Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ko Eh toh shikenan ai dubasa kawai xandauko ki kixo kiyi kwama gaisa da mummy kinga bata taba ganinki ba dama Muryar ta nadan rawa rawa Tace Ok...... Ok tohm sai anjima Takashe wayar tana cilla da ita kan gado tafara rera kuka tamkar ba xata daina wanne hali yake ciki me yasameshi toh baxan iya xuwa gurinsa ba sbda nayiwa kaina alkawarin baxan sake yadda yaganni arayuwarsa ba, duk da sonsa yagaxa futa acikin raina har yanxu kuma kara karuwa yake tamkar wutar da ake xubama fetur. Daga wurin Adeel kuwa yasauke wayar yana cewa Siyam Ai mutuniyar taka xuwa xatayi dubaka gobe xankawota tadubaka gashi kace gobe gida xaka koma Nagaji daxaman hospital dinnan Adeel shiyasa gwara naje gida naci gaba dajiyyar kaina sbd nasan iya raunin jikina ne xai warke bawaini din ba sbd cutar datake damuna acikin raina tafi wannan ciwon xafi, soyayya taxuba mun dafi Adeel tashina daga wannan cutar sai inwani ikon Allah amma tabbas maganin cuta ta yana nesa dani matuka, Xaro ido Adeel yayi tamkar yafashe dakuka yarike hannun abokin nasa Aaa karka ce haka brister babu wani abu daxaka nema yagagareka mutkar kagaya wa Allah Hawaye ne xafafa suka fara futa a idanun Siyam Nayi kuskure Adeel domin Allah ma nayimasa laifi duk wanda xai wulakanta dan adam komin yayi yake mailaifine awurin Allah Wa kakeso brister asanina baka soyayya dakowa Nima bansan yaushe yakamani ba nafarkane kawai daga nannauyan baccin dayadauke ni naganni acikin ta alokacin da damata tawuce ni Hmm Adeel yayi murmushi Aikai mutkar agurin matane babu wata dama daxata kure maka kowacce yarinyace kafi karfin ta. Kuma kanada alfarmar da agarin nan ba mutumin daxaka nemi auren 'yarsa yahanaka ba ai abin alfaharine agurin ahlin dakanemi irinsu kadaina kuka ni abokinkane kafadamun komi gameda ita xan nemo maka ita xan kawo maka ita xan iya SADAUKAR WA dakai dikkan lokacina harsaikasamu farincikin ka Rumgume sa Siyam yayi yana dansamun rilif axuciyar sa Nagode maka Adeel tabbas naji dadin kwantar mun da hankali dakayi sannan kuma inaso nafadamaka mutkar kasan lbri na da ita xakaji haushina zaka tsaneni xaka Allah wadai da halina na wulakanta 'yanmata insuka nuna suna sona shiyasa nayanke shawara kawai baxan taba fadawa kowa labarin abun dayafaru tsakanina da ita ba kawai xabar komi araina har cutar soyayyar ta takashe ni domin nasan komi dade komu juma mutkar banganta ba ciwon sonta ne ajalina. Aa haka vaxata taba faruwa ba brister kanadani ga mummy ga Abba ba abinxaifi karfin ka indai har yanxu ina nan amatsayin amininka bakasauyaniba dan Allah kabani labarin ka da ita wacce kake fadamun din. Hawayene sukacika masa ido yafara bawa Adeel labari tundaga farkon xuwan su mowana aiki gidansu harkawo yanxu dayake bada labari Adeel wanda gumi yashigakaryo masa tamkar ba sanyi ake yiba saiyanxu yagane komi saiyanxu yagane cewa ashe Siyam ne yakarya Mowana saiyanxu yagane cewa Mowana brister takeso abaya harta fada tarkon cutarsa Mowana nansa brister yake nema xahiri ko shakka babu itace abunda wani bangare naxuciyarsa yace kenan Muryar sa awani dakile kamar miciwon baki yakalli Siyam Karka damu abokina xankawo maka Mowana har gida kuma insha Allahu kamar kasame tane xanfita neman maka ita daganan innaje gida xanfita, Kafin Siyam yakuma wata magana Adeel yafuce yana maijin wani radadi acikin xuciyarsa kuma yayiwa kansa alkawarin SADAUKAR WA da brister soyayyarsa har abada sbd cancantarsa dakuma fuskantar cewa yafisa bukatar Mowana atare dashi dik da dinbin son dayakeyiwa Mowana yafukarfun akarasa da dankadan. Dakyar ya iya jan motar yakai kansa gida tare da taimakon Allah 😢😢 Adeel nafuta suka hadu da mummy da Abba sundawo yagaidasu sannan yayimusu yamaijiki Koda suka shigo ciki sunsamu yayi bacci donhaka xaunawa sukayi kusa dashi karfe hudu dai dai jawwa takaraso tare da 'yarta Rooofi'ah wacce baxata wuce shekara 2ba Abba ne yadauki roofi ah jawwa tagaidasu Mummy yajikin yayan Dasauki gobe ma xa asallamemu ya maigidan naki Lfyklau mummy yacema naimuku yamaijiki xaishigo anjima Abba yakalleta yana wasa da roofi ah Aidakin bari ma saigobe kyaxo tunda gobe xamu koma dashi gida Ashagwabe takalli Abba tana shirin yin kuka Abba xuciyata takasa jurewa baxan iya ba inajin yadda mummy tafadamun yaya yayi rauni bakidaya nafirgice da tun ranar xanxo abban roofi'ah shima toh ranar yayi dan fama da xaxxabi shiyasa na hakura naxauna, Ayya ashe shima baijidadi ba Wlh mummy Toh Allah yasauwake yanxu dai ya hajiar taku Abba lftyrsu klau wlh Saiwajen karfe biyar Siyam yafarka bakaramin dadi yajiba ganin kanwartasa itama dasauri taje tana rike hannayensa sai kuma tafara kuka Yaya sannu garin yaya haka yafaru yaya banji dadi ba dama kwana 2 bakaxo gidana ba nayi kewar ka dayawa yaya. Yadan rumgume ta da gefen hagunsa yana lallashinta Toh daina kukan ainaji sauki kinji my jawwa ina my baby roofy Tai murmushi tana dago kanta Yanxu suka fita da Abba xaisiyo mata choculet Ummm sarkin shan xaki kenan Mummy dake gefe tadauko abincin da jawwa taxo dashi tabude shinkaface soyayyiya jaluf tasha kifi da karos da kabej taxuba masa afilet tana mika mata Unguwa basa saikacinya abincinnan donkaga darana bakaci komiba Yalangwabar dakai Mummy pls yayimun yawa inaxankai wannan abincin Taharareshi Cikin ka mana Yakalli jawwa ashagwabe My jawwa kinji mummy ko kigayamata baxan iya cinyewa ba Jawwa tana dariya ta kalli mummy Mummy xamu ci tare kawai amma aikinsan yaya wannan abincin dakika xuba na ranar sa biyune ahakama sai in yakasance nawane abincin Ke tafican dabakyanan toh nawa yake ci, suka kyalkyale da dariya shi da jawwa Abba yaxo shigo wa yace Aa harda mara lfyr adariyar ko dayake kunhadu fa saidai asa muku ido kuma ammm Siyam Dr fa yace akula daraunin nan naka nagefen ciki sbd mutkar akayi wasa xaitaba maka ciki, ka kula naga kanawasa da wannan raunin Ya sunkuyar dakai Tohm Abba Roofi 'ah ce tatafi dugui dugui gurin Siyam tana bangala dariya yariketa dahannunsa nahagu yana mata wasa. Sai wajen karfe takwas mijin jawwa yaxo ya duba Siyam yadauki matarsa suka tafi. Adeel yakasance cikin wani mawuyacin hali bayan komawar sa gida ba abunyake kallo fari bakidaya kansan ya kulli wannan al amarin na Siyam da Mowana musalin karfe goma nadare mowana taga Adeel baikirata ba gashi har lokacin dasukeyin wayar xaiwuce don haka ita takirasa amma baidagaba takira yafi sau goma amma yaki dagawa saitadauka kawai koyayi barcine donhaka itama kawai takwanta bacci. 😢😢😢😢 yau aka sallami Siyam har sun koma gida wanka yayi amma ba normal wanka ba na watsa ruwa aa yagwaggoge jikinsane da tawul sannan yasa wando karami tree kwata jikinsa yanxu bayasa riga sbd yankan dake gefen cikinsa. Falo yafuto yakwanta nan yasamu mummy tanaxaune da filet din abinci ahannunta tana jiransa yafuto murmushi yasakar mata yana xauna wa kusa da ita Ka fito Yace Eh mummy kinatajira na ko Tai dariya tana shafa kansa Siyam karkadamu ga abincinka kaci bari nima naje nadan watsa ruwan xandawo anjima kadan nabaka magani kasha Tohm mummy Tafuce tana daga masa hannu yadaga mata shima tare dajanyo flet din abincin yafaraci yana lumshe idanunsa. Wayarsa ce tashiga kuka Ahankali yalallaba yadaukota sbd tana dan nesa dashi Adeel yaga sunan yabayyana agls din wayar dagawa yayi Slm Wslm Yah brister jikin naka Allahamdulillahi Gud yanxun kana hospital dinne ko kuma kundawo gida Mundawo daxu shikenan anjima xanshigo Tohm saikaxo. Kanaji kabiya ta wajen wannan baye rabiyar ta layinku kasiyomin dafaffiyar masara Adeel yayi dariya Tohm bari saina taho Umhum Yasauke wayar yanacigaba dacin abincin sa. Game da Adeel kuwa karfe biyu yaje gidansu Mowana bayansun gaisa da momma yake gayamata xasuje duba abokinsa da mowana tace ai shikenan sai sun dawo yana lekawa dakinta gamamakinsa saiyaganta ashirye cikin wani dankareren les baki mai ratsin milik da mayafi milik haka takalmima tana kokarin sa dankunne tagansa atsaye yaxuba mata ido. Takarasa sawa tana kallonsa YayaAdeel yadai kashigo bako sallama wlh kakusa tsoratani fa kiris xuciyata bata fasheba Ya lumshe ido sbd tayi kyau sosai baitaba ganin kyanta xir ba irin nayau Aa nayi bakiji bane Ta hararesa Kajikafa kunne nafa nakofar sbd tsaro Tohm naji tunda dai nasameki har kinshirya toh mutafi Takallesa tana jan birki kamaryafa inakuma xamu Hummm kinajina muje kawai duba brister mana damukayi maganar dake jiya awaya Ta lankwasar dakai Ayya namanta ma bantamvayeka mejiki ba, wlh kaga kuma yanxu jirana akeyi yaune kamun hubba kuma nice babbar kawar ta dan Allah kayi hakuri kace inamasa sannu idankaje Yabata rai sbd ganin yadda take tawani rawar jiki bakinta ma narawa Aibadadewa xamuyi ba dubasa kawai xami nadawo dake gidan bikin Tajuya masa baya tanaso taboye damuwarta amma yanaso saiya tilasta mata bayyanata, Dan Allah yaya Adeel katafi wlh baxaniba ina da uxiri kuma kaima kasan ko wacece hubba agurina Yayi murmushi Humm karki damu nasani sannan kuma inaso kitina kema dawaye brister agurina amma shikenan tunda sokike saikin nunamasa ban isa insakiba ko na hanaki ba nope Yanagama maganar yafice daga dakin Dasauri tabisa tana rike hannunsa Dan Allah yaya Adeel kayi hakuri muje kawai wlh banaso nabata maka rai koda saudaya nayi maka alkawari batun yanxuba xankasance mai biyayya agareka donhaka koda xanrusa wani kudirina xanmaka biyayya Kallonta yayi yadda ta kankame hannunsa anata tana kuka tamkar wacce aka yiwa dukan tsiya Xuciyar sa tayi rauni yaji dama yafasa SADAUKAR WA da brister ita sbd yafisa bukatarta yanajita har cikin hanjinsa, Game da Siyam kuwa yagama cin abinci kenan saiyatashi yashiga bedroom dinsa yana duba wasu takardu dake kanwani table bisetbed wata guntuwar takarda yagani tafado kasa yadaukota yana budewa Daya duba kwanan watan jikinta saiyaga tun lokacin da mowana ke aiki agidan sune sakone kamar haka DA SOYAYYAR KA NAKE KWANA NAKE TASHI RASAKA BABBAR MATSALA CE AGARENI INA MAISANAR MAKA DUK LOKACIN DAKA RASANI TOH KWA BAXAKATABA SAMUNA BA, XAN SADAUKAR WA DA WANI SOYAYYARKA KODAKWA KARSHEN NUMFASHI NA KENAN. akirjinsa ne yashiga bugawa fat fat dakarfi karfi kafin wani tari yataso masa maixafi dakyar yalallaba ya iya futowa falo daf da shugowar Abba da gudu yataresa yana jijjigasa amma ina tun Siyam yana nuna kirjinsa har yaxama hannun ma yayikasa yasaki tamkar ya mutu kuka sosai Abba yake kafin yakira dr mummy ma jin Abba shuru yasa tabiyo bayansa ganin halin datasamesa da Siyam yasa tafasa kuka tana kiran sunan Allah rumgume sa sukayi suna kuka tamkar ya mutu dr Abdurrahman ne yashigo hannunsa dauke da box din aiki yakaraso yana maisa Abba yakwantar da Siyam yafara duddubasa dakyar yasamo kan numfashinsa yadawo amma sama sama yakasa mikewa sai abin janyo numfashi yasamasa yadubi Abba Am pls Alhaji koxa abincika aga menene brister yake so baisamuba hartakaisa dafadawa wannan yanayi so agaskiya dai akwai matsala sosai mutkar ba akawo masa abundayake nema ba, sbd xuciyarsa daf take da samun matsala kuma xai iyasamun ciwon kwakwalwa sbd yawan tunani dayake maixafi. Abba yakalli mummy itama takalli Abba tana kara sakin wani sabon kukan takarasa inda Siyam yake akwance kamar gawa Wayyo Allah na Siyam Allah yabaka lafiya amma bansan indaxanje nanemo maka Mowana ba danaje nasan itace matsalar ka Abba yaklleta Wacece Mowana kuma Shiyasanta Alhaji wata yarinyace Daukar wayatayi takira Adeel alokacin yakusa ma karasowa yanadaga wayar mummy tafashe dakuka tanafada masa abundayake faruwa Hankalin sane yatashi yajuya yana kallon mowana wacce ke gefensa Mummy ina hanya gani nan xuwa yanxu insha Allahu Lfy yaya Adeel Mowana tatambayeshi Bai bata amsaba sbd tsabar tashin hankalin dayake ciki Gabantane yatsananta faduwa ganin sun isa bakin get din gidan su Siyam Tafashe dakuka dan Allah karka shiga dani dan Allah mukoma Kosauraronta baiba saidaya faka motar apaking space sannan yabude yafuto yanaxagayawa yabude bangaren maixaman banxa Yaya Adeel mekake nufi Xaki sani idan muka shiga cik karki tada hankalin ki bakomi Tashare fuskarta tana saukowa tabi bayansa suka nufi part din Siyam. Daf daxasu shiga kamar antaba SIYAM yafarfado yana rarraba ido mummy tatafi wajensa taji sallamar adeel tana dagowa taga Mowana abayan sa Xaro ido tayi MOWANA tafada dakarfi tana xuwa ta rumgume ta siyam kuwa kif kifta ido kawai yake yana kada hannu tare da nuni da mowana yayin da hawaye ke xuba ta gefen idanunsa Adeel yakarasa gabansa yana rike hannunsa cikin nasa alamar yakwantar da hankalin sa fixgewa yayi yana sa hannu yacire abunda akasa masa ahancin sa xuwa bakinsa yamike tamkar wanda yasha giya yana layi yanufi Mowana dake kusa da mummy taxama tamkar gawa don ko kwakkwaran motsi takasa yi. Yanaxuwa gabanta yaxube bisa gwiwoyinsa tare da hada dikkanin hannayensa guri daya hawaye nabin fuskarsa magana takasa futa abakinsa saidai motsa bakin dayake kamar maikokarin koyar magana Kallon Adeel tayi tana kallon mummy Abba ma taga ita yake kallo tafashe da kuka tana rugawa dagudu bayan Adeel tare da magana cikin tsoro Dan Allah kamayardani gida yaya Adeel narokeka Mummy dasauri tagirgixa kai Karki xama mara imani mana mowana komi Siyam yayimiki yakamata kiyafemasa xuwa yanxu tunda kinga halin dakikaxo kikasamesa badan xuwanki ba danarasa shi sbd tsananin so daya harbesa kodan haka kinyi masa afuwa bisa laifinsa ki amshe sa akaro nabiyu Adeel ta kalla tana girgixa kai Aa mummy aa mummy kiyi hakuri babu sauran wata dama yanxu tsakanina da Siyam mummy inada wanda xan aura ko yaya Adeel baifadamuku nice matar daxai aura ba Bakidaya suka xubawa Adeel ido ciki harda Siyam wanda ke tsugune yamike yana ja dabaya Ahankali saura kadan yadaki bango Abba yatarosa Adeel yayi murmushi yana neman gu yaxauna yakalli mummy da Abba da Siyam yayin da mowana shitake kallo idanunta basu bar xubarr da hawayeba Hakane mowana itace matar daxan aura mummy. Amma tunjuya daya bani labarin wacce yakeso nagane mowana tace hankalina yatashi mutka. Bankara tsorataba saidaya faramun wasu maganganu akanta wanda yafaru tsakanunsu abaya nagane cewa tabbas shine wanda mowana tafiso fiye daduk wanda xata nunawa somatsayin miji aduniya take nafara tunanin yadda take tilas tawa kanta da soyayya ta bawai don nine xabintaba tundaren jiya nake shawarar SADAUKAR WA da brister soyayya ta domin yafi karfin wannan daga gareni kuma ransa yafimana dik wani abu daxa musamu aduniya. Wani kuka Mowana tasaki mai ciwo tayo kan Adeel tana cukumo wuyan rigarsa Kacuceni kaci amanata Adeel baxantaba manta wannan wulakantarwa dakayi min ba agaban wanda dama can ni wulakantacciya ce a idanun sa. Kai harkana tunanin xan iya sauya wata sheka nakai kwaina bayantaka toh kasani SADAUKAR WA dakayi mutkar tanice batayuwuba wlh. Xatafuce Abba yaruko hannunta cak ta tsaya tana tsugunawa harkasa Baxanga laifinki ba yarinya sbd ba asan irin abubuwan dayayi mikiba abaya sbd haka wannan abundakika yi kinyi daidai amma kisani ran Siyam tamkar ledace akan ruwa koda yaushe xai iya tafiya duk dacewa kowanne dan adam ma ahaka yake ammakisani ke musulmace yakamata ki tuna Mummy kuka take kawai tana rike da Siyam wanda keta wani xaxxafan tari yarike kurjinsa da karfi yana kiran sunan Allah dasauri dasauri Kabarta tatafi Alhaji Siyam in Allah yayi mungama rayuwa dashi dole mu hakura dashi inko kwanansa baikare ba xaitashi komin wahala Adeel yakalleta afasace Xaki wahalar da shiri ane mowana amma har yanxu xuciyar cike take da soyayyar brister toh kisani mama da daddy tun daren jiya nafadamusu dik abundayake faruwa kuma adaren nadaukosu nakawo gidanku wajen momma sukayi magana ta amince da duk abindana fada kuma suduka nakirawosu yanxu nacewa mama subiya sudauko momma suxo tare nan atabbatar dakinxama mallakin Siyam yau basai gobe ba Harara tadoka masa tana share kwallar dakexubo mata Dama yaudara ta kayi yay Adeel dama basona kakeyiba sallamar su mama yadakatar da ita tana rugawa ta rumgume momma tana kuka Wayyo Allah momma kinga yadda rashin gata xaisa amin yankan kauna rashin gata xaisa amaidani tamkar wata kwallo, momma kitashi mubar wurin nan Daka mata tsawa tayi sannan ta nutsu Dr ne yashigo tare da wasu likitocin biyu suna gungura abundaukar maijinya daddy da Abba ne suka dorasa likitocin suka gungurasa suka fita mummy xata bisu Abba yadakatar da ita Kibarsu suje dashi nasan dukkan wata kulawa da inmuna tare dashi xasu bashi dr Abdur rahman xaikulada hakan Dagakai tayi alamuntagamsu amma idanunta basu fasa xubar kuka ba Alhaji Siyam nacikin mawuyacin hali ina tsoron inrasa yarona banida wani madadi bayan jawwa yaya rayuwata xata koma nasaba da dahna baxan iya jure ma rasashi ba Abba ya rumgume ta yana lallashi dakyar akasamu kanta sannan suka gaisa da mama da daddy da momma sannan taga momma kamar yadda Adeel yafada musu haka akasake tattaunawa mama da daddy suka amince da SADAUKAR WA da Adeel yayiwa Siyam na mowana momma ma ta amince jinhaka yasa mowana fashewa dawani kukan xuciya tana kankame momma Adeel ne yamatsa akan saidai adaura masu aure yanxu anan saidai kawai Siyam yafarka yaganta matsayin matarsa Abba yace toh nan yaje cikin gida yakirawo kawu babba da kawu salim da aminu sukaxo daddy shine yabada sadaki kawu babba ne waliyyin Siyam momma kuma mlm liman takira yaxo shine ya amsa waliyyin mowana. Anan aka daura auren Siyam Abdullateef da tasleem tujjani kabeer akan sadaki naira dubu dari da hamsin. Sabd daddy yace sune ajikinsa yanxu momma kin karbatayi tace sunyi yawa dakyar dai mama ta amsa tasa mata ajaka Mowana kuwa kuka harda turje turje daddy ne yamayar da momma gida ita da mowana sannan suka tafi hospital din da aka kwantar da Siyam shida mama da Adeel yanatasa wa dan nasa albarka sbd yadda yake ta kokarin ceton ran abokin nasa da dukkan damarsa yaji dadi dayau jininsa yaxama mai taimakon musulmi dan uwansa. Hawayen dake makale agurbin idon Adeel suka tsiyayo Daddy kutayanida addu ah Allah yakarbi SADAUKAR WA ta sannan yasamun kwarin gwiwa akanta karnaxama mairauni Mama tashafa kansa itama tana kara kwarara masagiwwa. Har akagama kamu amma amarya hubba bataga mowana ba kuma gashi har mangaruba yadoso takira wayarta takira amma akashe hankalin ta yatashi tafada daki inda tasamu kawarsu wacce suke ji da ita itada mowana takama hannunta Hamsa'u wai lfy kuwa Mowana tundaxu banganta ba agidan nan kinga har angama kamu gashi kinsan kuma gobe fati itaxataje wajen kboy ta amso mana getpas kardare yayi sannan taxo tace baxata iyaxuwa ba Hamsa'u takalleta Nima tundaxu nake kiran wayarta bata shiga ba tundanaxo naduba naga bangantaba kuma tunfa wajen karfe biyu mukayi waya da ita tace tashirya futowa kawai xatayi tataho Toh akwai matsala kuwa yanxu dan Allah kitaimaka mun kije gidan nasu kigano mana wlh hankalina baxai kwantaba harsai natabbatar da halin da 'yar uwata ke ciki Tohm shikenan bari naje. Tafuce tana kara gyara daurinta sbd batasan inda rabo yakeba watakil tagamu dawani Alhajin Tana futa titi tatari napep Hamsin ne xuwa hamsin dawowa cikin kankanin lokaci ta isa gidan Momma tafara tarar wa acikin gidan axaune tana laximi Suka gaisa tace momma ina Mowana fa Tanunamata dakinta tana cewa Tanaciki Shigewa Hamsa'u tayi tana kwala mata kira Ganin yadda tasametane yasa takarasa dasauri tana riketa Yaya dai mowana lfy kuwa naganki ahaka Kinyar da dankwali kinbarbaja gashin kanki gafuskarki fusassun hawaye why nakinsha kuka Babu lfy Hamsa'u kunji ni shuru ko Eh hubba duk hankalin ta yatashi kinga itace ma taturo ni naxo nadubaki lfy kuwa Ta lumshe ido kamar maijin bacci Ba lfy Hamsa'u kifadawa hubba yau aka daura mun aure da Siyam sauranxancan takira ni awaya gobe domin naji su momma namaganar nanda kwana uku xankoma gidan su siyam din Farinciki ne yabayyana afuskar Hamsa'u Woow Mowana kin auri namijin duniya kice saurayin da kowacce mace agarin nan harda ketare keta burin mallaka, burinki Allah yacika miki dole kisha kuka har ki koshi domin kuwa wannan wani burinkine namusamman auren Siyam MEKYAU Kinga da Allah kamakanki Hamsa'u dakika sani amma bayanxu ba kokadan bana kaunarsa yanxu natsanesa bakuma xaitaba samuna matarsa ba wlh Mikewa Hamsa'u tayi tana kallon mowana kamar amafarki take jin Mowana na ikirarin ta tsani Siyam lallai akwai wata akasa Allah yahuci xuciyarki nabarki lfy saimun xo kaiki Dagudu Mowana tabiyota aikwa dakyar takai kofa tana haki Momma taharari Mowana tana jallata Kewai yaushe kika lalacehaka Mowana yaushe kikaxama marajin magana au sbd wannan abun duk kikabi kikatada hankalin ki da gashin kanki sbd kin haukace toh kindade kina hauka kuma wlh don aure kan anriga da an daura idan kinje ki yankasa koki soyasa muji kamshin. suya tunda ke kinxama abundakika xama idanma banda muna funci dagulma data yi miki katutu yaron dakedakanki kika mutu asoyayyarsa tunfarko shine dan yanxu shima. yadawo hayyacinsa yanasonki. xaitaimaka miki xaki tsiri firirita da. iyayi toh wlh ahir dinki karki sake naji. akasin abunda kikataso kikasamu. inama mahaifinki Tafara dara kafa akasa tana kuka Wlh bataimakona xaiba nice xantaimakesa shi dayake akan gabar mutuwa akowanne lokaci kuma aidane naso shi ni yanxu ko kallonsa bana kauna arayuwata Dan uwanki toh ki kashesa kuma airai ahannun Allah yake fice kiban gu kona kakkaryaki yanxu agunnan. BAYAN KWANA BIYU. Siyam xaune hannunsa ansa masa karin ruwa dasauki yanxu jikin nasa domin kuwa yawarke harmagana yakeyi duk dabasosai ba sbd yawan surutu nasa jikin nasa yakara rikicewa yanxunma Adeel ne agefen damansa yana tabasa labarin abokanansu nakasuwa wadanda sukaxo dubasa lokacin dabaya hayyacinsa Yasakarwa Adeel murmushi yana lumshe ido kafun yace Abundakayimun naji agurin mummy jiyatake fadamun amma Adeel anya kayiwa kanka adalci kuwa bakaganin kai xaka cutu kanka nema min farinciki kaikuma ka kuntata atasanadin SADAUKAR WA abokina tabbas natabbatar da amintar mu lallai ta gaskiyace. Kuma bansan harnakai haka awajenka ba duk da dama ko agurina kaima kafi haka shiyasa mummy nafadamun nace aa kaima kanasonta kuma kafini dacewa da ita sbd kaine kanunamata kulawa da tararraya alokacin datake bukata kaine katareta alokacin dana koreta daga gareni kaxame mata gata alokacin data ke neman taimako duk kana nufin wannan xaitafi abanxa k.......... Ya isa Adeel yasa masa hannu abaki Nidakai duk dayane dan nayi wa mowana wani abu taxama taka aiba wanidamuwa bane tunda ni da duk wani avu dayadaya danganceka ne kaga xuwa yanxu mowana taharamta agareni sbd jiya saidana tabvatar taxama mallakin ka sannan hankalina yakwanta kariketa amana Mowana kanwatace domin tamkar Aslamiyya take awajena kodacan najingina soyayyar mu ahaka shiyasa batai karfin daxata iya illataniba so kagane brister kafini bukatar Mowana akusa dakai nina tabbatar dahakan, Shikenan Adeel amma da naso dawomaka da mowana gareka amma tunda nafahimceka sosai shikenan Allah yabamu xaman lfy Amin hakanake son naji ango kana samun kwarin gwiwa Yayi murmushi Kwarin gwiwa aikagama bani Adeel banida tamkarka bayan mummy da Abba da my jawwa Allah yabaka mace tagari Adeel Allah yabaka dauwamammen farinciki arayuwarka Amin nagode dawannan addu ah mai kyau haka fatana Allah yabada 'yan tagwaye. kwanan Siyam goma dasamun lfy yayinda mummy suka fara shirye shiryen shagalin bikin wanda xaikasance jibi anhada lefe dan ubansu wanda tsayawa lissafa maku abunda akaxuba aciki wani sabon lalene kunsandai waye Siyam da iyayensa kudi tamkar banxa suke agidansu. Akwatinana hadaddu guda 12,kowacce da abundayake ciki kuma cike cike suke dakayan kyale kyalen duniya, yau aka kai mowana gidan mummy sbd acan xa ashiryata hargidan mijin ta Dakyar tasaki momma tanakuka maitada hankali momma ma kukan take tana samata albarka danasiha mai shiga jiki innar hubba dawasu mata biyar kawayen momma sune suka shiryata cikin kaya masu kyau karfe hudu motocin biyu suka karaso wadanda xa adaukesu akaisu. Tasaki kuka tana kankame momma Momma tafashe dakuka tana xare jikinta daga nata tafada daki haka innar hubba takama hannunta suka fita tana kuka Basudade ba suka sauka matan duka bubbude ido sukeyi ganindaular dasuka shigo lallai yarinya tayi goshi fadar wata acikin matan innar hubba tace Gaskiya ubangiji Allah yasanya alkhairi bude musu motar akayi suka fiffito tsayawa sukayi sbd basu san part din daxasu nufa da itaba wata kyakkyawar mata suka gani tafuto daga wani waje tana murmushi taxo taimusu sannu daxuwa suka gaisa taimusu jagora xuwa part din hajia bera'u Xaune take cikin wani hadadden les gwaldin yasha dutsina gefenta matan su kawune sakina mariya suwaiba sunata faman gyara hadaddun abincinan da aka jere akayataccen falon domin tarar masu kawo amarya sai hira suke suna dariya da mummy kai bakace anta samun wata rigima atsakanisuba sbd yanxu suka dawo

Chapter 7 of 11