kula kowa,idan Inaas tafara zuba surutu saika dakatar da'ita hakan yasa takeda mutane sosai,shagwa6ar da Bilkisu tasaba mata dashi tun tana qarama hakan yasa data girma ma tacika shagwa6a,batajin kunyar kowa agaban kowa saita fara buga qafafu tana yiwa Mamanta Bilkisu shagwa6a,Allah yayi mata baiwar surar jiki da qira,uwa uba diri kamar budurwa me shekaru dayawa,tanada madedetan nashanunta wanda bazaka kirasu yan qananu can ba,kullum suna nan atsaye daram wanda yaci ace tun tuni tafara saka musu brezia amma qememe Inaas taqi sakawa ko irin na kayan gwanjonsu ne dasuke siyarwa,Bilkisu tayi mata magana harta gaji tarabu da'ita,gani take atsaye suke mezaisa tadinga saka wata brezia tana fama.
Sana'ar saida gwanjonsu tana nan sunayi babu abinda suka daina,sunan Bilkisu yakoma Bilkisu Me gwanjo,yayinda ita kuma Inaas yawancin mutane suke kiranta da 'YAR ME GWANJO.
kowanne lokaci Inaas bata kunyar kowa haka zata d'auki kayan gwanjonsu takai musu gida-gida kuma dayake tanada surutu nan da nan zatayi ciniki tadawo gida.
Sun tashi daga garin Dungas,sunkoma cikin Niamey,sakamakon aiki da Babanta Farouq yasamu yana koyarda yaran wani attajiri mesuna ALHAJI AUWAL..., "
(me karatu in baku manta ba Alhaji Auwal shine aminin Alhaji Mekudi,wanda yakira Alhaji Mekudi awaya cewa angama kammala komai na aikin kamfaninsa kawai shi ake jira yazo yabude,yazo nijar yabude kamfani a hanyarsa ta dawowa gida ya tsinci Jawad,to Alhaji Auwal yadauki Farouq Baban Inaas aikin koyawarwa,yana zuwa kullum yana yiwa yaransa lesson, kasancewar sa tsohon malamin makaranta)
Farouq yanema musu d'an qaramin gidan haya daidai na talakawa gida,gidan nasu yana daga can baya-bayan gari inda babu cukowar mutane dayawa a unguwar.
Suna rayuwar su cikin farinciki,Inaas bata barin Bilkisu tayi tunani tana qoqarin sanyata farinciki,tasan ba'itace ta haife taba,haka tasan labarin 6atan yaron ta,tasan komai kasancewar Bilkisu bata 6oye mataba,hakan yasa tadage wajan ganin ta maye mata gurbin d'anta data rasa,tana sata tanajin idan d'anta ya6ata to tanada wata yarinyar yanzu.
Kamar kullum,cikin sauri tashigo gidan nasu tana qwalawa Bilkisu kira "Ammiy.., Ammiy!"
Cikin sauri Bilkisu tafuto daga d'aki tana sake gyara d'aurin dankwalinta,tana nan har yanzu kyawunta bai gushe ba,mace mai haquri da hangen nesa,jikinta yana nan da kyansa kamar ba'ita ta haifi Jawad d'an shekaru 37 ba,kafin tayi magana Inaas tasaki kayan gwanjon su aqasa yayinda ta damqawa Bilkisu wasu takardu a hannunta,ita kuma tashige bandaki da gudu saboda wani mugun fitsari datake ji.
Bilkisu taja kujera ta zauna,ta ajiye takardun agefe sannan tabude qullin kayan gwanjon nasu tana dubawa.
Inaas tafuto daga bandaki tad'aga bakin buta ta wanke fararen qafafunta,sannan ta tsugunna tafara alwala,dogon gashinta kuwa Ammiy ta nannad'e matashi a qeyarta kamar ribon,saida tagama alwala sannan tadawo kusada Ammiy ta zauna tace"Ammiy albishir..."
Bilkisu tayi ajiyar zuciya tasan halin Inaas yanzu haka surutu zata fara, danhaka ta katseta tace"kafin albishir d'in de,yanaga kayan kin dawo dasu kwata-kwata baifi qwaya biyar kika siyar ba?"
'Dan qanqanin bakinta taturo gaba cikin shagwa6a sannan tace" Ammiyyyyy...."
taja sunan,sannan taci gaba da fadin"Ammiy ina miki maganar albishir kinata gwanjo,to kwanan nan za'a daina cemiki Me gwanjo nima adena cemin 'yar me gwanjo,nasamu aiki a kamfanin Mekud'i Oil,danaje na zauna Ina tsara wani ma'aikacin nasu,wallahi yana ganin takarduna ya kaiwa manager,bayan sunmin gwaje-gwaje kawai saiji nayi ance an daukeni"
Bilkisu ta zaro idonta cikin farinciki sannan tasaki murmushi tace"Inaas da gaske kinsamu aiki a wannan babban kamfanin? kai Alhamdulillah,to kuma sai akai Yaya? bani labari mana"
Inaas ta kwashe da dariya sannan tace"bakece kikemin maganar ban saida kayan gwanjonmu ba,to ai ajiyar kayan nabayar awani gida natafi kamfanin na basu takarduna,da har yafara yatsina fuska wai da secondary zamu daukeki aiki?"
(ta gwada yanda mutumin yake magana)sannan taci gaba da fad'in
"nikuwa danaga zai kwafsa min ai tuni nagyara zama naketa zuba masa zance wallahi Ammiy sai gashi yanata dariya,yanzu gobe babu zuwa tallar gwanjo,nazama ma'aikaciyar kamfani"
Ammiy tayi murmushi tana kallon Inaas tanajin wani irin farinciki,akoda yaushe tana Alfahri da Inaas,ajiyar zuciya ta sauke tace"to Allah yasanya Alkhairi,kidinga nutsuwa de idan kinje ba kowa zaki dinga sakewa dashi kina wannan surutun naki ba"
Inaas tayi fari da idonta tace"angama Ammiy"
Bilkisu tamiqe takawo mata abincinta, bayan tagama cin abincin tayi sallah, sannan suka zauna Bilkisu tafara gyara mata gashin kanta,already gashin nata a wanke yake,saita had'a wani turaren wuta na gashi me mutuqar qamshi,ta warware mata gashin tataje mata shi,gashin nata yayi wani irin tsawo har yanaso yawuce gadon bayanta yata6o mata duwawu kamar lokacin datake qarama, bayan tagama taje mata tadaga gashin sama tasaka turaren wuta aqasa tana turara mata gashin, yayinda Inaas ta lumshe idonta tanajin dadin yanda Ammiyn take gyara mata kanta.
*** *** ***
UAE.
(Abu Dhabi)
Ya kasance kowacce rana baya cikakkiyar awa biyar,batare da yaji muryar mahaifinsa ba,duk yawan ayyukan dake gabansa kokad'an baya sakaci da kiran Daddy,yana qaunar mahaifin nasu,kallo d'aya yayiwa P.a dinsa dake tsaye agefensa p.a yagane abinda yake nufi,cikin sauri yakira masa Alhaji Mekudi.
Adede lokacin Alhaji Mekudi yana cikin mota Malam Sulaiman yana jansa da sauran motoci a bayansu zasuje d'aurin auren yaron wani Sanata.
Cikin sauri Alhaji Mekudi yad'auka tareda fadin"Jawad"
Daga nasa 6angaren ya lumshe idonsa sannan yace"Daddy good afternoon"
Alhaji Mekudi yayi ajiyar zuciya,maimakon ya amsa masa gaisuwar tasa saiyace"Jawad Ina hanya zanje wajan d'aurin auren yaron Senator Hamza"
Jawad yanajin haka yasake lumshe idonsa fuskar nan tasa kokad'an babu walwala akanta,yasan cewa Daddy Ishara yake masa akan shi yaqi aure gashi zaije d'aurin auren yaron abokinsa.
Shima maimakon yabawa Daddy amsa sai yace"Daddy i hope you're fine...."
Alhaji Mekudi yace"maganar danakema kenan? yaushe zaka shigo Nigeria? ya kamata ka sassautawa kanka wannan aikin kadawo gida ka ajiye iyali kuma,Jawad shekarunka 37 yanzu,sai yaushe zakai aure? mahaifiyar ka kullum maganar datake kenan".
ME 'DEBE KEWA littafin kud'i ne,300 ne kacal,zaki biya ta wannan account number
0164549488
Amina muhammad
GTbank
Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034
Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034.
Amnah El Yaqoub✍🏻💝 *ME 'DEBE KEWA*💝
('yar me gwanjo)
Writing By Amnah El Yaqoub
Dedicated to Bilkisu's name
https://chat.whatsapp.com/FzjixDJbvvWCUd7az9a0K0
9&10
ME 'DEBE KEWA littafin kud'i ne,yanzu muna posting free page ne.
300 ne kacal,zaki biya ta wannan account number
0164549488
Amina muhammad
GTbank
Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034
Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034.
___
Runtse idonsa yayi sannan yabud'e,yanda ayyuka suke hanashi samun sukuni ina yaga lokacin dazaima fara duba yarinyar dayake so?,ita kanta soyaiyar idan yahad'u da yarinyar ma bazaice ga yanda zaiyi ba,ko irin kula 'yanmatan da samari sukeyi alokacin dasuke taashan balaga shikam baiyi ba,abinda yasani kawai shine kasuwanci,dashi aka bud'e masa ido,akan turbar kasuwanci aka fara d'orashi,baida lokacin dazai bawa mace,idan yace zai'iya kulawa da'ita ma to yayiwa kansa qarya,ahankali yayi ajiyar zuciya sannan yace"Daddy i don't have any girl friend,nabaku dama,kuza6omin duk wadda tamuku"
Alhaji Mekudi yakashe wayar cikin taqaici,sannan ya lumshe idonsa, Malam Manu dayake driving yanajin duk abinda yake faruwa,yayi murmushi yace"Alhaji aida kun barshi yakawo wacce yakeso da kansa,'ya'yan yau idan sukaqi mace abun ba dad'i,Jawad d'in har yanzu ai yaro ne,nawa yake?"
Alhaji Mekudi yabude idonsa yayi wani murmushi irin nasu na manya najin dad'i,duk wanda zai shagwa6a masa Jawad d'insa yana sonsa,aduniya in kanason kwanciyar hankalinsa to ka yabi d'ansa Jawad,ya kalli Manu driver yace"Man Sulaiman bakasan halin d'annaka ba,idan muka barshi to ina tabbatar ma ahaka zamuyi ta tafiya ba zaiyi auren ba,saboda agabanka yatashi shiyasa kake masa kallon qaramin yaro,duk sa'anninsa fa sunyi aure,wani lokacin idan na nutsu nayi duba akan sabgoginsa sai naga idan yazo qasar ma ko sau d'aya ba zakaji yana wayar nan irinta samari kaji Jawad yana waya da mace ba,sai Inga kamar ko bashida sha'awa ne"(🙈)
Malam Manu yayi murmushi baice komai ba,ganin yanda salon maganar Alhaji Mekudin ta sauya wannan maganar kuma tsakanin sane da d'ansa.
Alhaji Mekudi ya kalli Malam Manu wanda yake driving cikin qwarewa,yatuna lokacin daya daukeshi aiki alokacin baqi ne,amma yanzu ya washe yakoma chocolate,girma yafara futowa ajikin sa,amma yanayin jin dad'i da hutun dayake samu yasa girman ya 6uya,ga wani haqorin makka daya saka tun zuwansa Hajji da umara wanda Alhaji Mekudin shine yabiya masa,haqorin Makkan yasake qawata haqoransa yayi masa kyau sosai,ya sassauta muryarsa duk da su biyu ne amotar yace"nikam Man Sulaiman tsawon shekarun nan damuke tare banta6a jin kayi min maganar iyalinka ba,bakada yarinya ne ko yaro?sannan meyasa bazaka d'auko matarka kuci gaba da zama tareda muba?"
Gaban Malam Manu yayi wata irin bugawa,jikinsa yafara rawa cikin sauri yataka burkin mota yafashe da wani irin kuka,cikin sauri motocin dake biye dasu na security suma suka taka burki sannan suka futo da sauri suka fara duba motar ko wani abu ne yasamu Alhaji Mekudin.
Alhaji Mekudi yazuge glass d'in motar yayi qasa,sannna ya kallesu yace"no problem we're fine"
Security suka juya cikin sauri suka koma motarsu,Alhaji Mekudi yayi ajiyar zuciya ya kalli Malam Manu, wanda kai tsaye bazai ce Malam Sulaiman ba saide Man Sulaiman, yace"Man Sulaiman meyake faruwa haka?kode nayi laifi ne dalilin tambayar danayi ma?"
Cikin sauri Malam Manu ya girgiza kansa,sannan yashare hawayen idonsa yace"kodaya Alhaji,bakamin laifin komai ba Alhaji,tsakanina dakai saide nace Allah ya azurtaka da Aljanna mad'aukakiya,Alhaji kakaini Hajji,kakaini Umara,kabani muhalli nazauna tare daku,kabani ci da sha da kudi,saide duka abinda nasamu banida kwanciyar hankali,haqqin iyalina yana nan yana kan bibiyata,bana cikakkan kwana uku banyi mummunan mafarki ba"
Alhaji Mekudi yace"subhanallah duk me yayi zafi haka?"
Malam Manu yace"Alhaji na gudu nabar iyali na da tsohon ciki haihuwa yau ko gobe,talauci yamin katutu,bamuda cin yau bamuda na gobe,har takai takawo idan naci bashi banida wanda zai biyamin nima bazan Iya biyaba saide ayimin dukan kudin,iyayen Bilkisu sun damqamin amanarta a hannuna kafin su rasu,naci amanar Bilkisu natafi nabarta,bansani ba tana raye kota mutu,abinda tahaifa yana nan koya mutu,duk lokacin dana daura aniyar zuwa gida sai inji gabana yana faduwa inji tayaya ne zan iya kallon Bilkisu in fuskanceta in nemi yafiyarta?
da hannunta take aikin qarfi tatara mana kudi muyi buqatun gida dashi,kai hatta kudin motar dana samu nagudu Lagos itace tabani su alokacin kudin sunada daraja tace nafara tarawa dan musamu abinda za'a yankawa yaron cikinta na suna,Bilkisu tanada haquri,ta yarda dani,tana mutuqar sona amma duka na rusa komai,bazan iya kallon idon Bilkisu ba,hakan yasa nakasa zuwa gida nazauna anan ina jira kafin Allah ya dauki raina"
Alhaji Mekudi yacire medical glass din idonsa yagoge qwalla sannan yamaida glass din yace"Ash'sha,Man Sulaiman kayi kuskure,ai ba'a gudun annoba,Allah yana sane da halin dakuke ciki especially ma kaida Allah ya azurtaka da mace irin wannan,ya kamata ka shirya kaje ka fuskanci iyalinka karoqesu gafara sannan ka daukosu kudawo nan gaba dayanku"
Malam Manu yagoge hawayen idonsa yace"to Alhaji,insha Allah zanyi yanda kace, nagode"
Daga nan yaja motar suka qarasa wajan d'aurin auren,saide kafin su qarasa har anriga an d'aura sai gaggaisawa dasukai da mutane.
Da daddare wajan qarfe takwas,Alhaji Mekudi yana zaune acikin tangamemen falonsa na sama,wanda yaji wasu lafiyayiyun kujeru 'yan gajeru ruwan cement,fruit ne agabansa yanasha yayinda Hajiya Zaliha take gefensa a zaune tana ganin labarai a bbc.
Tasake zama hamshaqiyar uwa matar Alhaji,haka kuma uwar Alhaji,wuyanta da zoben hannunta da awarwaron hannunta gaba daya na gold ne,stone work din jikinta sai walwali yake.
Alhaji Mekudi ya'ajiye fork din hannunsa wanda yake daukan apple dashi, ya kalli Hajiya Zaliha yace"d'azu munyi magana da yaron ki,nayi masa maganar aure yace yabamu dama munema masa,lokaci yayi daya kamata ace yayi aure,muma muga 'yan jikokinmu agidan"
Hajiya Zaliha tasaki murmushin farinciki sannan ta d'aga hannunta sama tace "Alhamdulillah,Alhamdulillah,yau-yau d'innan kuwa zansa abinciko min yaran garinan,daga kan 'ya'yan 'yan kasuwa har zuwa na siyasa duk zanyi magana sai muga wacece ta dace dashi"
Alhaji Mekudi yagyad'a kansa cikin gamsuwa da bayanin nata yace"hakan yayi,nima munyi magana da Aminina Alhaji Auwal,saboda haka zan kira Jawad d'in insashi yakira can Nijar d'in su gaisa da Fauziya da Ummi ko za'a dace sai muyi musu had'in gida"
Hajiya Zaliha tace"hakanma yayi,nima daga nawa 6angaren zanta bincikawa,har muga abinda hali zaiyi, idan yaza6i 'ya'yan Alhaji Auwal d'in shikkenan,idan kuma na nan Nigeria yaza6a shikkenan"
Sunacikin wannan farinciki gidan tv na bbc suka fara karanta labarin Babban matashin d'an kasuwa Jawad Mekud'i yabiya wa yaran talakawa daliban University's kudin registration kimanin naira million talatin.
Alhaji Mekudi yayi murmushi yad'auki wayarsa yakira Jawad,bugu biyu Jawad yad'auka,cikin miskilancinsa kamar bayason yayi magana yace"Daddy..."
Alhaji Mekudi yace"yanzu nake ganin labarai kabiyawa yara kudin Registration,ka kyauta sosai,musanman yanzu dana samu labari ana cewa kud'in karatun yara yaqaru,kaci gaba da taimako idan da hali,na tabbatar kaima Allah zai taimaka maka"
Cikin tsananin biyaiya yace"ok Daddy insha Allah"
Alhaji Mekudi yasake cewa "yawwa idan kasamu dama kakira Babanka na Nijar yanzu-yanzu ku gaisa"
Cikin mamaki Jawad yace"Daddy Babana?"
Yayi tambayar cikin sigar rashin gane wanda ake magana a kansa.
Alhaji Mekudi yagane hakan,dan haka yace"Aminina Alhaji Auwal na Nijar"
"Daddy i don't have...."
Cikin sauri Alhaji Mekudi ya katse shi yace"you don't have his number,hakane?"
Cikin sauri Jawad yace"Yes Daddy"
Alhaji Mekudi ya girgiza kansa yace"you don't have a girl friend,you don't have his number,Jawad kai shikkenan komaima babu?,rayuwa zata iyu da haka? kaida ya kamata ace kacemin kanada number sa kana kiransa ma kuma gaisawa, wanne irin zumunci ne wannan,?zan turoma number sa yanzu,saika kirashi"
Yana fadin haka yakashe wayar, Jawad ya lumshe idonsa mecike da jin bacci,dan yanzu haka qarfe goma shadaya dayane na dare a agogon qasar Dubai.
Bayan yagama waya da Jawad kai tsaye Alhaji Auwal yakira, bayan sun gaisa yace masa "nasa Jawad yakira ka,idan yakira,ka had'ashi da yaran gaba d'ayansu su gaisa ko Allah zaisa su daidaita kansu da d'aya daga cikinsu"
Alhaji Auwal yayi godia daga nan suka kashe wayar.
Bayan Alhaji Mekudi ya ajiye wayarsa agefe Hajiya Zaliha tagyara zamanta ta kalleshi tace"Alhaji yaron nan fa yana kashe kudi dayawa"
Alhaji Mekudi yayi mata wani irin kallo sannan yace"gaskiya kam,amma kuma maimakon raguwa kullum kud'in sake qaruwa suke,kinga amfanin taimako ko?"
Hajiya Zaliha tayi wani irin murmushi mai ciwo ganin cewa cikin hikima Alhaji Mekudi kamar magana ya gwa6a mata,kokadan bataji dadi ba,tasaki ajiyar zuciya tasake cewa"to Alhaji mezai hana muyiwa Jawad magana Fu'ad ma a bashi wani 6angare na dukiyar yana juyawa?"
Kai tsaye yace"Fu'ad be goge akan kasuwanci ba"
Cikin damuwa ta sauya salon zancen nata tace"hakane,to amma Alhaji aikin yayiwa Jawad yawa,kana gani kwata-kwata baya samun damar da zaizo ya zauna tare damu,yaron nan tun yana qarami kakaishi wata qasa ka ajiye,yagama karatu ka d'orashi akan harkokin ka nacan,qarshe ma duka dukiyarka ka maidata hannunsa komai da komai yazama nasa,tokai mezai hana ka dinga tayashi dawani abun ko shima zai samu ya huta ya dinga zuwa gida muna ganinsa akai-kai yanzu fa tsakaninmu da d'anmu saide gani daga nesa,saide mu ganshi a tv"
Alhaji Mekud'i yasaki ajiyar zuciya sannan ya fuskanceta yace"nina tsufa,har yaushe ne zanci gaba da wannan harkar kasuwancin? Fu'ad kuma bai karanci kasuwanci ba idan zaiyi kasuwanci ma saide yayi abu daka,Jawad d'in de shine matashi beyi yarinta da kasuwanci da gwagwarmaya ba kuma baiyi tsufa ba,shine matashi sabon jini wanda zaiji da matasa da manyan 'yan kasuwa,ina ganin mubarshi yayi abinda yaga yadace kawai, maganar namaida sunansa akan dukiyata kuma idan kin manta bari in tuna miki yaron nan karki manta bashida gadona ko d'aya,kuma dukiyar tareda shi na tarata,abar maganar dukiya ko wani qyale-qyalen duniya ma mune iyayen Jawad,bayan mu bashida kowa,sannan karki manta Fu'ad da Jawad abu d'aya ne,yarannan sun taso suna son junansu,ko bayan babu ranmu NI DAKE,nasan cewa Jawad zaici gaba da kulawa da dan'uwan sa,hakane?"
Sai alokacin Hajiya Zaliha tasaki wata irin ajiyar zuciya,sannan tace"eto hakane kuma,to shikkenan,Allah ya tayashi ruqo,Allah yatemaka"
****
Acan Dubai kuwa Jawad yasa p.a dinsa yakira masa number da Daddy yaturo masa,kasancewar Alhaji Auwal yasan da kiran nasa hakan yasa bayan sun gaisa dashi yakira yaransa 'yanmata guda biyu yace"ku kar6i waya ku gaisa da yayanku"
Babbar ce tafara kar6a wato fauziya,ta gaida shi taji baya magana dajan zance irinna samari daga lafiya,sai kina karatu ko?,sai ok.... (♀️🤭)
To itama dayake bawani yawan magana ne da'ita ba kasancewar ta 'yar Alhaji Auwal babban attajiri a qasar Niger,abunka da 'ya'yan manya tataso cikin gata,sai kawai tace masa "ga qanwata Ummi bye bye" (🤭)
To itade Ummin tad'an jashi da surutu har tana tambayarsa yaushe zaizo qasar tasu,kasancewar bai iya qarya ba hakan yasa babu 6oye-6oye yace mata "babu rana"(🙆)
Baby dake zaune agefe 'yar gidan Antyn su ce,jikar gidan ce,tana zaune agefe tana jinsu dataga zasu kaiwa Alhaji Auwal waya cikin sauri ta wullar da teddy din hannunta tace"Anty Ummi bani shi,bani shi"
Ummi ta kalli Baby da sauri tana ganin ikon Allah, tasan halin Baby da surutu amma batayi tunanin abun nata yakai haka ba,babu musu tabata wayar.
Baby ta kara wayar a kunnanta tace"Hello Yaya,ni ba kace abaka niba gashinan ni nace subani kai,Sunana Baby"
Jawad yadaga girarsa guda d'aya yasaki wani miskilin murmushi,daga ji yarinyar irin yaran nan ne masu surutu da shiga rai,ahankali yace mata "ni Sunana Jawad Mekudi"
Baby tace"nasani,Yaya Jawad kasan me?jiya aka kaini wajan wasa,nayi wasa nahau doki,saboda nice nazo ta d'aya a ajinmu,kai nanawa kazo?"
Jawad yayi murmushi yace"nine na biyu,kinga kece first nikuma second"
Baby ta qyalqyale da dariya tace"to kaima ankaika wajan wasa ne?"
Wannan lokacin ma murmushi yayi yace"Daddy na bekaini ba, yace dole sainazo na d'aya,amma zan dage next time naqwace miki position d'inki nima sai akaini wajan wasa"
Baby tace"tabdi,wallahi bazan yarda ba,to bari kaji Kullum idan Uncle Farouq yazo nice nake fara yimasa bayanin lesson d'in dayayi mana abaya,nafi kowa qoqari,bazaka qwace min position ba"
Kai tsaye Jawaad yace mata "waye Uncle Farouq?"
(masu karatu Uncle Farouq d'innan da yarinyar nan take maganar sa shine Farouq mahaifin Inaas,Qanin Bilkisu me gwanjo,inba ku manta ba nace muku yana yiwa yaran Alhaji Auwal lesson,yawwa🤒)
Baby tace"shine yake mana lesson,shima yace nice best student d'insa"
Jawad yayi murmushi ya girgiza kansa yace"ok,tokici gaba da karatu,idan kika sake zuwa ta d'aya zan kawo miki chocolate da kaina"
Cikin murna Baby tasakar masa kiss ta wayar sannan tatafi da gudu ta kaiwa Alhaji Auwal wayarsa.
*** *** ***
Abuja Nigeria
Washegari sassafe Man Sulaiman yayi sallama da Abuja yatafi Jigawa kamar yanda Alhaji Mekudi yabashi shawara jiya.
Kasancewar jirgi yabi hakan yasa wajan shabiyu na rana ya isa garin,tunda yashigo garin yake kalle-kalle yana tuna baya,agefe guda kuma banda fad'uwa babu abinda gabansa yakeyi,duk wanda yake had'uwa dasu babu wanda yasani shima babu wanda yagane shi,kai tsaye gidansa yanufa anan yaga gida yazama gidan tarihi domin kuwa sai fili,d'akinsu qwaya d'aya na qasa shima babu yazube,nan take ya zube awajan yadira gwiwar sa aqasa yafashe dawani irin matsanancin kuka,hakan yasa yara suka fara taruwa a kansa ana kallonsa,daga nan manyan gari sukaji labari suka nufo wajan,d'aya daga cikin manyan ne yace"kamar Malam Manu"
Man Sulaiman yad'ago kansa da sauri ya kalleshi,kallo daya yayi masa yagane shi, cikin kuka yace"nine malam jafaru"
Mutumin da'aka kira da malam jafaru yace"ikon Allah,ashe muna raye Allah zai nuna mana wannan ranar,Malam Manu Ina kashige?munyi tunanin kaida Balki Me gwanjo rai yayi halinsa"
Cikin sauri malam Manu yanufeshi yace"Ina take? Bilkisu tana raye? meta haifa malam jafaru?"
Malam jafaru yagoge qwallar idonsa yace"malam Manu kad'au haqqi,Balki me gwanjo tatafi,haqqinta bazai barka ba,mu qarasa wajan Maigari sai kaji komai"
Tunda malam jafaru yace Balki me gwanjo tatafi daga nan jikinsa yayi sanyi,saboda yayi tunanin tafiyar mutuwa yake nufi.
Lokacin dasuka qarasa wajan Megari saiyaga ba Megari daya sani da bane,wancen Megarin yamutu,d'ansa ne akan kujerar yanzu,bayan kowa ya nutsu ya zauna daya daga cikin tsofaffin fada wanda yana raye akayi komai,ya girmi Manu sosai, tsoho ne, ya kalli Man Sulaiman yace"kalleni nan Manu,bakaji kunyar zuwa garin nan ba? Manu me Balki tama har haka dazaka gudu kabarta,Ina kakeso taje? gidan uwaka kakeso tatafi bayan kasan bayan kai batada kowa agarin nan? meyasa bazaka sata agaba kutafi ko nanda bangon duniya bane? to Balki ta haihu,da haifi d'anta namiji kuma Washegarin suna takama hanya tatafi qasar su,marigayi Megari yace tazauna damu abata jari har Allah yadawo dakai lafiya idan kana raye,amma Balki tace gida zata tafi,saboda haka bamu saniba itada abinda ta haifa suna raye ko sun mutu,sai kaje can qasar Niger din kaita bilayin nemanta qila ma idan kun had'u tahad'o maka matasan unguwa suyima shegen duka"(🤭😳😂)
Malam Manu ya sunkuyar da kansa qasa yana kuka,sosai yake kuka harda shashsheka yakasa cewa komai.
Maigari yayi gyaran murya yace"ayi haquri Baba Muntari,komai yawuce tunda gashi yatuba yadawo mahaifarsa,saide muyi masa Addu'ah Allah ya baiyana masa iyalinsa idan tana raye"
Gaba daya fada aka amsa da "Amin"
Megari ya kalli wani yaro yace"zakariyya a rakashi cikin gidana abashi masauqi da abinci"
Ahankali malam Manu yadago kansa yayi godia sannan yace"inaso nafara biyan bashin dana tafi nabari akaina"
Megari ya kalleshi yace"kaje kahuta Kaci abinci tukunna, zaka biyasu insha Allahu"
Malam Manu yatashi aka kaishi gidan Megari dakin da ake saukar baqi,yayi wanka yaci abinci yazauna yayi shiru yana tunanin baya,lokaci zuwa lokaci yanajin hawaye yana zubowa daga idonsa,acikin wannan garin yahadu da iyayen Bilkisu sun kawo tallar magani,kafin su rasu suka bashi ita tareda amanarta,a wannan Garin iyayen Bilkisu suka rasu,yasan cewa tanada qaninta wanda suke uwa daya uba daya dashi wato Farouq,yasan Farouq sosai tun kafin a bashi Bilkisu,bayan iyayensu sun rasu sai shi Farouq yakoma Niger,yanzu shekaru talatin da bakwai baisan ta'ina zai fara neman Bilkisu ba,dole zaije qasar Niger cikin garin Dungas yanemota aduk inda take, hawaye suka sake zubo masa,yabuga kansa da bangon dakin yanajin kamar yadawo da baya gaba.
Saida yayi sati daya agarin,duk wasu abokan sa nada dasuka gujeshi yanzu duk sun dawo,duk wani bashi da yasan ana binsa saida yabiya harda ninki,idan dubu daya kake binsa zai ninka maka saboda darajar kudin da d'in dana yanzu ba d'aya bane,abinda dubu d'ayan da zata maka yanzu saide dubu uku ko hud'u.
Filin gidansa yasa mutane suka sake gyara shi aka fara yimasa ginin cement,samarin dasuka suka masa dukan kudin bashi a wancen lokaci yanzu d'aya bayan d'aya suka dawo suna bashi haquri.
Saida yayi kwana goma cif,sannan yadora wani abokinsa akan harkar ginin gidansa, shikuma yayi sallama da mutane cikin aminci.
Daga nan kai tsaye qasar Niger yanufa,bai zame ko'inaba sai garin Dungas,saida yayi kwana biyu yana tambayar su Bilkisu da Farouq amma babu wanda yagane su saboda kawai suna yake fada babu inkiya,yasha wahala kafin yasamu wanda yagane su Bilkisu,hakan yasa mutumin yayi masa jagora har gidansu Bilkisu,saide basa gidan wasu 'yan haya ne aciki,maqotan su sun tabbatar masa cewa su Bilkisu sun saida gidan tun shekarun baya,sunkoma cikin Niamey da zama.
Man Sulaiman yarasa yanda zaiyi,acikin Dungas ma yayi kwana biyu yana nemansu,to idan yashiga Niamey ta'ina zai fara nemansu? wa zai kama?,hakan yasa yabi jirgi yakoma Abuja da nufin idan yasake shiryawa saiya dawo ya bazama neman Bilkisu.
*** *** ***
Niger Republic
Tana dawowa daga wajan aiki tafara warware laffayar jikinta fara,ya kasance sai wata riga aciki 'yar qarama,ta zauna a kusada Bilkisu tace"Mom kinsan me?"
Bilkisu tace"baki abun magana, yau kuma da mom kika dawo abakinki?"
Inaas tace"emana,ai talaucinmu bazai hanamu walwala ba"
Bilkisu tazuba mata ido tana kallonta,tana ganin tsantsar kyawun Inaas,kyawu me fizgar duk wanda yayi tozali da'ita,cikin farinciki tace"fad'amin,meyafaru yau kuma? yaya aikin naki?"
Inaas tace"yawwa Ammiy,aiba dole sai masu kudi ne sukeda damar dazasu ce mummy ba,muma zamu iya fad'a,aikina lafiya kalau,dad'i nakeji wata yakusa qarewa,nakusa jin qaramm.... albashi ya fad'o in siyo mana kayan kallo,kede kimin Addu'ah kawai"
Bilkisu tayi murmushi tace"tunda kikace zaki siyo mana kayan kallon nan nasan zaki iya Inaas,kina qoqarin sanyani farinciki,Allah yasa shima idan yana raye,yana qoqarin saka nakusa dashi a farinciki,saboda daga ke har yayanki Muhammad kuna zagaye da sanyawar albarka ta,kullum cikin saka muku ita nake babu ranar banza, Allah yasake yimuku albarka,yarinyata 'yar albarka ce,nasan duk mijinda kika aura yayi sa'ah"
Farinciki yakama Inaas,tana so taji Ammiy tana yabonta tana zuzutata fiyeda mijinda zata aura, cikin farinciki ta rungume ta, sannan tayi cikin daki.
*** *** ***
Zaune yake akan kujera,fuskarsa babu walwala kawai aiki yake yamaida hankalinsa kacokam kan laptop din dayake daddannawa qirar apple,yayinda guards guda biyu suke tsaye a kansa gaba d'ayansu su biyun suna sanye da baqaqen suit,p.a dinsa yana gefe shima a tsaye yana shafa wata babbar iPad d'in Jawad.
Yashiga cikin yanar gizon Jawad d'in yana fada masa abubuwan dake faruwa dakuma saqonnin da'aka tutturo masa,bayan yaci karo dawani posting da'akai a Instagram yadago ya kalli maigidan nasa yace"yalla6ai gawani masallaci yazube,mazauna wajan suna buqatar a tallafa musu zasu sabunta ginin"
Ba tareda yadago kansa ba,idonsa akan computer gabansa yace"atura musu"
Cikin sauri p.a ya russuna yace"ok sir"
Yaci gaba da duba saqonnin yana bawa mutane amsa, saida yadauki kusan minti ashirin sannna yasake kallon Jawad yace"yalla6ai gawani shafi sun dora photon