Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
juya ya fice yana murmushi sum tayi ta fadi sumammiya ajikin rumaisa data riqeta cike da mamakin aiman tor daman sun san junane yaushe hakan ta faru ina suke haduwa,tabbas baxata sanar a gidaba harsai ta tabbatar tace na'ima dan Allah ku kama akaita gida ahaka taro ya watse aka sanyata mota suka nufi gida da ita shi kuwa gogan ko ajikinsa yana jingine a motarsa sai faman fusgar da iska yake a bakinsa yana wani dauke kansa hr suka wuce da ita. abinda na bashi mamaki bai wuce ganin hrda rumaisa cikin masu kaita gidaba koda yake tare ma yagansu axaune, may be sunsan junane kokuma su qawayene,dama haka mata suke da shisshigi ya shigar motarsa yajata da qarfi kamar xai tashi sama fuuuuuuu... 3⃣2⃣ Yana isa gida trolley dinsa ya dauka da laptop da manyan wayoyinsa da duk wani abu da yake buqata yabar gidan ganin lokacin tashin jirginsu ya kusa bai ko nemi sarkiba saboda hr ynxu yana fushi dashi kai tsaye airport ya nufa cikin qanqani lokaci jirginsu na daga Tunda ya.iso pheonix ya soma kiran layin ummansa, tana dauka yake gayamata shi har ya iso skul kuma ta gayawa tsoho karma ya nemeshi, bai jira cewartaba ya tsinke wayarsa. [12:04AM, 10/25/2015] Pherty🎤 👯 : yaya mamakin samun nabila gidansa dakuma yanda akayi hrta sami shiga ta tare masa a gida alhali security nagidan har yaje xai tara security ya tambayi dalilinsu nabari mace ta xauna masa a gida sai kuma ya fasa acewar bayason hayaniya ko dogon turancin daxasu tsaya yimasa sannan ma idan ya tambayesu dalili tamkar ya xubar da ajinsa ne qasaitarsa ta xama ta bnxa itada ta kawo kanta idan ta gaji xata fita🙊 tana ganinsa ya shigo ta taso da karairayarta xata rungumesa,yasa hannu ya tureta ta fada a saman center table sai da qugunta ya bugu tace wash yaja tsaki ya fice fuskarsa a murtuqe shiru tayi bata damu ba amma tasa aranta sai ya sota kuma ya aureta ta dauki aniyar biyarsa gida nigeria domin ta cimma burinta kuma xata shanye duk wani wulaqanci daxai biyo baya daga garesa bayan qugunta yadaina xogi ta tashi tabishi har dakinsa yana qoqarin cire kayan jikinsa,ya dubeta cike damamaki karo na biyu a rayuwarsa da ya kebe da mace a daki bayan affiya ya gyara tsayuwarsa bayan ya maida rigar ya kafeta da narkakkun idanunsa dake rikitata yace ashe ke marar hankalice bansaniba ke wacece daxaki shigomin daki ba ixini ba komai angayamiki ko ummana na shigomin daki kasafai ballantana ke banxa bullshit hannunta a qugunta take kallonsa tace laifine prince dan na nuna qaun..........tas kakeji ya dauke fuskarta da mari kusan sau uku ina magana kina magana,ina baki umarni kina gardama dan kin rainani,fuskarsa a daure ya nuna mata hanyar waje yace get out of my room,kika sake gigin shigomin daki sai na karyamiki qafafu stupid a tsorace ta fice daga dakin jikinta na rawa hannunta dafe a kuncinta, ya soma safa da marwa yana yayyafe hannunsa da ya mareta gani yake ma taci amanarsa da hannunsa yakai a jikinta hr shikemata Allah ya isa yaja numfashi ya furxarda isaka daga bakinsa shi ala dole ransa bai baciba bai yarda da bacin raiba wai haushi tabashi yana mamakin yanda mata k bibiyar maxa,tor shi mema xaiyi dasu meye nashi da mata da suke matsar da kansu akansa.... 3⃣3⃣ Sunayin parking a harabar gidan suka fito da ita securities hankalinsu na tashi ganin yanda suka fito da ita a falo suka tadda president da ammi da aliyu duk suka tashi lokaci daya suna tambayar meya faru na'ima tayi masu bayanin komai dan rumaisa bata shigoba tanadaga waje tana tsoron su ammi su tambayeta, dai dai lokacin ta farfado nan da nan ran maxa na baci,ya rasa meke masa dadi a duniya ya riqa safa da marwa acikin katafaren falonsa kafin ya juyo idanu jawur yake kallonta dai dai lokacin qawayenta na fice da sauri yace ciki ciki affiya,waya maki cikin,menene dangantakarki dashi,waye ubansa a duk fadin garinnan dame kuma yake taqama? hawaye na xubo mata tasoma girgixa kanta cike da tashin hankali tace Allah baffa bansaniba.......ji kake gau ya dauketa da mari aliyu ya riqota cikin tashin hankali abinda bai taba gani.ba baffa yasa hannu akan autarsa jikin ammi nayi sanyi sosai kuka take kamar ranta tunda taxo duniyabata taba tsintar kanta cikin irin wannan yanayinba kin mantane kin manta duk gatandana ke baki bn manta tarbiyar dana baku ba meyasa kikaci amanata auta, meyasa kika nemi toxarta ni a idon duniya tana kuka tasanardashi komai sai dai bata fadi dan sarki bane gudun baffanta yaje bincike aje ahanasu bata rama ba waye mahaifinsa tace nima bansaniba tor meyasa kuke haka ynxu me gari ya waya tana kuka tace wlhh sai na rama baxan kyaleshi ba ta tashi ta haura step ta nufi dakinta tana kuka sosai [12:10AM, 10/25/2015] Pherty🎤 👯 : Tun daga ranar take nemansa ruwa a jallo ta baxa securities dinta ako ina suka gansa su xomata dashi duk inda takesa ran ganinsa ta duba bata ganshiba babu sa babu alamarsa batasan daliliba hakan ya qara qufular da ita sai take ganin kamar da gangan yanemi toxarta ta a idon duniya tunda gashi an nemesa ansa kamar walqiya tayi kuka kamar ranta hrta gode Allah ta tabbata baa taba cin xarafintaba irin wannan ta qudirava ranta baxata barshiba sai ta rama aduk lokacin da suka hadu sai ta nuna masa qarfin MULKI yafina SARAUTA. 📝 Hausa novel📚 [9:43AM, 2/26/2016] Bebinga: [12:45AM, 10/27/2015] Pherty 🎤 👯 : 3⃣4⃣MULKI KO SARAUTA💞 Na fertymerh xarah 💞 Yanda ya shigo gidan nasa a bace ya tabbatarwa masu kula dashi ba lfy duk suka sha jinin jikinsu ba wanda yayi yunqurin gaidashi tunda sunsan halin kayansu idan ransa ya baci ko mgn bayaso amasa tun daga falo ya soma cire kayansa yana wurgi da su kamar wani yaro ko kafin ya isa dakinsa ya cire komai ya koma dagashi sai vest da dogon wandon dake jikinsa, hr xai shiga dakin sai kuma ya fasa cikin husky voice dinsa ya soma kiran jabo mai kula da girkinsa kamar bayaso sai gata ta iso jikinta na rawa dan tunda take gidan shekara uku bai taba kiranta ba batamayi tunanin yasan sunanta ba ta xube qasa kanta a sunkuye tace gani ranka shi dade Allah yasa dai lfy? ya gyara tsayuwarsa yana kallonta kafin yace bani ruwa jikinta har kyarma yake ta tashi taje ta kawo masa ruwan ta sunkuya qasa tana jiran ixinin tfy amma ga mamakinta maimakon yasha ruwan sai taga ya juyesu akansa yana maida numfashi da kyar ya jefar da cup din ya fadi yayi ratsaratsa duk sai ta firgita dashi kome k damunsa waya bata masa rai tunda lfy lau yafita daga gidan ya soma safa da marwa xuciyarsa a dagule tunda yake a rayuwarsa wani bai taba cin nasara akansa ba sai yau taya xaace ya xauna ya bata lokacinsa a assignment amma ace wani yafishi da 1mark ko a tarihin rayuwarsa yana sane dacewa ba wanda ya taba wucesa sai wannan karon ya dubeta tana durqushe yace jabo tell me something dat will make me happy (abinka da wanda baiyi boko ba 😁 )sai ta soma bashi haquri a tunaninta tayi wani laifine yace ina mgnr abinda kike min kullum ne idan xnci abinci sai alokacin ta tuna ta gyara xamanta cike da mamaki yau yarima yayi mata mgn mai tsayi chab, wanda kullum mgnrsa baxai wuce uhm ko a'ah ba sai ko alama da hannu ta sadda kai qasa tace wasu mahaukatane su shidda ake ganin sun warke daga hauka dan haka sai shugaban gidan mahaukata ya kirasu don ya gwadasu ya tarasu yayi masu jawabin cewa tunda Allah yasa sun sami sauqi yanxu kowa xai tafi gidansa dayake an xana mota jikin katanga sai yace kowa yaje ya shiga mota akaishi gida ai kuwa suka fara rububi adole motar xasu shiga ta jikin katanga su tafi gida acikinsu akwai wanda yaja ya tsaya bai tafi ba sai shugaban yayi tunanin koshi ya sami lfy ne ya matsa ya tambayesa yaya dai kai bakaje ka shiga mota ba sai wannan mahaukaci ya soma murmushi yana fadin ai kawai kallonsu nake badai ance su shigaba tor ga makullin a hannuna jira nake su gama haukansu inje in bude inyi tfyta😳 😂 jabo na murmushi tana kallon yarima a xatonta wannan xai qayatar dashi ya sanyashi nishadi amma sai tasami akasarin haka ganin hr lokacin fuskarsa a daure take ya qara qawatata da baqin glass ynda ko idanunsa baxaa gani ba yau ana wata ga wata, ta sauke numfashi jikinta a sanyaye ta gyara xamanta hade da lankwashe qafafuwanta tace ranka shi dade akwai Wani Bature ne yazo Nigeria sai Tafiya ta kamashi zuwa Sokoto acikin tawagar da sukazo taryarsa harda wani SSS Bagoburi.Bayan sun gaggaisa sai Bature ya rike hannun bagoburi yana Kallon fuskarsa yana Mamakin Irin Tsagen dake fuskar wannan Bagobirin sai yake tambayarsa. My Friend Did u Fight wit a tiger..? Sai bagobiri cikin fushi yace No I Fight wit Ubanka ne..sai Bature ya sake Kallon Fuskar Bagori yace 'that Ubanka is a very Dangerious Animal. still fuskarsa a murtuqe take yana yatsina fuskarsa alamar yafara qosawa da labaran baiwarsa hauwa jabo batayi sanyi a gwiwa ba ta qara sunkuyarda kanta qasa jikinta hr rawa yake wannan karon tace wani matuqin jirgine aka ciko masa jirgi da mahaukata yana tfy sai mahaukatan suka hargitse da hayaniya acikinsu sai wani mahaukaci ya tsallako inda direban k tuqi yace yallabai jirgi nakeso a koyamin direban ya rasa ya xaiyi da mahaukacin nan ga sauran sunata hayaniya, sai dabara tafadowa driver ya dubi mahaukacin yace xn koyama amma sai kasa wadancan sunyi shiru mahaukacin yatashi ya nufi inda suke baa jima ba jirgin yayi tsit mahaukacin ya dawo inda driver driver yace amma ka kyauta tayaya kasasu sukayi shiru mahaukacin yayi dariya yace ai qofa na bude na korasu waje 😳 🙆 🏻 datagama bashi lbrn sai tayi kasake tana kallonsa ko xaiyi murmushi amma fir yaqi tace ranka shi dade ayimin afuwa yau kam na kasa da alama ranka ya baci sosai ayi haquri [1:01AM, 10/27/2015] Pherty 🎤 👯 : Lokaci daya ya saki murmushi ya juya ya fice dama bai taba xama da damuwa ba axuciyarsa shiyasa yakejin dadin aikin jabo fiye dana sauran maaikatansa dan tana sanyashi nishadi 3⃣5⃣ Da sauri ta isa cikin gidan cike da taqama da qasaita duk bayin dake gaidata ba wanda ta kula hankalinta nakan rumaisa shiyasa tayi sammakon xuwa kai tsaye dakin umma ta nufa a tsatsaye ta gaidata tana tmbyr rumaisa tace tana dakin yayanta tayi shiru tana tunani kullum safiya taxo rumaisa na dakin yayanta tarasa metakeyi acan bata kuma taba bibiyarta can ba sai dai tajirata hrtaxo,sai taji yau tanason xuwa taga me rumaisa keyi acan duk da tanason ganin yayan dan ta dade bata ganshi tun tana qarama sai ta juya ta fita ta nufi sashen datake tunanin nasa ne ta murqa kofar falon ta shiga sanyayyen a.c da qamshin turare mai qamshin gske ya doki ahancin sai taji falon na wani irin qamshin da kamar tasan turaren amma hankalinta ya hana ta gane inda tasan wannan qamshin ta shigo tsakiyar falon tana qare masa kallo, tana kallon yanayin falon da duk abinda ke ciki iri daya ne dana yayanta aliyu illah colour data banbanta sai yanayin tsarin jerin kayan falon da aka qara qayatashi da kayan sarauta amma komai iri dayane Numfashinta na sarqe lokacin da idanuwanta na sauka akan wani qaton tangamemen photonsa, yana sanye da alkyabba fuskarsa a murtuqe idanuwansa boye cikin wani darkspace yayi balain kyau da kwarjini yanda ya daure fuskar ba murmushi alamar jinin sarauta kenan tsoro da firgici qarara yabayyana a fuskarta dai dai lokacin rumaisa ta fito daga dakinsa hannunta dauke da turaren wuta, ta dubi affiya kamar bata cikin hayyacinta tace k affiya lafiyanki qlw kuwa,a firgice ta juyo tana kallonta tace rumaisa kardai wannan shine yaya maina tace shine, wai dan iskanci shine hr ynxu baki sanshiba baki taba ganin hotunansa a palace ba, ta girgixa kanta tana bin sauran hotunan da kallo tace ban taba lura dashi ba [1:10AM, 10/27/2015] Pherty 🎤 👯 : amma kinsan nasanshi na hadu dashi wurare da dama ashe ranar daya toxartani a idon jamaa da gayya kikayi da saninki aka cimin xarafi aka wulaqantani saboda kece kika nuna minshi amma kin cutar dani saboda shi yasanni ni bansanshi ba 3⃣6⃣ sai ga hawaye a idonta sharrrr nan da nan hankalin rumaisa na tashi ta soma rantse rantse tace tayaya xn bari ya wulaqantaki wlhy bai sankiba,baisan kece affiya qanwarsaba,nima ina cike da mamakin lokacin daya tunkaromu da kuma furucin da yayi akanki a idon jamaa, bai bani damar tambayarsa dalili ba cos koda na iso gida yabar garin amma wlhy baisan kece ba dabaxai soma ba nima bansan kinsanshi ba ya ma nake da niyar naje gidanku na tambayeki ta tsaida hawayenta bayan ta xube a lallausan carpet din, itama rumaisa tabita suka xauna tace tor wlhy baxan aureshi ba bana sonsa mugune na fasa auren rumaisa tace wai meke tsakaninkune ina kukasan juna nan affiya ta somayi mata bayanin tun farkon haduwarsu da marin dayayi mata har kawo ynxu da irin nemansa da take, ta qarasa mgnr tana kuka [8:29AM, 10/27/2015] Pherty 🎤 👯 : tace wlhy baxan aureshi ba rumaisa tace kidaina fadar haka kinsan baxa'a fasaba dan da xaa fasa da tun xuwansa anfasa duk da baisan kece ba bayanda baayi dashiba akan mgnr aurenku yace bayaso kuma sarki ya tabbata masa mgnr aure baxaa fasaba ta share hawayen fuskarta tace ni nace bana sonsa ba kuma xn auresa ba mugune kigayamin idan yaya aliyu ya taba dukanki tace kefa affiya bakida hankali wlhy na tabbata bakisan mekikeyiba saboda ya mareki xakice shi mugune ba yayanki bane bai isa ya dakeki bane kome? ni ingayamiki ko yaya aliyu ya dakeni baxan damu ba saboda ni dashi duk dayane jini dayane kallo daya nake masa da yaya maina ta dubeta a harxuqe 3⃣7⃣ tace nice bnda hankali ko xn nuna maki rashin hankalina na qara cewa bana sonshi baxan aureshiba rumaisa ta tabe bakinta tana fadin karkiso shi mana,miliyoyinki naso basu samu ba, wadanda ma suka fiki sun kawo kansu bai kula ba kuma ke kanki shaidace akan har ya'yan sarauta da mulki duk ankawo a gidan ba wadda ya xaba saboda baya raayinsu kema ai bacewa yayi yana sonki ba, ba kuma neman kai mukeyi dashi ba ballantana kiriqa tada jijiyoyi kice bakyayi kina goranta masa ta qara harxuqa idanunta kyam akan nata tace kigayamin shi yaya aliyu neman kai ake dashine ko kuma angayamiki shima ganinki yayi yace yanaso ba liqa masa k akayiba,idan ba neman kai ake dashiba tor a fasa auren nace banyi ko dolene? tace oho wannan damuwarkine sai kije kigayawa sarki haka bani xaki tasa gaba da fada ba [9:36AM, 10/27/2015] Pherty 🎤 👯 : amma kinsan yaya maina akwai farin jini kuma ga SARAUTA! tace haka yaya aliyu akwai kwarjini gun yan mata ga kuma MULKI rumaisa ta sake kallonta karo na biyu tace yaya maina dan sarkine jinin sarauta da kowacce macce ke burin ta mallaka maiji da sarauta da qasaita, affiya ta gyara tsayuwarta hannunta a qugunta idanunta tsam akan nata tace yaya aliyu dan president ne maijida da kudi da mulki rumaisa tace amma kinsan yaya aiman mutum ne kyakkyawa mai farinjini taqama ilimi kigayamin dame yayanki yafi nawa MULKI KO SARAUTA? MULKI! ta bata amsa kuma kema kinsan yaya aliyu kyakkyawan gaskene mai kwarjini tarbiya hankali da kuma biyayya shiru duk sunkayi na dan wani lokaci kafin su sauke ajiyar xuciya suka dauke dubansu ga junansu rumaisa tace nidai inason yaya aliyu tamkar raina kema kiso yaya aiman yanada sauqin kai kuma xai soki affiya ta yatsina fuskarta tana tabe bakinta a ranta taji dadin haka domin aurenta dashi wata damace ta samu daxata rama abinda yayi mata xata banbance masa tsakanin MULKI DA SARAUTA, tace na jahilci kaina rumaisa,lokacin da yake cemin sarautar mera ban taba kawo abba yake nufi ba saboda nasan sarautarmu ta gusau ce, na dauka sarautar garin merah yake nufi kinsan nan abuja wurin kowane akwai mutane iri iri daga wurare daban daban sannan mera kuma laqamin abba ne shiyasa na dauka tamkar sarkin garin mera yake nufi rumaisa ta girgixa kanta tace mera laqamin abbane sannan sarautar mu nakan gaba akanta garin mera affiya ta jinjina kanta tace mekike yi a dakinsa kullum sai naxo na gyara masa bai amince da bayi ko kuyangu su shigo masa sasheba saboda yana kyankyaminsu nikawai yaba umarni na riqa gyara masa affiya ta cije lebbanta tana qara bin falon da kallo aranta tana qiyasta irin xaman da xasuyi na kowa ya isa da kansa kuma kowa naji da MULKI DA SARAUTA tace muje rumaa inason yin brkfst suka fita a tare.... 📝 Hausa novel📚 [9:43AM, 2/26/2016] Bebinga: [6:29PM, 10/29/2015] Pherty 🎤 👯 : 3⃣8⃣MULKI KO SARAUTA💞 Na fertymerh xarah 💞 Ranar asabar data kasance babbar rana a birnin abuja ranar da akayi gaggarumin biki daya bar kundin tarihi a abuja ranace da jama'a talakkawa da manyan masu kudin nigeria suka halarta a abuja domin daurin auren ALIYU DA RUMAISA'U, AIMAN DA AFFIYA auren da akayishi bada sanin yarima ba gashi amarya bata son ango😁 ranar dinner mai martaba da president sun dauki nauyin talakka hamsin bayan yan uwa da abokan arxiki xuwa qasar cairo kwanansu biyu acan suka dira malesia yin mothers day a mumbai sukayi party qawaye👯👯👯kafin su dawo nigeria inda suka iyarda sauran event din amare sunyi kyau sunyi fes kamar ka sace ka gudu saboda haduwar da sukayi sai dai ba ango daya😒 kwanansu biyar a nigeria mai martaba ya turo da manyan motoci a dauki amarya kamar yanda president ya tura nashi manyan motoci a dauko a amarya kowanen su naji da MULKI DA SARAUTA affiya tayi kuka sosai musamman da baffanta ya kirata yayi mata nasihohi akan xamantakewar aure ya qara da fada mata yanxu bada MULKI xatayi taqama ba komai nata ya canxa ya koma SARAUTA, ta girgixa kanta tana hawaye nooooooo baffa MULKI ne nawa ba SARAUTA ba, yan uwa nane amma al'adarsu daban tamu daban, [10:38AM, 10/30/2015] Pherty🎤👯: duk inda na sami kaine no matter hw i am i will be proud of it, inason mulki sosai baffa yayi murmushi yace tor shikenan auta amma itama sarautar inason ki koyi al'adarsu tace olryt baffa i will try my best....... cikin lokaci qanqani aka shiryata cikin manyan kayan sarauta ta dora alkyabba akai kusan shigarsu iri daya da rumaisa, kan aka wuce da ita itama rumaisa aka wuce da ita gidanta dake gab dana president, qaton gidane mai kyan gske tun daga waje hr ciki dukiyace narke ko motocin dake gidan a qalla xasu kai goma koma fiye da hakan,qaramar cikinsu itace xata kai miliyan biyar da rabi.... 3⃣9⃣ Gidane qaton gaske qasaitaccen gida daya amsa sunansa gida, an xuba masa kayan alatu na qasar mouritania ciki da waje kamar aljannar duniya duk iri dayane dana aliyu ba abinda aka banbanta ciki da waje illah na aliyu na kusa dana president shi kuma aiman nashi na cikin masarautar gidansu an qara qayatashi da kayan sarauta, bayan kayan sarauta dake gidan aiman ba abinda aka banbantasu koda da tsinke ne tana xaune tasha lullubi hjy hadixa(abokiyar xaman mmn aiman)ta shigo ta xauna a kusa da affiya tare da yaye mata lullubin dake kanta tace tubarakallah autar ammi, yau kinfita daban kinyi kyau kamar bake ba naga hr kinason kifi yarona yarima affiya na murmushi take kallonta tace ynxu xaki fara damuna momy duk naxo gidannan sai kince yaronki yafini kyau shiyasa ma nadaina xuwa sashenki qasaitaccen murmushi tayi tana kallon affiya tace qarya xn miki ne gsky nake fada miki yarima yafiki kyau da aji.......nan da nan ta tunxuro bakinta sai ga hawaye na xubo mata ta soma kiciniyar cire alkyabbar jikinta momy ta riqeta tana dry tace wasa nake maki ai kyau mace daban yake dana namiji ballantana ma kinfisa kyau dadina dake saurin fushi amma ki tsaya xamuyi mgn mai muhimmanci ynxu tace tor momy gayamin ina jinki ta tashi batare da tayi mgn ba ta fita sai gata ta dawo ta xauna matane suka shigo falon cikin layi kansu a qasa da alama bayine kowacce na sanye da wani yadi mai dankaren kyau ga taushi duk kusan iri dayane dogayen rigunane yan kunnensu da sarqoqinsu da awarwaronsu ma duk iri dayane kuma xubin sarauta lokaci daya duk suka xube qasa suna kwasar gaisuwa [11:49AM, 10/30/2015] Pherty🎤👯: momy ta dubeta wannan karon fuskarta ba alamar wasa tace ynxu kintashi daga affiya kin koma GIMBIYA duk wadannan da kike gani bayinkine kuma kowacce xn gayamaki sunanta da aikinta 4⃣0⃣ a yatsine affiya k kallonsu kafin ta dauke kanta garesu tana kallon momy momy tace wadannan guda biyar din masu kula da qirkin kine,kausar, m.shakur, humaida, sirdee, sally wadannan kuma masu kula da kayan sawarkine chuchu,teemah, baby aysher, bena,na'imatu da atee sai wadannan masu kula da gyaran gashinki, yar baqa,mahasin, hafsisi, madugu an nusee wadannan kuma masu yi maki kwalliyane, xarah dange, baby bello, serdiya, miss aysher an mis amirah sai wadannan masu yankar maki qumba halamcy,khairiya,dota gimba,fido, dota samha,beebelo, an xee rogo inaji suke nan ne, sai wadancan xubin da kike gani wadanda kayan sawarsu dabanne da sauran duka gayyar yan hausa novel ne both 1,2&3 sune masu tayaki hira duk lokacin da kike ra'ayi nasan halinki ba hayaniya kike so ba ga kuma auta firdausi xata tayaki barci kafin yayanku ya dawo a hankali ta sauke nauyayyen numfashi tana kallonta kafin tace tnx cwt momy amma anya masu girkinnan sun iya kuwa kinsanni da abinci tace ina tunanin sun iya idan ma basu iyaba xaa canxa maki wasu, kinyi missing yarima ya rigaki samun gwanar girki m.jabo so duk inda xaije da ita yake xuwa acewar yanajin dadin aikinta duk cikin bayinsa ta tabe bakinta jin an ambaci yarima ta yatsina fuskarta tace bakomai xn gwada inga wadannan momy tace yauwa akwai wasu securities goma da baffanki ya bayar masu kula da duk inda xakije hakama ya bawa rumaisa nata ynxu haka suna gidanta maimartaba yabawa kowacenku miliyan goma goma da gidaje biyu tareda bayi goma maxa ga kowaccenku, ta miqo makullin mota ta bata tace baxan gayamaki ko wacce irin motace ba sai gobe xaki ganta iri daya da rumaisa kala ce banbanci da fatar xaki xamo mai biyayyar aurenki ki kuma riqe amanar aurenki tayi shiru tana tunani koda take gidan ubanta batasami wannan gatanba ace komai xatayi tanada mai yi mata numfashine kawai xatayi da kanta,ashe da gskyr yarima da yace komai xaa iya masa numfashine kawai ubansa ya amince yayi a doron qasa, chab wani abu sai SARAUTA amma bata yarda tafi MULKI ba. tace momy meyasa umma bataxo bane tace yau umma tana kunyar yar'ta tunda taxamo surukar dan farin affiya tayi murmushi kawai tana kallon qasa kafin kwallah ta taru a idonta ta dubi momy tace insha Allah momy xnyi biyayya dan farantawa iyayenmu kamar yanda suka farantamin duk da bana sonsa baya sona xn kwatanta momy tace affiya baki fahimci aiman bane dan baki xauna dashiba kuma baki sanshiba idan ya dawo xaku fahimci juna tunda ke jininsa ce ta tabe bakinta a ranta tace bana burin mu fahimci juna hr ynxu baxan kyaleshi ba sai na rama sai yaxama 3-3 baxan yrda yafi qarfin MULKI na ba a fili kuma murmushi tayi tace tor shikenan momy momy ta tashi ta fice da sauran bayi kafin masu kula da suturarta suka soma qoqarin ganin ta sauya kayanta xuwa na barci kana suka bar dakin suna mai mata fatan alheri atare suka kwanta da firdausi bayan doguwar hirar da sunkayi kafin suyi barci Asuba ta gari! GIMBIYA AFFIYA🙋🏻 📝Hausa novel 📚 [9:43AM, 2/26/2016] Bebinga: [2:59PM, 10/30/2015] Pherty🎤👯: 4⃣1⃣MULKI KO SARAUTA💞 Na fertymerh xarah💞 A hankali yake kallonsa cike da nutsuwa da mamaki yace prince mace fa nagani a gidanka,me haka ke nufi ya dan dubesa kafin ya kauda kansa gefe cikin rashin sanin wace macce yake mgn yace macce as in how kuma a ina yace nabila da ka ajiye anan gidan ba mace bace ko matarkace yayi shiru yana naxarin mgn hrga Allah ya manta datana gidan tuni ya shafe shafinta yace matata fa kace bilal,ynxu koni maxinacine xn rasa wacce xn aura sai wannan bullshit hr kake laqabamin ita a matata bilal yaja dogon tsaki sanin halin aminin nasa ya tashi batare da yayi mgn ba ya nufi dakin da yaga nabila take tana kwance tana game da wayarta ya shigo cikin tsawa yace keeeee! sai data tsorata fuska a daure yake kallonta qasa da sama yana yatsina fuskarsa yace amma kinyi kyan dan maciji wai ke musulmace kuwa? batayi mamakin jin kalamansa ba tunda tasan bilal tasan waye shi abokin yarima ne halinsu yaxo daya wurin wulaqanta mutum sai dai yarima yafishi aji da miskilance, wannan haka yake ko acikin maxa ba kowa yarima yake kulawa ba ba kowa yakewa mgn ba kuma bada kowa yake mu'amala ba sai wanda xuciyarsa taso tor ballantana wata mace da bata gabansa, matan dayake gani a banxa musamman ma matan arewa idanunta kyam anasa tace ko meye ruwanka dani da xaka tasani da tambaya kamar ubana yace tor uban waye ya kawo ki gidannan tunda nan gidan bana ubanki bane idanunta nayi jawur dai dai lokacin aiman ya iso wurin ta dubeshi idanunta sun ciko da kwallah tana tunani ko xaice wani abu akan abinda bilal k mata ne ga mamakinta space dinsa yasa yana yatsina fuskarsa yake kallonsa yace enough pls nan ba gidan haya bane,duk kufita can waje kuna damuna da hayaniya surutun ku ya hanamin kallon ball(ya fada cikin tsawa) nan take ta qara shaqa ta qulu shi kuwa bilal ko ajikinsa tunda yasan halin frnd dinsa kowaye kai inya tashi tsinka ka agaban kowa xai tsinkaka wulaqancin dama yafi wannan xai iyama amma yaji dadin halin ko in kula da ya nuna akan nabila, aiman yace i hope da mutane nake mgn kunmin tsaye kuna kallona nace ku fita can waje bama anan harabar gidan ba can outside gate bana son jin muryar ko dayanku umarni nake baku ynxu bilal yace cikin tsawa sai da aiman ya toshe kunnuwansa da hannunsa biyu yace bakiji bane akace kifita, taja dogon tsaki hade da jan jakarta ta hararesa ta fice tana qunquni,ya juya yana kallon yarima yace kai kafiye sanyin rai baka ajiye komai ba sai baqin mulki da qasaita,taya xaka ajiye mace a gidanka ba muharramarka ba idan kana tunanin nan rayuwar turawace ba wanda ya damu da wani baka tsoron wani na gida yaxo ya sameta kamar irin xiyarar baxata dinda mai martaba ya taba yima kwanankin baya ,idan yaxo ya sameta kace me? 4⃣2⃣ yaja hannunsa suka fito yana fadin hakane fa bilal sam hankalina da tunanina bai kawomin wannan ba tunda nadawo na sameta nan ban sake ganinta ba na dauka bata gidan kuma bndamu dana duba ba cos kasan bana bawa kowa lokacina koda kadan ne,sannan girmana ya fadi in tsaya neman mace a gida amma ai kasan ni bana xina ko? [3:46PM, 10/30/2015] Pherty🎤👯: Bilal yaja dogon tsaki,aiman yasa hannu ya mintsini bakinsa yace kadaina bilal kasan bana son tsaki hr cikin kaina nakejinsa bilal yajaye hannunsa ya sake tsaki a karo na biyu yace idan ni nasani sai akacema kowa yasan baka xina ne ko frnds dinmu suka xo gidannan suka sameta sai an xargeku, amma wlhy na sake ganinta anan gidan sai na ballata ko nasa securities su mata shegen duka inga uban da ya tsaya mata Aiman ya yatsina fuskarsa hade da da kafadunsa alamar ko ajikinsa kaike bata ranka akan mace yace wannan damuwar kane bnda case da mace kadaina min mgnr banaso bilal yayi kwafa xai fice yace ka shirya muje skul inason naje library kan wannan assignment bilal ya bata fuska baxan jeba aiman yace tor shikenan ka xauna ai kaima bakayi ba lokacin da xakaje nima baxan jeba bilal ya haura sama yana fadin yaushe xakayi assignment ka tasa kwallo a gabanka kai kullum bakada lokacin kanka sai karatu ko kaine qudan boko ai ya isa, amma dai jirani in sauko ynxu aiman ya juya ya fice yana fadin minti biyar ka qara baxaka sameni ba yace tor...... *BAYAN WATA BIYU* Kyakkyawan saurayine dan kimamin shekara ashirin

Chapter 3 of 7