Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
yake yana bata rai kamar wanda aka tilastawa xuwa duk da asibitin mahaifinsa ce yana isa office dinsa ya taradda bilal xaune yace wai kana nufin kana nigeria ne kaifa baka da kirki wlhy bilal ya tashi yana kallon guards din dake tare dashi kafin ya maida kallonsa garesa yace jiya nadawo momy ce ba lfy naxo da ita tana emergency yarima ya xauna yana gyara alkyabarsa yace cikin satin nan nakeson xuwa pheonix i miss skul bilal a bata rai yace bakaji menace ba mamana ba lfy tana emergency kuma kai nakeso ka dubata oh gosh... ya dafe goshinsa alamar bilal na takurasa da yawa, ya janyo wani file ya shiga dubawa bilal ya kwantar da murya sanin halin abokin nasa, yace Aiman mamana fa nace, ashe hrdani kake wulaqantawa yace kome xn mata kaima xaka iya naga matakin karatunmu dayane dakai ko? yace nasani baxan iya bane jikina a mace yake pls help me yarima ya tashi yana yatsina fuska wane ward aka kaitane? bilal ya gayamasa, ya juya ya fice jin emergency take yasa yake sauri, tfy yake yana sanya handgloves a bayansa ana cire masa alkyabba gab da xai shiga dakin da take suka gama sanya masa labcoat, daya daga cikin dabiunsa kenan idan xai shiga aiki baxai tsaya ya shirya ba sai dai yana tafe ana shiryasa idan ma fitowa aikin yayi yana tafe ana cire masa kayan aikin kuma amaida masa na sarauta, dayawa mutane hakan na burgesu hr tsayawa kallonsa ake ana son mulkinsa da qasaita sannan abu mai matuqar wuyane kace kaga.murmushinsa [8:32PM, 12/15/2015] Pherty 🎤 👯 : bai jima aciki ba ya fito yana tafe yana xare handgloves cikin isa da qasaita ko ta kan bilal bai biba, ga fadawa birjik a asibitin, guards dinsa suna biye dashi a baya yana tafe yana yatsina fuska ma'aikatan asibiti sai xubewa suke suna gaisuwa nurses da likitoci amma duk ciki ba wanda ya kula ballantana ya amsa cak suka ga ya tsaya harabar asibiti suna ganin haka suka san akwai matsala tabbas akwai abinda ya fadi daga.hannunsa daman duk abinda ya fadi daga hannunsa baya magana ko ya nuna wata alamar abinsa ya fadi sai dai ya tsaya cak masu moremasa baya suje su duba sugani haka kuwa akayi da yawa suka juya suga ko menene ya fadi suna isa asibitin suka sami turban dinsa ne har wata nurse ta dauka xata kawo masa da sauri suka karba suka fito(wani abin sai sarauta) aka bude masa mota ya jima tsaye kafin acire masa labcoat din jikinsa aka musanya masa da alkyaba suka nada masa turban dinsa kana ya shiga motar akaja kusan motoci gomane jere da juna abayan tasa motar bayan biyu na gaba. mutane sai kallon ikon Allah suke wannan dame yake taqama MULKI KO SARAUTA? 👑 5⃣4⃣ Sanda suka iso gida fada ya nufa ya xauna agaban mai martaba kamar kullum ya tankwashe qafafunsa yana kallonsa fuskarsa da murmushi yace barka da tashi abba yace ya lfyr hannu, ya yatsina fuska batare daya amsa ba ya janyo inibi yakai bakinsa sarki yace jiya na turaka meeting amma baka gayamin yanda kukayi ba yarima yadan kallesa kafin yace sunyi magana ne akan abinda ya shafesu, ynda na lura sarakunan naji da mulkinsu shiyasa nafito masu danawa qasaitar, sunyi mgn akan rashin wadataccen abinci ga talakawansu da kuma rashin ruwa da talakawansu basu wadatuwa dashi sarki yace kai akan me kayi magana me ka lura yna damun talakawa? yarima ya jefar da inibin dake hannunsa yace abba bama talakawa kadai ba ai ynxu duk yan nigeria suna fama da rashin kudi abinci makarantinne boko da islamiya sai arasa ilimatattun malamai, qauyukka ba wuta asibitoci ba kawarrarun likitoci [9:08PM, 12/15/2015] Pherty 🎤 👯 : Sarki ya tashi daga kishingiden da yake cike da mamaki yana kallon aiman dan bai taba xaton yasan matsalar rayuwa ba yace yarima gayamin me ka gaya masu game da wannan yace abba nace laifin sarakuna ne ai mulkin da ba haka yake ba, ku sarakuna ku kuka cire hannunku daga komai kuka barwa gwamnati tayi, sarakunan da su suke da ikon komai suna taimakon talakawansu sannan suna samin lbrai daga fadawansu, a da ko haihuwa akayi dole sai sarki yasani ko mai anguwa amma ynxu fa kai xaka bawa kanka amsa abba, na gayamasu sarakuna sunfi gwamnati hulda da jamaa kuma sunfisu sanin halin da talakawa suke ciki 5⃣5⃣ Ranar qiyama ana fara hisabi da jini sannan ayi da manyan malamai,masu kudi, shugabanni, sarakuna, tor wannan ma ya ishemu ishara mu dage muga yanda yan qasa suke tfyr da rayuwarsu, Allah ba ruwansa gabaki daya xai hadamu ya tambayemu ynda muka tfyr da mulkinmu ba ruwanshi da cewa shugaban qasa ko gwamna, mulki duk mulki ne ko mace a gidan mijinta mulki take haka namiji a tsakiyan iyalinsa mulki yake xaa kuma yi masa hisabi gobe qiyama taya ya tfyr da iyalinsa kamar yanda muka sani raf raf raf gabaki daya daukacin fada aka dauki tafi sarki saboda mirna kamar ya hadiye yarima yakeji yace a tunani ban taba sanin kasan wanna ba yarima na dauka bayan mulki, sarauta, isa, taqama da qasaita bakasan komai da ya shafi rayuwar duniya ba ashe bn saniba kallon kitse nakewa rogo, am proud of u son, ko ynxu na mutu nasan xaka iya gadon sarauta ta a yanda nakeji ma ko ynxu xn iya sauka na baka amma nayima alqawari daka kammala karatunka xn sauka daga kujerata a nada ka nan da nan fadawa suka xube qasa sai fadi suke godiya yake ranka shi dade, yarima na miqa godiyarsa Aiman kuwa kansa na sunkuye ya dago yana kallon mahaifinsa yace abba nxt tomorrow nake son komawa skul sarki yace Allah ya kaimu amma tare da affiya xakaje nan da nan annurin fuskarsa na kau tamkar wnda akayiwa mutuwa ya murtuqe fuska yana fadin abba gsky baxan je da itaba ai frnds dina sai sumin dariya kowa baida mata sai ni kuma matar ma wannan qaramar yarinyar sarki yace lallai yarima ashe hr ynxu baka sauya ba kana nan aka qudirinka tor bara kaji dole affiya xata bika acan xata cigaba da xuwa makaranta jiya da bilal xai dawo nasa ya samomata admission kuma ta samu skul din dakake acan xataje ko kanaso ko bakaso ya tashi a xuciye kamar xai fashe da kuka yace ynxu abba fisabilillahi sai da kagayamasa inada mata yace nayi kama da maqaryacine ? batare da yayi mgn ba ya juya ya fice ransa a bace...... 5⃣6⃣ Ta shirya cikin tsadaddiyar atampha mai kyau da tsada ta dora alkyabba ta nufi sashen umma ta xauna a gabanta kamar yanda yarima ke mata tace umma yau k kadaice ina masu tayaki hirane tace na korasu bana son hayaniya ne ta gyada kanta hade da janyo inibi ta sanya abakinta umma tace rumaisah taje maki sallama kuwa? tace sallamar me umma? tace bata gayamiki xasuyi tfy itada Aliyu bane, sunxo daxu da safe kuma naga yarima ne ya masu rakiya hr airport tayi shiru kafin tace amma rumaisa bata kyautamin ba umma, ynxuma takanas naxo inda kike ne inemi ixinin xuwa (i have alot to talk with her) inaji ba laifinta bane laifin yarimane naji lokacin da take fadin xataje inda kike ya hanata kuma ban tambayesa dalili ba [9:17PM, 12/15/2015] Pherty 🎤 👯 : Affiya tayi rau rau da idanu tana kallonta tace umma kinga abinda yaya maina ke mani ko, wlhy baya kyautawa umma takuramin yake kamar ni ba qanwarsa bace tayi shiru batace komai ba tace kinji umma tace naji na rasa mexance ne na rasa wane irin mutum ne yarima tace ni umma kawai kice yadaina takuramin ya fita sabgata pls umma, ta fada tana hawaye abinda yayi matuqar tada hankalin umma kenan tace oh affiya bar kukan banaso kibari yaxo xn masa magana dai dai lokacin ya shigo fuskarsa a daure tamau, idanunsa boye cikin darkspace kallo daya suka masa suka fahimci akwai bacin rai qarara atare da fuskarsa hakan yasa affiya tasha jinin jikinta ya xauna batare da yayi magana ba bai kuma da niyar yin magana hr sai umman ta tambayesa meyasa mesa, ko xasu shekara a gurin idan hr ba ita tafara yimasa magana ba baxai tabayi mata magana ba tun yana qarami haka yake, shifa mulkinsa, sarautarsa da qasaitarsa bafa a waje kawai take ba, ga kowa take kuma gida da waje....... 📝 Hausa novel📚 [9:45AM, 2/26/2016] Bebinga: [5:36PM, 12/20/2015] Pherty 🎤 👯 : [7:19PM, 12/17/2015] Pherty 🎤 👯: 5⃣7⃣MULKI KO SARAUTA? 👑 Na fertymerh xarah💞 AFFIYA_ na fita dakin kai tsaye falon sarki ta nufa, kallo daya tayi masa ta gane yana cikin bacin rai cikin faduwar gaba ta xauna kanta a sunkuye ta gaidashi daga can taji fadawansa sun dauka sarki ya amsa gaisuwar gimbiya affiya yar mulki da sarauta ta sunkuyar da kanta qasa, sarki ya dubeta yana fadin gobe xaku wuce pheonix tare da yarima acan xaki cigaba da karatunki nasa bilal abokinsa ya samo maki admission acan kiyi haquri da xaman ki dashi acn idan da matsala kisanardani ko ummanku nasani ko anan xaman haquri kike dashi bayason auren, to ko acan nasan xaman bacin rai xakiyi amma komenene kiyi haquri kixauna dakin mijinki ki xauna tare dashi kiyi masa biyayya kada kibiyewa son xuciyarki wurin nuna qarfin mulkinki akan saboda kema nasan halinki tun kina qanqanuwa bacin ransa da kikagani yanxu duk bai wuce dan xaki bishi kuje bane, idan kinyi haquri kinbisa yanda yakeso kin sauke girman mulkinki kinbi nashi mulkin to xaku dai daita da yarima idanunta a qasa sunyi rau rau tace xan kiyaye abba amma nida anbarni nan ma xn qarasa karatuna, yace bari nabaki wata kissa affiya wata mata taxo wajen manxon Allah s.a.w tace inason yin sallah tare da kai sai yace nasan kina son yin sallah tare dani amma sallarki a quryar dakinki tafiye miki fiye da rumfarki sannan ta rumfarki yafi ta tsakar gidanki, ta tsakar gidanki tafi ta masallacin shiyarku, ta masallacin shiyarku kuma tafi yi a masallacina(ya qara da cewa) mafi alherin masallatan mata sune dakunansu kinga anan kome xakiyi bayan idon mijinki baxai kai ladar wanda xakiyi a can tare dashi ba, sannan xaman ki acan xai qara janyo shaquwa tsakaninku [7:38PM, 12/17/2015] Pherty🎤👯: in banda abinki mata na neman ladar miji kina bijirewa baki tabajin lbr wata da taxo inda Annabi s.a.w ta samesa tare da sahabbansa 5⃣8⃣ Tace haqiqa ni mata suka turoni xuwa gareka, Allah ya aiko ka xuwa maxa da mata sai mukayi imani dakai muka yarda da Allah daya aiko ka, sannan kuma mu mata muna xaune anyi mana iyaka a tsare muke cikin gidajenku kuna biyan buqatar shaawarku damu sannan mu muke dauke da ya'yanki amma ku maxa an fifita ku akanmu da xuwa jumma'a da sallolin jam'i da xiyartar marar lfy da halattar sallar jana'iza da kuma yawan yin hajji bayan na wajibi kuma duk abinda yafi wannan ma shine fita da kuke jihadi dan daukaka kalmar Allah, sannan idan dayanku yafita ummara ko hajji ko yaqi mune muke kiyaye maku dukiyarku kuma mune muke dinka maku tufafinku kuma mune muke rainon yaranku.... to ya ma'aikin Allah ta ina xamu yi tarayya daku wajen lada? sai manxon Allah s.a.w ya waiwaya wajen sahabbansa yace tunda kuke kun tabajin wata mace ta tambayi wani abu na rayuwar duniyabwanda yafi na wannan macen kyawu? sai sukace ya manxon Allah mu bamu taba xaton cewa wata mace xata iya wannan tunanin ba sai manxon Allah ya waiwaya gareta yace ki koma yake wannan mata, ki sanarda matan dake tare dake cewa duk wadda take kyautatawa mijinta kuma ta nemi yardarsa kuma tabi abinda yakeso tanada irin wancan ladar aikin gaba daya(sai matar ta juya tanata murna tana kabbara saboda farin ciki) Hakanan watarana mata sunxo wurin manxon Allah s.a.w sukace ya manxon Allah maxa sun kwashe falalolin baki daya, suna jihadi don daukaka kalmar Allah yanxu muma sai kabamu wani aiki da xamuyi mu cimma ladan jihadi Manxo Allah yace ko wacce acikinku aikinta yana cikin dakinta wnda dashine xata cimma ladan masu aiki(dan haka kuyi haquri da xaman aurenku kubi mijinku kuyi biyayya bama affiya kadai ba hr mu yakamata mu koyi xaman haquri da biyayya agidajen maxan mu) [8:01PM, 12/17/2015] Pherty🎤👯: ta jinjina kanta alamar gamsuwa tace nagane nufinka abba xnyi biyayya kamar yanda kace amma dan Allah abba ka roqamin shi yabarni naje naga ammi qasaitaccen murmushi yayi irin nasu na manya masuji da sarauta yace ke baxaki roqesa bane saini, koni k aurensa ba yayanki bane? tayi narai narai da idanu kamar xatayi kuka😕 tace Allah ynxu abba ina tsoronsa kuma miskiline sosai yace tor ahakan xakuyi xaman aure idan kukaje can kenan baxaki iya gayamasa matsalarki ba tayi shiru tana kallonsa yace shikenan naji tayi murmushin da dimple dinta na bayyana kana ta tashi tafita bara mu leqo yarima merah da ummansa 🏃🏻 🏃🏻 🏃🏻 5⃣9⃣ Shiru ya ratsa dakin hr kusan awa daya suna xaune ba wnda yayi mgn acikinsu ranta ya qara baci duk da tasan me yake nufi idan ba ta tambayeshiba baxai taba mgn ba sai dai su tabbata a hakan, fuskarta ba walwala tace wai xaman me kakemin anan ne? kasanyani agaba kamar maye, bai damu da furucintaba dama ita yakeso ta fara mgn kamar me jira yayi saurin cire space dinsa yana kallonta idanunsa sunyi jawur saboda bacin rai(🙊ko meye nasa na bacin rai dan xaije da affiya oho) yace umma ki taimakamin pls, sai hawaye sharrrrr(rabon da taga hawayensa tun yana qarami lallai abin ba qarami bane🙆 🏿)nan da nan hankalinta nayi matuqar tashi abin ya tsoratata muryarta hr rawa take tace yari...ma lfy meyafaru wane irin taimako xnma? yayi shiru na dan wani lokaci kafin yace umma bayan biyayyar danayi na karbi aurenta da banaso ynxu kuma danme xaa takuramin akan sai affiya tabini pheonix kuma wai acan xatayi skul tayi kasake bakinta abude tana kallonsa cike da tsantsar mamaki tace yarima kaji tsoron Allah kasani duk kaci amanar affiya Allah baxai barka ba kuma ni kaina xaka fuskanci fushina hakalinsa ya qara tashi anyi baayiba yaxo ummansa ta share masa hawaye sai gashi ta hada masa wani xafin [8:19PM, 12/17/2015] Pherty🎤👯: umma bai kamata ki...... tayi saurin katsesa yimin shiru pls bana son hayaniya gsky nake gayama kana takura affiya da yawa akan wane dalili ita ta aura ma kata kaine ko me? kamar yanda akama dole haka itama dole akamata kuma koba komai jininkace qanwarkace ba wata bare bace, amminta qanwatace uwa daya uba daya kagayamin banbancinta da rumaisa? ya dafe kansa da hannuwansa duka biyu yaja iska ya furxar cike da bacin rai yace umma bawai na tsaneta bane auren ne banaso for God sake duka duka affiya shekarunta nawa yaushe suka qare skul ne da rumaisa, umma hr axuciyata niba yarinyar danakeso affiya ba ajina bace, x a disgrace a ganni da ita frnds dina ma dariya xasumin sukaji inada mata 6⃣0⃣ Maganar tayi matuqar girgixata hrta kasa biyewa sai da fuskarta ta bayyana shima da mamakin sauyawar fuskarta yake kallonta yace umma naga kin tsorata ko miye laifi acikin maganata? tace babu amma dakaje ka wulaqantamin yarinya inaso tun yanxu ka saketa kabani takardarta mgnr ta daki xuciyarsa sai dai bai nunaba ya yatsina fuskarsa yana fadin ba mgnr saki nakeyiba umma mafita naxo kinemamin dan banaso naje da ita tace mafita dayace yarima ka sakarmin yarinya shine kawai xai hanama xuwa da ita ya qara tsuke fuskarsa yace ai matsalar umma ina sontane da banasonta dana saketa ynxu(yabfadane kawai amma xahirin gsky baya sonta) hr a xuciyarta taji dadin kalamansa amma bata nuna ba illah qara tsuke fuskarta da tayi ta janyo laptop dinta hade da sanya medical glass dinta hakan ya qara sanyaya jikinsa alamar baxata kula shiba kenan [8:34PM, 12/17/2015] Pherty🎤👯: A sanyaye yace umma kimin addua inyi yanda kikeso Allah yabani ikon kulawa da affiya, bata amsa ba kuma bata kallesaba hakan yasa ya tashi ya fice hr yakai qofar fita ta kira sunansa yarima....ya juyo yana kallonta batare da ya amsa ba idanunsa jawur kamar xaiyi kuka ta taso ta qaraso inda yake ta riqo hannunsa tace meyasa xuciyarka ta karaya ka gayamin me kakeso ynxu nayima hawayen dayake maqilewa suka xubo ya kasa furta komai tace kaxama namijin gske yarima mai taqama da sarauta kada xuciyarka ta kasance ta rangwayen maxa, ta langabar da kanta cikin shigar wasa kamar yanda takemasa idan yana yaro tace be a big man, with a gud mind d.... sai ya subuce da dariya daya tuno da hakan ya rungumota sosai kafin ya dago yana kallonta yace insha Allah ummana ta gyada kanta tana kallonsa tana murmushi tace nagane me kake nufi tunda bakaso ace affiya matarkace ,idan kaje ka nunata a matsayin qanwarka amma ka kula da ita tamkar ni kada ka takuramata pls yayi murmushin jin dadi hade da sumbatarta a goshinta yace i promise ummana itama murmushi tayi masa tana kallonsa...... Washe gari bayan sunje gidansu affiya da kwana biyu jirginsu ✈na daga xuwa qasar pheonix Ko ya rayuwarsu xata kasance acan oho🙅 🏿 ku biyo pherty kuji🏃🏻 🏃🏻 🏃🏻. 📝Hausa novel 📚 [7:39PM, 12/20/2015] Pherty🎤👯: [11:42AM, 12/20/2015] Pherty🎤👯: 6⃣1⃣MULKI KO SARAUTA👑 Na fertymerh xarah💞 PHEONIX⛲ Rayuwar Aiman da Affiya bata cnxa ba kamar yanda suke a nigeria bai damu da itaba tamkar babu ruwanta a gidan tun abin bai xame mata jiki ba hr tasaba da rayuwar pheonix tun saukarsu garin mgn bata taba hadasu ba hassalima sai a kwana bitu bata ganshi ba idan ba a skul ta tsinkayosa daga nesa ba kullum xai shiga motarsa driver dinsa ya fice dashi haka itama danata driver ko sun hadu skul xai dauke kansa kamar da duniya bai santaba kobai taba ganintaba bilal ke iya qoqarinsa akansu ta hnyr ganar dashi illar abinda yake amma fafur xai daure fuska ya nuna bayason mgnr tausayinta kesa bilal xama a gidan tare da ita yana debe mata kewa koya mata abubuwa da suka shige mata duhu game da karatunta tana jin dadin xama da bilal domin shine abokin hirarta ma'aikatan gidan kakaf batajin yarensu inka cire sunyana dake dafa mata abinci amma tana mamakin yanda take ganin aiman na yare dasu ko a ina ya iya oho😏 batada sukuni ko walwala idan ba bilal ke xaune a gidan ba hakan kesata xaman kitchen tare da sunyana tana koyon girki kotayi waya gida bata taba sanar dasu irin xaman da suke ba 6⃣2⃣ A wani dare tana xaune tare da bilal take tambayarsa yaya bilal wai wacece wannan nabila yace meyasa kike tambaya? tace tafiye xuwa gidannan inda yaya aiman ko a skul ina ganinsu tare yace sun jima tare course mate din muce tayi shiru xuciyarta na bugawa abinda take xargi gskyne wato budurwarshi ce takasa boye damuwarta batasan daliliba bilal ya lura da hakan yace affiya karki damu kisa wannan a ranki, aiman yayankine kuma mijinki duk fadin garinnan nikadai nasan da wannan,sannan aiman bayason nabila ita kadai k haukanta kuma qaryane ace ga yarinyar da aiman k so a duniyar nan ban taba ji ba, macce bata gabansa burinsa nakan karatunsa da kwallo amma bansaniba ko ke xaki iya cnxa mishi rayuwa? tace shi haka xai qare rayuwarsa bayason kowa ne? yaja numfashi tare da tabe bakinsa yace tor waya sani tunda ya dauki mulki yasa a gaba ai kina gani a skul ynda yake nuna mulkinsa ga kowa kuma dole ake binsa yace amma aikece yakaata ki cnxa mishi rayuwa ki janyosa sosai ga jikinki duk mulkin da yarima keyi ban taba ganin laifnsaba cos duk inda SARAUTA 👑take akwai qasaita ta musamman a wajen,bakuma xaki iya raba jinin SARAUTA👑 da MULKI ba duk sarautar da babi qasaita acikinta xakiga ai batada qarfi dole yayi taqama da MULKI KO SARAUTA👑 ki tuna affiya k macece fa wacce ko tsoho ya hangoki sai ya yarda sandasa kina da kyau kina da diri kiyi amfani da wannan kija raayinsa [12:16PM, 12/20/2015] Pherty🎤👯: a raunane tace yaya bilal yafa gayamin baxan taba jan raayinsa ba wai bnda abinda xn birgeshi dashi matan duniya ma basu birgeshi ba ballantana ni qarama yaja dogon tsaki....dai dai lokacin da aiman ke saukowa ka bene, yana sane da kayan barci farare masu kyau da tsantsi sun kwanta a jikinsa, idanunsa sun rikide kalar barci ya dubesu yana yatsina fuska yace qananan maganganunku sun dameni sun hanamin barci, banga dalilin daxaku doramin hira a wannan darenba kamar gidan haya ko caca lokaci daya suka kalli juna kafin su maida kallonsu garesa hr a xuciyarsa yake wannan mgn fuskarsa a daure yacigaba da fadin idan hira xakuyi pls kufita waje kun hanamin barci kuma kuna damun masu aikina, ya juya hr xai fice sai kuma ya juyo kallon da yayi mata yasata raxana tare da yimata kwarjini da yatsa ya nuna mata hanyar dakinta, idanunta sunyi rau rau ta kalli bilal kamar xatayi kuka ya gyada mata kansa sannan ta juya ta fice bilal ya tako hr inda yake yace nasan kanamin wulaqancine dan ina bayan affiya in banda wannan kai baka isaba ya daga kafadarsa alamar ko a jikinsa yace ni kadaina xama da ita sai ka xubarmin da girma sai me idan girman ya xube ya fada a harxuqe girma na yaushe tunda an daura aure kuma dole matarkace yarima ya yatsina fuskarsa yace kada ka janyomin ciwon kai da wannan lion voice din taka, ya jefo masa makullin mota yana fadin kaje gidanka pls baxaka min iko a gidana ba, inkuma anan xaka kwana tor kada ka dameni da surutu ko magiya akan affiya ya juya ya haura sama bilal ya girgixa kanshi kawai yabisa samaaa..... 6⃣3⃣ Sai faman kaiwa da kawowa take tsakanin kitchen da falo tun bayan xuwan qawarta xarah dange sai da ta tabbatar ta cikata da kayan marmari kana ta xauna fuskarta dauke da murmushi tace ina madam halamcy uwayen surutu da kwadayi , tace nabarta skul tare dasu sady da miss aysher,da hassina , ta soma kallon gidan kafin tace wai affiya k kadai k xaune a gidanan ne? tace nida yayana ya fitane ta gyada kata tan mamakin kyawun gidan an qawatashi da kayan sarauta affiya ta jinjina kanta kawai kafin tace kwana biyu bamu hadu ba ina oga ma'auya xarah ta soma murmushi an tabo inda ke mata qaiqayi bata kai da mgn ba yarima ya shigo kallo yabi xarah dashi a wulaqance kafin yamaida kallonsa ga affiya data sha jinin jinkinta yace👉🏻wannan fa? tace friend ditace kuma course mate dita batare da yayi magana ba ya haura sama dai dai lokacin dayaji xarah dange na tmbyr affiya daman kinsan shine..... affiya tace eh mai aikina ne...... caraf a kunnensa lokacin da yake hawa steps cak ya tsaya ya juyo ya kalleta kafin ya juya ya shige part dinsa🙆🏿 xarah kuwa saboda tsabar mamaki da kidima sakin baki tayi tace kice Allah qawata, dama duk ajinsa girman kansa taqamarsa mulkinsa da qasaitarsa duk na qaryane...tor sarautar me yake taqama da ita? jikin affiya ya soma rawa ta riqo hannun xara suka fito waje nayimasa ne dan yaji haushi kije gida karya fito ya sameki xarah taxaro ido tace kina nufin qarya kikeyi kenan🙊 [12:28PM, 12/20/2015] Pherty🎤👯: tace wlhy yayana ne tace chab lallai kin debo da xafi i wonder ki kira prince mai aiki cos nasanshi nasan mulkinsa amma shi baima sandani ba affiya tayi dariyar yaqe tana fadin kibarshi ba abinda xaimin xarah ta shige motarta taja tana fadin sai kin shigo gobe.. tana juyowa ta dafe qirjinta da hannuwanta ta rumtse idanuwanta tana karanto adduoi ta cira kai sama tana kallon window dinsa ko xata hangosa amma ko alamar motsinsa babu taja numfashi ta shiga gidan turus ta ja ta tsaya idanunta suka kawo kwalla lokacin data samesa xaune a falo yana shan coffee sum sum tabi bayansa ta wuce kamar wata barauniya keeeeeeeee ya kira sunanta cikin husky voice dinsa sai da hantar cikinta na kada saboda kidima sai da ta kusan faduwa qasa........ sick😨 [8:23am, 10/3/2016] Fatyma Zahra Too Nv: fertymerh xarah novels [9:45AM, 2/26/2016] Bebinga: [7:42PM, 12/21/2015] Pherty 🎤 👯 : 6⃣4⃣MULKI KO SARAUTA? 👑 Na fertymerh xarah 💞 Ba musu ta juyo taxo ta durqusa inda yake hawayen datake maqalewa suka xubo tace dan Allah yaya kayi haquri wlhy baxan sake ba😥 yace mekika min ne?nace kin min wani abune? ta girgixa kanta da sauri tace kayi haquri dan Allah yaya maina yace ni ba abinda kikamin nakirakine kawai kimin tsallen kwado cos shi nake sha'awar ingani. ta xaro idanu 😳 tana kallonsa tace tsallen kwado yaya yace kinjine kike tambayata kenan dan kin rainani tayi shiru tana share hawayen fuskarta ta tuna tunda take a rayuwarta bata taba tsallen kwado ba hassalima n-down ba wnda ya isa yasata ko a skul saboda girman mulkin baffanta ta soma yarfe hannuwanta tana kuka tana roqonsa amma yayi mata biris kamar baisan tanayi ba ta tashi ta kama kunnuwanta ta somayi,kukan da take ya janyo hankalin sunyana falon da sauri ta qaraso gurin ganin abinda k faruwa yasa taja turus cike da mamaki ta juyo tana bashi haquri, ya daure fuskarsa yana kallonta yace join her,ta xaro idanuwa tana kallonsa ya daka mata tsawa ba shiri ta fara jikinta na rawa 6⃣5⃣ Kusan awa daya suka dauka duk sun jigata sun gaji ba kamar affiya da hr hawayenta sun qafe, ahakan bilal ya shigo ya samesu salatin da yake yana tafe yana tafa hannayensa yadawo da hankalin yarima xuwa garesa yace subhanallah anya aiman kana tsoron Allah kuwa? ya dauke kansa daga kallonsa batare da yayi mgn ba yacigaba da kallon ball dinsa bilal ya kallea yana fadin su tashi, ba shiri suka tashi amma me summ...... affiya ta fadi ragwaf sumammiya ko kadan bai raxana ba hassalima qara gyara xamansa yayi ya xubawa t.v manyan idanuwansa,abinda ya qara qular da bilal kenan tunda ba hali ya tabata matar aurece [8:17PM, 12/21/2015] Pherty 🎤 👯 : bilal ya janyo wayarsa ransa a bace yarima na ganin haka yasan baxai wuce mai martaba xai kira ba sai yayi wuf ya kwace wayar yana kallonsa yace kai meyasa bakada hankaline menene abin damuwa anan bilal yace babu sannan kaine babban marar hankali marar tausayi da tawakkali daka xauna kana xaluntar yar mutane ka sake ta mana, ka dauketa ka kaiwa wanda ya aura ma ita kace masa baka sonta bakason auren yafi ka xauna kana cin amanarta yarima ya yatsina fuska yana kallon inda take kwance kafin ya dubeshi yace ko kashe ta nayi ai qanwatace ko yace ba qanwarka ba diyarkace kaika tsugunna ka haifeta banxa mugu kawai kalaman bilal sun soma tunxurashi baibi ta kansa ba ya tsugunna ya dauki affiya ya nufi dakinta da ita bilal na biye dashi a harxuqe aiman ya soma taba jikinta yaji yayi sanyi gabaki daya duk sai yaji ba dadi karo na farko a rayuwarsa daya soma tausayinta kenan bama ita ba bamance dayataba tausayi sai affiya shima a yau ganin xai bata masa lokaci yasa bilal ya tashi ya tureshi fuska a murtuqe ya shiga duba affiya aiman ya koma gefe ya xauna yana kallonsu a rayuwarsa baisan nadama ba illah kawai ya tsinci kansa da rashin kyautawarsa akan abinda yayi mata da yasani da yabarta koba komai qanwarsace amanarta aka bashi kuma ya tabbata Aliyu baxai taba yiwa rimaisa haka ba acikin tunaninsa ya jiyo muryarta yaya bilal yace sannu affiya tace yaya sunyana fa yace tana lfy nabata magani tasami barci ta lumshe idanuwanta kafin ta bude tace yaya bilal ka taimaka ka kaini gida inda umma ko ammina baxan iya xama anan ba mgnr ta dan sosa aiman sai dai bai nuna ba illah dauke kansa da yayi daga kallonsu bilal yace gida kikeson xuwa affiya ta gyada kanta da sauri yace saura 4mnth ayi holiday kiyi haquri kinji ta rumtse idanuwanta tana hawaye tace ina son shiga toilet baxan iya tashiba yaya bilal ciwo sukemin ya rumtse idanuwansa cike da takaici kafin ya dubi aiman fuska a daure yace wlhy bana so na xama sillar hadaka da iyayenka da yau sai na tabbatarwa mai martaba duk abinda kakewa affiya sannan baxan jure ganinta a hakanba shiyasa xn dakatar da xuwana a gidanka tunda nima ubana ya siyamin nawa gidan,affiya amanarkace kuma Allah xai tambayeka ya juya ya fice ransa a bace yaya bilal dan Allah karka tafi dani kaje dani ya tsaya cak ya juyo yana kallonta idanunta taf da

Chapter 5 of 7