Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kansa horon yaki har ta iso daf dashi
sannan ya dubeta yace,"Yake 'yata,ina dalilin fitowarki
a wannan lokaci, kuma a cikin shigar yaki? "
Koda jin wannan tambaya sai lamirat tayi murmushi
tace,"Ya kai Abbana kayi sani cewa Yau kusan
shekaru uku kenan rabon da mu wasa jini ni da
kai,don haka ina son mu dan fafata domin na gani ko
na samu cigaba a koyon yaki na fiye da abinda ka
koya mini a baya tunda a kullum a cikin neman Karin
ilimi nake."
Koda jin haka sai sarki gurzalu yayi murmushi yace,
"Wannan ba laifi".
Nan take ya gyara tsayuwarsa, ita ma sai ta tsaya a
nesa kadan dashi ta gyara tsayuwarta suka fuskanci
juna,Daga can kuma sai suka fara zagaya juna,
Kamar hadin baki sai suka ka da baya a lokaci guda
sukayi taku uku kacal, sannan suka rugo da gudu
izuwa kan juna suka kacame da masifaffen yaki, ya
zamana cewa suna kaiwa juna SARA DA SUKA cikin
azababben zafin nama,juriya da bajinta, suna neman
hallaka juna da dukkan karfinsu tamkar sun kasance
tsofaffin abokan gaba,
Tunda suka fara wannan gumurzu sarki gurzalu ya
cika da tsananin mamaki, domin a saninsa Sam
gimbiya lamirat bata da zafin nama irin na yanzu,
kuma kwarewarta a yaki ba ta kai hakan ba.
Abu dai kamar a mafarki sai gashi karfinsu ma yazo
daya,an rasa wanda zai iya cutar da dayan.
Sai da suka shafe rabin sa'a suna fafatawa a cikin
wannan hali, Al'amarin da ya fusata sarki gurzalu
kenan, ya sauya salon yakin ya hada da kai mata bugu
da naushi hannu da kafa.
Kawai sai yaga ita ma ta koma irin salon da ya koma
kuma ya kasa cutar da ita,da kyar da sidin goshi ya
shammaceta ya daka wawan tsalle sama ya doketa da
kafa a fuska,
Tana faduwa kasa a lokacin da lebenta ya tsage, jini
ya dan zubo, sai ita ma ta kwarfi kafafunsa yai sama
ya rikito kasa,amma sai ya duro bisa kan tafin
hannunsa guda cikin bajinta ya doki kasa da tafin
hannun nasa yai sama ya dawo kasa bisa kafafunsa.
A dai-dai wannan lokaci ne suka ji ana yi musu tafi,
suna waigowa baya suka ga Ashe sarki taryan ne tare
da 'yarsa Gimbiya Shumaira suka durfafo inda suke,
cikin hanzari lamirat ta mike tsaye tana mai goge dan
jinin da ke kan lebenta da tafin hannunta.
Sarki taryan ya dubi Gimbiya lamirat yace,"Hakika
wannan 'ya ta gaji ubanta a jarumtaka, lallai yanzu ne
nasan cewa kin cancanci ki shiga.,...."
Kafin ya karasa fadin abinda ke bakinsa sai Gimbiya
lamirat ta tari numfashinsa don kada ya tona ma ta
asiri tace,"Ai barewa ba ta gudu danta yayi rarrafe.
Ya shugabana me yasa kazo ka katse mana wannan
horon yaki da muke yi?"
Koda jin wannan tambaya sai sarki taryan yayi ajiyar
zuciya yace, "Ai wani gagarumin abin mamaki ne ya
faru yanzu shine nace lallai sai nazo na sanar da Ku,
yanzun nan na kaiwa jarumi Imhal ziyara a dakin da
aka tsareshi, ina zuwa sai na iske likitana yana cire
zaren da aka dinke wannan rauni na kirjin sa,ina mai
tabbatar muku da cewa raunin ya hade ya warke
sumul tamkar ma bai taba yin sa ba".
Koda jin wannan labari sai sarki gurzalu da Gimbiya
LAMIRAT suka kallo junansu cikin fargaba da
tsananin mamaki.
Sarki taryan yaci gaba da cewa," A halin yanzu dai
jarumi Imhal yace a shirye yake ya cigaba da wannan
gasa gobe, don haka na sanar da duk Alkalan gasar
tuni ma an cigaba da shirye-shirye."
Koda sarki taryan yazo nan a zancen sa sai sarki
gurzalu yayi ajiyar dogon numfashi yace,"Wace irin
magana kake yi haka kamar Almara? Ya za ayi ace
mutum ya samu irin wannan babban rauni, kuma ace
ya warke a cikin kwanaki uku kacal? "
Sarki taryan yace ai kada kayi mamaki da hakan,
domin akwai mutane masu baiwar saurin warkewa
daga ciwo, idan baka manta ba ai har a cikin RIJIYA
GABA DUBU ta kurkukun DARUL MAUT aka sa jarumi
Imhal ana yi masa azaba har tsawon kwanaki, amma
aka fito dashi a cikin kwanaki kadan duk raunin dake
jikinsa suka warke, kuma ya samu lafiyar jikinsa.
Koda jin wannan batu sai sarki gurzalu da gimbiya
lamirat suka kalli juna cikin alamun damuwa da
takaici, sannan lamirat ta dubi sarki taryan
tace,"Wanene wannan jarumin da zai fafata da Imhal
gobe? "
Sarki taryan ya jinjina kai yace "Wani bakin jarumi ne
shima daga birnin Askandariyya,nima ban taba
ganinsa ba,sai gobe a filin gasar za muga ko wane
ne".
Koda gama fadin haka sai sarki taryan ya kama
hannun gimbiya Shumaira suka juya suka nufi inda
suka fito.
Suna cikin tafiya ne Gimbiya Shumaira ta juyo ta kalli
sarki gurzalu da Gimbiya lamirat ta ga ko kadan babu
annuri akan fuskokinsu, tamkar an aiko musu da
sakon mutuwa, kawai sai tayi musu wani irin guntun
murmushi wanda suka kasa fahimtar ko na mene ne
tsakanin na mugunta ko na alhini.
Shi kuwa sarki taryan sai ya dubi Shumaira yace,
Hakika yanzu na fara yarda da zargin da nake yi akan
sarki gurzalu, domin ban ga dalilin da yasa suka
tsananta kiyayya ba akan jarumi Imhal,bisa binciken
da nayi ma tun farkon haduwar Imhal da sarki
gurzalu laifin da yayi masa bai kamata ayi masa
hukuncin dauri a kurkukun Darul Maut ba balle har a
sanyashi a cikin RIJIYA GABA DUBU a azabtar dashi
na tsawon kwanaki ba,tabbas an zalunceshi, ni kuwa
a rayuwata bana son zaluntar mutumin da yake kasa
dani,musamman wanda ya kasance talaka na".
Koda Gimbiya Shumaira taji wannan batu daga bakin
mahaifinta sai farin ciki ya lullube ta domin ta
fuskanci cewa hakanta zai cimma ruwa a kokarin da
take yi na raba alakar da ke tsananin sa da sarki
gurzalu, tunda gashi shi da kansa ma ya fara gano
irin zaluncin sarki gurzalu.
A daren wannan rana aka cigaba da shela a cikin
birane da kauyukan kasar misra ana sanar da cewa,
"Lallai gobe da safe za a cigaba da gasar kambun
JARUMTA.
Ai kuwa tun a cikin daren 'Yan kallo suka dinga
tururuwa a cikin filin gasar don kada su rasa inda za
su zauna suyi kallo.
yayin da gari ya waye kuwa sai ya zamana cewa duk
inda mutum ya duba a filin gasar babu masakar
tsinke, ko ina kawunan bil'adama ne rututu.
Kai! har kan katangar filin gasar mutane ne a
zazzaune maza da mata,a tsakiyar filin ne kawai aka
bar hanyar da za a wuce don shigowar sarakai gami
da jaruman gasa da alkalai.
Sai da aka shafe kusan rabin sa'a ana jira sannan aka
ji tambura na tashi gami da bushin Algaita alamar
cewa sarakai za su shigo filin gasa,Nan fa filin gasar
ya rude da shewar jama'a suka kamu da tsananin
murna don sanin cewa yanzun nan za a fara gasar.
Ai kuwa sai ga sarki taryan, sarki gurzalu, da
'ya'yayensu mata tare da sauran manyan sarakuna na
nahiyar sun shigo cikin filin gasar dakaru na biye da
su a gaba da baya, gefe da gefe, ana cigaba da buga
tambura, har sai da suka isa inda mazauninsu yake
suka zauna.
Zaman su ke da wuya sai mai gabatar da gasar ya
mike ya fara jawabi yana mai yiwa manyan baki barka
da zuwa, sannan ya sanar da cewar jarumin da ya
fara wannan gasa,wato jarumi Imhal ya warke daga
raunin da ya samu a cikin kwanaki uku kacal,kuma da
shi za ayi wannan gasa ta Yau kamar yadda dokar
gasar ta tanadar cewa,duk jarumin da ya samu
nasarar lashe gasar ba zai yi fashin wasa ba face
baya numfashi a doron kasa,kuma komai yawan
raunikan da ke jikinsa indai zai iya warkewa sai an
jira shi ya warke har izuwa tsawon mako biyu, idan ya
wuce mako biyu ne bai warke ba an cire shi daga
cikin jaruman gasar,
Lokacin da jama'a suka ji cewar jarumi Imhal ya
warke daga ciwon sa a cikin kwanaki uku kacal sai
kowa ya kamu da tsananin mamaki aka shiga yi masa
jinjina da kirari tun kafin ma ya fito filin gasar,nan fa
filin ya rude da shewa gami da hayaniyar mutane har
sai da aka buga gangar fara gasa sannan aka yi tsit!
tamkar mutuwa ta fado filin gasar.
A sannan ne mai gabatarwa ya kirawo sunan bakon
jarumin da yazo daga birnin Askandariyya wai shi
ZAMBARU IBINI KULSAS.
Kawai sai aka ga wani bajimin katon mutum mai
tsawon kamu ashirin da bakwai ya fito daga cikin
dakin jaruman gasa wanda ya kasance mai kauri da
fadin kirji, inda za a yanke kafarsa guda a dorawa
mutum dakon ta a kansa,ji zai yi kamar an Dora masa
cinyar katuwar giwa.
Koda jama'a suka yi arba da wannan narkeken kato
mai kirar mutanen farko, sai suka firgice suka
dimauce ainun, domin gani suka yi kamar zai baje
filin gasar gaba daya ya mutsittsike kowa da komai da
ke filin.
Nan fa jama'a suka kama mikewa tsaye domin su
ruga da gudu izuwa wajen filin gasar,sai da dakaru
suka hau daka musu tsawa sannan kowa ya nutsu ya
koma mazauninsa.
Duk sanda Zambaru yayi tafiya taku daya sai a ji
birnin gaba daya yayi girgiza kamar kasa za ta tsage
komai da ke samanta ya rufta cikin ta, Kai hatta sarki
Gurzalu da ya kasance jarumin da ke rike da
KAMBUN JARUMTAKA sai da ya firgita bisa ganin
Zambaru, Ya Sha jinin jikin sa,ya ayyana cewar lallai
babu tabbacin shi kansa zai iya hallaka wannan
basamuden kato Koda kuwa da karfin sihirin tsafi ne.
Bayan Zambaru ya iso tsakiyar filin gasar sai ya tsaya
ya daga kansa sama yayi wata irin kururuwa mai
tsananin kara da firgitarwa wacce ta cika cikin birnin
misra da duk kauyukan da ke kewayensa da amsa
kuwwa, kuma ta firgita mutane da dabbobi har ma da
aljanun dake kawayen wajen.
Al'amarin da ya janyo hargitsewar birnin kenan,
mutane suka dinga guje-guje da iface-iface, matan
dake dauke da tsohon juna biyu kuwa ba shiri suka
kama yin nakuda ta ba zato suka dinga haife abinda
ke cikin duba tare da lokacin haihuwar yayi ba,Har sai
da Zambaru ya tsuke bakinsa sannan komai ya lafa,
mutane suka dawo cikin hayyacinsu.
A wannan lokaci ne mai gabatarwa ya kirawo jarumi
Imhal, kawai sai aka ga jarumi Imhal ya fito da gudu
daga cikin dakin jaruman gasa rike da takobi da
garkuwa cikin shigar yaki ba tare da shakkar komai
ba.
Koda ganinsa sai filin gasar ya rude da shewa aka
kama yi masa jinjina da kirari, mawaka na yi masa
lakabi da SABON JARUMI MAI ABIN AL'AJABI,
Koda Zambaru ya hango jarumi Imhal ya nufo cikin
filin gasar a guje rike da wata takobi sai ya zura
hannun sa izuwa bayan sa ya fiddo wata lafceciyar
takobi wadda inda za a ajiye ta a kasa karti ashirin
majiya karfi basa su iya dagata sama ba.
Maimakon jarumi Imhal ya tsaya a sake buga
tambarin fara gumurzu, kawai sai ya cigaba da gudu
ya tunkaro inda jarumi Zambaru yake tsaye.
Shi kuwa Zambaru sai ya fara wulwula takobinsa a
sama yana jiran isowar Imhal.
Yayin da ya rage saura bai fi taku shida ba kacal
Imhal ya iso inda Zambaru yake sai ya daka wawan
tsalle sama kamar an cilloshi daga baka sai gashi ya
iso dai-dai wuyan Zambaru.
Ai kuwa sai ya dankara masa Sara a wuya, take
takobin ta makale a jikin wuyan Zambaru tamkar a
jikin bishiya mai kauri ta nutse.
Imhal ya finciko takobinsa da hannayensa biyu da
dukkan karfinsa amma sai ya kasa Ciro takobin.
Kafin ya sake yin wani yunkuri tuni Zambaru ya mako
shi da hannun sa na hagu wanda baya rike da
makami, take Imhal ya fado kasa ba shiri ya duro
akan kafarsa ta hagu,ai kuwa sai kafar tasa ta karye
ya kurma uban ihu sakamakon tsananin zafi da zogin
da ya ji ya sulale kasa a matukar galabaice ya kasa
mikewa tsaye.
Koda ganin abinda ya faru sai Zambaru ya bushe da
mahaukaciyar dariya ta mugunta, sannan yasa
hannun sa na hagun ya zare takobin Imhal wacce ta
makale a wuyan sa, jini yayi tsartuwa daga jikin
wuyan nasa,amma ko a jikinsa.
Kawai sai yayi jifa da takobin ya nufi jarumi Imhal
wanda ke zaune a kasa, yana mai daga lafceciyar
takobinsa.
Gaba daya 'Yan kallon da ke cikin filin gasar sai suka
dafe kai suka fara ihu da kururuwa domin sun San
cewa lallai Imhal ya zama gawa tasa ta kare.
Su kuwa attajiran da suka zabi Zambaru a matsayin
jarumin gasar su suka sa kudin su na caca a kansa
sai suka fara yin tsalle da murna suna kida da rawa
don sun San cewar kakarsu ta yanke saka, sun gama
zamowa manyan attajirai.
Wadan da suka zabi jarumi Imhal kuwa a matsayin
jarumin gasar su sai suka fara kuka suka kamu da
tsananin bakin ciki sabo da sun San cewa lallai
karayar arziki ta zo musu!!!
YAYA KARSHEN WANNAN GASA ZA TA KASANCE
TSAKANIN JARUMI ZAMBARU DA JARUMI IMHAL? TA
YAYA JARUMI IMHAL ZAI TILASTAWA GIMBIYA
LAMIRAT TA KAMU DA SONSA? SHIN IMHAL ZAI
RASA RAYUWARSA NE A CIKIN WANNAN GASA TA
KAMBUN JARUMTA KO KUWA ZAI LASHE GASAR NE
HAR TA CIKA BURIKAN DA KE GABANSA?INA
LABARIN TSOHO IMZANU KUMA A CIKIN WANE HALI
YAKE YANZU A CAN BIRNIN KISRA?
Mu hadu a RIJIYA GABA DUBU 4 don jin cigaban
wannan kasaitaccen labarin.
.
Toh jama'a gashi mun kawo gargada na wannan littafi
Amma kuma an samu tsaiko a dalilin bani da littafi na
Hudu
Don haka nake baku hakuri
.
Izan kuwa acikin members ko Admins an samu wanda
yake da shi sai ya taimaka ya kawo maku
.Shuraih
Aka
99%
.
.

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


4 Comments On RIJIYA GABA DUBU
avatar
mlm

2 years ago

Reply

Next please

avatar
khadija-1-4

2 years ago

Reply

??????

avatar
muhammad-musa

1 year ago

Reply

Good book

avatar
ismail-9-8

1 year ago

Reply

Please Login or Register in order to submit comment