Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ƘANWAR SOJA ✍️✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC 🎇BAYAN WATA 🎇 ( Beyouda ‘yan gudun hijira. ALƘALAMIN NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️✍️✍️ng the moon ). SABON SALO Labari da tsarawa Narnah ƙanwar soja ( Sayeedan Adda ) ********* HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya. *****"" Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏 ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 Page 54 / 55 SECOND TO THE LAST PAGE BARKA DA JUMA'ATU BABBAN RANA Washegari bayan dawowa daga ziyarar kabari da buɗe gida, Maryam ta buƙaci su tafi wani wuri — wani wuri mai nauyi a zuciyarta, inda duk wasu damuwa da jin ƙasa suka fara a rayuwarta. Su Munir da Iman da Najeeb da sauran ‘yan gida suka rakata cikin nutsuwa. Motoci suka nufi tsohuwar unguwar su Maryam, anguwa da yanzu lokaci ya sha kanta amma ƙuruciyar rayuwa ta Maryam ta tsaya a cikinta har yanzu. Gidan da suka tsaya ba babba ba ne. Gida ne da duwatsu da tubali suka hau a kai, buhun shara ya makale a jikin bango, ruwan famfo na zubowa a gefe. Wani ƙaramin bishiya ya toshe rabin kofar gidan. Amma duk da haka, akwai ɗan ginin tarihi da ke bayyana cewa: "Wannan gida na Maryam ce — iyayenta suka gina shi da hannu, da jinƙai da addu’a." Maryam ta tsaya gaban ƙofar gida, tana kallon fatar bango da ke fallarwa kamar yana faɗin: "Kin dawo, ‘yar gida. Mun kiraki shekaru talatin da suka wuce." An shiga ciki. Duk da cewa gidan yana buƙatar gyara, amma yana cike da numfashin ƙuruciya bango da aka daɗe ba a shafa ba, ɗakin da ta taɓa kwana a ciki tana kuka da yunwa, da kwandon da mahaifiyarta ke ajiyewa shinkafa. Maryam ta tsuguna a ɗaya daga cikin dakuna tana shafa ƙasa. Munir ya tsaya yana kallonta. Iman ta kama hannunta tana kuka. Maryam ta ce a hankali: "Wannan ƙasa ce ta rayuwata. Duk duniya na zagaya, amma ina da iyaye da suka fara gina mini mafarki a nan — duk da ba su da komai sai kauna." Motar Maryam ta tsaya a ƙofar tsohon gidan mahaifinta. Wata ƙaramar kofa ce amma har yanzu tana da ƙwanƙwasa da ke sa mutum ya dakata kafin shiga. Duk gidan yana da warin tarihi, ko ƙamshin ƙasa mai ɗumi da fatar mutane masu tawali’u. Tana fita daga mota, sai zuciyarta ta ɗauki wani irin nauyi mai nauyi da sauƙi a lokaci guda. “Baba…” Kafin ta kai kofa, wani dattijo ya fito daga tsakar gida. Fatar jikinsa mai tsufa, kayan jikinsa daɗɗaɗɗu amma tsaftattu. Idanunsa suka sauka a kanta cikin mamaki da ƙanƙan da kai. “Maryam?” ya furta da wata murya mai karkarwa, kamar wanda ya kira mafarki ya amsa masa. Maryam ba ta iya jurewa ba. Ta yo guje kamar ƴar shekara goma, ta faɗa jikinsa tana fadin: “Na dawo Baba… Na dawo daga duniyar da ta raba ni da ku.” ya rungume ta, yana hawaye kamar karamin yaro. “Ashe ke kike nan? Ashe haka kika wahala? Ashe auren tsoho ya mayar da ke arziki da sayar da raina? Maryam… na rasa ke tsawon shekaru talatin. Kamar yau aka yanke ni daga zuciya ke gafarta min tursasawa da na miji a baya .” Daga cikin gida, sai ga wasu matasa guda uku sun fito da mace guda. Maza ukun ƙanninta ne — yara da suka tashi ba tare da cikakkiyar uwa da ta ci zarafinsu da azaba. Duk sun girma, amma zuciyarsu har yanzu da raunin rashin Maryam. Maryam ta zuba musu ido. Ta fahimce su — kamar yadda take fahimtar wuta idan ta ga hayaki. Ta rungume su ɗaya bayan ɗaya tana kuka, tana cewa: “Ku gafarceni. Na yi tafiya da ba zan iya bayani ba amma daga yau, zan zame muku uwa da ‘yar’uwa.” Matar kuwa, ‘yar kishiyar da ta wahala da Maryam, ta tsaya gefe tana kallon su. Maryam ta matso kusa, ta kama hannunta da ƙyautatawa tana fadin: “Kin sha wahala a nan, ba laifinki ba ne. Amma yanzu ba za mu sake rayuwa da ƙiyayya ba wannan gida zai koma gida na kowa da kowa.” Maryam ta ce da mahaifinta:“Baba, daga yau wannan gida zai zama Cibiyar Azanci da Kyautata Rayuwa. Za mu gina masa dakin koyon sana’a, dakin karatu, Kuma za mu sanya sunan ka a ƙofar gidan." Mahaifinta ya fashe da kuka yana fadin: “Maryam, ke ce ƙarshen mafarki. Wannan mutunci ya fi na duniya.” Munir da Iman da Najeeb da su Ado da Ihsan suna kallon abin cikin jin daɗi da girman zuciya. Duk suka yarda cewa gidan da aka barwa Maryam da hawaye, yanzu ta dawo da shi da alfahari. Dukkan maƙwabtan tsohon unguwar Maryam sun fito don maraba da ita. Kamar ba ita ba ce da aka manta shekaru talatin da suka wuce. Da wuya a tantance tsakanin hawaye da murmushi a fuskar mutane, domin dawowar Maryam tamkar dawowar haske ce bayan duhun shekaru. “Maryam, wannan gida har yanzu gida ne. Kuma yanzu mu ne za mu taimaka miki, ba ke kadai ba,” in ji wata tsohuwa da ke tsaye da kwanon tuwo a hannunta. Wani dattijo ya kawo jakar shinkafa. Wata mace ta kawo masara. Sauran suka kawo barguna, kwanuka, da kayayyakin amfani. Wasu kuma suka bada ginin da za a dawo da su ciki su huta kafin tafiya. “Wannan gari ba zai sake barinki ki fita da hawaye ba, Maryam,” cewar wani saurayi da ya taba kasancewa ɗan ƙaramin yaro lokacin Maryam tana da shekaru goma. Maryam ta juyar da idonta zuwa danginta: “zamu kwashe ku gabaɗaya zuwa Abuja. komai ya canza wannan gidan zai zauna a matsayin alamar juriya, amma zamu tafi domin a ji daɗi da walwala.” Bayan makonni biyu a Abuja, inda suka samu nutsuwa da kwanciyar hankali, sai abubuwa suka ɗauki sabon salo. Iman, ƴar jarida ce mai kwazo wadda ta tattara tarihin tafiyar su biyar cikin littafi a kafar BBC Hausa, an shirya ƙaddamar da litattafin mai suna: "BAYAN WATA" Labarin Gaskiya da Ƙalubalen Rayuwa Littafin ya ƙunshi: Tafiyar su daga Najeriya har zuwa Dubai Wahalar da suka sha Soyayya da ya fito daga cikin ƙura Mutuwar Yazid da yanda sunansa ya rayu Sabon duniya da suka buɗe a gida da ƙasashen waje, an gayyaci manyan mutane daga hukumomin lafiya, walwala, ma’aikata, da jaridu. Maryam, Ihsan, Ado, Munir, Najeeb da Iman sun zauna a gaban dandalin BBC suna kallon yadda littafin da Iman ta rubuta ke zama abin magana a duniya. “Labarin mu ba wai don a tayar da hankalin mutane ba ne, amma domin a fahimci cewa tafiya mai wahala ba dole ta ƙare da baƙin ciki ba. Akwai haske... a bayan wata,” cewar Iman cikin ladabi da ƙwarewar jarida. An kawata harabar BBC Hausa da tulin furanni, red carpet, da hoton murfin littafi "BAYAN WATA" a babbar bango. Dandazon mutane sun cika wajen. Ana watsa shirye-shiryen kai tsaye. Manyan mutane daga duniya suka halarta: Ƴan jarida, malamai, kungiyoyi masu tallafa wa matafiya, da wakilan kasashen waje. MC: “Bismillah… a yau muna maraba da labari wanda ya gigita zukata – da rai ya rayu cikin littafi. Mun haɗu domin ƙaddamar da BAYAN WATA, littafin Iman Ado matafiya” Da shigowar Maryam cikin shadda ta alfarma, sai aka ɗaga murya da tafi. Ihsan da Ado cikin zinariya da kayan alfarma. Munir da Najeeb cikin rigunan zamani masu kamshi. Iman kuwa cikin launin kore na natsuwa, tare da takalmanta masu walƙiya, ta shigo da dariya tana nuna tawali’u. JAWABI DAGA IMAN: “Na rubuta wannan littafi ne ba wai don in shahara ba, sai don duniya ta ji cewa rayuwa tana da tafarki — kuma a ƙasan ƙura akwai zinariya. Wannan littafi na fatan zai kasance haske ga masu rasa fata.” Maryam ta shafa hawaye tace: “Bana tunanin wata rana zan tsaya a gaban duniya in faɗi abinda na tsira dashi. Amma Allah ya kawo wannan rana.” NAJEEB & SOYAYYA Najeeb ya kalli Iman yana murmushi. Iman ta juya kanta, amma fuskarta na nuna jin daɗi. Bayan kammala jawabi, sai Najeeb ya miƙa mata furanni a gaban kowa: “Kin cika da ƙarfin hali. Littafinki ba kawai ya ba mutane ilimi ba, ya koya mana cewa soyayya tana da tushe.” Jama’a suka ɗaga hannu da tafi. An ɗauki hoto na musamman da hoton littafin, duka su biyar sun tsaya a gaban frame mai rubutu: 🖋️ “To all who walked in the dark, may you find your moon – Bayan Wata.” A cikin satin da ya biyo bayan launching, sun ƙaddamar da YAZID FOUNDATION a Kano: Gidan marayu Masallaci Makaranta Ruwan sha Tallafi ga mata da marasa galihu An buɗe kamfanoni a Abuja, Kano da Dubai. Littafin Bayan Wata ya zama sabon abun karatu a makarantu da kwasa-kwasai na lafiyar kwakwalwa da juriya. SECOND TO THE LAST PAGE BAYAN WATA NA BANKWANA FAN'S NARNAH ƘANWAR SOJA 🖋️💞 https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC 🎇BAYAN WATA 🎇 ( Beyoung the moon ). SABON SALO Labari da tsarawa Narnah ƙanwar soja ( Sayeedan Adda ) ********* HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya. *****"" Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏 ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 Page 56 / 57 THE LAST PAGE 23 / jun / 2025 Littafin Bayan Wata ya zama wani katafaren abin koyi a duniya baki ɗaya. Bayan an fassara shi zuwa harsunan Larabci da Turanci, ya zamo abin karatu na dalibai a makarantu, musamman a shirin JAMB Novel da darussan Hausa na zamani. Haka kuma, an ɗauki labarin zuwa tashoshin rediyo da talabijin inda aka shirya series na musamman da ke bayyana ƙalubale, soyayya da juriya, yana ja hankalin matasa da manya. Masu taimako da suka bayar da gudummawa a rayuwar Iman, Maryam, Najeeb da sauran su, an saka sunayensu cikin littafin da aka wallafa, da kuma nuna godiya ta musamman a cikin shirye-shiryen rediyo da fim-fim. Wannan ya ƙara musu ƙarfafa gwiwa da farin ciki, suna ganin yadda labarinsu ya taimaka wajen kawo canji da haske ga al’umma. An shirya gasa na maida labarin zuwa wasan kwaikwayo (drama/series) a cikin gida da kasashen waje, inda matasa da masu sha’awar adabi ke yin wasan kwaikwayo kan kowane muhimmin sashe na littafin. Wannan ya haɓaka sha’awar karatu da koyon darussa masu amfani cikin salo mai jan hankali. 1. Princess Rahilat Labari: Rahilat, yarinya mai zurfin hankali da jarumta , ta fuskanci ƙalubale da yawa a rayuwarta, musamman a cikin masarauta . Duk da haka, ta yi amfani da hikima da jajircewa wajen canza tsarin da ke kawo rashin da’a. Darasi: Adalci da kishin al’umma su ne ginshiƙan cigaba; kowa na da rawar da zai taka wajen tabbatar da gaskiya da tausayi. 2. Halimatu Sadiya Labari: Halimatu Sadiya, mace mai ƙarfi da himma, ta tashi daga ƙanana cikin talauci da ƙauyanci soyayya ce tsaftaciciya Amman kash mutuwa da rashin rabo shine sillar komai Darasi: Juriya, haƙuri da dogaro ga Allah sune makullin cimma nasara, musamman ga mata masu neman zaman kansu. 3. Aljannin Sajida Labari: Sajida ta samu wata aljaanin tun na kakan ta , wanda ya hana mata samun sukunin a zuciyar saurayin ta ko nace mijin ta . Darasi: Tsarkin zuciya da nufin alheri suna kawo kariya daga munanan abubuwa; addu’a da imani na da muhimmanci sosai shi kuɗi ba sai kayi tsafi kasa dangin ka cikin fitina ba . 4. Masarautar Zakar Labari: Masarautar Zakar ta kasance tana fama da rikici da rashin zaman lafiya, har sai wata mace mai hikima ta samu damar kawo sulhu da hada kan jama’a. Ta yi amfani da ilimi da sulhu don kawo zaman lafiya. Darasi: Sulhu da fahimtar juna sune mafita mafi inganci wajen magance rikice-rikice a kowanne mataki na rayuwa. 5. Kashifa Labari: Kashifa ta yi tafiya mai wahala dgaa satar Mangoro zuwa tsibirin aljannu Darasi: Fahimtar kai da taimako ga sauran mutane su ne tushen rayuwa mai ma’ana da jin dadi yafiya shine matakin rayuwa mai tsafta . Bayan Shekara Biyu AFTER TWO YEAR'S Bayan shekara biyu na aiki tukuru da bautar Umrah, rayuwar matafiya ta fara samun nutsuwa. A cikin wannan lokaci, an fara shirye-shiryen aure tsakanin Iman da Najeeb a Makka, cikin farin ciki da annashuwa. Duk da cewa sun sha ƙalubale, soyayyarsu ta ƙaru har ta kai ga wannan mataki na rayuwa. A cikin wannan lokaci, Yazid kuma bai tsaya ba. ya afka cikin soyayya da wata balarabiya mai ɗaukar hankali, mai ɗabi'a da mutunci a Makka wannan sabon soyayya ya ba shi sabon salo da sabon burin rayuwa, inda yake ganin wannan soyayya zata ciyar da shi gaba. Ana cikin shirin aure na Iman da Najeeb, yayin da Yazid ke cikin sabuwar soyayyar da ta ba shi kwarin gwiwa. Rayuwa ta ƙara ɗanɗano, kowane daga cikinsu yana cikin sabuwar babi na soyayya da ƙauna. Bayan bikin auren Iman da Najeeb, labarinsu ya bazu kamar wutar daji a kafafen sada zumunta — TikTok, Instagram, Facebook, Twitter, da duk wani shafin yanar gizo. Hotunansu suna ta yawo, mutane suna murna, wasu kuma suna kwaikwayon salon suturarsu da yadda suke nuna soyayya mai tsafta da ƙayatarwa. Suna sanya kaya iri ɗaya, masu launi da ƙayatarwa, sun yi fitowa cikin wani shahararren lambu mai tsarki a tsakiyar Dubai, inda hasken rana ke ta yi wasan launuka a cikin shuke-shuke masu ƙyalli. Najeeb, Iman, Yazid, da Muhibbat suna zaune a kan kujeru na fure, suna shan shayi da kayan zaki, suna hira cikin annashuwa. Najeeb ya mike ya ja hankalin kowa, ya ce, "Wannan shi ne farkon sabon rayuwa, ba kawai aure ba, har ma da soyayya da abokantaka. Mu kasance masu godiya ga juna da ga Allah." Iman ta yi murmushi mai cike da ƙauna, ta miƙa hannunta, suka rike hannu. "Na gode maka Najeeb, ka zama hasken zuciyata, abokin rayuwata." A gefe Yazid ya dube Muhibbat yana dariya, "Kin san dai, soyayya tana zuwa da ban dariya, kamar yadda kika kawo min farin ciki a Makkah." Muhibbat ta mayar da martani cikin wasa, "Toh, zan ci gaba da kawo maka farin ciki har abada." Sai su duka suka yi dariya, har wurin ya cika da annashuwa. Daga nan suka tashi suka fara rawa cikin salo na zamani, sai kuma suka yi wasan kwaikwayo na kalaman soyayya da barkwanci, inda kowa ya fara kwaikwayon yadda suke furta kalmomin ƙauna a lokutan ban dariya. Kowa na nuna salon sa na musamman, har suka jawo hankalin masu shan shayi a lambun da ke kusa. Bidiyon rawar su da nishadi ya bazu a dandalin yanar gizo, ya zama trending, inda mutane ke maimaita bidiyon, suna yi wa junansu tag, kuma suna ƙara godiya da fatan alheri. Hashtag ɗin #SoyayyaDaFarinCiki ya kasance a saman jerin abubuwan da ake ta hira akai a duniya, mutane suna aika hotuna, bidiyo da labarun soyayya da nishadi. Su ne jaruman soyayya, abokantaka, da farin ciki a duniya, kuma wannan rana ta kasance abin tunawa, wanda za a rika tunawa da shi a cikin zukatan masu karatu, a matsayin ƙarshen labarin da aka soma da ƙalubale amma aka ƙare da nasara da farin ciki. Duk wanda ya karanta wannan labari, ya fahimci cewa soyayya ta gaskiya tana buƙatar hakuri, tsayayye, da girmama juna, kuma farin ciki yana zuwa ne idan aka hada zuciya da zuciya cikin gaskiya da amana. Sakon Godiya daga Marubuciya: Sayeeda Assalamu alaikum wa rahmatullah, ALHAMDULLAH ALHAMDULLAH ALHAMDULLAH Ina mai mika gaisuwa da godiya ta musamman ga ku duka – masoya, masu karatu, da waɗanda suka ɗauki Bayan Wata ba kawai a matsayin littafi ba, har ma a matsayin aboki, mai karantarwa da mai tausasa zuciya. Nayi amfani da sako ukku Tunani bada labarin cikin labari rayuwa kamar ta gaskiya Labarin Bayan Wata ya fara ne daga tunani, ya zama kalmomi, daga kalmomi ya zama rayuwa. Kuna daga cikin waɗanda suka ba shi rai. Na gode da yadda kuka bi tare da shakku, hawaye, murmushi da daɗin zuciya. Na gode da comments ɗinku, da shawarwarinku, da jin dadinku a kowane page. Kun sa ni jin cewa kowanne rubutu yana da daraja, kowanne labari yana da tasiri. Ina mika godiya ga: Masoyan da suka tsaya tare da ni daga shafin farko har ƙarshe; Masu sharhi da karfafa gwiwa; Da wadanda suka raba littafin ga wasu har ya kai duniya. "Bayan Wata" ba zai tsaya nan ba. Wannan shi ne matakin farko. Ina fatan cewa zaku kasance tare da ni a sabbin littattafai da labarai da nake shiryawa – waɗanda za su ci gaba da nuna gaskiyar rayuwa, kalubale, da fatan nasara. Rayuwa cike take da darussa — daga soyayya, gwagwarmaya, da mafarki. Dukkan ku kun zama wani bangare na mafarkin nan. A karshe, ina cewa: Ku ci gaba da karatu kuci gaba da ƙarfafawa. Ku ci gaba da kasancewa sassa na zuciyata. Da soyayya mai tsarki, MY NEXT MOVE ZAƁIN ZUCIYA KADANGARE BAKIN TULU RUHIN MARAICE ZAƁIN ZUCIYA ZAI FARA ZUWA MUKU 1 GA WATAN BAKWAI Sayeedan Adda ❤️✍🏽 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 18 of 18