Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 10
gidan mu haka kawai ban san hawa ba ban san sauka ba wadanda suka kawo kayan suka zo suka ce a yi hakuri a basu bisa wasu dalilai da suka ce wai su ne sukayi dalilin in sa auren nashi a wannan lokacin. 123 Yakumbo Halima dai ta ce min wai yayi mata bayani da cewar ya fasa auren ne a dalilin akwai wani dodo dake biye da ni mai tsoratar da mutane matukar kuma ba a tsaya an rabani da wannan dodon ba to aure na zai yi wuya. Bayanin 1ashi ya yi tasiri mai karfi a zuciyar Yakumbo don salati ta rinka yi tana fadin, wai dama tuni ta dade tana tunanin watakila aljani ne da ni wanda ya hanan11 yin aure. Ni kam tattara maganar nayi na ajiye a gefe ban yarda ba ban kuma karyata ba don ban san komai a kan irin wedannan al'arauran ba, abu guda daya dana sani na kuma yarda na tsaya a kan shine gaba daya mu mutane da kuma aljanu dukkanmu bayi ne na Ubangiji babu mai ikon cutar da wani a tsakani sai da abin da Ubangiji ya yarda ya kuma kaddara fil azal wannan din zai cutu da shi, wannan shi ne bayanin da kullum malamin mu na tauhidi yake yi mana da sai kuma na yarda sai na samu natsuwa da kwanciyar hankalin dana fuskanci al'amurana na dai san kawai na koyi yin addu'a. Sai dai kuma tawakkalin da sanin da nayi cewar babu mai yi ko hanawa sai Ubangiji bai hana zuciyata kuntata ba a dalilin aure nake so auren kawai nake so, SO nake in ganni nima a zaune a nawa dakin ina zaune ina aurena ga Asabe tunda ta yi aurenta tana dakinta ban sake ganinta ba, kullum kuma sai uwarta ta yada 124 magana a tsakar gida ta ce, yin aure ai rufin asiri ne Asabe asirinta ya rufu tana can dakinta cikin ntin asiri, ubangiji ya sanwaka ace yar mutum tayi ta galantoyi a gaban shi, yana kallonta kowa ya zo ya yi kamar zai aureta in ya taya ta sallama yaga araha sai kawai ya yi dani ya tafi. Tin, ta ja tsaki fa ci gaba da harkokinta. Cikin zuciyata dai na kan yi mamakin al'amarinta saboda a farkon abinda ya faru da Asabe na dauka zata fita banyar irin wadannan abubuwan sai ya zamo ko a jikinta ba ta ma tuna nata sai dai na wani dama bai karasa natan lalacewa ba. Ana cikin haka watan azumin ramadan ya iso sayaiya sosai Mansur ya yi min, ina zaune a dakina ina. buda baki mun kai azumi na biyu ina jin baba Lantana tana cewa babana wai ita din ai rabon wahala ne ya se ta aurenshi in banda haka ai shima ya san irin zaurawan da tayi, cikin zuciyata na ce ob oh kowa da irin yanda babu take zuwa mishi, watni ta kara mishi natsuwa wani kuma ta yis anadin wargajcwarshi, wata mai daraja irin' na azumi bai sa ta dan rusunawa al' amiaranta ba. Isiyaku ya yi sallama a kofar dakima ya shigo, anti ina wuni? An sha ruwa lafiya? Na amsa gaisuwar tashi ina mai kallonshi. Ya yi fes da shi ya yi kyau kamar in tambayeshi ka samu wani abin yi ne Isiyaku, sai na yi maza na fasa a dalilin ba wani shiri muke yi 125 ba a yanzu saboda gaba daya al'amuranshi na Mubarak ne. Ya karkata ya zaro envelop daga aljihun shi ya ajiye a gefena, wai gashi in kawo miki. Da sauri na ce mishi, Isiyaku ashe ban ce maka kar ka sake karbo wani abu daga wurin mutumin nan ka kawo min ba? To dauki maza-naza ka tafi mishi da shi ka kuma gaya nishi inji ni na ce ya fita hanyata ya daina shiga harkokina in bai sani ba ko bai gane ba to bari ni da kaina in gaya mishi na tsaneshi, na tsani al'amuranshi, na kuma tsani duk wani abinda ya shafe shi, in ya kuskura ya sake aikoka da wani abu wurina to zan karbi abin in aikawa matarshi don tasan yanda zatayi da shi, ya daina kula al'amarin. Wani irin lalataccen kallo Isiyaku ya yi min da ya yi dalilin da nan take na warware hannu na sheka mishi mari mai kyau a kumatunshi har sau biyu, ina wasa da kai ne da zaka yi min irin wannan kallon? Bai cc min komai ba sa hannu ya yi ya dauki envelop in ya sa kai ya fita ya bar gidan, ya barni ina huci da tunanin haka zan rinka yi mishi duk lokacin da ya kawo min wani sako tunda nace msihi ya daina yaki. Washegari mun taso daga wurin tafsir nufina in taff gidan yaya Dija don in yi mata barka da shiga tamadan mai albarka sai kawai naga Mubarak ya yi fakin din motarshi kusa da hanyar da muke wucewa 126 bai ii tsoron cincirindon matan da suke wucewa su na hangenshi ba ko don kar su gayawa matarshi. Yana ganina zan wuce ya yi maza ya fito daga cikin motar tashi ya tsareni, nmagana yake yi cikin natsuwa ta yanda na nesa ba za1 gane bakar magana yake yi ba. Malamin naki ne ya koya miki rashin kunya da rashin mutuncin da kike yiwa mutane ko? Na daggo ido na kalleshi saboda ambaton malamina da ya yi. Eh ai kafin kullewarku ke da shi rashin kunyarhi ba ta kai haka ba, ki mari Isiyaku, gansamemen saurayi kamar Isiyaku ki mareshi dame kika girmeshi? Kina nuiin in banda shf din yaro ne mai mutunci za a yi hakan'? Kina mace ki mari namiji kina nufin in ina da iko da ke ba zan yi miki hukunci mai tsanani na ladabtarwa ba? Sakarya kawai sokuwa, shasha:ha wacce rashin mafadi ya hanata sanin abinda ya dace da ita. Wani lalataccen kallo ya yi min gami da jan mummunan tsaki kafin ya wuce ya tafi ya barni, ance miki matata irinki ce. Haushi da takaicin kaina suka hadu suka kamani kan yanda akayi ya gama gaya nun bakaken magangnaunshi ya wuce ya tafi ba, tare da na iya ce mishi koami ba, babu kuma abinda yafi komai kona min rai irin cewar da ya yi wai matarshi ba irina ba ce, to wacce iri ce? Me yake nufi da wannan maganar ta 127 shi? Babu irin alkawarin da ban yiwa kaina ba a kan ba zan sake barinshi ya gayamin magana in kyaleshi ba amma gashi na kasa gaya mishi komai. Baba Lantana a wanann lokacin tsula tsiyarta take yi irin yanda ta ga dama, da yake Asabe mai imani ce da tayi cikinta sai ta reni abinta ta haif abinta ba ta je ta zubar da shi ba balle ta je tana dauka wani zunubin na kisan kai, gashi kuma a saradin hakas ai ta yi aurenta tanan an goye da danta tukarballa ta bar wasu a titi suna ta tanbele basu ga tsuntsu basu ga tarko. Da bain nata ya tsaya a kaina ni kadai da sauki yanzu yanzun nan ne zata sa shi a gaba ta sulleshi sai dai in ba zan leka kofar gida ba ko ka ji tana cewa, to ni in banda na lissafa naga duk tsiyarka kai da ya'yanka zan iya cinye wannan daki da nake ciki tunda dai su din mata ne ai da tuni na dade da rabuwa da kai in yi tafiyata yaushe zan iya zaman jinya, to ba zan tafi ba ne in bar kasona a ce rashin bhakuri doon haka nake zaune daram ina jira sai naga kwal uwar daka. Wadannan kalaman da na ji baba Lantanan tana furtawa wadanda na tabatar ba ta san na ji ta ba su ne suka yi dalilin da na yi sammaon zuwa gidan yaya Dija na bata labari. Shiru tayi tana kallona cikin wani irin yanayi, Jimawa can sai naji ta ce, i tsorona ma kar ta karasa 128 mana shi ba mu sani ba tunda take mapganar gadon dan wannan gidan wato ita idonta yana kanshi ta sake nisawa kafm ta ce, nifa da baba zai yarda ma de wani auren kawai ya kara. Da sauri na zaro ido ina kallonte cikin razana, aure kuma? Shi baba ya ce miki zai fya yin mata biyu ne? Hankalinta a kwance ta ce min to ba shi kenan ba in ba zai iya biyun mai zama ta zauna mai tafiya taa tafi, amma wannan fitina har ina? Daka akwai wata yarinyar bazawara nan kusa da ma takaba ta gama tana kuma da' ya'yanta biyu k inga in Akayi sa'a ma sai ya kara haihuwa ya ma huta da sharrin da take kulla mishi na baya iya tsinans mata komai, baba ai ba tsoho bane in ma bakan ne bakin cikin ta ne ya maidashi hakan, na dai ja bakina nayi shiru ina jinta tana maganganunta bance mata komai ba. Rannan ranar wata juma'a da yamna bayan saukowa daga sallar Juma'a naji babena ya karbi wasu baki a zaurenshi wadanda na tabbatar iyayen Mubarak ne wato Alhaji Muhammadu da amininshi ban san takamaiman abinda ya kawo sun ba na dai gane su din ne kawai ta dalilin ambaton sunansu da na ji baban nawa ya yi. Nayi maza na mike na shigs gida na basu wuri, can cikin zcuiyata dai ina taunsnin wanene kume Alhaji Muhammadu? A sanina a unguwarmu baban Mubarak ake kira haka to amma shi me zai kawoshi 129 gidanau? Yana dai zuwa duba babana daga baya bayan nan tare da Mubarak to amma wannan ai zai iya Z8ma makwabtaka ne ko kuma kwadayin alherin da ake samu wurin gaida mara lafiya. Ina ganin sanda babana ya shigo gida rike da tabarmarshi a hannu bai ma tarota inje in hade ba bai ce min komai ba nima kuma ban tambayeshi ba don dama can babu irin wannan mu' annaiar a tsakaninmu don haka sai kawai na ci gaba da harkokina. Da daddare ina zaune dakina takarduna na makaranta nake dubawa lokacin da na ji sallama a cikin zauren gidanmu gabana ya yanke ya fadi saboda jin da nayi tamkar muryar Mubarak ce da sauri na mike na fito da ita. Uhh lalle al'amarin babba ne har cicin zare kuma yanzu kake shigo mana? Ta yi kwafa ta ce ko baka yi haka ba ai an kuma hade. Tsayuwar da baba Lantana ta yi a wurin wai sai ta ji abinda ya kawoslhi ko zai fadi ya hanani tafiya in barshi don ba zan 6ata mishi rai a gabanta ba, wucewa na yi nace mishi muje daga waje mana, don haka muka fito. Tun kafin in tambayeshi abinda ya kawo shi gidanmu ta tsareni dai danuwanshi wai ni me baba yake nufi da ni ne? Tambayar tashi ta sanyani yi mishi tambayar wane baba? Da saurinshi cikin wani irin yanayi ya ce min, babanki mana. 130 Gabana ya yi mummunan faduwa jin yanda ya ambaci baban nawa, cikin zuciyata na ce, lalle mutumin nan yau yana jin rashin mutunci amma babu laifi, na kawar da tunanin nawa na naida hankalina Wajen sauraron abinda Zai gaya min a kAn baban nawa wanda na tabbatar ba mai dadi bane. Na rasa me nayi nish na rasa wane irin laifi na yi mishi wanda ya wuce gabai yafewa, tun aurena bai wuce wata uku ba na turo aminin babans ya zo wurinshi.kan maganar ni da ke bai saurari maganar ba na koma na sake rokon babane ya zo da kanshi ya yi mishi magana don ya fi ganin abin da muhimmanci ya zo ya sameshi bai ji kunyar idonshi ba ya ce mishi ba zai bani ke ba yau ya sake dawowa saboda na sake komawa gabanshi na rokeshi ya dawo ya sake rokonshi to ya sake dawowa shi kuma ya sake cewa matukar shi ne zai daura miki aure da kanshi to ba zai daura auren da ni ba, saboda na ci mutuncunshi na keta mishi haddin yarshi nayi sanadin da sai dake kuna wulakanta shi ne na ce bari in zo in ji me na yi? Me nayi miki na haka ni na taba ki ne? Ke baki gaya mishi babu komai tsakanina da ke ba sharri kawai matar shi ta kulla mana. Cikin natsuwa na tambayycshi, to in baka yi komai ba sai me? Dole ne sai ya baka aurena da za a je ana ta yi mishi zirga-zirga a gida? Sauran iyaye da sukayi hukunci a kan ya'yansu haka aka yi musu 131 Naga shima shi ya haifeni ko kuwa don an ganshi yana saida turmatir sai a ce bai isa ya zartar da hukunci a kan tashi 'yar ya zaunu ba sai an canza mishi? Bai nuna bacin rai da jin maganar tawa ba sai ya ce min, 1yaye suna zartar da hukunci mai tsanani a kan ya'yansu, Maryam yin hakan ba laifi bane amna kuma da yawansu sukan ciza ne sai kuma su hura a mati yawancin lokaci ma suikan taya ya'ya son abinda sukc so matukar sun gane babu cutuwa a cikin lamarin, me yasa shi ba zai yi hakan ab? Me ya sa ba zai tayaki son abinda kike so ba ya baki mijind a kika rayu kina so? Na ce, ai abinda nake son yake taya ni shi din ya san ban taba sonka ba ya kuma san duk wani abinda ya gudana tsakanina da ka ya faru e a dalilin kuruciya da kurna kuskure. To babu laifi, ya fadi hakan cikin wani yanayi don baka nayi maza na juya da nufin shiga gida sai naji yayi maza ya ce min to, uan dakata mana ki ji abinda Zan gaya miki. Na dan ja na tsaya ba tare dan a waiwaya na kalleshi ba, sai naji ya ce min, to amma ai shi baba yana da labarin rabo yana kashe mutane ko? Gabana ya sake yankewa ya fadi jin da na yi ya ambaci mutuwà a tsorace kwarai na tarabaye shi, me kake nufi da wannan maganar? 132 A natse ya ce min, abinda naken ufi kenan ki buda baki ki yi mishi m agana ki gaya mishi gaskiya babu komai tsakanina da ke ban taba mishi ke ba, na ce to in baá haka ba fa? Ya ce shi kenan sai ki yi ta zama sau goma in z2 a kawo miki kaya sau goman kuma za a zo a karbe. Gabana ya sake faduwa, kar dar ace Mubarak ne ya yi dalilin fasa aurena da Halliru? Kar dai a ce Mubarak ne dodon da Halliru ke gayawa Yakumbo Halima wanda ita ta dauka dodon dodanni ne ko wani aljani. Rasa abinda zan cewa Mubarak nayi in dan ji saukin abinda ke cin zuciyata don haka sai na ce mishi, a sanina dai baba na shi ne mahaifina yana da iko a kaina kamar yanda kowane uba yake iko da danshi saboda randa ya yis anadin zuwana duniyar nan babu wanda ya taya shi don haka in bar rabon wani ya zama sanadinshi to na rantse har abada ba zan auri wannan din ba sai dai ni ma rabon nashi ya sa yanda zai yi da ni kuma karka sake kulani. Ina fadin haka na yi maza na shige cikin gidanmu na barshi a nan wurin yana tsaye. Ko badan ban i haushin hana Mubarak aurena da babana yayi ba saboda tuni ya riga ya fita min a rai bana kallonshi inji zuciyata ta rayamin abubuwan da ta saba raya mina game da shi a baya sai dai in ganshi in ji faduwar 133 gaba ko in ganshi in ji haushi da takaicin shi sun kamani. A wannan lokacin ne kuma baba Lantana ta fito da wani irin salo a gidanmu duk wani wanda ya zo wurinta in suna hira bata kai karshen hirar sai ka ita tana gaya mishic ewar ita wannan zama da take yi ma ai ya kusa ya zama haramtaccen zarna, abokin hirar ta ta ya ce, haramtaccen zama kuma, Lantana sai ta ce eh to haramtacce mana tunda abinda ake yiwa zaman yayi karanci ace niji kana kallonshi yana kallonka shimfidarku daya amma sai ya sahfe kwana da kwanaki babu komai, babu wani motsi a can babu a tukubya ma babu ana yin zaman haka ne ai ni yanzu kiris nake jira don ma dai kawai kar ka tafi ne ya zama ka tafi ka bar ladanka. Haba Lantana haba Lantana yanzu ke a yanda kike din nan sai kin yi korafi kan irin wadannan al'amuran, m utumin da ko lafiya bata isheshi ba, tace a'a ni ban wuce ba sannan tun a can baya ma da yake da lafiyar me aka yi ne da za a ce yanzu in hakan ta faru kar in yi magana? Yaya Dija na baiwa labarin kalaman nata ita ce ta faiyacemin abinda take nufi, kasar kullum sai ta tasa babana a gaba tana yi mishi hirar gidan mijinta na baya, haushi da takaici ya yi ta kama ni na yanda sau daya babana ya kasa cewa ya sauwake mata nashi auren taje ta koma gidan mijin nata na bayan, yawan 134 fadan da take sashi a gaba da yi kIsaa kulium da yi ya sani bashi shawarar dawo da kwana dakin Sallau don ya rinka samun wadataccen bacci saboda mas' alar hawan jininshi, kamar bai ji shawarar tawa ba daga baya kuma sai naga ya koma dakin. Wata gomas ha daya cif nayi ina zuwa makarantar koyon sana'a ta Markas kafin aka yayemu saboda yarda da aka yi cewar mun iya mu gomas ba biyar aka yiwa yayen aka kuma yi mana kyautar dinki saboda gamsuwar da akayi da kwarewarmu, ko kafin nan kuwa nikam na dan dau loakci ina taba dinkina a gida a kekcn da yaya Dija ta saya min don haka dana samu wannan kyautar sai kekunana suka'zama guda biyu. Naso kwarai in koma Karkas in sake shiga wani ajin daga cikin azuzuwan sana'o'in dake wurin in kara koyon wata sana'ar haikan bai yiwu ba saboda karatun da nake yi a makarantar asidini mai zurfi, karatu ne dake bukatar sadaukarwa mai yawa banda haka kuma ga lalurar babana ta yawan rashin lafiya don haka sai na hakura. Tunda aka yayena a wuTin koyon dinki na soma yin dinkin sosa a gida sai mas'alolin da suka danganci babu sia yi matukar yi min sauki bana asa na sabulun wanka ko wanki bana rasa ta yin break a makaranta wani lokaci ma nakan raka babana asibiti ne ba tare da na shedawa yaya D1ja ba balle inje ina 135 jiran abinda zata bamu wannan-shi ne abidna yafi komai faranta min rai na. Shekaru uku ne yau tun bayan faruwar abinda ya faru tsakanina da Mubarak cikin shekarun nan kuwa nayi abubuwa masu yawa wanda kasancewata a yau ni din kwararriyar tela tace gani a fada a kuma kwaikwaya, ni din kuma gwanar girki ce saboda na koma makarantar Markas na sake shiga ajin koyon girki nau'o'inshi kuma malamaina na Markas irinsu malama Hindu da Basma wadanda mukayi matukar shakuwa a dalilin kulawar da suka nuna a kaina sunyi min taimako mai karfi wanda a daliiinshi na samu shiga exam center dake kusa da Markas din na samu rubuta jarrabawar dana samu mallakar takardar shedar gama karatun secondary indana samu credit guda hudu da pass biyu saura f9. A 6angaren da nake ganin kamar na yi nasara kenan, a daya bangaren kuwa Ina nan kamar yanda dama nake aure ya gagara babu kurna yanda banyi ba in yi shi hakan bai yiwi ba, zan iya cewa garama da da yanzu a lokacin da kuka sanni samarin sukan dan zo auren ne basa tsayawa a yi saboda wasu dalilai to a yanzu babu bani da wani wanda zan ce wannan saurayina ne. Mutanen unguwarmu tun suna nunani suna yin bayant a kaina zuciyata tana lissafi ta karyata maganar 136 ta su har na hakura na fita harkarsu ta barsu su fadi duk abinda suka ga dama. Tun ban a kama maganar mutane irin su Yakumbo Halima da suke fadin cikin biyu dai alkwai abu daya ko dai anyi min sihiri ne ko kuma ma aljani ne ya aureni ya hanani yin aure har na soma shiga rudani ina tambayar kaina to menene mas'alata, tuni dai na daina yin kawaye don na gaji da aurar da su da akeyi ana barina a wannan lokacin in har ina da wata kawa to kekena ne da kuma dinkina sai ko kwalliyar da nakeyi don kuwa ba sai an gaya min ni da kaina na san mu'amalar da nayi da malamaina na Markas irinsu Malama Hindu da Basma ya koya mina bubuwa iri-iri da suka danganci mace kwalliya, kamewa, mutunta kai, iyaka dai har yanzu hakan baisa na samu mijin da ya tsaya ya aureni ba su ma kamar yaya Dija sukan ce min wai lokacin auren nawa ne bai zo ba sai in yi murmushi kawai in yi shiru cikin zuciyata kuwa tambayar kaina nake yi ko yaushe ne lokacin oho? Saboda a wannan lokacin har na gaji na soma tambayar kain to koma dai ni din ina cikin matan nan ne da ba a halitt musu mazan auren ba? Tun ina kin yarda in yi amfani da abubuwan da Yakumbo Halima take bani in yi amfani da su na farin jini da wai maganin sihiri da kullum take zargin wai Mubarak ne ya yi min in yi murmushi in ce mata Mubarka bai ma yarda da irin wadannan abubuwan ba 137 Yakumbo shi fa dan boko ne ma digiri biyu ne da shi ya ma sake komawa karatunshi don neman na u yaushe zai zauna yana irin wadanann abubuwan? Sai ta ja tsaki bayan ta gallamin uban harara ta ce, ai sai ki yi dama in kana son mutum ai baka iya ganin laifnishi, ince mata ba haka bane Yakumbo ai ni yanzu bana son Mubarak abin da na sani ne kawai nake gaya miki, ta ce to baki san komai ba incem ata to na yarda. A wannan lokacin ta kaima ina zama in yi kuka ins hare bawayena tun ina yi ni kadai har ta kaima ina yi a gaban yaya Dija, menene mas'alar da ta hanani yin aure? Bani da fasali ne? Ta girgiza kai uh uh kina da shi daidai gwargwado, bani da tsabta ne? Ta sake cewa uh h kina da ita kin kuma iya kwalliya kina kuma yi iina da kamun kai da natsuwa gashi kin yi karatunki kina ma kai tunda har yanzu kina yi to amma lokacin auren bai zo ba, Maryam mijin naki ne baizo ba d on haka bani da yanda zai yi sai dai in yi ta baki hakuri in kuma kara rokon ki ki kara tsare mutuncinki komai zai wuce har kiga kina bayar da labarin al'amarin, ni dai nasan duk waenda ya yi dace da samun babbar mata mai aikairori iri-iri, in yi murmusbi ince yaya Dija kenan kenan kina dai gaya min hakan ne kawai don in ji sanyi a raina. Ita dakanta yaya Dija duk da irin wadannan kalaman sanyaya zuciyar da take yi min ta sha gaya 138 min cewar rashin aurena ya katse mata baccinta ya gusar mata da nishadinta ya sanyata ta ji zuciyarta ta kutata don haka mu yi ta istigfari muna rokon gafarar Ubangiji, in ce mata to wataran kuma in dan zolayeta ince mata ba kince zai wuce ba? Ta yi maza ta ce, kamar yanzu kuwa in har muna raye to zamu sheda wucewarshi. Yaya Dija ya ce a wurina da ta zame min uwa ita nake kallo a matsyain uwa saboda duk abinda take yi min yi take yi da iyakacin iyawarta tana da ya'ya maza da mata amma bata hada su da ni ba, na sha jin matan gidansu suna cewa ai ita wai kanwarta ta fiye mata kowa tunda ita ita kadai ke gareta ba kuma zata sake 'yar uwa irinta ba tunda uwar da zata haifar mata wata bata nan ba wadannan kalaman ne suka sa zuciyata yarda da yaya Dija bata hadani da kowa ba a aiyukanta ne a kaina shi yas anima bana wasa da ita duk abinda tace min to káwai nake cewa bana yi mata musu. Ina zaune a dakin ina yankan kayan da nake nufin dinkawa a wannan satin wanda na ankon wani biki da za a yi ne a unguwarsu aya Dija aka kawomin ina yankan cikin natsuwa da kwanciyar hankali saboda daga ni har dakin nawa tsab muke sai kanshi muke yi, bana tunanin komai cikin raina aiki na kawai nake yi sanda Asabe tayi sallama ta shigo cikin dakin, ashe kina ciki? Nace eh Asabe ki zo ne? Ta ce min, 139 ina kwana? Ina amsawa ina matukar jin tausayinta gaba daya t a canza ko rigar nono a wannan lokacin na ganiyar kuruciya bata iya sakawa, tsabtar ta duk ta kare kullum ka ganta gara jiya da yau ba ita ba ba 'ya'yanta kullum yanzu sai tazo gida kullum kuma da mas'alar da zaka ji tana fadi baba Lantana tayi tayi ta daina shiga dakina tana gaisheni ta ki dainawa, ban sani ba ta canza hali ne ko kuma sule biyun da nake baiwa ya'yanta in zasu tafi ne ya hanata daina wa oho? A wannan lokacin wanda. bai yiwa Asabe sani na hakika ba ba zai ganta ya ganerta ba ga karni da take yawo a ciki. Kin fito daga dakin kanwar uwar taki ne? Ban ji abinda tace ba naci gaba da aikina ina istigfari kan yawan damuwar da nake yi a kan rashin aurena, na yi imani da in yi aure irin wanda sabe tayi gara ma ina zaune a gida gaban iyayena ckin haiyacina da rufin asirina, tunda ba cewa akayi in ba a yi auren ba ba za a samu rahama ba sai dai in ba a yi aikin neman rahamar ba, ba kuma raina auren Asaben nayi ba yasa na fadi haka tunda na san darajar aure yawa ne da shi ko banyi shi ba kuma na karantashi a ganewa kawai a yanda ka'idar auren yake da bayanin shi da akayi a tsari irinw anda auren Asabe ka tafiya zai yi wuya kwarai in har ana samun ladan da ake nema din kullum a cikin korafi ake a zagi miji a zagi kishiya a 140 gaya mata irnin tsiyar da zataje ta yiwa mijin, ni kuwa ina zaune gaban iyayena cikin rufin asiri ina addinina daidai gwargwado ina neman ilimi, ina sana'ata ina kyautatawa mahaifina gwargwadon iyawa ta, a wannan loakcin banda sutura da hidimominshi har runfa nayi: nsihi sabuwa ciki da falo, kayanshi suna can ciki shi da Sallau suna wuri daya, Salau kuma yana iyakacin kokarinshi kullum babsn ayaną yi min addu'a yana samin albarka. Na karaa kallon al'amarin Asabe da aurenta wanda da ni aka so a tura cikin wannan wahalar Ubangiji ya tsarcni,

Chapter 8 of 10