ashe kai ne?! Wannan ba mafarki bane?"
Munir ya ce cikin natsuwa:
"Rayuwa ce Ado, sai da ta ɗauki ruwa, sai yanzu ta dawo da iska mai sanyi."
Little Yazid kuwa ya kwaso gudu ya faɗa jikin Munir suka rungume juna sosai.
Najeeb ya dafa kan sa yana murmushi:
"Kai Yazid! Ashe yanzu kai ne ƙaramim Yazid namu da na rasa shekaru da dama?"
Iman kuwa... ta tsaya daga nesa, tana kallonsu kamar wanda ke kallon fim.
Ta ɗauki wayarta, ta fara ɗaukar hoto da hawaye a idanuwanta — hawaye masu daɗin gaske.
tana ɗaukar hoton komai da komai — kama daga Ihsan da Maryam, zuwa Ado da Munir, har zuwa Yazid da Najeeb.
Sai ta ce da zuciyarta:
"Wannan hoton, ba kawai na dauka bane. Na ɗauki tarihi ne... labari ne da zan tuna har ƙarshen rayuwata."
AFTER SOME HOUR'S
Motoci uku ne suka ratsa cikin wani sanannen layi na 'Yan larabawa a Makka. Layin da kowanne gida ke da masallaci a ciki, kuma gidaje masu ƙamshi da tsari na Musulunci da larabci irin na asali.
A cikin mota ta farko akwai:
Maryam, tana riƙe da hannun Ihsan, sai Iman dake gefe tana kallon titin da shakku da tsoro da farin ciki ke rikicewa a fuskarta.
Mota ta biyu:
Najeeb a kujerar direba, sai little Yazid
Motar ƙarshe:
Ado da Munir suna hira da dariya irin wacce ba su yi tsawon shekaru goma ba.
A karshe suka tsaya a gaban wani katafaren gida mai babbar ƙofa da alamomin larabawa a jiki — filastik na zinariya da yashi.
Kofar gidan har da gardin larabawa biyu masu rawani da alamomin tsaro. Gidan yana da babbar alamar "Bayt Al-Rahma" — Gidan Rahama.
Sun shigo babban parlour mai faɗi kamar fili — fentin fari, ja da zinariya, fitilun chandelier guda biyu sun rataye daga saman rufin da ke da ado na gold calligraphy (zane na kalmomin larabci).
Cikin gidan akwai:
Sofa masu launin beige da ruwan zinariya.
Big-screen plasma TV a bango, yana nuna hoton Ka’aba kai tsaye daga Masjid al-Haram.
A tsakiyar bango babban Frame da aka rubuta “After the Moon – Bayan Wata”, tare da hoto na matafiya biyar a cikin sahara – Ihsan, Maryam, Munir, Yazid Ado.
Haddimai larabawa biyu suka karɓi jakunkunansu, suka miƙa musu ruwa da gahwa a gilashin zinariya.
Sautin oud (wakar larabawa) mai sanyi na fita a hankali daga bangon waje.
Maryam ta kama hannun Ihsan suka zauna akan kujera, Iman ta zuba ido tana kallon bangon da hoton su.
"Wallahi... wannan gida ne na gaskiya," Ihsan ta faɗa cikin sauke numfashi.
Najeeb ya kalli frame ɗin hoton da ke bango ya ce "Wannan shine burin Mahaifiyata – a taƙaice rayuwar ta na baya ya dawo a zahiri cikin hoton da zai zauna har abada."
Munir ya dafa kafadar Ado ya ce "Ado, yanzu gaskiya ta bayyana. Rayuwa ta gyaru mun dawo gida."
Yazid kuwa yana zagaye da dariya, yana shan juice, yana cewa:
"Daddy Najeeb, ni yanzu na zama ɗan gida biyu fa!"
Idan har kunjee daɗin page nin naga alert a opay na 🤣🤣🤣🤣
Narnah ƙanwar soja ✍️✍️
https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC
🎇BAYAN WATA 🎇
( Beyoung the moon ).
SABON SALO
Labari da tsarawa
Narnah ƙanwar soja
( Sayeedan Adda )
*********
HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA
Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya.
*****""
Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏
ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫
Page 52 / 53
Yau da rana bayan sun sauke kaya, sun yi wanka sun ɗan huta, gidan ya dauki shiru mai daɗi irin wanda yake zuwa ne kawai bayan gajiya da soyayya, a ɗayan zauren falon, little Yazid da Najeeb suna zaune akan ɗaya daga cikin ƙananan kujeru kusa da window mai labulen zare.
Yazid: “kamar ka taɓa zama dan sanda fa, yadda kake tafiya da tsari.”
Najeeb (yana dariya): “kai kuma kamar ka taɓa zama dan leƙen asiri – sai ka ce kana da sirrin duniya.”
Suna nan suna dariya, kamar yara biyu da Allah ya haɗa saboda zuciyarsu ta dace – duk da cewar yau ne haɗuwarsu ta farko.
IHSAN & MARYAM
A ɗaki mai launin sanyi da kyawawan labule masu zinariya da shukoki na artificial, Ihsan da Maryam suna zaune akan gado suna shan gahwa da busassun ƙwai da miya.
Ihsan (ta kama hannun Maryam): “Maryam... ashe rayuwa zata dawo da mu haka?”
Maryam: “Ni ma ban taɓa tsammanin ba. Amma in Allah yana rubuta abu – zai faru ko ina, ko ta yaya.”
Suka yi shiru na lokaci, suna kallon juna da hawaye masu ɗauke da dariya a cikin idonsu.
A wani ɗaki na yara da aka kawata da ‘yan teddy bear da ƙamshi na vanilla, Iman ta zauna tare da wata yarinya mai shekaru 12 mai farin fata da dogon gashi.
Yarinyar: “Sunana Layan Momi Maryam ce ta ce ki zauna da ni har sai kin huta sosai.”
Iman (ta rike hannunta): “Na gode Layan. Kin daɗe a nan gidan?”
Layan (ta murmusa): “Tun ina shekara shida. Gidanmu ne yanzu.”
Suka zauna suna hira, har Layan ta kawo mata hijabi mai launin ruwa da hoda. Iman ta sanya shi a kai, suka kallon juna cikin madubi suka ce a tare “Beautiful!”
DA DARE DINING ROOM
Ana kwana biyu da isowarsu, da dare suka haɗu a babban daining table mai zagaye. Fitilun zinariya suna kan low dimming, kamar cikin film Abincin da ke jikin table:
Kabsa mai daddawa da nuts
Maraq da lamb
Hummus, tabouleh, da fatayer
Kunun zaƙi da dates
Laban (madarar larabawa mai sanyi)
Maryam ta zauna gefen Ihsan, Najeeb kusa da Yazid, Munir da Ado a gefen hagu. Iman da Layan suna gefe suna dariya a hankali kamar ‘yan mata masu sabuwar ƙawance.
Ado: “To yau mun huta gobe mu fita ziyara!”
Ihsan (ta ɗaga glass ɗinta): “Ga rayuwar da muka dade muna mafarki da ita.”
Suka ɗaga hannu suna yi wa Allah godiya. Duniya ta dawo da murmushi bayan Wata ya ɓullo.
Suna zaune a falon da yake kallon ka’aba daga tagar gilashi mai shara-shara kowa na sanye cikin kayan sanyi masu kyau, dakin na ƙamshi da turaren Oud da jasmine.
Dining table na jiya an gyara shi yanzu zuwa karamin round-table mai coffee da snacks. Iman ta ɗauko karamar wayarta ta ajiye a gefenta.
Ta gyara zama, ta gyara murya, ta ɗan tabe hancinta da style irin na ‘yan jarida Iman (ta kalli Munir):
“Daddy Munir, kafin mu fita ziyara — ni dama akwai tambaya mai nauyi a zuciyata tun jiya.
*Yaya kuka tsira daga ‘trailer’? Bayan aka kwashe ku — me ya faru da ku da Aunty Maryam?
Bayan wata… yaya ‘bayan watan’ naku ya kasance?”
Ɗakin yayi shiru. Kamar ana sauraron azan daga sama Munir ya kalli Maryam, ta gyada kai da idon da ke cike da kewa.
Ya lumshe ido sai ya fara da muryar tausayi wanda zuciyarsa ke da ƙarfi, amma yana ɗauke da raunukan tunani:
“Bayan mun rasa motar nan… bayan an kwashe mu daga trailer ɗin nan da ba zan taɓa mantawa da wari da zufan cikinta ba — sai muka tashi ne a wani sansani a chan gabashin Makka, inda aka ware mu daga juna.
Ban san inda Maryam take ba ban san ko tana raye ba kuma lokaci bai tsaya mana ba — sai ya cigaba da juyawa.”
Ya cigaba da cewa:
“Wata mata Balarabiya ce — ba ta da haihuwa, ta karɓe ni a matsayin ɗanta a lokacin da nake a asibitin da suka ajiye mu bayan mugun ciwon da na sha.
A can na girma... amma zuciyata kullum na mafarkin wani abu daban. Na san ban da cikakkiyar dangantaka da kowa a can — amma rayuwa ta tilasta in gamsu.”
Maryam ta ɗora:
“Ni kuma na samu wani bawan Allah da ya kai ni hospital a Isra'ila. Daga baya ya shirya min takardun tafiya Makka inda na zauna a gidan wata tsohuwa har muka sake haduwa da Munir inda yake aiki a ɓoye kamar ne wasa da gaske muka bayyana wa junnan mu sha'awar aure bayan wani lokaci kadan na samu cikin NAJEEB kuɗi ya fara budewa mukaye biza har muka samu Manyan manyan dama na samun kuɗi Muka koma Saudi da aka ba shi aiki.”
Duk suka juya suna kallonta. Maryam ta kama hannun Munir.
Maryam (cikin shashsheƙar murya):
“Mun shafe shekaru muna addu’a mu sake haɗuwa. Sai Dubai — sannan Makkah — yanzu Allah ya cika mana.”
Iman tana ta rubutu da ido da zuciya.
NAJEEB kuwa — sai kallon Iman yake yi. Yadda take saurare da nutsuwa, yadda kukan ta ke boyewa cikin dan murmushi — ya tabbatar da wani abu:
Soyayyarta na fizgar zuciyarsa fiye da duk wata sanarwa da ya taɓa karantawa.
Sai yace a cikin zuciyarsa “Bari na bayyana komai… amma a lokacin da zai dace — tunda yanzu na san ina da muhimmiyar mace a gabana.”
Ado ya gyaɗa kai. Yazid ya shaƙe gaban Najeeb yana kallon sa kamar jarumi a cikin fim.
Layan da Iman suka kama juna da ido suka ɗan yi dariya.
Falon ya cika da nutsuwa — kamar an yanke ruwan rahama aka zuba.
Wannan lokacin — ba wai shiru suka yi ba — sai hawaye da murmushi. Bayan jawabin Munir da Maryam, sai kowa yayi shiru yana ƙoƙarin lissafa irin wahalar da suka sha kafin su haɗu.
Nan fa Ihsan da Ado suka ɗago kai.
Ihsan (ta dafe kirjinta):
“Wannan labarin sai dai a jikin zuciya — wallahi rayuwa ta juyi ne da kaddara. Amma yanzu, tunda Allah ya haɗa mu, zamu ci gaba da zama tamkar iyali.”
Ado ya ɗan share kwalla, sannan ya kalli su Maryam da Munir yana murmushi.
Ado:
“Mun shirya gayyatar ku zuwa gida da gobe — domin yanzu muna da kamfani mai suna “TALLAFI MATAFIYA” a Najeriya mun kirkire shi domin taimaka wa matasa da suka shiga wahalar neman visa ko tafiya ba bisa ka’ida ba. Mun riga mun buɗe rassan Lagos, Abuja da Kaduna.”
Maryam da Munir suna kallon juna, sai suka murmusa. Maryam ta kama hannun Iman tana kallonta da dariya.
Maryam:
“Ke dai ƴar jarida ce, amma sai kin ji namu ma. Komai da muke da shi yanzu yana nan a Makkah — ba Dubai ba.
Mun mallaki gida, kamfani mai suna Zauren Tafiya, inda muke bayar da training ga matafiya kafin hajji da umrah da kuma ‘yan kasuwa.
A nan Makkah muke — gida ne nan, kasuwanci na nan.”
Ihsan ta lumshe ido tana dariya, tana kallon Ado Ihsan:
“Toh mu fa arzikinmu na Dubai ne — nan da har sai an kira mu a Tashar Arabiya suna ce mana “Ƴan Kasuwar Duniya”.” suka yi dariya gaba ɗaya.
“Bari in faɗi gaskiya nan da nan: kun zama labari, darasi, da abin alfahari a rayuwata. Na gane cewa arziki ba Dubai ba, ko gida mai hawa goma ba — arziki shine lokacin da Allah ya yarda ka tsira kuma ya haɗa ka da mutanen da ka rasa.”
Sai Iman ta ce da murmushi tana kunna recorder Iman:
An gama ziyarar Ka’aba da sallar harami, sun gama siyayya — kaya na larabawa, turaruka, agogo, ababen tunawa. Fuskokin su cike da annuri da kwanciyar hankali.
Motoci sun shiryu a gaban katafaren gidan da suka sauka. Ƴan haddimai na jera akwatuna cikin natsuwa. Ihsan da Maryam na cikin motar gaba suna sanye da kayan hula da tabarau masu kyau. Iman da yarinyar gida na gefe suna dariya. Najeeb da Yazid suna musayar waya kamar tsofaffin abokai. Ado da Munir suna kallon komai da jin daɗin cikar buri.
Yazid (yana kwala kira):
“Dubai... we are coming!”
Iman ta fito daga wanka cikin hanzari, ruwan zafi na ci gaba da fita da ƙamshi a dakin. Guntun tawul ɗin da ta ɗaura a jikinta ya janyo hankalin numfashinta da gaggawa. Gashinta ya barbaje bisa kafadunta, yana ɗiga ruwan sabulu mai ƙamshi kamar 'attar Halabi'.
Tana juyawa zata ɗauki doguwar rigarta kenan —
Sai taji an bubbuga ƙofar sau biyu, da ƙarfi, kamar ana neman rai.
Ta tsaya cak Gabanta ya fadi.
“Iman…” murya ce daga waje — muryar da take gudu tun jiya. Najeeb.
Yadda muryar tasa ta fito, a matakin da ke tsakanin tausayi da ƙauna, sai zuciyar Iman ta shiga wani sabon yanayi. Ba ta buɗe ba, sai dai ta jingina da bango, zuciyarta na bugawa.
“Ba wai zan tilasta ki ba, amma… Iman, ki saurare ni. Idan ma zan bar duniya ne da kaina, zan fi so na bar ta bayan kin ji gaskiyar zuciyata.”
Shiru. Sai murya mai rauni daga cikin ɗaki:
“Kayi tafiyarka Najeeb babu wani abu da ya rage tsakaninmu.”
Shiru sai dai a zuciyar ta, Iman ba ta iya kwantar da ruwan da ke motsa a kirjinta ba. bai ce uffan ba — ya bar kofar a hankali.
Ita kuma ta zauna kusa da gadonta, tana matse tawul ɗin jikinta, tana kallon hular gashinta da ke gefen madubi, tana tunanin yadda zuciya ke da rauni fiye da fata.
Iman ta juya da sauri, tana ƙoƙarin buya, amma ruwan da ke ratsawar jikinta da tawul ɗaya ya hana ta daidaituwa. Sai wani yatsin ƙafarta ya kwace...
Wuffff!
Kafin ta faɗi — hannunsa ya kama ta. Ya tallabe ta da ƙarfi, jikinta ya sauka daidai a ƙirjinsa, inda fuskarsu ta gogar juna.
Shiru...
Numfashinsu na haɗuwa, kamar ana karanta sirrin zuciya a cikin iska mai dumi.
Gashinta mai ɗumi da kamshin sabulu ya rataya a gefen fuskarsa, yana bin ƙamshi kamar furanni masu tsiro bayan ruwan sama.
Idanunta biyu sun lumshe, na shi kuma suna kallonta — a tare da mamaki da al'ajabi.
“Iman…” ya ce da ƙasa-ƙasar murya, kalmomin da suka fita daga cikin zuciyarsa kamar kirari.
“Na…na faɗi,” ta ce a hankali, tana juyar da kanta a hankali cikin kunya.
Ya jinjina kai “Na kamaki ne... ba don na shirya ba, sai don zuciyata ta kasa bari ki faɗi.”
Zuciyarta na dukan wani irin bugun da ya saba da kwanciyar hankali. Ya lumshe ido, ya dan ja numfashi — kamar yana gasa da zuciyarsa ta gaskiya da wuta.
“Ki yarda da ni Iman... Ina sonki ba son da ya zo da ido ba — son da ya fara da tsoro, ya girma da ƙauna, kuma yanzu ya zama imanina.”
Ta ɗago kanta da ɗan sauri, tana kallonsa.
sai ya janye hannunsa cikin nutsuwa da ladabi “Ina jiran lokacin da zaki so na... da zuciyarki. Amma har yanzu — bari na tsaya a gefe.”
Ya juyawa ƙofar baya yana tafiya, amma a karon nan, ita ce ta kalla bayansa.
Kafin ya fice, ta ce cikin siririyar murya:
“ba zan manta wannan rana ba.”
Ya tsaya kadan, ya dan lumshe ido. Sannan ya fice Ƙofa ta rufe, zuciya ta buɗe.
Iman ta zauna a gefen gadonta, tana matse tawul ɗin jikinta, amma ba sanyi take ji ba — zuciyarta ce ke tafasa. A tsakankanin kaifin tunani da sanyin zuciya, kalaman Najeeb suna maimaituwa a kwakwalwarta kamar faifan waka mai raɗaɗi:
"Idan zan bar duniya... zan fi so na bar ta bayan kin ji gaskiyar zuciyata."
Ta runtse ido.
Ta tuna lokacin farko da suka haɗu, lokacin da zuciyarta ta fara dukan wani irin bugun da bata taɓa saninsa ba. Duk da girman laifin da ya taɓa aikatawa a baya, zuciyarta ta ƙi daina tuna shi da haske fiye da duhu.
Sai kawai...
Ƙofar ta bude.
Iman na zaune a bakin gado, lulluɓe da dogon veil mai launin zinariya, amma ba zuciyarta bace da launin farin ciki ta rasa yadda zata warware duniyar da take ciki — soyayya, kunya, da wani abu da ya fi ƙarfi da kalmomi.
Kallon da ya biyo bayanta a jiya har yanzu yana ratsawa a kwakwalwarta. Murmushinsa, shigarsa, murya mai natsuwa... da hannunsa da ya riƙe ta a lokacin da zata faɗi.
Tunani ke nan har sai ga ƙaran takun sa na shigowa falo.
Najeeb.
Ya shigo cikin shigar jallabiya ta larabawa, farin karfi, gwanin burgewa, da hula mai ƙyalli a kansa. Fuskarsa ta shafa attar mai ƙamshi, gashinsa yana kwance a gefe, idanunsa kuwa su ne suka dawo da ita daga cikin tunani kamar an buɗe kofar sirri a zuciyarta.
Ta ɗan girgiza kai, tana maida hankali.
Ya ce da murya mai nutsuwa:
“Iman, lokaci ya yi muna shirye tafiya.”
Ta ɗan gyaɗa kai, tana ƙoƙarin ƙyale kallonsa, amma bai yiwu ba kallon da yake mata yanzu… shi ya fi duk wanda ya mata a baya girma da nauyi.
Ta miƙe tana kallon ƙasa, zuciyarta na rawa kamar rigar ruwa.
Suka kama hanya zuwa filin jirgi a cikin mota ana dariya da raha. Ihsan da Maryam a gaba, Ado da Munir a wata motar, sai su Najeeb da Yazid a motar su.
Iman na zaune kusa da Najeeb, amma sai da nisa — kamar tana jin ana karanta sirrinta.
A cikin jirgi, komai ya lafa. An zauna cikin nutsuwa. Ana cikin iska mai sanyi, ana kallon ƙasa daga sama.
Ta juya ta leƙa Najeeb da sauri, sai suka haɗa ido.
Bai ɗauke nashi ba.
Ita kam sai ta kauda nata, amma zuciyarta na ambato: “Wannan kallon, me yake nufi? Me yasa yaki sauka?”
Ta daure zuciyarta, ta kifa kai, amma numfashin zuciyarta na tafasa kamar ba jirgi suke ciki ba — kamar zuciya ce a gaban gobara.
An sauka.
Sun sauka lafiya a Dubai.
Wata babbar motar kirar Rolls-Royce Phantom ce ta karɓo su daga filin jirgi — sai wata bus mai zaman kansa don ɗaukar kayayyaki da sauran su.
Iman ta kalli birnin daga cikin gilashin motar. Hasken fitilu yana walƙiya kamar taurari sun gangaro duniya. Dukkan alamun birni mai wayewa da yalwar arziki ne — amma zuciyarta… zuciyarta ba fitilu take gani ba, kallon Najeeb ne kawai ke mata haske da duhu a lokaci guda.
Bayan mintuna talatin, suka isa.
Gidan ya tashi har sama:
Ginin bene ne na falon hawa biyu, fentin launin shunayya da zinariya, tare da fitilun chandelier masu launin blue crystal daga Austria. Kofar gidan ba ƙaramar ƙofa bace —
ta sarauta ce! A saman kofar, an sassaka sunan:
"Bayt Al-Hikmah — The House of Wisdom & Grace."
Falon shiga kuwa… babu inda za ka kalla ba tare da ka tsaya ba. Kushin Turkish, gilashi na Paris, shinfidar Morocco, bust of love carved in white marble — komai na nuna cewa Ado da Ihsan sun mallaki duniya da duniyar zuciya.
Wata sabuwar mace ta karɓi Iman, ta ce:
“Welcome, beautiful lady. Your room is this way…”
An kai Iman wani ɗaki da ya dace da sarauniyar larabawa. Gado mai launin milk gold, labule mai sheƙi, da jakuzi a wani sashe mai moonlight tiles. Ta tsaya tana kallon kanta a madubi, sai kuma taga Najeeb a baya.
“Iman,” ya ce da wata murya mai sanyi, “zaki iya hutawa yanzu. Amma bana tunanin zan iya hutawa idan har...”
Sai ya tsaya. Ita ma bata ce komai ba.
Zuciyarta sai harbawa take kamar ana bugunta da rawani.
Ya ɗan matso kusa “Na san akwai abinda ke yawo a zuciyarki, Iman. Amma ki sani — tun farko ba zato ba tsammani na faɗa tarkon da ba zan so kubuta ba...”
Ta juya a hankali, idanunta sun cika da soyayya da tsoro.
Ya matso. Kamar ba kowa a duniya sai su biyu.
Sai yayi murmushi yana faɗin:
“Jiya... lokacin da na tare ki daga faɗuwa, na fāɗa — a zuciyarki. Kuma har yanzu ban samu hanyar fita ba.”
Iman ta kauda kai, amma fuskarta na fashe da laushi da launin fatan so. Kafin ya ce wani abu, sai wata yarinyar gida ta shigo da ruwa mai sanyi da kunu, tace:
“Ma’am, dinner is ready. Everyone is at the table.”
Najeeb ya janye a hankali, yana kallonta har ya fita. Ita kuwa ta zube a jikin madubi, zuciyarta na bugun kalmarsa. “Na faɗa… kuma ban fita ba.”
Dinning Hall — Cikin Dare, Cikin Rabo
Wurin cin abinci kuwa wani sashe ne daban. Babban teburin marble mai siffar daraja, fitilu a sama kamar taurarin Burj Khalifa, abinci kuwa larabci da na Nigeria sun gauraya — hummus, lamb mandi, dankali spicy, tuwon shinkafa da miya.
Maryam da Munir, Ado da Ihsan, su Yazid da Najeeb da Iman — sun zauna cikin farin ciki da raha.
Amma idanun Iman da Najeeb… su kadai suka fi magana a ɗakin. Kallon da bai da kalma, murya da bai da lafazi.
Sai zuciya da zuciya ke karɓar saƙo.
Washegari da safe.
An shirya. An sa kaya masu kama da casual official. Iman na cikin wando mai siririyar fata da riga mai launin cream, gashinta a daure cikin salo na 'Elegant Bun', Najeeb kuma cikin farin shirt da bakar wando, sai turaren sa mai sanyi da gwaninta ya gama janye hankalinta.
Sun fito tare da Maryam, Munir, Ihsan da Ado. Motoci biyu suka nufi katafaren “Al-Manāra Travel Support Holdings”, wato Company ɗin da ke taimaka wa matafiya da kuma masu neman mafita daga wahalhalu irin su hijira, asara, da barazana.
AL-MANĀRA HOLDINGS — CIGABA DA JINƘAI
Ginin yana tsakiyar Dubai, kusa da Business Bay. An yi masa gini mai siffar fatauci da aiki — amma cikin aminci da kamala. Ko da suka sauka, wasu ma’aikata suka fito da gaisuwa da fara’a.
“Marhaban! Mr. Ado, Mrs. Ihsan! Welcome home!”
An yi musu jagora zuwa babban hall — inda hotunan matafiya biyar (Maryam, Munir, Ihsan, Ado da Yazid) suke rataye cikin manyan frame, suna wakiltar labarin gaske da azanci.
Najeeb da Iman na tafiya gefe guda.
A lokacin da ake gaisawa da shugabannin ma’aikata, Iman da Najeeb suka ɗan ja gefe suka tsaya a wani corridor wanda aka kawata da window masu kallon Emirates Tower.
Kamar daga sama aka saukar da nutsuwa — babu hayaniya, babu kururuwar birni. Sai numfashin juna kawai.
Najeeb ya ce da ita a hankali:
"Iman, na fahimci duniya ba ta da wani armashi idan babu wanda kake so a cikinta."
Ta kalle shi kamar tana ƙoƙarin musun kanta.
“Ka tabbata kuwa?” ta ce, idonta a rufe, muryarta na raɗa.
Ya matso kadan, ya kama hannunta cikin nata:
“A cikin wahala na rayuwa, Allah ya ajiye min ke a matsayin rahama kuma soyayyarki… tafi Dubai da duk daular duniya daraja a zuciyata.”
Ta fashe da murmushi, sai hawaye suka gangaro kadan.
“Na so ka tun farkon haduwarmu, Najeeb. Amma tsoro ne ya hanani furtawa.”
Sai suka rungume juna a hankali — hug mai cike da soyayyar gaskiya ba wani lallata ba.
Kamar komai ya tsaya sai su biyu.
Sai shiru sai bugun zuciya.
A wannan lokacin ne Ado ya leƙo daga gefe, sai ya kalli Maryam yana faɗin:
“Na ga hasken soyayya. Yau kam, mun cika alkawari — daga wahala zuwa farin ciki.”
An yi hoto tare a gaban ginin, tare da ɗaukar documentary short daga Iman, domin jaridar da take aiki da ita a Najeriya. Ta bayyana cewa yanzu Al-Manāra Holdings za ta buɗe reshe a Abuja domin taimakawa matafiya marasa galihu.
Iman ta juya ta ce:
“A duk inda mutum yake a duniya, akwai fata. Amma idan aka ba mutum ƙauna da dama — sai ya zama tauraro da kansa.”
Najeeb ya ce “Iman… ke tauraruwa ce da ba zata taɓa dushewa ba.”
DUBAI TO ABUJA
Bayan dawowa daga Dubai, su Najeeb da Iman da sauran iyalai sun huta a wani katafaren gida a Asokoro, Abuja — gidan Ihsan da Ado suka mallaka tun kafin tafiyarsu. Lokacin da aka shakata, sai suka shirya tafiya Kano domin cika wata alkawari da suka ɗauka tun lokacin da suka sha wahala.
Yazid ya mutu a hanya — mutuwar da ke ɗaya daga cikin manyan tabo da suka ɓata zuciyar su. Amma yanzu lokaci ne na fansa, na lada da alheri.
KANO – GIDAN YAZID FOUNDATION
Sun iso cikin manyan motocin girmamawa. Wani sabon katafaren gini da ke gabar kwanar Hadejia Road, an ɗora Foundation ɗin da sunan:
Yazid Foundation — Gida na Ƙauna da Taimako.
Cikin gidan marayu da dakunan kwana da nishaɗi.
Makarantar addini da boko mai girma da aka rubuta a saman kofar sa:
"Wannan gida ne na kyautatawa domin ladar rayuwar Yarima Yazid — wanda bai rayu ba amma ya bar daraja."
Maryam ta tsaya a bakin kofar masallacin da hawaye suka cika idonta. Munir ya riketa a hankali. Ihsan da Ado na tsaye gefensu, suna fuskantar sabuwar hanyar alheri.
A CIKIN MASALLACI
An gudanar da walimar saukar Alkur’ani daga yara marayu guda goma sha biyu da suka rigaya suka haddace., domin girmama sunan marigayin.
Najeeb da Iman sun zauna gefe a gaban masallaci. Lokacin addu’ar kabari, Iman ta saka ƙwalla cikin zuciya ta ce:
"Ya Allah, ka bawa Yarima Yazid mafaka mai albarka. Ka sanya wannan gida hujja mai haske gare shi."
Najeeb ya kama hannunta a hankali, ya ce:
"Yazid ba ya nan da jiki, amma ran mu cike yake da shi. Kuma wannan gida, wannan aiki, ya fi duk daular duniya."
a nan aka roƙi addu'a, aka karanta suratul Mulk, sannan aka watse da nutsuwa da tausayi.
Gida ya cika da yara marayu. Najeeb da Iman sun kafa wani shiri mai suna "Matafiya Cikin Ƙauna" wanda ke ba da tallafi da damar rayuwa ga marasa galihu da ‘yan gudun h
da ‘yan gudun hijira.
ALƘALAMIN NARNAH
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 18