Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
10 / 10
wasan ki ce?.'' Mommy tace '' wallahi bazan yarda ba ku mai damin da gida sansanin yan dambe .'' ahlam tashi tayi tace '' ni wallahi wannan hayaniyar ma hawa min kai take aneesah idan ya kawo trolley ɗi'ta ki kai min daki na.'' to tace mata ahlam tashi tayi ta rataya jakar ta ta hau sama kai tsaye dakin ta , ta shiga yana nan yadda yake komai a gyare kamar ko da yaushe tana amfani da , dakin zama tayi a kan gado tana sauke ajiyar zuciya buɗe jakar ta , tayi ta dauko waya, ta number aunty yaseerah ta buga, bugu ɗaya biyu ta ɗauka kuka ta fashe dashi tace '' aunty kina ina yaya zai zubar mana da mutunci mommy kuma ta zuba mai ido?.'' cikin tashin hankali aunty yaseerah tace '' innalillahi wa'inna ilaihir raji'un me ya faru ? Ko jiya naso na kirawo ta muka shiga meeting da gwamna sai yanzu na samu kaina kwana biyu bana samun zama naji ance aseem zai yi aure, ba dai wannan yar iskar zai aura ba me yawan banza ? Ki nutsu kiyi min bayani dalla dalla dan wallahi ko da ubanta take yawa auren nan ba zai yiwu ba.'' share hawaye tayi tace '' baroroji zai aura mazauna daji dan Allah be zubar da mutuncinta gidan nan ba ? ki duba ki gani yadda mata masu aji suke son sa , ko a biki na sai da wata yar uwar nadeem ta gan'sa tana son sa amma fafur yaki ya dinga yi mata hulakanci dole ta hakura ta bar'sa badan ta so ba.'' aunty yaseerah tace '' a'a ahlam inhar mutuniyar kirki ce ba wani abu bane wato ku kin fi son rayuwar kwarya tabi ƙwarya, ke dai abin da nake so dake Allah ya saka ta gari ce Ubangiji Allah ya saka abokiyar zama ce amma wannan abin duk bashi bane ...'' ahlam wani takaici ne ya tokare ta , tace '' tom shikenan zan ciga ba dayi.'' yauwa ɗiyata Allah yayi muku albarka ki gaida aunty Zainab uhmmhmmm za taji ta faɗa tana kashe wayar, tashin hankali ba'a saka maka rana haka ta fadi a fili ta gumi tayi tun da har aunty yaseerah bata saka baki ba to fa akwai gagarumar matsala , da ace ta saka baki ne to yar tujara ce tsaf zata iya sakawa a fasa auren to itama ta mara baya yake nan? da sauri ta ɗago aneesah ce tana jan trolley din ta , ta shigo da ita ahlam tace '' aneesah aunty yaseerah ta marawa yaya baya , ya auri bararoji.'' na shiga uku itama kenan tabi sahun su mommy shikkenan abin mu ba tasiri zai yi ba. aneesah ta faɗa tana zama kusa da ahlam. ahlam tace '' aneesah mene abin yi? Ni dai bazan yiwa kahu sani magana ba balle aunty jidda su kaɗai zasu iya fadan nan to kwanaki , ya kira ni naki ɗagawa , saboda nasan faɗa zai tayi min yanzu kuwa idan na neme shi wallahi sai ya wanke ni tas ya cimin mutunci.'' Hmmm wallahi bazai ma zo ba ko da ba kuyi haka ba , aljanuna ne suka naɗa mai duka shi da aunty jidda. zaro ido ahlam tayi tace '' garin yaya aka yi haka ta faru tab dama ina nan wayyo Allah.'' bata labari tayi ahlam kwanciya , tayi tana dariya har da hawaye. wannan kenan. flash back. bayan fitar su daga asibiti mota suka tsayar, suka ciniki suka yi suhaila tace '' amma gaskiya bamu da kudi a hannu sai dai mu tura maka ta account yanzun nan aka sallamomu daga asibiti.'' P-cap ɗin sa ya cire, ya yiwa SUHAILA wani irin kallo yace '' kut melesin me kuka ce ? amma dai baku da hankali ni zaku turawa kudi ta waya saboda ku a cikin ɓarayin ma na dabam ne.'' wata tsoho da take ciki tace ''gaskiya jikana la faɗa yaushe zaka yarda a tura maka kudi ta cikin salula, anya kuwa ku ba yan sane bane? , ga kunan dai kamar mutanen arziki ko da yake yan jami'a ne lalatattu duk sune suke, suka fitowa suna yin raye raye suna zama yan film , shi ya saka na cewa jikata inhar zata yi karatu ta kwashe kayan ta , tabar min gida, aure shine darajar mace.'' we'll done baba tela musu dai , ba jami'ar birmu zan kai su ba wallahi duk rabi da kwatanta yan shan jini ne akwai kungiyoyin asiri. zaro ido tsohuwar nan tayi ta rungume kayan ta ai bata san haka abin yake ba da ba za tayi magana ba , Suhaila da ranta ya gama ɓaci tace '' wallahi sharri kuke mana ke kuna uwa ce a gare mu amma kikai mana wannan sharrin kuje ku da Allah.'' Me mashin din ne ya fito zai mari suhaila ji yayi an rike mai hannu suhaila da sauri ta kalli mukhtar tace '' barshi ya mare Ni wallahi da yau na nuna masa wace ce ni a cikin garin nan na nuna mai gata n ban da tsabar rashin mutunci ya za ayi ne dauke mu ba ya dinga faɗa mana bakar magana wallahi yau da ka aikata dana sani mara iya ka kuma Allah ya isa mu ba karuwai , bane duk macen da kuka ji tana makaranta , sai kuce mata karuwa.'' mukhtar yace '' kuyi hakuri ku nuna mai tarbiyyar ku kai kuma idan halin kane Allah zai haɗa ka da, dai-dai kai.'' da hallacan malam sakar min hannu ko yanzu na yanke ka da huƙa. idan naki fa mukhtar ya fadi haka cikin taurin zuciya. Asim da ya gaji da jiran mukhtar ya fito daga motar da shi yace bazai fito ba tun da dai su basu san darajar kan su ba , a ko ina fada suke yi shi in ban da dole me zai da yarinyar nan kallon mukhtar yayi yace '' kai fa nake jira.'' Mukhtar sakin mai napep yayi yace '' okay Ina zuwa.'' zagin da yayi ya tayar da mashin ɗin sa ya tafi mukhtar yace '' me ya haɗa ku dashi?.'' SUHAILA tace '' babu kudi a hannun mu sai nace zan tura mai shi ne ya fara zage zage tsohuwar nan , ta taya shi.'' bata ƙarasa zancen ta ba , ta kasa rufa baki dukkan su, suka tawo a guje zasu rike mardiyya cikin zafin nama da sauri asim ya taro ta, zafin ranar da ake yi shi ya haifar mata da jiri da sauri afiyah ta fito daga cikin motar ta , idanuwanta basa ganu wani irin dishi dishi take gani Allah, Allah take wata babbar mota ta huce sai ta tsallaka da yake titin gida biyu ne ita tana bangaren dama su, suna hagu. tun da take da asim be taɓa rungume ta a kirjin sa ba , ko arzikin rike mata hannu bata samu ba. Bagaren asim kuwa jin wani irin shock yayi sakamakon rungume ta da yayi a jikin sa , abin da be taɓa yiwa wata mace ba , ko su adyan da suka fara girma dena rungume su yayi saboda matsalar da yake fama da ita. MARDIYYAH da kan'ta yake tsananin sara mata, ta saki wani irin kuka me ban tausayi ga kafar ta , da take mata wani irin ciwo. mukhtar shiru yayi yana kallon su haka ma SUHAILA wani irin farin ciki ne ya mamaye ta , ganin afiyaah ta , tawo gadan gadan tamkar wacce take da cutar hauka, da alama ba a cikin hayyacinta, take ba. a guje ta tsallako wani me mashin ya bige ta Allah ya rufa asiri bata ji ciwo ba ko a jikin ta haka ta , taso tana tangadi ga takalmin kafar ta me uban tsini ne cikin bala'i tace '' asim me zan gani a ga bana ka rungumi wata macen sai kuma ta finciko mardiyya rikon da yayi mata bana wasa bane dan haka hijabin ta ne ya yake hullar da hijabin tayi. gashin mardiyya yane ya zubo har gadon baya sosai ran asim ya ɓaci kishi hauka ne ya za ayi ta yaye mata jiki a bainar jama'a cikin ɓacin rai yace '' haba afiyah baki ga halin da take ciki ba ya za a yi ki buɗe mata jiki akan titi.'' da sauri ta kalli jikin ta wani irin banzan wando ne a jikin ta wandon duk a bule yake irin crazy din nan ne cikin ɓacin rai tace '' yayi kyau nu namin halin ku na maza asim idan ba kai min haka ba , baka nuna min ka cika namiji ba amfanin me wannan kwailar za tayi maka idan tsirara nayi mata anan ne mutane za suyi da ita amma shi ne ka rungume ta a jiki kamar jaririya kana balokoko an buɗe mata jiki a bainar jama'a yayi kyau ni ba kaga abin da ya same ni ba , ko da yake ba laifin ka bane chaji ka ke tun da gashi nan ka rungume ta a kirji ka rage zafi.'' da sauri ya ɗagi da jajayen idanuwansa duk a a cikin glasses suke hakan be hana jan su ya fito ba , fuskar sama tayi ja daga gani maganar da afiyaaaah ta gasa mai tayi mai ciwo a cikin zuciyar sa gadai shinan ya kasa raba ta da jikin sa balle ya dauki action akan Afiyaah. Mukhtar ne ya katsai shirun da yayi yace '' ka barta a cikin rana ciwon ta , zai ƙara tsananta.'' tamkar wata jariri haka ya dauke ta ita lokacin kuma ta riga da ta , suma. a fusace afiyah ta fisgo ta fadi ƙasa tace '' wato ga mahaukaciya ko tana magana kayi min shiru ?.'' ai bata karasa ba ya wanke ta da mari har guda hudu hagu da dama sai da ta kifa jinta da ganin ta ya dauke na wani lokaci hawaye ne suka shiga bin kuncin'ta, dad'i ne ya kama suhaila. Asim daukan mardiyya yayi da ya fadi ƙasa ya shigar da ita cikin motar sa , kan'ta ya fashe gashin ta ya tattare ya mai dashi guri daya saboda ya rufe mata fuska ga shi kuma goshin ta yana fitar da jini ya fashe. SUHAILA shiga cikin motar tayi haka mukhtar cikin Asibitin ya komar dasu be bari anzo daukar taba ya , ɗauke ta ya rungume ta , ya fara tafiya da ita cikin sauri Saboda numfashin ta da yake sama yana ƙasa tana fisgar'sa da kyar.'' bangaren AFIYA kuwa suman zaune tayi, ta kasa ko da motsi ne mamaki take Asim ne yayi mata haka ko kuwa mugayen mafarkan ne da ta saba yi, idan kuwa ido biyu ne dole taje a ƙara yi mata abin da aka yi mata baya ganin lefin ta , ta shiga uku idan asim ya guje ta ya za tayi ? ta gama shirya komai ina ba zai yiwu ba yadda asim ya mare ta , sai ta saka ya yiwa mardiyya hulakanci da yafi nata in har tana numfashi a doran duniya , dole ta koma South Africa shiri ya lalace.'' Amina alhasan Muhammad opay 1k 8141785374 ku turo da shedar biya ta wannan number 08141785374. Alhamdulillah a yau na kawo karshen free page duk meson karanta wa ya biya na saka shi a group ya dinga ganin posting. 8141785374 Yan Niger 1000fcfah ku turo da shedar biya ta wannan number 08141785374. 1:.Binta yar jagaliya 300 2:.Mu zuba mu gani 200 3:.Yar hannu a Lagos 1k 4:.KARUWAN CIKIN GIDA 1k 5:.Jikar Mamman 1k 6:.Destiny love 400 7:.GIDAN magajiya 1k 8:.Women leader 500 9:.Bakin shafi 1k 10:.Uwar gafalallu 1k 11:. YAN ZAMAN MAKKA duk me bukatar wa'yannan littattafan sun zama complete document ya turo da kuɗin'sa kar ku bari a baku labari Wannan tafiyar ta dabam ce. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 10 of 10