Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
nuna godiyarsa ga ubangiji a bisa wannan baiwa da Ubangijin ya yi masa, na mallaka masa gwarzuwar mata mai cikar halitta da wadatacciyar ni'ima. A hankali ya zare jawahir daga jikinsa ya kara mata fulo don kar ta farka ya nufi toilet ya dauro kyakkyawar alwala ya zo ya fara nafula raka'a goma sha biyu ya yi wa Annabi salati kafa dubu, ya daga hannuwansa sama yai ta kwaraea addu'a, yana yiwa Allah kirari da yaba su zaman lafiya da zuri'a me albarka shi da matarsa jawahir. Sai da aka yi kiran assalatu ya tashi jawahir suka yi sallar asuba, suka koma suka kwanta. Sha daya na safe Haidar ya farka ya zare jikinsa a hankali ya nufi toilet ya fara wanka Jawahir ta bude idonta ta tashi ta daddogara a hankali ta fito daga wannan dakin ta shiga dayan itama ta fada toilet Da yake falo ne da dakuna biyu a cikin falon wanda suka kama. Jawahir ta fito daga wanka ta tsane jikinta da tawul, ta shafe jikinta da hadaddun mayukanta masu kamshi da sa taushin fata hade da santsin jiki. Ta rinka mulke gabobinta da hadaddun turaruka na jiki masu dadin kamshi. Ta tsala kwalliyar fuskarta yanda yaka mata fuskar sai sheki take yi ta yi sumul sumul abun sha awa. Ta saka wani tsadaddan farin yadi sol mai dishi- dishin gwal din a jiki 'yar karamar riga ce fitet me dan guntun hannu rigar ta yi mata cif a jikinta. Sai siket din da ya yi mata tsantsan duk wata sura ta jikinta ta bayyana ba ma kamar kirjinta da yake cike da dukiyar fulani a tsattsaye suna barazanar tsokane idon me kallon su. Ta sha adon gwal yari da sarka manya ga awarwaro da zobuna tuni ta dauki kyalli tana sheki Tasa farin takalmi tana fesa turare ta ji dhigowar Haidar ta yi saurin boyewa a cikin labulaye: Haidar shima ya shirya cikin wani lafiyayyen boyel fari kal me laushi sai fitinan nan kamshi ne yake tashi a jikinsa kamar ya yi barin turare. Ya shigo dakin ya kama wara ido don ganin in da zai hango tauraruwarsa ga shi dai duk kamshinta ya cika dakin. Kafarta ya hango ta kasan labulan ya nufo wajen ya janye labulan tasa hannu rufe fuskarta. Ya tsane yana karo mata kallo cikin zafaffiyar kaunarta da matsananciyar sha'awarta. Ya jawo ta jikinsa ya manne ta a kirjinsa yayin da kaunar ta take dada ratsa zuciyarsa. Cak ya dauke ta yayo falo da ita suka zube akan kafet don karyawa, tana makale a jikinsa shi ji yake ina ma zai iya tsaga jikinsa ya tura ta ciki da sai ya fi masa sauki da yanda kaunarta take addabarsa a zuciyarsa. A baki ya rinka ba ta break din cikin lallashi da lallama don shi da da hali ma tauna mata zai rinka yi don ta samu saukin hadiya. Sai da ya tabbatar ta koshi sannan ya rabu da ita shima ya ci ya yi kat. Ya shiga wasanni da sassan jikinta in da ita kuma ta takure waje daya ta ki bude fuskarta. Ya dauke ta cak ya yi gado da ita yana cewa "To bari mu maimaita abun jiya tun da kin fi so ko?' Cikin marairaitar murya ta ce, "Wayyo Yaya don Allah ka kyale ni bana so yayin da ta kwabe fuska take kokarin yin kuka. Ya rungume ta "Sorry bebi na kada ki yi kuka da gangan nake yi miki. Rufe idonki, "Ta rufe yayin da ya saka mata 'yar batta guda biyu manya a hannun nata duk ya bude su. Ya ce ta bude idonta tana budewa taga custume yari da sarka da zobe manya tafka tafka kirar dubai sarkar mai harafin H/J, sai daya battar kuma manyan warwaraye ne guda hudu gaba daya Daimond kudinsu a kalla zasu yi dubu dari biyar da doriya. Bude baki tare da kwalalo ido ta ce "Yaya wannan fa? "Kyauta ce nayi miki don farin cikin yanda na riske ki. Ta kankame shi cikin murna yayin da ta lalubi bakinsa ta yi masa kyakkyawar sumbata, ta ce "Yaya na gode Allah ya saka maka alheri Ubangiji ya raba ka da sharrin makiya." Ya ce "Amin babyna, na gode da addu'arki Allah yasa mun samu rabon bebi a daren jiya ko kuma in an jima mu samu." Cikin shagwaba ta bigi kirjinsa "Um, um ni dai yaya ba za'a kuma ba da ciwo." "To shi kenan kada ki yi min kuka ma arahar hawaye." "Yaya ya aka yi ka samu masu harafin sunanmu.?" Ya ce, "Ai tun ranar da muka fara ziyartar asibitin kafin ayi min aikin nan naje gurin da suke kerawar nasa su kera min don zuwan wannan rana. "Kai Yaya amma kuwa na gode Allah ya saka da alheri Ya dora hannunsa akan bakinta ya ce "Shit bana son yawan godiyar nan kuma ki cire wannan Yayan da kike gaya min bana so. Cikin kashe murya da kissa ta ce, "To me zan dinga ce maka? "Ke za ki zabo da kanki ki rada min. Ya kawo kunnansa daidai bakinta "To gaya min naji". Cikin kasa kasa da murya ta ce, "My love yayi maka?" Ya rungume ta yana ihun murna yayi ya yi kwarai babyna kin iya zaben suna. Ta rufe idonta tana dariya. Ta kama lumshe ido irin na me jin bacci. Ya ce, "Bacci babyna.?" Ta daga kai kwantar da ita a kan gadon to kwanta na yi miki tausa. A hankali ya rinka yi mata tausar yana dan matsa mata jikinta. Sannu a hankali bacci yayi awon gaba da ita ya zuba mata ido yana kallon tsabagen kyau da Allah ya bata. Ga komai nata cif-cif ba abin da ya fi ba shi mamaki yanda ya jita tamtsan cike da ni'ima ga kirjinta cike da dukiyar fulani abun da yafi sha'awa da daukar hankalinsa a jikinta. Shima kwanciyar ya yi ya manne a jikinta ya kankame ta har sai da ta yi 'yar kara ta ce my love sannan ya sassauta mata rikon. Sai bayan Azahar suka tashi suka sake sabon wanka tare da yin alwala ya ja musu limanci suka yi sallar Azahar. Daga nan suka sake sabon shiri shigar kananan kaya suka yi ke in kin gansu sai ki zata Indiyawa ne. Suka ci kayataccen abinci me rai da lafiya, Haidar ya jawo ta jikinsa babyna mu dan fita mu zaga gari ko? In nuna miki wajajen ban sha awa da na kayatarwa. Ta noke a jikinsa tare da cewa "my love ka bari sai gobe jikina har yanxu yana yi min ciwo." "Ciwo babyna! Kada fa ya kawo mana matsala in an jima fa.? Ta bigi kirjinsa cikin wasa tana harararsa, "Allah Allah my love ka bari zan yi maka kuka. To na bari na bari babyna, tana langabe a jikinsa sai shagwaba take yi masa du ta wani narke masa sai zuba masa sangarta. Shi kuwa gogan ya rikice duk ta burkita masa tunani da sha'awarta sai riritata yake yi yana lallaminta, tare da taba wasanni a jikinsa nata ko zai samu 'yar nutsuwa kwana hudu yana jirarta ba tare da ya kuma neman yin wani abu da ita ba, sai yai ta faman riritata yana sangartata yayin da take zuba masa shagwaba son ranta shi kuwa yai ta biye mata don bata da masaukin da ya wuce jikinsa, ko yaushe tana manne a jikinsa yanayi mata tausa ko wasanninsu na ma'aurata. Aha har yanxun xa'a bani ko kuwa sai na kuuma? Idan kuuma ba'a bani ba............ hmmmmmmmmm . ((((( SALON SO)))) ((((((PART 35))))) : . Kamar yau ta sha wankanta ta kayata fuskarta da dogon wandon ta shima pick colour me baza daga kasa sai bakin gashinta da ya kwanta a bayanta yana ta zuba kamshi da sheki. Ta yi tsananin kyau irin kyan da baya misaltuwa, ta zira siririyar sarkarta da yari da abun hannu duk na gwal, jikinta sai ni:imtaccen kamshi ne yake tashi kamar anyi barin turare a jikinta. Ta fito falon in da yake zaune yana kallon wakoki cikin tashar turawa. Ta zo ta zauna a cinyarsa ta sakalo wuyansa da hannuwanta ta yi kasa-kasa da muryarta yayin da take kashe masa ido daya ta ce "My love ince ko dai baka yi fushi ba na barka kai kadai? Ya rungume ta tsantsan a jikinsa "Babyna ina sonki da yawa kina sani farin ciki koda yaushe duk sanda na kalle ki ina kasancewa cikin nishadi da annushuwa, bebi na ki yi wani abu akan yawan kaunarki da nake na zarme da yawa." Ta hada fuskarta da tasa ta tallafa kansa ta zira harshenta a bakinsa ta shiga juyawa cikin wani irin yanayi na SALON SO." Ta fa gigita shi ya ji wani abu yana tsikarar zuciyarsa ya rikide mata ya shiga sumbatarta ba kakkautawa, ya zira hannunshi cikin rigarta yana wasa da yana mata wani shu'umin kallo mai burkita kwakwalwa cikin kunnanta ya rinka rada mata kiyi hakuri bebi na ki bani hadin kai na nuna miki irin tsantsar kaunar da nake yi miki, ki taimake ni bebi na muraya daren yau don samun ladan sunnah". Ta yi zumbur ta mike cikin yanayi na tsoro da jin kalamansa, shima ya mike ya riko hannunta ta marairaice fuska tana son yin kuka, "Ka tausaya min Yaya wallahi akwai ciwo." Ya rungume ta ya dora kanta kan kafar shi yana rarrashinta "Ki yi hakuri babyna ba zaki ji ciwo ba, wancan ma don na farko ne shi yasa ki ka wahala amma ba zaki sake jin ciwo ba, ki taimaka min ki bani hadin kai gudun kada ciwon mara ya dame ni kin ji bebi na kin amince? Ta daga kai cikin yanayi na rauni da damuwa. Ta bashi tausayi ya san bata so don ta wahala ranar nan, ga shi, shi kuma tun da ya dandani yanda take ba zai iya hakure mata ya sa mata ido kamar da daya zuba wauta ba. Amma insha Allahu zai bi ta a sannu don ta samu sassauci. Haka ya rinka lallabata yana bata damammiyar madara da gasasshen nama mai ruwa ruwa. Duk wani abu da zasu gudanar sun gudanar, wanke baki shafa turaren gabobi, matsa mounth freshner a baki fesa Air freshner, a kowacce kusurwa ta dakin inda sanyin dadin ya rinka fita sabo da sanyin AC da dadadan kamshi da ya hadu ya dauke ta cak yayi gado da ita ya rinka yi mata wasanni ya taba can, ya tsotsi can ya murza nan cikin dan lokaci kankani ya kashe mata jikinta da salon kaunarshi. Tana jin shi yana zame mata kayan jikinta amma bata da wani katabus bare ta yi yunkurin hanawa, sannu a hankali ya rinka binta har ya cimma burinsa. Ga mamakinta sai ta ji bata ji ciwo da zafi kamar na ranar nan ba. Bayan hankalinsa ya dawo jikinsa ya rinka rarrashinta da lallaminta yana yu mata tausa har bacci me nauyi ya dauke ta. Yayin da shima ya manneta a kirjinsa hannunsa yana kan nononta yana wasa da shi har bacci ya yi awon gaba da shi. Karfe bakwai ta farka ta ji ta manne a kirjin Haidar ta rasa yanda zata yi don ba taso ta yi motsi don kada ta yi motsi don kada ya farka saboda yau wata irin kunyarsa take ji tare da wata irin zazzafar kaunarsa da take ratsa dukkan gabobin jikinta. Ya bude idonsa ya rinka dubata cikin sha awa yayin da tasa hannuwanta biyu ta rufe fuskarta tana murmushi da ita zata shi a jikinsa suka shiga bandaki tare suka gudanar da wankan lokaci daya suka dauro alwala suka fito suka gudanar da sallar asuba a makare. Ya matsa kusa da ita ya zare hijabin da ta yi sallar ya kwanto da ita kan cinyarsa ya kura wa kirjinta ido. Yana kallon manyan mamanta da suke cike jajir da su a tsattsaye basu da niyar rankwafawa kamar wanda aka da sa su ko da yake dashin Allah ne Jawahir tasa hannunta ta rufe masa idonsa don ganin irin shaidancin kallon da yake yi mata ta san ba za su waye lafiya ba. Ya dan ciji hannun nata ta janye cikin sauri ya tsirawa fuskarta ido yana kallon kyakkyawar fuskarta. Ta lumshe idanuwanta ya zura harshensa yana lasar girarta zuwa kumatunta Ta sakala hannuwanta a bayansa ta tallabe shi sosai ya zira harshensa cikin bakinta suka ci gaba da farantawa juna rai. Bacci ya kuma kwashe su sai shabiyu suka tarka lokacin suka tsala wanka suka shirya Haidar ya shirya cikin jins da damammiyar T-shirt me gajeran hannu jikinta layi layi ne na fari da ja, ya yi kyau sai kamshi yake kwararawa. Ya dawo falo ta kwanta a doguwar kujera yayin da ya kunna T.V yana kallon tashoshin Turawa yana jiran jawahir ta fito suyi break. Jawahir ta gama shirinta cikin damamman guntun wando da 'yar bingilar riga iya cibiya, gashinta ya sha gyaran sai sheki yake zubawa da kamshi jikinta kuwa sai fitar da nau'ikan kamshi suke yi masu narkar da zuciya. Ta ta ko a hankali kamar bata son taka kasar ta fito falon tun kafin ta karaso falon Haidar ya kafa mata ido, kaunarta tana kara ratsa shi kamar ya hadiye ta don so. Ta tako a hankali har zuwa kan kujerar da yake ta kwanta dai dai a cinyarsa, ya yi wata irin wawar a jiyar zuciya, ya kuma rungume ta babyna zo muje na baki break kada yunwa a illata min ke, ta langabe a jikinsa tare da kiransa "My love ya ce "Na'am bebyna ya aka yi? "Wallahi my love gida nake tunani yaushe za mu koma mu ga iyayenmu da 'yan uwanmu? Ya kara rungumarta "Haba Bebyna muna tare da ke ki ke son koma wa gida ki yi min adalci mana ya kike so nayi da dinbin kaunarki na ga baki damu dani ba." Ta yi saurin sa tattausan hannunta ta rufe masa baki "Yi hakuri my love ba nufina ba kenan wallahi ina sonka ina kaunarka zuciyata tana son kasancewa tare da kai koda yaushe. Ya yi mata kyakkyawar runguma yana sumbatarta da haka suka je suka yi kataccen break. Ya dauko abayarta ya sa mata ya rufe mata kanta da karamar hijabi fari mai kyau yaja hannunta suka fice yawon zaga gari. Hakika ta sha kallo ta yaba da tsarin kasar London gari ne me kyau da ban sha awa. Ita dai ba don tunanin iyayenta da 'yan uwanta ba, da ta roki Haidar su dawo kasar nan da zama sai dai ba za ta iya ba saboda kulafucin iyaye da 'yan uwanta. Sun zaga sosai daga nan suka dire a wani hadadden gidan abinci girke girkensu sun kayatar da jawahir ta ji dadin abincin sosai har ta rinka santi. Sai yamma likis sannan suka koma masaukinsu. Washe gari ma wajen sga biyu suka fita, ya rinka zagayawa da ita suka dire a wasu kamfani na kera akwatuna ya zabo mata set biyu masu kyau sabon dizayin don a lokacin ma ba su zo nan ba. Da masu ruwan zuma da masu ruwan toka. Daga nan suka wuce wani tafkeken shago na saida gwala gwalai, tare suka rinka zagayawa, duk in da ya hango me kyau in dai ta bashi sha'awa ba ruwansa da tsadarta sai ya dauko mata sarkar kafa me kyau ya kara a kafar jawahir tuni ya ga sun kara haskakat kafar tata Ya kuma dakko sarkar hannu itama ya kara mata subuhanallah tuni yaga kyakkyawar matar tasa ta sake fitowa sosai Abin ya ba wa jawahir mamaki, yanda ta ji an buga kudin mai yawa taga ya biya duk tsadarsu bata re da ya damu ba. Ta matso dab da shi ta kwantar da kanta akan kafadarsa ya sa hannu biyu ya rungmeta "My love don Allah ka daina yawan kashe min kudi don hidimar da kake yi min ta yi yawa. Ya dada rungume ta yana dan bubbuga bayanta kada ki damu bebyna komai na mallaka a duniyar nan naki ne ki daina damun kanki don na kashe miki 'yan kalilan din kudi." "To Yayana na gode Allah saka da alheri Ubangiji ya kara budi. "Yauwa Bebyna, amin" Ta rada masa a kunnensa "My love" mu koma gida abincin jiya." Cikin dariya ya kama bakinta wannan bakin ya iya kwadayi ko, ta manne kanta a kirjinsa tana murmushi suka wuce gidan abincin. "Yan kwana biyun nan jawahir tana fama da yawan kasala da lalaci ga yawan bacci, yanxu basu fi ya dadewa hira ba sai jawahir ta kama bacci. . SALON SO . PART 36 . Abin da Haidar yake dauka yawan gajiyar da ita da yake yi ne shi yake yawan sa mata kasala. Yau ma tare suka shiga toilet wanka suka yi suka cuda junansu cikin farin ciki tare da wasanninsu na ma'aurata. Ya kinkimota ya fito da ita ta zille daga cikin sa ta koma daya dakin don ta shirya. Haidar ya gama shirin cikin wando iya gwiwa wato tree gwata da riga marar hannu me kyau yana ta kyalli don shima fatarsa ta kara gogewa. Kowa ya kalli shi yasan fatarsa ta kara goge da hutu da jin dadi irin na masu da shi. Jawahir ta gama shirinta wani mini siket iya cinya da ya matse mata cinyoyi sai dai yana da tsaga gaba da baya. Rigarta iya kirjinta ta tsaya cibiyarta a waje ta ke fuskarta ta kara haske da kyau da kuruciya yarintarta ta kara fitowa fili. Jikinta sai fitinannen kamshi ne yake tashi me ta da sha awa. Ta dawo dakin da ta bar shi saboda zazzabi da ta ke ji ga ta shin zuciya, yana tsaye yana fesa turare ta zo ta kwanta a bayansa tare da zagaye shi da hannuwanta ya kamo ta ya zagayo da ita gabansa tare da cewa "Bebina lafiya me yake faruwa ne da ke, jikinki duk ya canja ga yawan lalaci da bacci.? Ya dauke ta suka koma kan kujera suka zauna yana lallatse jikinta don ganin ta kamaimai me yake damunta, duk ta narke a jikinsa ta langabe tana ta zuba masa shagwaba tare da marairaita. "Bebina muje asibiti a duba min ke don na san me yake damunki. Cikin ma rairaita ta ce "My love ni bana so muje asibiti don kada suyi min allura idan na sha fanadol ma zan samu sauki" Ya ce "Haba bebyna ya za ayi na barki haka kin ji jikinki kuwa yanda ya dau zafi ya kama lallatsa wayar likitan Hotel din ta rike hunnansa kamar za tayi kuka. Don Allah "My love kada ka kirawo shi wallahi na sha magani zan ji garau. Ya ce ke dai kin fiye tsoron Allura." Ya hada mata break yana bata a hankali tana kau da kai alamar ba ta so don bata jin dadinsa ya rinka lallaba ta yana ririta ta har ya samu ta dan ci. Ya bata magani ta sha ta kwanta a jikinsa tana dan yi mata tausa tare da mammatsa mata jikinta. Bacci ya kuma dauke ta ya gyara mata kwanciya a jikinsa lokacin da ta tashi jikin nata da sauki daga nan London suka wuce kasar America jawahir tayi mamakin yanda taga Amerika ashe itama haka take da kyau gaskiya kasar ta bata sha awa. Nan ma Haidar ya bude bakin aljihu yai ta narka mata kudi kamar vai san zafin nema ba. Watan su daya a Amerika suka dire kasar Saudiya jawahir tayi kyau har taga ji da kyau ta kara haske da kuruciya, duk wanda ya kalle ta zai gano yaron ciki a jikinta don wani dan ya cewa da ta yi da wani shirtaccen kyau da ta kara, nonuwanta sun sake cikowa suna tsaye kyam da su. Haidar yana ji da ita yana lailanta duk da canjawar da jawahir ta yi hakan bai sa Haidar ya gano ajiyar da ya yi a jikinta ba, bare ita da kuruciya ta yi mata yawa ita dai tana jin canji a jikinta amma bata dauke shi a komai ba, bare ta kula. Suna ta shirye shiryen dawowa gida sun sayi tsaraba ta 'yan uwa da abokan arziki kamar masu shirin bude kamfanin sutura, da kayan kyale kyale. Jawahir tana kwance lamo a kan gado zazzabi ne me zafi ya rufe ta lokaci daya Haidar ya shigo ya zauna gefen gadon yana cewa kasa uwar bacci ba dai daga wannan 'yar fitar tawa har kin koma baccinba.? Ya sa hannu zai dago ta ya ji jikinta da zafi. A gigice ya dako ta ya rungume ta a jikinsa yana jero mata tambayoyi "Bebina me ya same ki daman vaki da lafiya, baki gaya min ba daurewa kawai kika yi?" Bai jira amsar ta ba ya sabe ta a kafada ya yi waje da ita, motar Hotel din ya yi amfani da ita ta xuwa asibitin. Likita Bilkisu muhd Adam ta karbe ta cikin gaggawa ta shiga yi mata tambayoyi da gwaje gwaje a lokacin ta yi mata sukanin ta hango karamin ciki dan wata uku a jikinta. Haidar ya juyo cikin farin ciki ya dako kan jawahir yasa harshensa yana lashe hawayen nata. Yasa hannunsa kasar mararta yana dan shafawa ya rada mata a kunnenta babyna mu duka mun yi kuruciya da wauta sai dai mu kiyaye gaba sai dai mi ta addu'a Allah ya raya mana Bebinmu Allah ya fito mana da shi lafiya." Ta ce, "Amin cikin shagwaba ta ce ka huce my love." Ya sake rungumarta na hakura bebina tun da ke ma ba laifinki ba ne na mune da rashin kulawarnu. Nan fa sabon tattali da ririta suka tashi don Haidar daga kansa yake yiwa jawahir wanka wai don kada ta wahala duk wani abu da take yi masa yanzu shi ya dauke mata nauyinsa. Ita kuma ta kan shagwabe masa ta ce yana ta aikin lada haka yake so ta zauna ba nono. Ya ce "Ai aikin lada da yawa yi min kiss shima lada zaki samu. Ya turo mata kumatu ta cije shi ya da fe wajen a'a a'a bazan yarda ba sai na rama. Da ya yi kanta zai turmusheta sai ta daga hannu sama tana cewa bebinka bebinka zaka wahalar dashi ya yi dariya ya dumgure ta." Ta yi dariya don Allah yaya mu goma gida mana. Ya zaro ido "Ke yaushe zan yarda mu shiga jirgi da wannan dan ta yin cikin nawa." Salon kisa wabi abun ya faru da shi ai mu da mu koma gida sai kin haihu su ganmu da bebinmu. Ta marairaice ta fada jikinsa ta saka kuka ya dagota yana dariya to to sarkin shagwaba yi shiru da gangan nake yi rana ita yau jirgin mu zai daga zuwa Nigeria Ta kuma kankame shi tana kyal kyala dariya, Haidar ya gama luguiguita jawahir dukjansu zube a gado suna mayar da numfashi. Hannun Haidar yana kasan marar jawahir yana shafa bebinsa. Ya ce ko kin san wani abu? Ta girgiza kai ya ce sai da likitan nan ta fara gaya min kina da cikinsa nan na gani alamomin hakan daga jikinki. Ga shi yanzu har ya fara fitowa kamar ba dan wata hudu ba, ta marairaice murya cikin shagwaba ta ce wallahi ni kunya nake ji su ganni da cikib nan ai sai suce vani da kunya daga zuwa jinya, na koma da dan rakiya. Haidar ya dada jawo ta jikinsa yana shafa bayinta tare da dariya yace in banda abinki ni shi ne shedar na warke. "Kinga duk wanda ya kalle ki ba sai ya tambaye mu an samu nasarar aiki ko ba'a samu ba, ta dada shigewa jikinsa ta ce yanzu shi kenan kowa yasan abin da muka yi ko? Ya kara tun tsirewa da dariya yanzu bebina in banda abin ki akwai wanda ya taba sha a ruwa ne?" Kowa kika ganshi da ciki ai ta haka ya samu ta ce "Na shiga uku yanzu momyna da Dadyna da Anty da Inna da Abbanka haka za su ganni da ciki gaskiya zan sha kunya kai ku wa ka yi min wayyo babu ruwanka ko? Washegari jirginsu ya daga zuwa Nigeria da yake an san da dawowarsu 'yan uwa iyayensu sun zo taryarsu babu wanda yasan jawahir tana da ciki sai dai idonsu ya gane musu. A cikin jirgi, jirgi yana jama'a aka fara sakkowa, Haidar ne a gaba jawahir tana biye da shi sun yi kyau sun dade kara ja da fari jin dadi da hutu ya sa sun haske wajen kowa ya kalle su sai ya sake duban su ba don murmushin da su ke dokawa ba, da iyayensu basu gane su ba. Suna sakkowa jawahir zata kwasa da gudu ganin iyayenta Haidar ya riko ta yana ce matw ki kula kada ki yi min ganganci da ciki." 'Yan uwa suka yunkuro gaba daya suka taro su jawahir ta durkusa kasa ta kama kafar babanta ta rike tana me jin dadi da murnar ganinsu. Ya sa hannu ya dagota yana kallonta fuskarsa cike da murmushi na yanda yaga 'yarsa ta kwantar da hankalinta gashi yanda ta kara kyau da haske kamar balarabiya. Inna ta dafa kafadarta jawahir ta juyo ta rungume ta tana murna Inna ta dako ta cikin dariya ta ce ke taurin me nake ji haka? Ko dai kin samo mana dan London? Kai amma abu ya yi kyau." Dady ya ce "Menene?" Inna ta ce, "Ciki ne da ita da sauri jawahir ta fuzge jikinta cikin jin kunya taje ta rungume Mominta da Antinta, ta je ta gaisa da Abban Haidar. Nan fa sukai ta gaisawa da 'yan uwa ana murnar ganin juna. Daga nan suka rankaya gaba daya don raka su gidansu. Jawahir ta yi mamakin canja fasalin gidan nasu da aka yi, ya yi masifar tsaruwa, don ya fi na da ma kyau, tsadaddun kujerun da kayan kyale kyalen da suka suyo a kasar waje. An kawata babban falon da su, sai ka ce falon sarauniya America don tsananin tsaruwa da kyau da ya yi sai da aka ci aka sha sannan iyayensu suka taya su murnar samun lafiyar. Haidar da karuwar da suka samu. Kowa ya fashe, sun tattafi ma'aikatan gidan suka kara gyara gidan ko ina ya kara yin fes sai sheki da kyalli ne yake tashi da hadadden kamshi. Da daddare "Faruk ya zo suka rungume juna shi da Haidar suna murnar sake ganin juna. . SALON SO PART 37 . Jawahir ta shigo masa da kayan ciye ciye suka shiga gaisawa. Faruk ya ce "Mutumin lallai naga alamar ka warke har da tsarabar dan london ne ko jafan ko dan ijift ne ko America? Naga alamar kamar jawahir tana da ciki ko?" Haidar ya yi dariya ya ce "Ai ma ganinku nayi masu tambaya yanxu kuwa kowa ya kalle ta yaga shedar aiki ya yi kyau. Suka kyalkyale da dariya tare da tafawa Faruk ya ce, "Bakinmu da nayi muku dai

Chapter 10 of 13