tukuna ta girma da sauri, amma zuciyarta har yanzu karama ce, tamkar macen da bata fara sanin al'amuran soyayya ba. Sai dai kuma, Moddibbo mutum ne mai daraja da mutunci ya rike amanar Alhaji Saminu fiye da yadda wasu ke rike 'ya'yansu. Yana fatan Alhaji Saminu zai kare martaba da tsaron Halima kamar yadda ya rike alkawari na shekaru goma sha biyar. Wani iska ya buso daga arewa, ya kada ganyen kuka da ke bakin ruga Halima ta lumshe ido, tana jin iskar kamar wata alama ce daga sama ko soyayya zata zo daga baya? ko kuwa hakan nan ne rayuwa ta rubuce mata? Bayan sati biyu da cikar alkawari, ƙauyen Gembò ya sake fuskantar wata rana da ba za a taɓa mantawa da ita ba rana ce da komai ya sauya—rana da tarihi ya ƙara rubutun zinariya cikin ƙwarya mai ƙyalli. A safiyar ranar asabar, tun ƙarfe tara da mintuna goma, sai ga jere-jeren motoci guda shida masu sheƙi da ƙyalli irin wanda bai saba zuwa ƙauyen ba, motoci ne kirar Lexus LX 570 guda biyu, guda bakar fata, guda kuma fari ɗan haske mai cike da adon zinariya. Sauran kuwa motoci ne kirar Hilux da Toyota Highlander, dukkansu cike da kaya, kujerun zamani, manyan jakunkuna da akwatuna masu lulluɓe da furen ado da yajin rawaya. A wata ƙaramar Prado, wanda aka ɗora babban laifan jajjayen furanni da tutar Kaunar aure, Alhaji Saminu ne ya fito sanye da babban ɗan-baban Shadda mai launin zinariya da ruwan hoda , babbar hula ce ta fulani bisa kansa, mai ɗinki na musamman da adon sarka fitarsa daga mota ta sa yara suka yi tsalle, mata suka fara cewa: “Ga angonmu ya iso! Allah ya sa a dace!” Shi kuwa, yana da murmushin da ba'a san a zuciya akwai tsoro da jin nauyin amanar da ya ɗauka ba bayansa, abokansa biyu da shaidu—Alhaji Babangida da Alhaji Laushi—duk sun fito cikin kayan zamani ƙauyen ya sha ado kamar an shirya masa sallah gari ya ɗau shela da kade-kade na kalangu da waka: “Alhaji Saminu yazo! angon Halima yazo!” Tun daga makon da ya wuce, iyayen Halima sun ɗora shagalin al'ada, mata na unguwa sun taru kullum ana sallake, ana gasa binkami, koskoso, da kilishi. Halima tana zaune cikin ɗakin mahaifiyarta marigayiya, cikin duhun tunani da zumudin rayuwar da ba ta san me take cike da ita ba ,aka yi mata lalle, aka sa mata ƙwarya ta ruwan turaren wuta a gefenta, aka shafa mata manshanu a fata, aka ɗinke mata zani da riga mai alamar Fulani na gargajiya—jar zani mai adon ratsi da santali na tsaf. An saka ta cikin wani ɗaki mai ƙyalli da kilishi, ana yayyafa mata ƙamshi da bakhour, ana duba fatarta da gashinta, yarinyar ce kyakkyawa da kyau na halitta, ba ado ke ƙawata ta ba—rashin yawan maganganu da nutsuwar ta ce abin kallo. A gaban limamin ƙauye da shaidu, aka daura auren Halima da Alhaji Saminu da sadaki naira dubu ɗari biyar, da sarkar zinari da kayan gida., adaidai lokacin da aka furta "na ɗaura", Halima ta fashe da kuka mai ƙarfi. Sai dai ba kuka na soyayya ko jin daɗin aure ba ne—kuka ne na rabuwa da matar mahaifinta, wacce ta raineta tun rasuwar mahaifiyarta, wani kuzarin tunani ya cika ta, kamar tana jin kamar yanzu rayuwarta ta sauya daga yarinya zuwa amarya, daga ƙauye zuwa birni. Moddibbo ya share hawayen sa da alwala, yana murmushi mai cike da damuwa, yana fatan Halima zata dace da sabon rayuwar da zata tafi ciki, a zuciyarsa yana fatan Alhaji Saminu zai rike ta fiye da yadda aka rike ’yar sarki. Alhaji Saminu ya bar ƙauyen ba da hannu ba. Ya bar da ɗimbin kyaututtuka: kudi ga matan unguwa, jakunkunan shinkafa, kayan abinci, sabbin riguna da ɗinkin zamani ga matasa, har da jakunkuna ga yara da aka ce "na makaranta". Wajen fitarsu, aka shigo da sabuwar amarya cikin sabuwar rigar aso-ebi da kwalliyar santali, aka ɗaura mata gyale mai nauyin zinariya, aka raka ta da kalangu da wake-wake, aka saka ta cikin motar farin Lexus, sai ga kafila ta nufi birnin Abuja. Amarya ta fito daga ƙauye—amma fuskarta na cike da tambayoyi. Shin me birnin ke ɓoye mata? Me Alhaji Saminu zai kasance gareta? shin wannan aure zai fassara soyayya ne, ko wata kyauta ta biyayya ce da ba zata taɓa jin daɗin ta ba? ********************************* Juyawa tayi da ƙarfi kamar wadda aka hangi zuciyarta ta nitse cikin ruwan kogin ɓacin rai. tana mai huci da numfashi mai nauyi, ta faɗa jikin Moddibbo kamar jaririya, ta rungume shi da ƙarfi, tana kuka mai girgiza zuciya dukkan gangar jikinta na rawar jiki, murya na rawa kamar ana buɗe gidan hawaye a zuciya. Moddibbo ya kama kanta yana bubbuga bayanta da hannunsa mai sanyi da tausayawa. "Allah ya sa ki dace Halimatu," ya faɗa da wani murya da yafi shiru nauyi. "ki rike mutunci, ki tsaya da imani kiye koyar da mahaifiyar ke a fagen haƙuri zaki ci ribar zaman duniya ... rayuwa ce bata da tabbas." Shi kansa idonsa cike da ruwa, kodayake zuciyarsa ta taɓu sosai—ya jima yana kallon Halima tamkar zinariyar sa wanda yanzu ya mika hannunsa ya mika ta ga duniya. ya mika al’amuranta ga wani mutum da ya fi shi daraja da kima, amma ba shi da tabbacin soyayya. Bayan kuka da ban kwana mai cin rai, sai Halima ta shige cikin motar Alhaji Saminu da zuciyar da ba a iya fassara. Alhaji yana ƙoƙarin rarrashi da annuri, yana ƙyalƙyala dariya mai taushi yana faɗin: "Amaryata kada ki damu, Abuja ba abin tsoro ba ne ke zauna lafiya, za ki ga alheri." Halima bata ce komai ba ta fuskanci gilashin motar tana kallon ƙauyen su da ke raguwa a bayanta kamar mafarkin da ya ɓace. hannunta na cikin haɗaɗɗiyar rigarta, amma zuciyarta na cikin tsohon zanin ƙauyenta. Motoci suka fice daga Gembò, suka fasa hanyoyi masu kura, suka dosa garin Yola inda jirgi zai tashi zuwa Abuja. Halima na zaune cikin mota, amma kamar a mafarki

Chapter 4 of 18