Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
"" gabanta yana faduwa dole takoma wajen bokan nan tunkafin abun nan yayi nisa yakareshi "" Nikam nace kinmanta kincemasa Wanda bayida makari sai mutuwa?? Dama ance idan zakagina ramin mugunta kaginashi gajere dankoda kai kafada zaiyimaka saukin fita Wanka tasakeyi saboda kaikayin tasaka kaya masudan tsayi duka sunrufemata jiki tayanda babu Wanda zaiganie Karamin hijab tasaka saboda wadanda suke awuyanta"" tana zaune sai sake sake takeyi har haske yafito Usman ne yashigo dakin da sallama ta amsa tana dago kanta Kusa da itah yazauna race masà inakwana" yace lafiya qalau kintashi lafiya?? Aranta tace bakalauba shegiyar matarka tanason ganin bayana"" 🙄 Afili kuma tace qalau saidai kewarka"" murmushi yasaki cikin jindadi yace kitaso mukarya Dan khadija Niger zataje wajen dangin mahaifiyarta" Tace waidama ita Yar Niger ce??? Yace ah kishiryamun kayana kafin nakaita airport Dan nima tafiyace takamanie mutanenda nafadamaki sunzo company jiya tosune sukahada mana zama a America akalla zanyi sati acen Lubabatu tace shikenan suka tashi suka sauka kasa sunsamu su khadija harsun soma karyawa tazuba masu sannan tacigaba daci Duk da zumudi baibarta taci dayawaba"" tana gamawa labila tatayata suka dauko kayan labila taso tabita suje tare Amman gobe zasufara jarabawa shiyasa kawai bazata bitaba harbakin mota lubabatu tarakasu tanayiwa su anwar adawo lafiya Abunda zaibaku mamaki su anwar basayarda lubabatu tadaukesu dazaran tadaukesu saisukama ihu dole sai an karbesu hakan yasakama tadaina daukarsu Khadija tace shegiyar kiuya kamar wadanda akexizo lubabatu saidai tace hmm kawai saida motarsu tabar gidan sannan takoma cikin gida . Sunje adaidai kuwa suna isah akagama komai khadija takude jirgi su labila sunatsaye hargirjinsu yadaga nikam nace khadija dakarfin hali yara uku kuma babu mairike mata kodaya Amman tunda tasaka ranta datafiyar aisaitayi tanason ganin kaleed ne sosai "" Karfe biyu jirginsu yasauka" Niger tana saukowa tasoma kalle kalle inama zataga mutumen jitayi anyimata sallama"" ta amsa dafara a yace madam nine Wanda akace zankaiki gidan Tace okay anwar dayake hannunta nadama yakarba"" tanagoye da sapna husna kuma tana rike gahannunta nahagu motarsa yabude tashiga yasaka Kayanta bayan motar tareyake dawani da alamu driver sane sukashiga motar yatayar Sukahau hanya"" sunatafiya khadija kam sai kalle kalle takeyi " harsuka kaigidan sarautar mutumen yace wajenwa kikazo??? Tace sunanta Hauwa u yace shikenan fita yayi yayiwa maidagin bayani akasheka akasanarda sarki yanada baki daga Nigeria sunzo wajen hajiya babbane"" Yace ayisauri ashigo dasu nantake fadawa sukayimasu iso sarkin Wanda yake kan kagarar dazaran kadubeshi kaga khadija saikace shine yahaifeta dankamar tasuma tabaci yana ganinta yamike yasaki fara a Yanayimata lale marhabin"" anwar yakarba yana kallo yacewa fadawa yau manyan bakine dasu danhaka zaigana da bakinsa kaitsaye cikin gidan yawuce dasu wajen matansa sukuma wadanda suka rakota yace akaisu falon baki akarramasu Sosai khadija tashiga mamaki ya akai yasanda zuwanta babban gidan sarautar cike yake damanyan ginuka ko ina Kaduba bayine gasunan sunata aiyuka Kaitsaye turakar Fulani yanufa itace uwargida "" itama tanaganinsu tatashi daga kishin gidenda take tace wanakegani kamar khadija?? Maimartaba yakalleta da murmushi akan fuskarsa yace itace ina hajiya?? Tace yanzun nan takoma bangarenta saimuje cen kawai tamike ta umurci sauran bayin dasu sanarda Amarya gabadaya suka rankaya dakin hajiya Duka yaran khadijar andaukesu anwar yana hannun mai martaba husna tana hannun Fulani sapna Amarya takarbeta Ita haryanzu mamakine kwance akan fuskarta sunashiga tayi arba da dattijuwar data taimaka mata lokacinda take nakudarsu Husaini Itama tana ganinta tasaki fara a"" dasauri khadija taruga tarungumeta saikuma tafashe dakuka"" tashafa bayanta tace menene nakuka aikindawo cikin yan uwanki Cikin kuka tace dama Ashe kece kikahaifi mamana meyasa bakifadamun hakanba lokacinda muke cikin dajin zaune??? Tadago da itah tana murmushi tace khadija kenan ba maimunatu tasanardakeba abunda yasaka banfadamakiba nasan idan kikaji zakiji haushina saboda duk nice silar shigarku wannan damuwar Saiga hawaye sunabin fuskarta Fulani da mai martaba suka zauna tareda Amarya"" Khadija tasharemata hawaye tana girgiza kai tace kokadan bakece silar damuwar muba kowa naduniya bayawuce kaddararsa Kaddararmuce tazo dahakan"" Hauwa u tafashe dakuka tace inada laifi sosai gashi asanadin rashin bin iyayena nayisanadin da yata Tarasa ranta bazantaba gafartawa kainaba wannan bakincikin dashinake kwana naketashi Najamaki gashike bakisan dadin uwaba kowayanaso yatashi tareda mahaifiyarsa itah tarayu babuni kekuma kinrayu babu itah mezaisa bazanyi kukaba kaichoni hauwa Nina San har abada bazandaina kukan nanba"" khadija tace dangirman Allah kidaina cewa hakan babufa Wanda ya isah yakaucewa kaddararsa Kinmanta da Allah yadauke ummana yabarmun Yayana Wanda yakesona fiyedakomai yazamemun uwa uba Bantaba kukan maraiciba harnakanji araina abunda yakemun komai uwama bazata samu hakanba Yayimun abunda babu Wanda zaiyimun sannan Allah yahadanie da labila wacce takesona fiyeda kanta ""saikuma yasake hadani da Miji nagari"maisona duk wannan gatane da""Allah yayimun"aiwan nan kadai ya isah ingodemasa "" Hauwa ta share hawayenta tace hakane Amman nikam inaji ajikina bankyautaba gashi naja kinrabuda yayanki yan kananu lokacinda yadace kirungumesu sunyi nisa dake Khadija tayi dariya tace kuma Allah saiyasake bani wasu tayi maganar tana kallonsu anwar sai lokacin Hauwa tagansu daibayan daya take kallonsu baki bude tace yara uku kikasake Haifa?? Kai masha Allah "" Allah abun godiya mikomunshi Muhammad inganie tayi maganar tana kallon mai martaba yatashi yakarasa gabanta yaduka sannan yamika mata Tace barakallah kyakkyawa dashi shiru tayi tace kuganemun nikuwa kamar nasan maiwan nan fuskar??? Fulani tace nikaina hakan nakerayawa araina Maimartaba yace narigaku azuciya tunsanda sukashigo naraya hakan" Amarya tace waiku bakugane dawa yake kamaba?? Ai ina ganinsa naga kamannin sultan"" Maimaitaba yace wanne sultan din??? Tace nagidan Yaya Husaini mana"" Hauwa tace hakane Kuwa wlh sunyi kama da kaleed ikon Allah kunga yanda akeyin kama Khadija tana saurarensu saiyanzu tayi magana tace aidole suyi kama mana tunda kaninsane"babansu daya Gabadaya suka kalleta da mamaki sukace taya zasuzama uba daya kuma bayan ba ubansu dayaba??? Khadija Tanisa tace abunda yakawoni kasar nan kenan akan maganar kaleed din tanisa mahaifin kaleed shine mijinda nake aure Idanuwanta suka kawo kwalla tacigaba matar uba wacce takeneman ganin bayana itace tarabashi da mahaifiyarsa aka kasheta sannan shima tasaka akasheshi saita fashe dakuka Tundanake arayuwata bantaba ganin mace marar imaniba irin lubabatu gabadaya jikinsu yayi sanyi tasoma basu labari duk yanda aljana maimunatu tasanarda itah Aisha✍🏼 [3/30, 6:14 AM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 017 By Gentle Lady💃🏽 Mai martaba yajinjina kansa yace Amman kewayafada maki wannan labarin??? Ko wajensa kikaji??? Tagirgiza kai tace shiyanzu baimasan yanada yaro kaleed ba haka baisan yataba aureba kamar yanda suka mantardashi matarsa mahaifiyar kaleed Nikaina hakan taso ayimun saidai Allah baicika mata burintaba"" mainartaba yace lallai nayarda haryanzun akwai sauran jahilai aduniyar nan kodayake bazasu kareba ai yanisa Amman taya zakifahimtar da yaron nan dantunda yake baitaba sanin basune suka haifeshiba yanada shekara biyar aikomai yamanta Amman bari akirah yayan kiji yakalli fulanie yace saka akirashi yanzun harda maidakinsa tace to sannan tamike tafita Wata baiwa takirah tace tayimaza gidan sarkin fada tace anakiransa inji mai martaba"" tace angama rankiyadade dasaurinta tahanzarta domin cika umurnin uwar dakinta. Ba adauki tsayin mintuna ashirinba sukashigo tareda sallama Sundaukama ciwon Hauwa ne yatashi da akace anakiransu yanzu yanzu Ganinta zaune yasaka suka saukarda. Ajiyar zuciya"" mai martaba yanuna masu waje suka zauna " yakalleshi yace kokasan wannan??? Yayi nunida khadija Da mamaki yace wannan kamar na ima Amman tafi na ima fari kodai itace idanuwana ne suka soma ganin buji buji gabadaya sukasa dariya"" yakalli Hauwa yace inna koban fadi gaskiyaba??? Mai martaba yace kafada kam Amman kamace kawai wannan ba na ima bace sunanta Khadija Yar fateema yayarka wacce hajiya tabaro a najeria Zunbur yamike yace Allahu Akbar Allah maiyin yanda yaso ashedai darabon zanga jinin Yar uwata "" yamatsa yana kallon khadijar maimartaba yace bawan nan ba tazone akan maganar yaronka sultan Yace tofa Allah yasa lafiya "" yace qalauma kuwa kalli wannan yaron"" yayimasa nuni da anwar dayake hannun Hauwa" hassan yace tsarki yatabbata ga mahaliccin kowa dakomai ai wannan photocopy din sultan ne"" Yayi maganar yana Daukar anwar yana kallonsa"" mai martaba yace wadan nan yaran Na khadijane Mahaifin wadan nan yarankuma shine mahaifin kaleed tazone sabodashi tanaso tasanardashi ainahin tarihinsa ..gadai yartaka nan kaji daga bakinta" Hassan yakalli khadija yace ikon Allah sanardani yata menene gaskiyar lamarin"" ?? Khadija tasake sanardashi komai kamar yanda tafadamasu takai karshen maganarta dacewa shikanshi Mahaifinsu baisan meyakawoni nandinba dankoda nafadamashi ma zaice baidawani yaro kaleed Hassan yace babbar magana yata sultan baisan ainahin tarihinsaba nikaina naso sanardashi ganin yanda yakeson Zainab kamar me ammankuma yanaganin tunda iyayensu daya babu aure tsakaninsu Amman dagashi har itah suna mutuwar son junansu duk dabasufito suka fadaba itah yanzunhaka takasa tsayawa dakowane saurayi shidinma yanzun yakeson yayi aure danyakaucewa soyayyarta Naso infadamasa gaskiya mamanshi tahana waizantono masa miki tayiyuma idan yaji bamu muka haifeshiba yagudu yabarmu tunda bamusan inda zamuga iyayenshiba Amman yanzun tunda kinsan asalinsa komai yazogidan sauki zuginda zaiji kadanne" Khadija tace hakane yanxun yana ina??? Hassan yace sarkin buga boll aiyana filin wasa bakyarabashi da kwallo yaro kamar Dan danbe sukasa dariya khadija tace shikenan idan yadawo zanso ganinsa Wata baiwace tashigo taduka tace sarkin gida yace mutanenda suke tare da bakuwar hajiya sunce zasuwuce" khadija tamike Sam tamanta dasu Mai martaba yace batare kuke dasubane zasuwuce tunyanzu??? Tace ah ah batare mukeba abokin babansune dayake kasuwanci anan shine yacemasa idan nazo yadaukeni yakawo nan bari nayimasa godiya. Tayi maganar tanafira Sam tama rasa hanyarda zatabi tamiyarda itah waje saida tatambayi wata acikin bayin gidan tanuna mata""" bakin kofar fadar tasamesu dafara a takarasa wajensu tace harzaka wuce ??? Yace ah maigidanki yakirah yace meyasa kika kashe wayarki yakirah yaji kinsauka Nacemasa harkintsufa gidan sarauta murmushi tayi tace kaga kuwa wlh tunda nakasheta dazamu shiga jirgi namanta inkunna nafa gode yace bakomai Allah yahutarda gajiya tace ameen Sukai sallama takoma cikin gidan falon Hauwa u tasamu anjeramata kayan abinci da abubuwan motsa baki kayan marmari dasauransu"" sallah tafara gabatarwa tadan watsa ruwa taji sanyi jikinta sannan taci abincin saida takoshi tayi hamdala kuyangin gidan suka kwashe kayan dataci abincin Wayarta tadauko takunna takamo lambar Usman takirah tanasoma ringing yadaga cikin murmushi tace amincin Allah yatabbata agareka dan autan maxa Sosai tabashi dariya dansaida yadara yace kema aminci yatabbata agareki sarauniyar mata"" tace tofa yaukuma sarauniya nasamu yace sosai aikin koma gidan sarauta danhaka kedin sarauniyace Tace ah ah kam kamanta bakunta nazo haryanxu inanan matsayina"" yagidan??? Yanisa gida yayi fadi sosai kamar Rabin gari Tarausayarda idanuwanta tace bayan mom tana nan taya zaiyimaka fadi"?? Maganar kikeso kenan Aimuddin bakece awajeba komaima fadi yakemun Deejarh na nakanga duhu ya yawaita koda kuwa ranace Komai hasken waje banaganin komai kece pitilarda ke haskakamun gabana"" khadija tasake gyara kwanciya sosai kalaman mijinta suna isarda sakonda yakamata su Isar sunabin kowanne bango lungu dasako na zuciyarta Tasaukarda ajiyar zuciya tace Nima hakanne hubbyna"" yagyara kwancinsa yace dagaske bayan kuma kedin kinacikin danginki anyama zakituna dani??? Wainikam zan iyah sati dayan nan bangankiba?? Wlh yanxun ma dabanajin motsinki wani iri nakeji " Takwantarda murya karka damu nawan kaima ba anjima zakatafiba aizamudinga yin waya akai akai Yayi shiru tace banjikace komaiba"??? Tomezance Deejarh na gaskiya zanyi hakuri nasatin nan daya dole asaka sunana cikin jarumai Khadija tasoma dariya yace mekikewa dariya kuma??? Tace ah ah bakomai Kaine za asaka Cikin jarumai tosaika fadamun jarumtarda kayi ??? Murmushi yayi yagyara kwanciya yace jarumtar hakurin rashinki akusa danie mana kinsan bakaramin kokari zanyiba harsati daya banjini alallausar fatarkiba Haba dolema ayimun jaje bayan anbanie kyautar karramawa dajinjina Tace hakane zakasamu shakuruminka "" Amman saikaje filin daga tukun"" yayi saurin Tatar nunfashinta yace dama ainidin jarumine nasaba zuwa yakiiii kobaki saniba Dariya tayi tace habadai"" bakiyardaba kenan bari nafadamaki tace ah ah basaika fadaba nagane "" shima kanshi dariyar yakeyi Yace ina yarana banji motsinsuba??? Wlh nikaina bansan inasukeba tunsanda mukashigo aka karbesu bansake ganinsuba"" dasauri yatashi zaune yace yaran nawa toke kina ina zakibarmun yara kowa yana dauka Tace kwantar bawan Allah iyayena suka daukesu kokuma zuwa zan nakarbosu daga kawai anhutardanie Yace hakanma zakice kinsan bazaki iyah dawainiyar suba meyasa kika tsiri tafiyar"" dariya take ciki ciki tace waikai saikace gareka farau yaya bayan kanada wasu bayansu Yace nasanda haka Amman wadan nan namusammanne "" tace saboda??? Sunfito ta karkashin macenda nakeso fiye dakomai "" kuma jinin jikinta yagauraya da nasu kingane ai"" Tace hmm barci nakeji gashi sai hamma nake" yace badai yanzuba kyabari saidare"" tace hakane nikaina banda niyar yinsa yanzu sundan jima suna fira sannan sukai sallama taka she lambar ya muktar takirah Aisha✍🏼 [3/30, 6:14 AM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 018 By Gentle Lady💃🏽 Tana soma ringing yadauka tayi sallama ya amsa ya aiki yace alhamdulillah ina yarana tace basa kusa danie Ansama maki masu rainone??? Tace ah ah banagida yanzun haka ina dakin hajiya"! Yace kano kikaje kenan" Ah ah ba hajiya ta kano ba ina nufin kakata"" wacce tahaifi maman mu Muktar dasauri yamike yace waikina nufin kinganta???😀 Tagyada kai kamar yana ganinta yanzun hakama ina dakinta kwance gaskiya Yaya yakamata kaima kazo bagaka dangin muba kuma kowa naganie muna kama dashi Duk da banga yaran gidan ba da alamu basa nan nijinakema kamar nazauna anan🙂 Muktar baki harkunne yace Alhamdulillah koba komai munsamu dangin mahaifiyarmu Tace hakane yaushe zakazo?? Yadan shafo kansa yace inaso nadawo kano gabaya nacigaba da aiki hospital saboda wani dalili Khadija tace kai Amman danaji dadi Amman meye dalilin?? Yadanyi Jim sannan yace aure nakeso zanyi"" ! Khadija tace badai kasamu matarba ??? Ah to nasamu Amman gaskiya haryanzun bansanarda itah ba saboda batasona naso sanardake Amman nakasa Banaso nafada daga karshe tace batasona zanji natsanie kaina"" khadija tace karma kafara sanarda itah aini nayimaka mata Yayana"" tayi maganar tana murmushi"" Shiru yayi daga bisanie yace kowakika zabamun yazama dole agareni nasota"" khadija tace ainasani Yayana kasan Kuwa wacece?? Murmushi yayi yace basaikin fadaba nasan labila kike nufi Danban manta alkawarinku da itah ba nikuma itace nakeso saidai inaganin bazata soniba kinaganin duk sanda tasamemu tare dake saitafasa zama idankuma nasameta agurin Danashigo take tashi"hakan bayamun dadi" Khadija tayi murmushin jindadi tace"" karka damu indai sahibace zataso ka Muktar yace anya kinmanta shiso ba ayinsa dole"" Hakane Amman batadawani zabi tunda nima ta tursasanie na auri babanta aikuwa dole ta auri Yayana"" muktar abun na khadija dariya yabashi Yace batada laifi damacen kinasonsa"" kunya taji tace to aikaima tana sonka"" Itah tafadamaki hakan?? Aikobata fadaba indai tanasona zatasoka Dan kamanninmu iri dayane idan tana taredakai zataji kamar nice Muktar dai dariya kawai yayi yacedai Allah yasatasoni shine kawai fatana"" kasa aranka kasameta ya muktar. Yace shikenan adaitayani addua idan kinje wajensu hajiyar kice inagaidasu duka Tace zasuji sukai sallama takirah labila shukasha firah Amman batayimata maganar muktar ba hardare ba adawoda su anwar ba""" dayake yaran basuda fitina basa Neman mama "" Dadare tana falon Hauwa sai shigowa akeyi ganinta"" yara da manya sosai khadija tasake cikin yan uwanta harwajen takwas sannan akadaina taruwa sosai harda na ima taganie diyar inna Husaina "" tagakuma zainab dakannensu da yayyunsu kaleed ne kawai bataganie ba"" Tanashan tupa yashigo gidan da sallama yana sanye da kananun kaya sunbala in karbarsa tunda yashigo yakafama khadija ido kamar yasanta kodan tana yanayi da zainab dinsa Itama shitake kallo tana tasbihi ga Allah dayayi wannan halitta Kama iri daya kamar wada kani Haka zalika bazakace Usman ya isah haihuwar saba"" kujerar kusa da hajiya yazauna haryanzu baidaina kallonta ba,"" idanunsa suna sauka akan anwar dayake kwance yana wasa da kafafunsa Yazaro ido"" saikuma yasake murzasu hakan bai wadatarba yamike yadaukeshi yakuramasa ido daga Hauwa har khadija shisuke kallo"" Yajuya wajen Hauwa yace matar kinga abunda nakeganie kuwa??? Kodayake kinada matsalar ido balallai kiganiba "Ta harareshi tace ja irin yaro nadaifi matarka ganie idanuwa kamar gwazalma"" Dariya yayi yace haba kinsan kuwa wacce zan aurah aiduk kasarnan babu kamarta"" Tace wajen munintaba"" aikowa zaka aura bayana take dannice uwargida dariya yayi yace hajiya nashiga mamaki Ashe akwai Irina aduniya??? Yazauna kusa da itah yace daxun naga nshi ahannun baba Amman banlurah dashi sosaiba inasauri zanje siyowa zainab"" maganie ikon Allah yasake kallon shi yace wannan itace mamansa??? Hauwa tace itace sarkin surutu kanaganin baki kogaisheta bakayiba kakatse kaiko ina kaje saika saida halinka"" Baki yarike yace ikon Allah yaunaga inda akehana mutum yayi magana dashi dabakinshi wannan tsohuwar akwai takurah inbakiyi wasaba sainadauke kafata daga shashenki Tace dagadai nahuta kullum saika shanyemun furah"" yace najidai yaukam bazanshaba anyimun gori Amman zuwa gobe zanhuce""yayi maganar yana shafo cikinsa""" gabadaya sukasa dariya khadija kam bakibude takebinsa dakallo Idanma baiyi surutuba ai dasauransa Dan Usman ma surutune dashi harta muryansu iri dayane"" Kallon anwar kawai yakeyi shikuwa sai wangale bakiyake yana dariya kamar wasa yakemasa"" yace Kinganie ko hajiya shima yasan muna kama gashi yanamun dariya😁 Hajiya tace nidai kadameni da surutu katashi katafi gidanku"" ido yadanturo yace ko ina gidane awajena inama zantafi bakisanardani inda wannan lu"u"lu"un yafitoba Tace saiyanzu kagadamar tambaya to jikatace diyar antyn babanka wacce tarasu a Nigeria !" Kaleed yace haba no wonder naga muna matukar kama dawan nan yaron Ashe danane Khadija kam aranta tace kaninkadai"" yace hajiya kinsan me??? Tace ah ah saikafada"" Yace duk su fauziya da bilkisu da yaya ahmad kaf jikokin gidan nan basu iyah haihuwaba"" tace sabodame zakace haka Yace wannan Mamar lu u"lu"u itace kawai ta iyah haihuwa aceduk fadin masarautar nan babuwanda yayimun kara yahaifi maikama danie aini karnake kallon kowa dannima idan nai aure Yayana kamannina kawai zasuyi Hajiya tace to alhuda huda katashi dareyayi wannan firar ta asheni kullum sai anzohirah acikamaka kunne dasurutu babu Dan abun tabawa Kaleed yamike ya aje anwar yace tosaida safe bakuwa tunda korata akeyi yakalli anwar yace night diamond yawuce abunshi"" yana kwala kirah ina beranyar gidan nan take Kaitsaye bangaren Fulani yatafi yatasota yabata kaza gasassa yace takaiwa hajiya"" tace ya sultan assignment dinfa"" Yadafa kanta yace kikaiwa Aisha tayimaki sauri nake wajen abokina zanje"" tabata fuska nidai ah ah idan nacesuyimun dariya sukemun"" yace tokawo littafin idan nadawo zanyimaki sainaba Yar dasafe akawomaki tace yee nagode yayana Tasheka dakinsu tadauko littafin takawo masa sannan tasheka takaiwa hajiya Hajiya tace tatsaya takarba tace takoshi tajuya takoma"" khadija tace badai wannan yakecewa beranyaba??? Hajiya tace itace bakisanshi da shegantakaba"" abokiyar wasar sace incemaki duk bayakiran sunansu kowa dakalar sunanda yake Kira kema idan bakiyi saurin sanardashi ainahin matsayinkiba nanda kwana biyu zaiyimaki suna Shi bakinsa bayako ciwo kullum hakamuke dashi dadina dashi abudayane baruwansa dashiga sabgarda bata shafeshiba nitunda nakema bantabajin yayi koda musayar yawu dawaniba shiyasa yaran gidan nan suke sonsa Danyanda yake sakemasu fuska duka sauran yaran basa sakemasu kinsan manya akwai jangirma khadija tace aihakan yayi bari nakwanta barci nakeji gashi anwar yakibarci Tace aidole dazun barcinsa yatirga koda kawunki yakawoshi yayi barci"" kidau kazar dandan naki kichi"" tace nikam koshe nake hajiya kedai kici tunda tatoshiyar bakice🙊 Tasa dariya tace karkisa na ajeta gobe idan yazo inyaba masa itah afuska Khadija tana dariya tadauki anwar tace dadai kinci kinrage zafi danko bakiciba. Sai anmaki kishiyar tawuce tana dariya Saida tawatsa ruwa takwanta dayake takwashi gajiya babu jimawa barci yadauketa dawaya ahannunta tanason Kira taji ko Usman yakai Al amarin lubabatu kuwa daren sai ahankali domin kaikayin kamar jirayake takwanta yanda taga safiya haka taga dare "" Washe gari tunda safe kurajen sunsake girma hardawasu kananun Abu suna yawo acikin kurajen kamar tsutsotsi sai tsikaranta sukeyi"" illai kuwa tana sosawa daya yafashe saiga kananun tsutsa ruwan suna taba jikinta wani kurjin yabullo tashin hankali lubabatu Batasan sanda tafashe dakukaba kaya tasaka harda nikaf Dan kurajen sunfara fitowa agefen fuskarta tadauki key din motarta takama hanyar katsina *Ganie gawanie*ya ishi wane tsoron Allah Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ Chapter 019 By Gentle Lady💃🏽 Koda ta isah katsina khairat tana lankwashe saman gado tana barci mijinta yana kitchen yana hadamata abun karyawa"" kamar anjeho lubabatu tafado gidan Ko sallama babu tasoma kwalawa khairat Kira mijin yace tana daki barci take kizauna kamin tafarka " lubabatu ko arzikin kallonsa batayiba tafada dakin khairat Tace tashi khairat kitashi"" tasoma bubbugarta mikatayi tana mutsutsuka ido ganin lubabatu yasaka tayi zunbur tace lafiya Kawata kikadako wannan sammakon😳 Lubabatu tace inafa lafiya khairat nashiga uku nikam wajen bokan nan zakirakani"" khairat tace kina nufin maganin baiyiba nikuwa nasan maganinsa yanaci Dan inada tabbacin haka Lubabatu tace Nima ainatabbata tunda nakai kaina nabaro kitashi muje Dan Allah" khairat tace haba Kawata komadai menene kikwantarda hankalinki dazaran muntafi komai yawuce kijirah mukarya nasan kekanki bakici komaiba kikafito Lubabatu tace wanne irin abinci zanci inacikin tashin hankali khairat dubafa kiga yanda nakoma"" tayi maganar tanacire likaf din tanuna mata hannunta dubi jikina kurajen harda tsutsotsi acikinsu Saiga khairat tafado tui akan gado tace munshiga uku garin Yaya hakan yasameki??? Wayayimaki wannan danyen aikin??? Lubabatu tamatso kwalla tace kamardai yanda bokan yace nayi hakan nayi saidai ansamu matsala maimakon itah tataka maganin nicenan nataka Khairat tahau sallallami tace haba Kawata meyakaiki yin wannan danyen aikin"??? Ta share hawaye tace tsautsayi mana kawaifa nakirah sunanta bata amsaba sainaje kofar dakin nasake kiranta dan ina tsammanin batajibane Ashe yaronta yayi fitsari tazuba ruwa tashafe baishafuba kinsan santsin tayil kawai sainaji yajani inataba maganin akasoma mirgina dani kamar cincin Nafasa kuwa khadijar tafito inajinta tafadi wata kalma sainaji andaina jujuyani ina zarginma anya bawajen boka takainiba??? Biri yayikam da mutum Khairat tace aini banga zamaba tashi muje tamike kobakinta bata wankeba taja mayafi suka fito Tacewa mijinta zataraka kawarta wani gurin idan yagama hadawa yaci yawuce wajen aiki yace to"" sukasa kai suka fita wannan karon motar lubabatu sukashiga'' Koda sukaje dajin sunsamu mace hudu"" gefe sukatsaya lubabatu kamar tatashi sama takeji bayan an gama dasu suka shiga tunkafin bokan yabasu damar magana lubabatu takwaye hannun rigarta tace boka kalli yanda nakoma kataimakeni kakare wannan asirin Tsuru yayi yana kallon kurajen daga bisani yace garin Yaya kika kuskure bayan kuma saida nafadamaki karki kuskura wani yataka sai itah.. Tace tsautsayine karabani dawannan masifar wlh ko barci rabonda yadaukeni tunshekaran jiya Kai yagirgiza yace yamukai dake??? Saida nacemaki ayimai makari kikace ah ah sai mutuwa Tayi saurin tarar nunfashinsa tace yanzun ahakan kakenufin zan tabbata??? 🙆🏿 Yagyada kai hakkun Dan banida maganinsa saidai zan iyah maki taimako daya"" tace namenene nidai bukatata inrabu dashi Yace bazaki rabudashiba sai dai kiji sauki wannan kece kikajawa kanki dakince ayimai makari dayanzu saina warware taimakonda zan iyah yimaki shine zanbaki maganie dai yanzun kijikashi saikiyi wanka dashi zakiji sauki Amman ciwon nan naki yadauremun kai ciwonda yakamata kiyi ba irin wannan bane Shi kurajene kawai Kuma bazasu dameki da kaikayiba tonaga wadan nan harda mugunyar tsutsa maicin jikin Dan Adam wannan tsutsarda kike ganie tsapappace sannan kullum karagirma takeyi Kuma duk bayan awadaya saita haihu ahankali zasuyita daduwa ajikinki gaskiya banine nayimaki hakanba kije kiyi bincike Wanda yayimaki wannan aikin bakaramin matsafi bane lubabatu bakiyamutu haka yabasu sukashiga motar lubabatu Sai sharar kwallah takeyi khairat ma takasa magana suna kawowa gida bata tsaya shiga gidan khairat ba tashiga motarta sukai sallama tawuce gida Tanazuwa tajika maganin tayi wanka dashi takoji sauki danharda barci yadan dauketa"" labila tana gidan Amman batasan meke faruwaba Danbata ganinta kodakuma tashiga dakin kwance takesamun ta batalura Sam dakurajenba . Kuma itama boyesu takeyi danbataso yarta taganie"" Khadija bayan takarya dasafe tayiwa yaran wanka "" tana zaune dahajiya kaleed yashigo centajiyo muryansa yana magana da yaran gidan"" Yadade sosai kafin yashigo bangaren hajiya yagaida itah tareda khadija suka amsa"" hajiya tace yau bazakaje kwallon bane naga kashigo tunda safe?? Yace ohh nikam ansamin ido kinmaidani mayen kwallo kinmanta yau ana aiki idan banje office dinba kece zakiyimun aikin Baki tatabe tace zuwa aikin naka naganin dama "" tonidai bawajenki naxoba mai kamadani nazo dauka dashi zantafi"" Yakalli Khadija yace maman lu"u "lu"u baya kuka ko??? Hajiya tace kaci gidanku anwar sunansa bazaka kirashi da sunansaba saiwani lu'u'lu'u"" ohhh!!! Aibansan sunansa hakaba suna maidadi yalakuci kumatun anwar shikuma saidariya yakeyi tun zuwansa"" Yaduka yadaukeshi su sapna suka kafamasa ido"" yace kudaina kallona bana daukar mata duk dadai kuma kuna kamadanie bansan yazanyi nadaukeku Ku ukuba Yasaba anwar ga kafadarsa yace kayiwa mom bye mumuntafii yayi maganar yana daga mashi hannunshi suka fita" Hajiya tace waike saiyaushe zakisanardashi ?? Mumushi tayi tace yau zanje gidan uncle idan yadawomun da anwar saikice inacen Nafiso ayi komai agabansu danzai iyah cewa bagaskiya bane"" hajiya tace kema kinsan saihakan tafaru ni wlh tausayi yakebanie wannan mata wannan mata ta cuceshi" " Basujima suna firaba hajiya takirah daya dagacikin masuyimata hidima tace tadauki sapna saita rakata gidan tace to Khadija tana gaba tana biyeda ita batakoso sujera da khadija harsuka kaigidan shikanshi babban gidane kuma jere suke dajuna Amman saboda tsayin gidan sarautar saikayi tafiya mainisa kamin kakai dayan Kamar iri dayane Amman wancen yafi girma dakyau"" suna shiga

Chapter 30 of 31