Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 10
tana yiwa baffa magana idan be gadama ba cewa zai yi ta dawo ba zai iya ba. Ramsi ce ta fito ɗaure da towel zama tayi tace '' na lura da ku kwana biyun nan akwai abin da kuke boye min sai na bar guri ku dinga zance ƙasa ƙasa me yake faruwa ne ?.'' tashi mardiyya ta yi tace '' babu komai kawai tsarguwa kike yi.'' ramsi tace '' zancen bikin naki ne ba kya so ayi dani?.'' dariya tayi sosai tace '' bikina kuma? Ramsi a bikina kece sahun gaba.'' tashi ramsi tayi tana cewa Allah ya saka haka. suhaila tace '' amin.'' Wannan kenan. A.E.M BIRMU HOSPITAL Fitowa yayi daga theatre room cire Hand glove yayi, ya saka a shara kai tsaya office ɗin sa ya wuce wani farin kati da rubutu golding colour a jiki ya saka a jikin kofar , juyi ta dinga yi sannan ta kawo green ɗin danja sannan ta buɗe shiga yayi ta rufe kanta, zama yayi akan kujera yana daukan wayar sa , da take kan table miss Call ya tarar da dama ganin kiran mukhtar yafi na kowa yawa . danna number yayi bugu ɗaya biyu ya ɗaga sallama mukhtar yayi, mai . ASIM ya amsa yana cewa mukhtar ina theatre room ne jiya bana faɗa maka ba ina da operation na gaggawa ba. Mukhtar yace '' eh anyi haka daman na kira ka ne ka jawa afiyaah kunne ta , takurawa wannan yarinyar ɗazu fa har sai da muka tafi police station afiyaah ta faɗa mata bakar magana ta dauki dutsai ta buga a motar ta , glass ɗin motar ya fashe kanta da bakin ta , ya fashe.'' Ran asim ne ya ɓaci yace '' mukhtar wacce yarinya ce tayi wa afiyaah haka ?.'' MARDIYYAH ce. Mukhtar ya bashi amsa. asim yace '' dafa tan dai afiyaah ta karya mata kafafuwa?.'' Mukhtar yace '' haba asim me ya saka soyayyah ta rufe maka ido, ina nuna maka hanya kana rintsai ido? baka ga abin da afiyaaaah tayi mata ba?.'' kaga ni bama wannan ba kasan mun gama magana to tace min wai akwai wanda yake son ta dan haka dole sai anyi shaɗi ta dai fadi wasu maganganu kasan bana jin fulatanci to ban gane abin da take faɗa ba. da sauri mukhtar ya cire wayar sa , daga kan kunnen sa , sai kuma ya mayar yace '' asim shaɗi fa kace ?.'' Asim yace '' mukhtar zan faɗa maka karya ne?.'' Mukhtar yace '' a'a amma asim kai ne ya saka ka amince da kayi mata wani wayon mana ni gwara a daura auren daga baya iyayen ta , sai su sani amma kamar kai da fuskarka ba boyayyiya bace za kayi shadi.'' yar dariyar rainin hankali asim yayi yace '' ta dauke nima rago kenan ta raina ni mukhtar ina da fa kudi kuma kasan kudi ba yaren da basa ji, zan bawa saurayin ta ta hakura yabar min ita.'' Uhmm uhmm asim kasan me ake nufi da bararo (bararoji ) ? Wallahi Allah ba jinsin da yakai su taurin kai da kafiya da tsayawa akan ra'ayi ɗaya karka taro abin da zai fi karfin ka ba ko wanne yare, kudi yake ji ba wallahi ko anan akwai wa'yanda kudin ka ba abin da za su yi musu kai duk talaucin su asim baka gogu da jama'a ba , rayuwar da kayi rayuwar jin dad'i ce baka san wannan hali al'umma suke ciki ba ka tashi girman turai ka dawo nan ka buɗe asibiti ka fara aiki a jami'a dan haka , duk a bin da na faɗa maka kayi shiru kawai. ASIM yace '' kaga kan ka ake ji yanzu gida zan tafi gwara ayi ta da zafi zafi zan fadawa mommy kaga sati na gaba tafiyar ta america ta fadawa su kahu sunusi suje sune mo min auren ta kai shadin ma zan iya tun da afiyaaaah ta faɗa min amfanin auren ta.'' Mukhtar yace '' ashe itama ta gano amfanin auren ta?.'' Yayi hakane domin ya lura asim baya cikin hayyacin sa kai wannan AFIYAH Ubangiji Allah ya kawo silar rabuwar su , ya raya wannan a cikin zuciyar'sa ASIM yace '' eh wallahi.'' Sallama suka yi ya kashe wayar. shiga toilet yayi, ya wanke hannun sa ya fito haɗa kayan sa yayi, ya fita daga office ɗin kai tsaye inda ya ajiye motar sa ya nufa, buɗe wa yayi ya shiga. cikin kwanciyar hankali yake tuki ba wani abin da yake damun da har ya isa gidan su horn yayi me gadi ya buɗe mai. tura hancin motar sa yayi ciki har ya isa parking space. parking yayi, ya fito ganin motar aunty jidda yasan boom ta zo baya jin tsoran kowa amma ita da kahu sunusi za su iya cewa basu yarda ba fitowa yayi ya dauki brief case ɗin'sa ya rufe kofar motar 'tasa. cikin izza da katsai ta haka yake tafiyar sa, komai nasa abin sha'awa ne kofar da zata sada shi da parlour mommy ya nufa. shiga yayi bakin sa , dauke da sallama aunty jidda ta ture dauri gaban goshi da sauri tace '' yauwa zo idan ita uwar taka , ta zuba maka ido to mu ba zamu zuba maka ido ba wallahi nan ba DUBAI bace da zata barka sangameme dakai babu aure.'' ASIM ransa ne ya ɓaci tun yana yaro ya ƙi su aunty jidda saboda a gaban kowa cin mutuncin mahaifiyar sa, suke ya rasa wannan ɗabi'ar tasu da mahaifinsa ya faɗi ya mutu tamkar an tunzura su, suka ƙara ƙarfin ci mata mutunci musamman ma kahu sani da yace zai auri mommy ta ƙi yarda shikkenan ta ƙara bakin jini a gurin su. Littafi fa ya kusan karewa free page me kuke jura ku hanzarta biyan kudi kar ayi babu ku. Amina alhasan Muhammad opay 1k 8141785374 Ku turo da shedar biya ta wannan number 08141785374. *JAMI'A* 📢 Shin kana son koyon yadda ake ƙirƙirar Website ko App da kanka? 🖥️ Tare da waya ko computer zaka iya fara gina naka shafin yanar gizo (website) ko application! 👨‍💻 A cikin wannan Group ɗinmu, zaka koyi: ✅ Yadda ake gina website daga farko har ƙarshe ✅ Yadda ake haɗa website da App ✅ Yadda zaka iya amfani da skill ɗinka ka fara samun kuɗi online 📌 Abu mafi kyau shi ne duk darasin a Hausa zai kasance, domin kowa ya iya fahimta cikin sauƙi. 👉 Ka shiga yanzu kafin mu fara darussa masu muhimmanci. 🟢 Link na group: [https://chat.whatsapp.com/FTmYGbIya5J490GLcZmdY4?mode=ems_copy_t Ina hajjiyo da yan kwalisa to ku garzayo OUMYASMEEN COLLECTION domin samun kaya na kerewa Sa'a ki zama fitila wajen oga ba abin da bana siyarwa cikin fara shi me sauki https://chat.whatsapp.com/DSd6g96hO2F41IG6k43rEl?mode=ems_copy_t *Episode 8* Rintsai ido yayi yana jin maganar aunty jidda nayi mai ɗaci a zuciya cire takalmin'sa yayi ya ajiye shi a gefe. Aunty jidda ta ci gaba da cewa ka raina mutane ko wacce mace aka kawo maka kace a'a yan mata nawa na kawo maka cikin gidan nan kace basu yi maka ba , ko dan kun ga ba ran mahaifin ka ne ? to wallahi Allah ba zan bar gidan nan ba sai an tsayar da maganar auren ka , da rafi'a yarinyar kirki. da sauri Asim ya ɗago idanuwansa tab lallai aikuwa zata dade a zaune a cikin gidan nan ya raya wannan a cikin zuciyar sa afili kuwa nunawa yayi bema san ina maganar'ta ta dosa ba. duk da ƙafar'sa a cikin safa take so sai laushin carpet din parlour yake jin sa ƙafafuwan sa sun nutsu cikin gashin carpet ɗin. ɗursawa yayi yace '' barka da zuwa aunty.'' cikin bala'i aunty jidda tace '' bazan amsa ba ungo dan uwar ka , ni sa'ar wasan kace ina magana kama nuna baka san me nake faɗa ba wallahi Allah asim ka kiyaye ni ?.'' ASIM ɗago limshasshshun idanuwansa yayi masu kama da jin bacci yace '' mommy barka da wannan lokaci ya jikin naki ?.'' salati aunty jidda ta saki tace '' aunty Zainab a gaban ki ɗanki yake hulakanta ni? ina magana ya share ni.'' Mommy kallon Asim tayi ranta a ɓace tace '' jidda ba ruwana maganar ku ce ke dashi Allah ya sani ko kafin ki zo mun yi wannan maganar dashi ya kuma ce min ya sami wacce yake so ranar Litinin ma sai da yaje gurin ta zance.'' sakar baki tayi rafi'a tana jin haka ta rushe da kuka, aunty jidda tace '' yi shiru badai mune dangin ubansa ba muga shegen da zai ɗaura mai aure.'' Asim tashi yayi ransa a ɓace aunty jidda tace '' shege yaro taurin kai kamar jinjirin jaki, anya kuwa yaron nan yana da lafiya aunty Zainab mutum yakai kamar sa babu aure, ni wannan azumin da yake yi bana kau da idon mutane ne ba dan Wallahi idan ya biyo zuri'ar mu da tuni yayi aure domin kaf mazan zuri'ar mu harijai ne ke kanki sheda ce kinsan waye uban sa ko kuma aljana ce ta aure shi ne ni ban sani ba ....?.'' Asim da maganar ta , taso ta bashi dariya wai harijai saka takalmin da yayi yabi ta wata kofa ya wuce party din'sa Mommy kauda kan'ta tayi daga kallon jidda saboda idon ta , ya kawo kwallah sharewa tayi, Allah sarki rayuwa mutuwa me tonan asiri ba ranar da zata fito bata tuna da mahaifin su asim ba. Adiyan kallon mommy tayi tace '' na kaiwa yaya abinci ?.'' Mommy kallon autar tata tayi, da cikin adiyan EL'BASHIR ya mutu saurin kau da wannan tunani tayi tace '' to Ubangiji Allah ya kawo mafita.'' ta bawa aunty jidda amsa. aunty jidda ɗora kafa ɗaya kan ɗaya tayi tace '' amin ba zai yiwu ba Bara na kirawo yaya sani itama wannan yarinyar a gidan mijin ta zata ƙarasa karatu haka kurum duk yara sun balaga babu zancen aure sai bakar hakidar boko a cikin zuciyar su.'' da sauri mommy ta kalle ta sai kuma ta kalli adiyan tace '' dauki abincin sa ki kai mai.'' to tace , ta tashi tabar gurin mommy sai da ta , tabbatar tabar gurin ta kalli cikin idon aunty jidda tace '' ban ga uban da ya isa ya aurar min da ya'ta ba shekarar ta nawa ma idan kuma da wanda ya zauna ya haifar min ita sai naji labari adiyan ɗiyata ce takarda har yanzu tana nan , duk wanda yayi yunkurin aikata wani abu ya jishi a prison .'' tana kaiwa nan ta tashi ta dauki sandan'ta , ta fara tafiya. iyeee tofa ashe daman baki da mutunci rafi'a ni matar dan uwana take cewa Zata kai ni prison kan uban can lallai bata san suwa ye dangin MANSUR TURAI Bayahude ba ni da ita shege ka fasa dole yarinyar nan ta aure *NA'EEM* bara na kira yaya sani ashe bakim cikin haɗa zuri'a take damu yadda muka so hada zumunci ba uban da ya isa yace a'a ai wannan sai yan uban mu suyi mana dariya ni dai ni na haife ki share hawayen ki dan uban sa sai ya aure ki. share hawayen ta , tayi zuciyar ta nayi mata suya. Aunty jidda ƙara turo ɗaurin'ta tayi gaban goshi ta dauko wayar ta ta suma laluban number Alhaji sani uban tujara da yake da wannan sunan tayi saving number sa. ɗanna mai kira tayi tana ci gaba da girgiza kafar'ta. Bugu ɗaya biyu ya ɗauka yana cewa kulu kefa shegiyar yarinyar ce ba'a jin ki ko ganin ki sai ƙura ta , tashi yau wanne fadan kuma kika janyi kina police station ne to wallahi bani da kudin belin ki ni na gaji da wannan halin naki kulu bakya tsayawa iya albashin ki sai kin dinga cin uban rance ke ranki ɗaya ba abin da mijin ki baya ajiye miki ace miliyan ɗaya tayi miki kaɗan sai kin haɗa da bashi. dafa kan'ta tayi tace '' yaya sani ni ba , bashin da naci saboda ka zayi zaton sabgar kudi ce , shi ya saka kake min wannan fadan ni yaushe rabon da nace maka matsala ta samu sau daya ba naci bashi har aka kai ni gurin yan sanda amma ga yadda kake magana salon ka jamin raini gurin matar ka ga wannan matar ma ta riga ta ga makwanci na ina da kai a gari har zainan zata ce min bata ga uban da ya isa yayi wa yar ta aure yanzu ba dan na faɗa mata NA'EEM ɗan mu yana son yar'ta.'' Alhaji sani yace '' kulu kina ina ?.'' cikin jin daɗin tace '' gidan yaya mana.'' ''Alhaji sani,, yace '' yice ko kin kifa mata maro nifa wallahi wannan matar ina gab da fyato'ta domin wallahi ta kusan kawo ni bango gani nan zuwa.'' Ƙit ya kashe wayar dad'i ne ya kama ta , ta cire wayar daga kunnen ta tace '' kin ga ko abin da nake faɗa miki karki yi mamaki zuwa gobe a ɗaura muku aure.'' wani dad'i ne ya kama rafi'a kwantar da kan'ta tayi a cinyar mahaifiyar ta , tace '' Allah ya amince kinga dole yayi ya gaji ya fara sona.'' hnmmm kedai a ɗaura auren komai zai zo mana da sauki. Cewar aunty jidda. ★★★ Bangaren ASIM kuwa yana shiga ya kulle kofar sa , ransa duk a ɓace kasa yin komai yayi, kowa na dangin mahaifin su yana son mahaifiyar su basu da wani kalubale da ya huce kahu sani sai aunty jidda mutum ɗaya ne yake taka musu burki kahu sunusi wanda yake bin mahaifin'su wayar sa ya ciro a aljihu ya danna mai kira. ringing ɗaya ya dauka cikin girammawa asim ya gaishe shi Kahu sunusi yace '' lafiya qalau alhamdulillah yakuke kai da yan uwan naka ya jikin mahaifiyar ku?.'' Asim yace '' alhamdulillah kowa yana lafiya qalau.'' Kahu sunusi yace '' yice ko ba wata matsala ? domin naji labari kulu tazo ko daman baka kira ni ba zan kira ka karka ɓoye min komai nasan halin kulu ba son zaman lafiya take ba.'' ASIM yace '' tazo ne akan maganar aure na , ni yanzu na samu wacce zan aura amma yar kasar mali ce ta bani address din gidan iyayen ta daliba ta ce .'' Cikin jin dadi kahu sunusi yace '' Masha Allah turo min address din'ta zamu yi bincike kafin mu je.'' to yace sannan sukai sallama, ajiye wayar sa yayi tashi zai yi sai kuma yaji anmai knocking. tsaki yaja yace '' waye?.''' Adiyan tace '' nice yaya abinci na kawo maka.'' adeeyaaan bana ci ku kai wa masu gadi, kar ki sake na fito naga baki kai musu ba , ranki sai ya ɓaci. adiyan turo baki tayi tace '' yaya daga aiki fa ka dawo nasan baka cin abincin restaurant idan bana gida ba Please kai hakuri kaci karka sauke fushin ka akan abinci.'' idon sane yayi ja hatta jijiyoyin huyansa da na kansa sun fito raɗa raɗa yace '' nace ki tafi bana so...'' tasan halin sa , sarai zai iya mammake'ta barin idan ransa ya ɓaci da sauri ta dauki basket food ɗin da ta ajiye a ƙasa ta ta fara tafiya, bibbiyu uku uku haka ta dinga haɗa staircase tana sauka ko kallon inda aunty jidda. take ba tayi ba , ta fita gurin masu yi musu wanki da guga takai musu. godiya suka yi mata suka amsa bakin su a washe. da gudu ta ƙarasa gurin aneesah da take fitowa daga mota rungume'ta, tayi aneesah tace '' ya jikin mommy take ?.'' adiyan tace '' da sauki wallahi .'' kallon motar asim tayi tace '' yaya asim ya dawo gida?.'' Adiyan ta cika ta , tana cewa eh ya dawo. Aneesah tace '' yauwa kinsan me gobe da wuri zamu tashi muyi mai breakfast.'' da sauri aneesah ta kalle ta , tace '' sister aneesah daman kin iya girki...?.'' ke koya nayi muje ciki ko?'' ko order za mu yi ne ?'' fara tafiya suke yi anisa tace '' a'a mu dai yi mai.'' to kinga ma na dauko video kala kala na girki. Aneesah ta fadi haka tana rike hannun adiyan. dariya adiyan tayi tace '' hmmm Allah ya kyauta.'' Amin ya Allah ta faɗa tana shiga cikin parlour da sauri aneesa ta , matsa sakamakon ji da tayi an buge ta kahu sani ne hannun malin malin sa a sake yana tafiya kamar zai tashi sama. cikin hargagi yace '' zainab zainab zainab Wallahi baki isa ba ki raba zumuncin Allah yau dole a daura auren nan tun da ke dai ba yar'mutunci bace..'' Mommy da sauri ta fito yanke jiki tayi ta fadi da sauri adiyan ta saka kuka haka ma aneesa sukai kan'ta. Rafi'a da sauri ta shiga kitchen ta buɗe fridge ta dauko robar ruwa me uban sanyi a guje ta fito ko rufe fridge din ba tayi ba ta buɗe robar ruwan tayi ta zuba a fuskar mommy atishawa tayi ta dinga jera ta , Alhaji sani gyara zaman malin malin ɗin'sa yayi yace '' uwar bakin hali kinsan wannan shure shuren ba tsoratar da ni da zai yi aure ne ba fashi ya'ya namu ne ba naki ba..'' mommy cikin danne zuciyar tace '' sannu da zuwa.'' tunda ko ba komai, yana matsayin uban ya'yan ta. zama yayi akan kujera yana cewa ke kulu wanne lokaci kika saka ne ?.'' cikin daure fuska ya faɗi haka. Adiyan har yanzu bata dena kuka ba , kama mommy tayi, ta tashi tsaye hawa kan kujera tayi tana mai da numfashi aneesa kuwa ki tayi kamar ta fasawa kahu sani kai . Aunty jidda tace '' aje a kirawo wancan uban taurin kai din.'' hannun babbar rigar'sa ya gyara yace '' barni da shege shi ƙaramin ƙwaro ne ai tun ba yau na na faɗa mai haka ke me zabin yan duniya kirawo min asim.'' Ya fadi haka yana kallon tsakiyar idon aneesah. aneesah ranta ne ya ɓaci zubewa tayi a ƙasa ta saki wani irin ihu. da yake tana da aljanu wasu irin sururai ta fara tana nuna kahu sani da hannu. wata dariya ya sheƙe da ita , yace '' aikin banza mu za ayi wa karyar aljanu ke dauko min sanda na ci kuttumar uban su karya nayi ...? jibi kan'ta kamar shekar tsuntsu ga uban faratunan hannun ta kamar mayyar da take shirin cin naman mutun wallahi kulu tir da auren irin zuri'ar su zainab.'' cikin wata iriyar murya tace '' wallahi ka sake ƙara magana sai mun shanye naka baki tas sai mun kwashe maka ya'yan hanji kaga ƙarshen maita dan buhun uban ka dan jakar'uba.'' buɗe baki yayi zai yi magana kamar daga sama yaji an fillamai mari ta hagu ta dama sai da ya yi sujja a ƙasa fuskar sa ta duku da tile habawa ji yayi tamkar an barbaɗa mai barkono..... Aunty jidda tsoro ne ya mamaye ta sai uban zare ido take tamkar ƙibtawar ido haka abin nan ya faru da sani bude baki tayi za , tayi magana taji.... Amina alhasan Muhammad opay 1k 8141785374 domin turo da shedar biya ku ta wannan number. 08141785374 Yan niger 1000fcfah jaka ɗaya Ku turo da wannan number 08141785374 *JAMI'A* OUMYASMEEN 🗣️Ina hajjiyo da yan kwalisa to ku garzayo OUMYASMEEN COLLECTION domin samun kaya na kerewa Sa'a ki zama fitila wajen oga ba abin da bana siyarwa cikin fara shi me sauki https://chat.whatsapp.com/DSd6g96hO2F41IG6k43rEl?mode=ems_copy_t *Episode 9* Za, tayi magana taji saukar bulala a gadon bayan'ta ba shiri ta gantsare tare da zuba uban yar ihu kai kace ƙaƙule mata ido ake yi. Mommy tashi tayi hankalin ta a tashi ta kalli adeeyan tace '' adeeyan maza kije ki , kirawo liman innalillahi wa'inna ilaihir raji'un.'' Kahu sani tashi yayi yana cire babbar rigar sa yace '' a'a basai ankai da kiran liman ba tafiya zan yi.'' yana ƙarasa maganar'sa ya ƙara ji an kifa mai mari a guje ya fita yana numfashi domin wannan dukkan da aljanu sukai mai ba ƙaramin shigar'sa yayi ba. yana fita yaci karo da me bawa shukoki ruwa yana riƙe da mesa yana bawa shukoki ruwa rungume shi yayi yana cewa dan girman Allah temaka ka , kashe min wutar da take ci a fuska'ta wallahi ji nake kamar na saki kashi a wando. da sauri ya saki mesar hannun'sa ya ture kahu sani domin a zaton sa hauka ya fara yi ganin hajiya kulu a guje shima ma murtala me bawa shukoki ruwa ya zuba a guje yabar gurin domin yana kyautata zaton duk yadda aka yi akwai abin da yake faruwa idan Alhaji sani ba haukacewa yayi ba. to ba shakka akwai abin da ta ɗimauta shi, shi da hajiya kulu , gwara yayi taƙan'sa. saboda duk abin da ya razana wa'yannan jarabubbun mutanen masifaffu, to shi ne karamar zuciya. zai iya kashe shi ko ya kamu da wani ciwon gwara ya gudu Alhaji sani da yake da shegen taurin kai da kafiya ranar sadakar ukun Alhaji mansur suna cin abinci aka ya dinga bi yana karbar kwano a hannun Mutane yana cewa lada ya isa haka , su da radadin mutuwa Mutane da wage baki suna cin abinci musamman ma wa'yanda yaga basu dashi har da danƙo ya dinga yawo akan mutane yana baza babbar riga. haka kowa ya tashi da bakin cikin Alhaji sani ba irin bakar addu'ar da ba'a yi mai ba. Aunty jidda jidda riko rigar Alhaji sani tayi tace '' yaya ina zaka ?, ka tsaya ni mu tafi.'' a fusace ya doke hannun ta cikin ɓacin rai yace '' kulu ban taba sanin ke yar kutumar uba bace billahilazi sai yau dan bura'uban ki kulu kin san haka gidan nan ya koma kika kira ni ? ni wallahi Allah dama ke suke dinga kifawa mari da , da sauki ban da sha'anin aljanu ni ai dan gayyata ne ke kanwa uwar gami ya kama su kakkarya miki kashi shegiya wallahi kin cuce ni kulu ji nake fuska'ta kamar ana barbaɗa min barkono.'' sakar baki aunty jidda tayi cikin masifa tace, '' haba yaya sani wannan wanne irin cin mutunci ne ? baka ga dukan da sukai min ba ? ni kai na da nasan haka zata faru zan zo ne naga duk wannan bala'in kai , ka jawo mana kace mata me zubin mutanen banza badai asim bane in ma ƙaruwar Chicago zai auro dai-dai da shi ne wallahi ba abin da ya dame ni itama kan'ta rafi'a zance ta fita a sabgar gidan nan tun da dai zainab ta fara yi mana turen aljanu kar wata ran na wayi gari na ganni a tsakanin tukwane rai yayi halin sa aljanu ba jin wuyar kisa suke ba.'' zaro ido kahu sani yayi yace '' kai kulu karuwa fa kika ce a'a wallahi dole na tsaya tsayin daka na zaɓawa asim mace ta gari dan , dan wannan abin ya faru sai nace shikkenan na fita daga sabgar sa , karki manta fa dan uwan mu zamu duba ba waccan yar bakin cikin ba me mugun hali.'' be ƙara'sa zancen sa ba yaji saukar duka a bakin sa da sauri aunty jidda ta ja baya tace '' to haka abin yake ? ,wallahi na tafi gidana daman mijina besan na zo ba yasin ka gudu yaya sani sun fusata ka fusata su.'' ji tayi an ɗuma mata dundun a gadon baya da sauri ta fita a guje tana cewa idi idi zo ka mai dani gida wayyo Allah, Allah na tuba ka yafe min innalillahi wa'inna ilaihir raji'un. Rafi'a da sauri ta fito tana cewa mama mama mama, jin maganar rafi'a da sauri aunty jidda ta shiga mota domin bata ƙaunar abin da zai tsayar da ita , babban burin'ta tabar gidan nan gwara duk maganar da za su yi to fa suyi ta a waje. idi shiga yayi yana cewa Hajiya ko ba da rafi'atu zaki tafi bane ?.'' cikin wahala da ciwon da bayan ta yake mata tace '' a'a idi, idi kayi wa Allah ka fitar dani daga cikin gidan nan yau ina ganin bala'i.'' to yace yana yin horn security ya buɗe mai gate ya fita a guje. da sauri rafi'a ta ja burki tace '' kahu sani dan Allah zan bika ka sauke ni a gida.'' owo be jita ba banda rawar sanyi da yake ba , abin da yake yi, ta harɗe hannuwan'sa a kirji haƙoran'sa sai gwaruwa suke da juna suna ba da wata ƙara me wani irin sauti. taɓa shi tayi aikuwa lailayo wani uban ashar yayi yace '' ba inda zan kai ki , wallahi ki shidawa kulu bani ba ita ni anya kuwa ma gidan yaya mansur ta kawo ni..? ke a ina nake nan? nifa ba tun yau fa , na fahimci bakin iyaye ke dawainiya da kulu dana baƙota.'' me rafi'a za tayi

Chapter 6 of 10