An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT
🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗
AFTER THE MOON🌕
BY
NARNAH KANWAR SOJA
MARUBUCIYAR
MIJIN MAGE
FARASHIN SO
BIYAYYA GA UWA
DUHU CIKIN HASKE
RUHI BIYU
HANYAR RUWA
MAI CIKI CE
MADOBIN IDO
AHLIN LASHKAR
PRINCESSS RAHILAT
RAYUWAR UMMAH
BAYAN WATA
SADAUKARWA
Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕
Zahrah Royal Star
GABATARWA
Wanan Labarin zai fara zuwa muku Ranar Litinin da yardar Allah shafin shine asalin gundarin labarin matafiya ne wanda suka bar kasar su zuwa wata ƙasa domin muradun su, a sannan labarin ne cikin labari domin dukkanin su zasu bamu labari mabanbanta daga cikin tafiyar su
sanin haƙiƙanin labarin lallai sun mun shiga ciki domin karatu tare....
Masu laɓe a cikin group wanan sabon littafi ku fitoo kafin ayi waje daku fatan zaku na sharhi da share Nagode..
Chapter 1 & 2
Tafiya Mabuɗin ilimi
بسم الله الرحمن الرحيم
اللهم صل على محمد وسلم
Ƙara duba email nasa yayi nan John ya dafa kafaɗar sa " Common man muna late fa " ajiyar zuciya ya sauke mai nauyin gaske cikin tunani tsarin ɓarauniyar hanyar da zasu bi daga Kano zuwa Dubai cikin kwana 150
Addu'a suka fara bayan kammala wa motar tasu ta zubin taxi ya tashe da matuƙar gudu
Duk wani abun buƙatar su na abinci kuɗi sutura tare da abun bukatar su na yau da gobe yana cikin wannan motar
Hannu tasa tana lissafi cikin buguwar zuciya
" Kano (Nigeria) Yobe → Chad → Libya → Egypt → Israel → Jordan → Saudi Arabia → United Arab Emirates (Dubai)
Yanzu wanan ƙasasshen dukka sai mun tsallake su Innallilahi wai'na illaihin rajiuon " take hawaye ya fara zubuwa a idon ta, harara Maryam ta buga mata " Haba Ihsan meyasa kina da saurin kuka ne tafiya ce kawai duk da munsan akwai wahala a hanyar mu amman ai muna tare ke tuna buri da muke dashi a rayuwar mu idan bamubar Nigeria ba ina zake samu bukatar aikin da muke so " ..
Tunda suke magana Yazid na latsa wayar sa wanda yake buga game nasa cikin nishadi sosai
Yazid ,
Yaro ne mai shekaru 25 a rayuwar sa ya gama makarantar secondary school sai dai yana da Babban buri a rayuwar sa ma buɗe katafaren Company gine gine hakan yasa ya yanke shawarar zuwa ƙasar Dubai inda suka samu labarin ana zuwa neman kuɗi sosai kuma ana dace domin kuɗaɗen su mai matukar girgiza ruhin mai neman kuɗi da wanan niyyar ya baro gida
Ihsan
Yarinya ce wacce take da shekaru ashirin a rayuwar ta sai dai ta tasu daga gidan marayu na nan Kano tabbas Ihsan yarinya ce mai basira sosai ga kuma kyau da ilimi sai dai Ihsan yarinya ce mai neman na kanta duk inda taga zata samu kuɗi tana zuwa neman aiki lungu da sako Ihsan yanzu babban burin ta shine ta samu jari sosai wanda zata fara kasuwanci gari zuwa gari har ma da ƙasasshen waje Amman yanzu dole sai ta tafe Dubai domin samun aiki ko na aikatau ne domin cikkar muradun ta.....
John
Idan ana neman yaro mai karfe da fikira to John ya samu wanan shaidar babban abokin Yazid kinan wanda suka ye makarantar tare sai dai shi ya samu aikin soja wanda aka Kore sa daga aiki dalilin mugun ƙazafin da abokan sa suka masa shi kuwa ya yanke hukuncin baren ƙasar domin ya tafe nemo kuɗi kodon huci takaice abinda aka masa .....
MARYAM
Kuna neman matsoraciyya yarinya ga tsoro ga rashin jin magana ga kuma taurin kai sai Maryam wacce take da shekaru ashirin da ɗaya chifff Maryam ta tasu gaban muguwar kishiyar uwa wacce sai abinda tace baban ta zaiyu hakan yasa take azabtar da Maryam ta kowani yanayi kyakkyawan yarinya ce ga ilimi boko da na arabiyya sanan tayi karatun health care ƙaramar nurse ce dalilin barin ta gida kuwa kishiyar uwarta ne ta yanke mata hukuncin auren wani tsoho a unguwar sa wanda baban ta ya amince hakan yasa ta gudu tabar gidan sai gashi ta haɗu da ƙawa a titti wato Ihsan wanan yasa ta yanke shawarar binsu chan ko ita ma zata tsira da gujje gujje da take ye akan hanya ..
ADO
Engineer kinan saurayi mai shekaru ashirin da tara mai hazaƙa da basira baiye makarantar ba sabo da tsananin talauci wa da bai san uwar sa ko uban sa ba a kan titti ya gansa yana tafiya bashi da kowa ko komai Amman ko wacce mota ce ya iya gyara ta sanan ya iya duk wani abinda ya shafe igiyar wuta, sanan ya taɓa shiga ƙasar Chad neman kuɗi a takaice dai Ado yana cikin wanan sahun tafiyar domin yana da buri mai yawa a rayuwar sa ...
A haka suka kama hanyar Yobe state domin fara tafiya zuwa Chad, muna fatan tafiya yayi kyau a dawo da cikakkiyar nasara...
Please don't forget to comment and share
Continued........
Narnah ƙanwar soja ✍️✍️
—
🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗
AFTER THE MOON
BY
NARNAH KANWAR SOJA
💫Royal Star Association,💫
SADAUKARWA
Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕
Zahrah Royal Star
Page 1 & 2
Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba ,
mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya
show me some love guy's 🩷
بسم الله الرحمن الرحيم
اللهم صل على محمد وسلم
Zaman motar ya fara yi musu nauyi tun kafin su iso Yobe daga nan sai suka shiga ƙasar Chad da yamma, rana ta fara dusashewa cikin baƙin gajimare da iska mai ɗauke da ƙura gaba ɗaya zuciyar su ta fara karaya koda kuwa basu furta ba.
John ne ya fara gyara zaman sa yana duba agogon hannunsa.
"Wannan hanya wallahi kamar babu wanda ke bi ta yanzu," ya faɗa cikin ƙaramin murya
Maryam ta kama hannun Ihsan tana danne tsoro da karfin hali, "Mun riga mun fito, ai sai gaba."
Motar ta dinga kutsawa cikin kura da kankara, har aka kusa tsallaka wata ƙaramar kwazazzaba da aka samu a tsakiyar duwatsu. wani ƙara mai firgita ya tashi daga motar.
"Grrrrkkk—krrr!"
Kafin su fahimta, tayar gaba ta tsinke da wani ƙarfi motar ta faɗi gefe kamar zata tintsire Yazid ya damƙe sitiyari yana ƙoƙarin tsayar da ita amma komai ya gagara Ado ya rike bangon motar yana fadin:
"ALLAHU AKBAR!"
Sai kawai suka ji "dduuummm!", motar ta buge da wata babbar dutse, ta tsaya cak anan ne shiru ya biyo baya, babu motsi, sai sheshshekar Ihsan da Maryam suna kuka.
Yazid ya fito daga motar yana duba tayoyi, idanuwansa sun cika da 'kura. "tayar gaba da gefe duk sun ƙone clutch ɗin ma ya tarwatse. muna cikin matsala mun rasa motar mu."
John ya farka daga karyewar da ya sha, ya dubi hanya yana shan iska mai zafi, sannan yace:
"Wannan ba hanya ba ce, wannan tabo ne. mu kwashe kayanmu mu shiga cikin dajin nan idan muka tsaya nan dare zai riske mu, barayi ko dabbobi za su iya far wa."
Babu wanda ya musa kowa ya ɗauki nashi kaya cikin tsoro da damuwa. Ihsan na riƙe da kwalbar ruwa, Maryam na lulluɓe da veil tana kare jikinta daga cizo.sun fara takawa cikin ƙaton daji, cike da raɗaɗin ƙasa mai kaifi da ciyayi masu yankan ƙafa Ado na gaba yana amfani da torchlight wayarsa yana duba hanyar da zasu bi tsakar dare ne lokacin da suka hango wani tsohon baranda kamar dafa-gari. ba za a iya ce masa gida ba, amma yana da rufi da bango.
"Mu tsaya nan mu huta. Allah ya kawo safiya lafiya," Yazid ya faɗa.
Maryam ta kifa kanta a kafadar Ihsan, tana kuka cikin salo mai ciwo, "Idan na mutu a hanya ki ba baba sanina... ki ce Maryam ba ta jure tsanani ba." John ya dan murmusa cikin firgici, "Zamu mutu fa kafin mu isa Dubai idan muke tsoron hanya haka tun a Chad."a haka dare ya cigaba da raguwa, zafin rana ya mayar da dare sanyi mai shigowa jiki kowa ya kwanta da kaya a jikinsa yana jiran asuba da fata, da addu’a, da fargaba.
Dare ya yi tsayin gaske kamar zai hana wayewar gari ,sanyi ya ratsa kowane sassa na jikinsu, kowane yana neman ɗan nutsuwa da kwanciyar hankali, amma babu shi.
sai dai ƙasa mai kaifi da raɗaɗin tunani.
Asuba na ƙaratowa, Ado ya farkar da su ɗaya bayan ɗaya.
"Ku tashi, lokaci yayi... sai mu yi sallah kafin rana ta fito."
Sun fito daga barandar ruwan zufa da ƙura na hade da jikinsu. kowa ya shimfiɗa ɗan zane a ƙasa, suka gabatar da sallah da natsuwa da ƙasƙantar da kai. bayan sun idar, Yazid ya zaro ɗan kwali daga cikin jakarsa.
"Ga ruwa nan da snacks ɗin biscuit da gurasa. Amma sai mu kiyaye amfani da su, ba mu san inda zamu isa da kafafu ba."
Ihsan ta amsa kwalbar ruwa tana goge fuskarta da tissue, Maryam na gefenta, kukan jiya ya bar wani ɗan kumburi a idonta.
"Da gaske zamu ci gaba da tafiya ne?" Ta faɗa da rauni.
"Me kike tunani?" John ya juyo yana gyara jakarta. "Za mu jira motar da ba za ta zo ba? Ko barayi su zo su kwashe mu da kaya?"
hka suka kammala shiryawa, suka kwashe komai da suka iya dauka akwai leda mai ɗauke da tuwo da miya wanda suka saya kafin shiga Chad, ruwan robobi guda shida, da wasu kuɗaɗen kasar da suka musanya kafin barin Nigeria.
Ado ya latsa map ɗin da ya saukar a waya, duk da babu signal sosai, yana ƙoƙarin duba hanya mafi kusa da wata rijiya ko gari “wannan hanyar zata kaisu cikin wata ciyawa mai tsayi—amma akwai wata ma'boyar ruwa da nake tunawa da ita daga lokacin da na taba zuwa Chad.”sai suka kama hanya, dajin yana cike da tsuntsaye masu shewa, ƙasasshiyar ƙasa na sa ƙafafunsu zubar da gajiya. Ciyayi na yanka ƙafafun su, ganyaye na goce su a fuska.
Yazid ya riƙe jakar abinci yana gaba, John na gefe yana duba kowane motsi, kamar soja na sahun fama. Maryam na tsakiyar Ihsan da Ado, amma ita ce ta fi fitar da kuka.
"Gsky, idan Dubai ne zai kashe mu haka, to wallahi zan koma gida."
"To sai a auri tsoho, ko?" Ihsan ta harare ta cikin dariya mai taɓarɓarewa.
Maryam ta kyalkyale da dariya cikin hawaye" ke Ihsan wallahi da aure Baba audu gwanda na mutu a hanyar nan"
Sun dauki kusan awa biyu suna tafiya cikin daji kafin suka kai ga wani tabo mai ɗan sanyi, kamar ruwan fanfo ya ƙyalƙyala sama, suka zauna a can suka sha ruwa suka ci ɗan abu.
Yazid ya duba agogon sa. "Zamu ci gaba da tafiya bayan minti talatin... don kada rana ta fara zafi mu gaji."
Cikin wannan rana, sun fara fahimtar cewa tafiyar nan ba zango ba ce, ba yawon shaƙatawa ba ce hanya ce ta ƙalubale da jarumta, da fahimtar juna. Kuma suna cikin ita....
Garin da suka zauna sun ɗan ji sanyi da natsuwa bai kai awa biyu ba, sai ga wani ƙara ya karad'e sararin samaniya. wani irin hadari ne ke tasowa daga gabashin jeji, ganye na yaye sama, ciyayi na karyewa, iska na tashi da kura mai kauri "Na shiga uku! wannan fa kamar guguwar jeji ce!" Ado ya faɗa yana rintse ido "Ku tattara kayan nan! Ku kamo jakunkunan ku!" Yazid ya ɗaga murya.
Cikin daƙilewar lokaci suka fara tattare kayan su, Maryam ta faɗi jakar ruwa, sai kuma aka jiyo busa kamar karar motar iska tana fashewa wata bishiya ta karye tana gangarowa da sauri!
John ya ɗago Maryam da sauri suka fice daga wajen,kowa ya rikice.ƙasa ta ɗan girgiza, sai ƙara da kuma wata shanya mai ɗauke da ganye da ƙasa ta tashi ta rufe hanya.
"Wayyo Allah na! kayi mana sauƙi!" Ihsan ta yi ihu.
Kowa da nashi, sai suka gudu sun rarrabu kadan, amma a ƙarshe suka taru bayan sun kusan rasa juna. tafe suke da keɓaɓɓen numfashi, zuciya cike da tsoro da gajiya, bayan tafiya mai nisa da hawan ƙasa da tsallake kwari, sai suka hangi wani ƙauye a can gefe da daji. wurin tamkar ya zauna a gaban dutse ne, akwai ɗan ruwa yana kwarara daga wani ƙanƙanin dutse.
Ado ya saki numfashi. "Wannan tamkar lahira muka tsira daga ciki muka dawo duniya ne wallahi."Yazid ya yi dariya. "Kai dai karka fara wahalar da mu da falsafa yanzu shin ka taɓa zuwa lahira ne."
Ihsan ta tura masa kafa, "Wai yanzu ni dai idan na nitsu zan rubutta wanan hargitsen cikin wannan littafin domin tarihi sai na rubuta wani Irin Jeji da na shiga."suka tafi da dariya, duk da gajiya ta cika jiki.
Sun isa ƙauyen, mutanen gari suka karɓe su da jinkai, suna ba su ruwa da wuri su huta. Sun zauna suka ci abu kaɗan, suka kwanta ƙarƙashin inuwa, Ihsan na kwance a gefe ta ce, "Wallahi idan na isa Dubai, zan fara kasuwancin ganyen magarya na gaji da dogon buri."dariyar su tashi, kowa ya ƙwalla dariya mai sa hawayen idanu.
Bayan hutu da shan ruwa, suka sake tashi da niyyar cigaba da tafiya gobe da safe. kamar ba suba, suna dariya, suna kwance da juna kamar ƴan uwa, daga cikin hargitsi da wahala, nishad'i ya fara zame musu masoyi.
Kwanaki sun shige suna lissafa wa cikin jeji da ƙasa marar alamar birni, bayan haɗari da suka fuskanta, motar su ta hantsila a ƙasar Jamhuriyar Chad, suka kasa gyara ta, sai suka bar ta can da ƙyallen tarihi suka fara tafe da ƙafa, kamar masu hijira daga duniya zuwa mafarki.tun daga lokacin ne suka soma 'kulla wani ɗaurewa da ba wai jinƙai kaɗai ba, amma kamar ana zuba wani zuma a zukatansu, suka zama kamar ƴan uwa da aka haifa daga ciki guda.
Maryam, mai natsuwa da laushin murya, ita ce jinyar jikin su duk sanda ciwon tafiya ya kama daya, za ta tsaya ta fidda ƙananan kayan asibiti daga cikin jakar matafiyar ta—ta fiddo da tawul, ta sha da ruwa, ta gyara bandage. Ita ce ta fi sanin yadda ake shafe jiki da ganyen da suka ci karo da shi a hanya domin rage raɗaɗi.
Ihsan kuwa ta fara zama ƙawarta ta gaskiya. su biyu idan suka haɗu sai dariya da tsokana, suna ƙoƙarin mantar da sauran wahala. Ihsan da bakinta mai ɗaukar dariya, ita ce ke ba su nishadi, tare da Yazid wanda kullum da sabuwar waka a bakinsa. Yazid na iya busa leda da furar baki har kowa ya manta da gajiyar tafiya.
John, babban mutumin da ke ɗauke da baƙin laya a wuyansa, shi ke gaba da su a koda yaushe ƙarfin jikinsa da jajircewarsa ke kare su daga tsoron jeji da dabbobi. Idan dare ya fado, John ne ke ɗebo itace, yana hura wuta, yana saka su su ji kamar gida suke ciki.
Ado, ƙwararren masanin hanya, shi ke tsara hanya. Duk sanda suka tsaya yana fiddo taswira ko yana duba taurari da rana don sanin gabas da yamma,baya cika surutu, amma idan ya buɗe baki, kalmarsa zata zama haske.
A daren da abinci ya ƙare, sukayi shiru gaba ɗaya. ba kowa da bakin magana sai ƙarar cikin da ke ɗaukar wululu. Maryam ta rufe idonta da ƙirjinta, tana share hawayen da ba kowa ya gani ba. zai dai Ihsan ta ɗan matsa kusa da Yazid, suka fara raira waka:
"A cikin duhu akwai fata,
A cikin yunwa akwai madara,
Rana ta fito daga bayan wata..."
John ya sa dariya, ya ce:
"Kun sani, idan muka tsira daga wannan tafiyar, zaku fi daraja fiye da zinariya a gare ni."
Ado ya duba sama, yana murmushi da ƙyamshi, sannan ya ce:
"Idan muka kai Libya lafiya, zan gaya muku sirrin da ya sa na bar gida."
John ya ɗago kansa, ya ce:
"To, mu haɗa zuciyarmu." suka kama tare da muryar da ke daɗi ga kunne, duk da gajiya da yunwa, suka rera:
Bayan wata akwai dare,
Bayan dare akwai haske,
Bayan yunwa akwai cika,
Bayan hawaye akwai dariya.
Idan rana ta ɓuya,
Mun san wata zai leƙo,
Idan hanya ta dushe,
Mun san ƙafafunmu zasu kai.
Bamu daina ba, bamu ja baya ba,
Zamu cigaba har gobe ta zo.
Mu da juna, zuciya ɗaya,
Rana ta fito daga bayan wata"…
Yayinda suka rufe baitin ƙarshe, wutar da John ya kunna ta ƙara walƙiya, kamar yadda wata ke ɗaukaka cikin dare.
Tun daga wannan daren, wannan waƙa ta zama taken tafiyarsu duk sanda sun gaji, ko dare ya musu tsayi, ko cikin su ya fara kuka, sai daya daga cikinsu ya fara:
> “Bayan wata…”
sauran su kuwa sai su ɗaga murya cikin amsa, kamar ruwa da tsuntsu:
“…akwai dare… bayan dare akwai haske…”
suna shiga cikin sabuwar rana da sabuwar fata.
continued..... narnah ƙanwar soja ✍️
https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT
🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗
AFTER THE MOON
BY
NARNAH KANWAR SOJA
💫Royal Star Association,💫
SADAUKARWA
Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕
Zahrah Royal Star
Page 3 & 4
28 / 4/ 2025
Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba ,
mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya
show me some love guy's 🩷
بسم الله الرحمن الرحيم
اللهم صل على محمد وسلم
Wurin da suka iso na kusa da bodar Libya da Niger wata ƙaramar unguwa ce dake shan gajiyar gabar duniya motar da ta biyo hanya daga Agadez zuwa kusa da Libya ta sauke su a unguwar Sakar, inda suka ce daga nan za a wuce da ƙafa har zuwa Sabha a cikin Sahara.
Yayinda dare ke neman yin nisa, suka haɗu da wasu 'yan tsirarun matafiya da suka ce akwai hanya ta gefen jeji wacce ake bi don gudun jami'an tsaro.
John ya ja su a gaba, yana ɗauke da wata ƙaramin ƙaho na ruwa da bag ɗin burodi guda ɗaya kacal. Yazid da Ihsan na bayansa suna rera wasu baitin Bayan Wata da karfin zuciya, yayinda Maryam ke sanye da hijabi mai kauri, tana riƙe da Ado a hannu, suna tafiya a hankali cikin duhun dare.
Amma a kwana na biyar a cikin Sahara, bayan sun wuce wani yashi mai launin toka, a lokacin da rana ke ƙoƙarin ɓullo daga gabas,
Maryam ta hantsila ƙasa da karfi, “Aaaaaaah…!” ta fasa ƙara, jikinta na karkarwa kamar daji na girgiza, gaba ɗaya suka tsaya cak.
Ihsan ta durƙusa da sauri, tana girgiza ta. “Maryam! me ya faru?”
Maryam ta duba ƙafarta—tsohuwar alƙalamin takalmi ya tsinke, kuma dutsen da ta taka ya huda tafin ƙafarta, jini na zuba kamar famfo.
Sai hawaye suka cika idon Ihsan
Ado kuwa ya durƙusa yana duba ciwon da kwarewa kamar ƙwararren likita “Dole ne mu tsaya nan ba za ta iya cigaba da tafiya ba ” ya faɗa don yagaji da dogon tafiyar da babo matsaya,
John ya kalli yamma, inda duhun jeji da yashi ke cike da sauti marar ƙauna. “ba mu da lokaci… idan muka tsaya, mayakan macijin nan zasu iso.”
“mayakan macijin?” Ihsan ta tambaya da fargaba,
“'Yan fashin daji Idan suka same mu, ba abinci ba ruwa ba 'yanci...” ya dakata yana ɗauke numfashi
Yazid ya ɗago kai, idanunsa na cike da yaji ya ce:
“To a ɗauketa ba zamu tafi mu bar Maryam ba !” yana kauda fuska don dai har ga Allah cikin wanan yunwar bashi da kuzarir ɗaukar ta ,sai John ya ce da karfi “Ni zan ɗauketa!”
Bai jira amsa ba, ya ɗauki Maryam sama kamar jaririya, jikinta yana rawa saboda zafi da ciwon da ke yawo cikin jinin jikinta suka cigaba da tafiya , duhu ya koma, rana ta sake bayyana da ƙyalli, amma zuciyarsu na makare da tsoro da azaba.
Lokacin da rana ta ɗora bisa tsakiyar sararin sama, Ado ya sha ruwan ƙarshe da suka rage ya yayyafa kan Maryam.
Yazid kuwa ya saka dariya duk da gajiya yana cewa “Yau rana na cin mutum, amma jiki na cin gado…” sai Ihsan ta hau waka a hankali:
“Bayan wata… akwai dare…”
John ya karɓa cikin murya mai ƙarfi kamar jarumi
“Bayan dare… akwai haske…”
Suka kama waƙar cikin kuka da dariya a lokaci guda waƙar ta zama mafakar zuciya.
Maryam da aka daura a bayan John, tana raɗa wa kanta:
“Zan rayu… saboda ku…”
Washe gari rana na haskakawa cikin yashi kamar zinariya, suka iso wata ƙaramar sansanin ‘yan gudun hijira da ke bakin Libya, wanda wasu likitoci daga ƙungiyoyin jinkai ke taimaka wa nan ne aka kwantar da Maryam cikin wani tantin asibiti na wucin gadi An gyara ciwonta da tsafta, aka bata allurai da ruwa, har ta fara murmushi.
John da Ado suka sauke ajiyar zuciya. Yazid kuwa ya durƙusa ya shafa gashinta yana cewa: a cikin kunnen ta “kin tsira Maryam… ki tabbata za ki rayu har mu ga Dubai!”
Ihsan kuwa, da ta zauna a jikin wata tsohuwar matashiya mai suna Mama Simbi—wacce itama gudun hijira ce daga Ghana ta kalli sauran matafiya da kuma wasu daga cikin mutanen sansani, sai ta ce da natsuwa:
“Kafin rana ta sauka yau… zan ba ku wani labari. Labari ne wanda ban taɓa fitar da shi ba… kuma shine zuciyata ke ɓoyewa tun ina zan bayyana labarin da Narnah ƙanwar soja ke da burrin fitarwa sai dai bata samu dama ba ne Ihsan zanyi amfani da wannan damar.”
Gaba ɗaya suka zauna, wasu suka ɗebo ruwa, wasu kuma suka jera kan buhuna da katifu. cikin nutsuwa da natsuwa, Ihsan ta gyara zama, idonta na kallon nesa kamar tana komawa zamanin da ya wuce.
Sauran matafiya suka runtuma cikin nishadi, wasu suna cewa, “Labarin fa kenan!” wasu na gyara zama kamar za su rubuta da likitochin da tawagar Bayan wata duk suna sauraron ta
(Yanzu fa lokaci yayi na shigowar sabuwar rayuwa cikin Bayan Wata—wannan labarin Ihsan da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 1 Chapter of 18