Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bata san ina nan ba”
“karki damu zan kirata yanzu,bari nasa Ishrat ta kawo maki breakfast” gyaɗa kai tayi a hankali,ficewa mom tayi daga bedroom ɗin,da kallo laatifa ta bita.
komawa tayi ta kwanta,lumshe ido tayi kamar mai bacci.
*Wai waye*
Bayan ta ajiye wayar ta shiga toilet,ta shafe kusan 10 minutes a toilet ba tare da tana wani uzuri ba,tunanin yanda zata samu mafita daga wannan tashin hankalin kawai take,saƙe saƙe take kan yanda zata samu mafitar abun,zuciya bata da ƙashi babu irin tunanin da bai zo mata ba amma data tuna illar dake cikin hakan sai ta ture shi gefe.
ganin ɓatama kanta lokaci kawai take kowace mafita zata zo mata da illa a cikin ta,haƙura tayi ta fito tana share hawayen ta,gaban dressing mirror ɗinta ta nufa,zama tayi saman stool ɗin dake wurin tana kifa kanta saman mirror table ɗin, ringing ɗin wayarta ne yasa ta ɗan ɗagowa,ɗaukar wayar tayi ganin mai kiran nata ne yasa tayi saurin picking call tana ƙara wayar a kunne,cikin muryarta da tayi laushe saboda kukan data sha tayi mashi sallama,cike da kulawa ya amsa “how are u,I hope u are fine” a hankali tace mashi “am fine”
“what are doing in this time da ba kiyi bacci ba?” ya tambaya,shiru tayi ba ta bashi amsa ba “laatifa!” ya kira sunanta a hankali,lokaci ɗaya taji wani kuka ya zo mata wanda ta kasa controling,kawai ta fashe mashi da kuka,ajiyar zuciya ya sauke “dama naji a jikina akwai abunda ke faruwa dake a cikin daren nan that's why I call u, please stop cry and tell me what happens to u kinji” kuka kawai take tama kasa buɗe baki ta sanar dashi abunda ke damunta, ajiyar zuciya ya sauke in a cool voice yace “stop cry please,it's paining me” jin abunda yace ne yasa ta sassauta kukan da take tana sauke ajiyar zuciya
“ke da dadynki ne?” ya jefa mata tambaya,gyaɗa mashi kai tayi kamar tana a gabanshi “ya yi man iyaka da ƙanwata” kaf abunda ya faru ta sanar da shi sai dai bata sanar dashi a game da soyayya Balqis ba.
“i told u in several times Laatifa,that guy u think is your father baya sonki ki bar masa gidan sa but kin ƙi fahimta”
“sam saboda momy nake zaune”
“but hakan ya hana tsanar da yayi maki ne?”
“A'a,amma...” da katar da ita yayi
“wait,give me a tow minutes I will call” ok tace mashi, rejecting kiran yayi,tagumi tayi tana zuba ma wayar ido,bayan kamar five minutes sai ga kiranshi ya shigo wayar, picking tayi ta kai wayar a kunne “nayi maki booking flight At eight o'clock in the morning zai tashi,ki bar masa gidansa,kije wajen mom ki kwana in the morning sai ki tafi airport ɗin,I will send the ticket for u” bata da wani zaɓi bayan tayi nesa da dadyn nata ko hakan zai sa ya yafe mata “ok, thank u Sam”
“u have a special place in my heart,see u California soon,make sure u live that house,take care,bye” yana gama faɗa yayi rejecting kiran,zubama wayar ido tayi kamar zata ganshi,ta gumi ta zuba ba komai take ji ba face momyn ta,tasan ba za ta juri rashinta a kusa da ita ba amma bata da wata mafita bayan tayi nesa da dadyn ta ko hakan zai sama mata salama a rayuwarta da shi kanshi dadyn nata,ta ɗan jima tana a haka kafin ta miƙa ta shiga haɗa duk wani abunta mai mahimmanci,box biyu tayi na kayanta,kafin ta ɗauki passport ɗinta,bayan data kammala haɗa kayanta,ta ɗan jima tana kallon ɗakin kafin ta fice,a parlor ta ci karo da laure kamar yanda lauren ta sanar ma momy,bayan ta yi bankwana ta roƙeta da kar ta sanar da kowa ta fice daga gidan baki ɗaya,a motar ta ta tafi gidan big dady, Estate tsit kamar babu kowa a cikinta sai yan tsirarun securitys dake kai kawo,lokacin data shiga gidan bata haɗu da kowa,da tayi deciding zuwa ɗakin Yumnah amma sai ta fasa kawai tayi zamanta a parlorn tunda zuwa safe zata wuce ko boxs ɗin ta a booth ta barsu.

*Back to story*

“look Sam,wai kai baka san matsalar dake cikin zuwanta nan ba ne?,karka manta har yanzu Uncles ɗinka da wannan tabon su ke kallon ka,kai ko dan saboda hakan baza ka ƙyale masu ƴar su ba”
“mom i don't care about yanda su ke kallona,ni wannan bai shafe Ni ba,saboda babu wani wanda yake da wani mahimmanci a rayuwata, Please ki bar Laatifa ta zo,zata cigaba da aikinta ne a nan”
“wai mi yasa ka kasa understanding abunda nake son ka gane ne,zuwanta zai ƙara masu tabbaci akan zargin da su ke maka,mi yasa ba zaka gane ba ne,Sam bana son abunda zaiyi affecting mutuncinka,kai wai ba ka jin komai ne da ka yi nesa dani??”
“mom ina ji mana,ke ki ka zaɓi mijinki sama dani”
“sam ina son mahaifinku dole na dawo gare shi” ɗan ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin “love birds,soyayyan da bata maki amfani ba”
“wait idan kana da matsala dashi ni bana da matsala dashi,mahaifinku is a kindnesses parson,har yau ka kasa fahimta hakan ka daina wannan fushin mara amfani da shi,ba dan yana so ba yayi maka haka,sai dan ƙin magana da kayi da kowa,kaƙi faɗan gaskiyar abunda ya faru Sam,har yau kaƙi magana da kowa sai fushi ka ke,baka san halin da ka ke jefa mahaifinka akan wannan fushin da ka ke da shi ba,kana son Allah ya yi fushi da kai saboda wannan halin?” dakatawa tayi tana sauraran ma zai ce,ɗan ajiyar zuciya ya sauke ba tare da yace komai ba, girgiza kai kawai mom tayi
“kasan haƙƙin iyaye akan yaran su Sam amma mi yasa ka ke haka,mahaifinka yana matuƙar sonka fiye da sauran ƴan uwanka,har yau ya kasa yafe ma kanshi akan abunda yayi maka,kullum cikin azabtuwa yake da soyayyarka,Sam baka san ya muke ji a zukatan mu ba saboda nesan da kayi da mu,please ka daina wannan fushin kaji,ka dawo gare mu, jin mu muke uncompleted saboda rashin ka”
“shikenan mom,yanzu ya maganan zuwan Laatifa” ya faɗa hakan ne kawai dan ya kauda zancen
“na riga na gama magana,baza ta zo ba” mom ta faɗa rai a ɓace
“ok,zan kwanta bacci sai anjima”
“baka bani amsa tambayata ba”
“mom bacci fa nace maki ina ji,yanzu fa 1:00 Am ne, mom I will call u” yana faɗa yayi rejecting kiran, girgiza kai kawai mom tayi ta san maganar ce kawai baya so.
tashi tayi daga parlorn ta nufi bedroom ɗinta,a kwance ta samu Laatifa bacci ya ɗauketa bayan ta kammala breakfast,wayanta ta ajiye saman Nightstand ta nufi toilet.
Nainarh zaune take saman bed kusa da Yumnah tunda ɗazu take tashinta saboda gyaran part ɗin sam da za suyi kasancewar yau Friday,tashinta take amma ko motsi Yumnah ta ƙi yi
“please Dan Allah ki tashi muje time fa na ƙurewa” ta faɗa tana kallon fuskar yumnah da ko motsi taƙi,ɗan bubbuga kafaɗarta tayi
“na san fa kina jina,dan Allah yumnah ki tashi” ya mutse fuska tayi tana juya mata baya “ki bari sai 10:30 tayi Please” wani kallo Nainarh ta mata ita tunda su ka yi sallah bata koma bacci ba saboda ƙwallafa rai da tayi na zuwa part ɗin amma yumnah na wani ja mata rai.
“wai minene haka ne Yumnah”
“bacci fa nake Nainarh,dan Allah ki ƙyale ni ki tafi wajen dady ki amshi key ɗin mana ni ba yanzu zan zo ba” hararar ta Nainarh tayi,wata dabara ce ta faɗo mata,da sauri ta kai bakinta saitin kunnen yumnah ƙara tayi wacce tasa yumnah tashi a firgice,fashewa da dariya Nainarh tayi,ɓata fuska yumnah tayi “gaskiya baki kyauta man ba,ji fa yanda ki ka tsorata ni”
“ai maganinki kenan sai magana nake kinyi banza dani”
“to ba sai kije wajen dady ki amshi key ɗin ba”
“ai ba ni ke amsa ba” harararta yumnah tayi “Allah sai nayi maganinki akan ya Sam,kin fa soma takura man akan shi”
“oho dai,ni dai yanzu tashi muje” tsaki yumnah taja,ba dan ta so ba ta tashi,hijab ta zura a jikinta,ficewa su kayi zuwa part ɗin dady,sai da yayi ma yumnah faɗa kan sun ja time,dariya Nainarh tayi mata.
lokacin da su ka isa part ɗin a bakin ƙofa su ka samu su Ishrat su kawai su ke jira,buɗe masu part ɗin tayi, Nainarh da su Ishrat kawai su ka shiga amma ita kitchen ta nufa wai zata sha coffee,part ɗin ta dawo bayan ta kammala haɗa coffeen,samun Nainarh tayi ta zage tare da ita ake aikin, murmushi yumnah tayi ta rasa wane irin ji Nainarh ke yima yayan nata.
jawo hannunta tayi “madam irin wannan haƙilo haka,sai anyi magana kice ke ba haka ba”
“yumnah bana son wulaƙanci,kawai aikin nake so ba wai dan wani abu ba”
“oh ni zaki maida bican ko”
“ke wallahi kin cika matsala,ni dai yanzu ki ƙyale ni”
“yanzu dai ajiye aikin soyayyar ga coffee ki sha” yumnah ta faɗa tana miƙa mata mug ɗin coffee dake hannunta, hararar ta Nainarh tayi tana amsar coffeen,zama su ka yi anan parlon su Ishrat kuma na ciki suna aikin.
nainarh jujjuya mug ɗin dake hannunta ta shiga yi ba tare da ta sha ba,kallonta yumnah tayi tana faɗin'
“ya dai mrs Samad, ko coffeen bai maki ba a canzo maki wani?” harara Nainarh ta watsa mata
“wai mi yasa kin cika wasa ne yumnah?” Nainarh ta faɗa babu alamun wasa, ƴar dariya yumnah tayi “kema mi yasa kin cika rainin hankali?” tsaki kawai Nainarh tayi mata
“Nainarh!” yumnah ta kira sunanta, kallon yumnah tayi ba tare da ta amsa kiran ba
“ina so na tambaye ki please yanzu ki faɗa man gaskiya” stuke fuska Nainarh tayi tun kafin taji ma mi yumnah zata faɗa
“maganar hankali ce za muyi naga kin wani ɓata rai, da gaske ne ba son ya Sam ke ki ba kamar yanda ki ka faɗa man ko dai kawai baki son sanar da ni ne??” yumnah ta faɗa tana wani tsareta da ido,mug ɗin da tun ɗazu bata sha ba ta kai bakinta tana kauda ma yumnah fuska,murmushi yumnah tayi tana ajiye mug ɗin dake hannunta saman table, amshe na hannun Nainarh tayi ta ajiye, da mamaki kawai Nainarh ke kallonta.
kamo hannunta tayi cikin nata
“please Nainarh ki faɗa man, ki ka sani ko da akwai wani abu da zan taimaka maki dashi” yar ajiyar zuciya Nainarh ta sauke
“yumnah idan nace maki bana son ya Sam nayi maki ƙarya, amma yumnah ke kanki kin san bazan samu soyayyar shi ba, wahalar da kaina kawai zanyi shiyyasa duk time ɗin da ki ka man magana nake kauda zancen”
“saboda mi ki ka ce baza ki samu soyayyar shi ba?”
“da bakin ki fa ki ka faɗa man shekarun da ya ɗauka rabonshi da ƙasar nan, kuma ni ko waya banga anyi da shi ba, sau ɗaya naji ya Naeem na waya da shi, a haka taya ki ke tunanin zan samu soyayyar shi?”
“ki ka sani ko Allah ya dubi zuciyarki wata rana kawai ya wanko ƙafa ya zo” murmushi kawai Nainarh ta saki tana girgiza kai
“kina ganin wasa ko?”
“babu wasa a cikin lamarin ubangiji, idan hakan ta kasance zanfi kowa farin cikin”
“in sha Allah wata rana zaki tuna wannan maganan dana faɗa maki”
“Allah ya Amince”
“Ameen,yanzu ki tashi muje mu shirya na san zuwa lokacin da zamu gama sun kammala gyaran”
“amma tun yanzu zamu tafi”
“eh akwai family meeting ne, shiyyasa zamu tafi da wuri”
“family meeting!,anya yumnah baza ku tafi ku barni ba,ni kawai prison zanje wajen momy”
“gobe fa mu ka yi dake zamu je,dan Allah karki man gardama ki zo kawai muje” tashi tayi su ka fice ba tare da ta sake cewa komai ba,sai da yumnah ta fara ajiye mugs ɗin da su ka sha coffee tukun.
shiryawa su ka yi, kamar yanda yumnah ta faɗa lokacin da su ka koma su Ishrat har sun kammala gyaran,rufe part ɗin kawai tayi ta maida key ɗin part ɗin dady da har ya fice daga gidan,bedroom ɗin mom su ka nufa, harta kammala nata shirin itama,Laatifa ce kawai ta so gardama ba zata ba amma ganin mom ta dage ne yasa ta shirya,a parlor su ka ci karo da Fa'iza itama ta shirya
“mom Irfan bai shigo ba ne?” fa'iza ta tambaya sanin duk za su tafi tare su ke tafiya
“bai shigo ba,ku mu tafi kawai” mom ta faɗa,tun ranar da ya ƙone Nainarh yake fushi da su bai sake dawowa gidan ba.
ficewa su ka yi daga gidan,motar yumnah Fa'iza da Nainarh su ka shiga mom da laatifa kuma su ka shiga motar mom da driver zaiyi driving ɗin su,motar su mom na gaba ta su yumnah na baya su ka fice daga gidan zuwa gidan Abbah.

*UNITED STATE❤*

_*Las Vegas (Nevada)*_


tsit gidan yake baka jin motsin komai kasancewar dare ne sosai,duhu ne ya mamaye ko ina sai ɗan hasken bulbs ɗin dake compound da ya haska gidan kamar rana,ɗai ɗai kun securitys ne ke kai kawo a compound ɗin.
A tsaye take cikin garden ɗin da haske kaɗan ne a ciki,riga da wando ne haɗe da mayafi a jikinta masu santsi,ta rufe rabin fuskarta da mayafin,hannun ta riƙe da ƴar madaidaiciyar leda,ta kai tsawan minti 30 a cikin garden sai safa da marwa take da alama akwai wanda take jira,time to time take duba wristwatch ɗin dake hannuta haɗe da kallon ƙofar shigowa garden ɗin.
ganin har 2:45Am tayi yasa kawai ta yanke shawarar bazai zo ba,harta juya da nufin barin garden ɗin ta hangoshi yana shigowa.
ɗaya daga cikin securitys ɗin gidan ne,baƙaƙen kaya ne a jikinshi yayinda ya rufe fuskarshi da face mask,ko Ina na jikinshi a rufe,nannauyar ajiyar ta sauke,ƙarasowa yayi har in da take.
“am sorry ma'am”
“wannan wane irin shirme ne baka san ina jiran ka bane?” ta faɗa rai a ɓace
“tun around 1:30 am nake nan jiranka amma har tsawan 45 minutes baka zo ba”
“am very sorry ma'am,na tsaya ne dan na tabbatar babu wanda yaga shigowata nan ne,am sorry” tsaki kawai taja,leda dake hannuta ta miƙa mashi,amsa yayi yana zuba mata ido dan jin ƙarin bayani
“please ka tabbatar ka bata zuwa gobe,I hope baka manta yanda plan ɗin yake ba”
“yeah ban manta ba”
“okay,Ina wanda ya kawo shi?”
“yana bedroom”
“ohk kana iya tafiya kar su fahimci baka nan” ok ya ce yana zura leda cikin aljihun rigar dake jikinshi,ta hanyar da ya shigo ya bi ya fice,har sai da taga ficewarsa tukun itama ta bi ta wata ƙofar ta fice,cikin gidan ta nufa ta ƙofar wacce zata sadata da ɗakinta,a hankali take tafiya har ta kawo bakin ƙofar ɗakinta ba taci karo da kowa ba,kama handle ɗin ƙofar ɗakin tayi “Mrs Sophia!”
kamar daga sama taji an ambaci sunanta,wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi,a hankali ta sakin handle ɗin ƙofar,juyowa tayi tana kallon luna data ambacin sunanta,a tsaye take hannunta riƙe da bottle water
“daga Ina ki ke haka a wannan lokacin?” luna ta faɗa tana tsareta da ido
“na duba jikin Nailarh ne” ta faɗa tana juya,saurin buɗe ɗakinta tayi ta shiga,barin wurin itama luna tayi ta nufi ɗakin su.

*Washe gari*

A zaune su ke saman dinning chairs a katafaren dinning room ɗin gidan,Aunty Sophia na kusa da Nailarh tana bata abinci,kwata kwata hankalinta baya kan abincin yana kana momynta da har yanzu take fushi da ita,ko kallon in da take bata son yi.
Tissue ta yaga ta goge bakinta “sophia”ta kira sunanta,kallon malika tayi tana ba Nailarh abinci “i will travel tomorrow please take care of her”
“ok ma'am safe trave” jinjina mata kai Malika tayi,Nailarh kasa haɗiye bread ɗin dake bakinta tayi jin abun da Momyn tata tace,fushin da take da ita har ya kai ta tafi ta barta, tissue hannunta ta ajiye haɗi da ficewa daga dinning room ɗin,miƙewa itama Nailarh tayi tabi bayanta,a bedroom ɗinta ta sameta, saurin juyowa tayi jin an buɗe ƙofar ɗakin,idanunta ne suka sauka akan Nailarh dake binta da wani kallo,juya mata baya tayi tana nufar bakin window ɗakin.
A hankali ta taka har izuwa inda take,hugging ɗinta tayi ta baya tana zagayo da hannunta saman flat tummy ɗinta
“am sorry momy” Nailarh ta faɗa tana langwaɓar da kanta saman shoulder malika
“sorry mom” ta sake faɗa, ajiyar zuciya Malika ta sauke,zame hannun Nailarh dake kana tummy ɗinta tayi,juyo da ita tayi suna facing juna,zuba mata ido tayi tana kallo itama Nailarh kallonta take
“momy I'm sorry if I hurt u” kamo hannun Nailarh tayi “sorry for what?” Malika ta faɗa
“na san kina fushi dani saboda rabuwa da mijinki da na saki”
“I'm not angry with you”
“idan har baki fushi da ni mi yasa za ki yi tafiya bayan kin sa I'm not completely healed?”
“important issue ne that's why”
“please ki sa su Joseph su yi reflecting naki mana”
“dole da kaina zanje” kallonta Nailarh tayi kamar za tayi kuka “please momy ki zauna a tare dani”
“bazai yiwu ba baby,dole na tafi,but if you follow me then” Malika ta faɗa tana kallonta duk da ta san da wahala ne Nailarh ta amince zata bita, duk da itama ta fi son hakan tana so ta bata space ne ko hakan zai sa taji sauƙin abunda ke damunta
“zan biki” Nailarh ta faɗa,kallonta Malika tayi da mamaki “are u sure?”
“yeah am sure,zan tafi tare da ke”
murmushin Malika tayi mata,saurin shigewa tayi jikinta tana sake hugging ɗinta,a hankali ta ɗaura hannunta saman head ɗinta,shafa sumar kanta ta shiga yi
“baby wane lokaci ki ke ganin ya kamata muyi Aure?”
“you said next year”
“na canza ra'ayi yanzu kuma,da mun dawo daga wannan tafiyar kawai tunda kin sa na rabu da mijina”
“am sorry” Nailarh ta faɗa
“alright” nocking ƙofar ɗakin aka yi
“who there?” Malika ta faɗa
“ma'am its me,Noah” sakin Nailarh tayi ta nufi bakin ƙofar,buɗe ƙofar tayi
“is they anything?” ta faɗa tana kallonshi,ledan dake hannunshi ya miƙa mata “saƙo ne daga Dr Daniel, injection ɗin Madam Nailarh ce ya aiko da ita” amsar leda Malika tayi tana duba kwalin alluran dake ciki
“thank You” ta faɗa tana maida ƙofar ɗakin ta rufe,in da Nailarh take ta nufa
“i think tafiyar mu tare bazata yiwuba”
“why” Nailarh ta faɗa tana kallonta,leda dake hannunta ta nuna mata “allurace Daniel ya aiko da ita yanzu”
“ni fa am fine yanzu,babu wata allaura da za'a man”
“no Nailarh tunda ki ka ga ya aiko da ita tana da mahimmanci ne a gareki,kiyi haƙuri kawai ai ba jimawa zanyi ba zan dawo,karki manta we will get married soon” turo baki Nailarh tayi
“kiyi haƙuri kinji,zan ba Sophia sai ta dinga yi maki naga kamar towce ne far day, morning and evening”
“mu tafi tare da ita mana sai ta dinga man acan”
zama malika tayi tana kama hannunta “please Nailarh ki bari na tafi,time ɗin da zan dawo kinga kin ƙara samun sauƙi” lallashin Malika tayi har ta samu ta haƙura da tafiya.
Aunty Sophia Malika taba injection ɗin kamar yanda tace.
Aunty a salinta kafin ta zama nanny Nailarh a orpernage take aiki a matsayin Nurse anan Malika ta ganta har ta ɗauketa aikin nanny lokacin Nailarh na da shekara 3 a duniya,tunda ta dawo gidan Malika dan kula da Nailarh ta ajiye aikinta na Nurse,sai ta jima ba tayi allura ba ko wani abu daya shafi aikinta.

*ABUJA NIGERIA💋*


After Asr prayer gaba ɗayan su su ka hallara a katafaren meeting room ɗin gidan dake part ɗin Abbah.
Abbah na daga kan royel sofa a zaune yayin da gaba ɗayansu suke zaune a ƙasa saman rug carpet sun harɗe ƙafafunsu kamar ma su ɗaukar karatu,Nainarh na daga zaune kusa da Aunty Mariya da tunda ta zo gidan take maƙele da ita,har da ɗan faɗa ta mata saboda rashin zuwa gidanta da bata sake yi ba,mom a zaune take kusa da dady idanunta ta sauke akan Irfan da kwana biyu kenan rabon data sa shi a idonta,yana na daga zaune gefen ƙafanfun Abbah,kanshi a ƙasa,ƙallo ɗaya zaka mashi ka hango tsantsar damuwar da yake ciki,kwana biyu kacal amma duk yabi ya rame kamar ba shi ba,wani irin tausayin shi ne ya rufeta,amma ya za tayi,rabashi da Noor shi yafi Alkairi a gare shi,kallon ɗin Noor dake kwance saman jikin momynta tayi,itama duk ta fita hayyacinta,itama ba ƙaramar rama tayi ba abunka da mara jiki duk sai ta koma wani iri,har wani haske ta ƙara,sauke idanunta tayi ƙasa tana jin wani iri a zuciyarta.
Mama Ameenah tunda ta zauna wajen idanunta ke kan mom tana Binta da wani kallo mai cike da tsana,gaba ɗaya kallon da tayi ma Irfan da Noor akan idonta.
Laatifa suna wuri ɗaya zaune ita da su Aunty Nafisat,Aunty Nadeya da Aunty kainart sai Noha matar ya Usman ɗiyar Aunty Safeenah, baiwar Allah tunda su ka shigo parlorn idanunta ke kan dadynta da yayi kamar bai san da zamanta ba ko kallon inda take baiyi ba,idan ka cire su mamy da mom data san abunda ke faruwa,ba bu wanda bai tambayi ina mom maimunatu da Balqis ba, amma sai uncle Hashim yace ma su Balqis ce ba lafiya shiyyasa ba su samu zuwa ba.
Laatifa sosai hankalinta ya tashi jin ƴar uwarta ba lafiya,ta kira wayar su ya fi a ƙirga amma bata samu ba,wayar balqis na ringing amma ba tayi picking ba,mom maimunatu kuma tata a kashe,hakan ba ƙaramin ɗaga hankalinta ya yi ba.
Gyaran murya Abbah yayi gaba ɗayan su su ka kai dubansu gare shi,ya Naeem dake ɗayan gefenshi ya kalla yace ya buɗe masu taro da Adu'a,tashi yayi kamar yanda Abbah ya umarta,tsit parlorn yayi har ya kammala Adu'a ya koma mazaunin sa, gyara zama Abbah yayi cike da Dattaku da kamala ya fara magana
“Alhmdllh gaba ɗayan ku ina maku Barka da juma'a,da yawan ku nan sun san maƙasudin wannan zaman ɗai ɗai kun cikin ku ne ba su sani ba” tsit parlorn ya sake yi kamar mutuwa ta gitta “na tara ku nan ne saboda abun farin cikin daya same mu wanda nake fatan ɗorewar sa har bayan raina” tunda Abbah ya fara magana mom fatilah ta haɗe girar sama da ƙasa irin ba mutuncin nan
“shekarun baya da su ka wuce munyi ire ire wannan taron wanda da yawan ku sun hallara ƙalilan daga cikin ku ne basa nan,to kamar dai shekarun baya yau ma cike da farin ciki da fatan ɗorewar irin wannan taro nake sanar daku maganar Auren ƴan uwanku Irfan da Nurjahan . wanda za'ayi nan da wata uku idan Allah ya sa muna da rai da lafiya sai Waseef da Kairiyyah” Abbah na kaiwa nan yayi shiru, murmushi farin ciki ne ya bayyana akan fuskokin su dady,babu wanda a cikin su baiyi farin ciki da wannan haɗin ba,Irfan da Noor bugun zuciyarsu ne ya tsananta,abunda zai biyo baya daga iyayensu mata kawai su ke tsoro,ɗaga ido ya Naeem yayi yana kallon mom da kallo ɗaya zaka mata ka hango tsantsar damuwar da take ciki,mom fatilah tunda Abbah yayi shiru ta shiga aikama Irfan harara Kamar zata tashi ta rufe shi da duka.
“kamar ko wane lokaci bazan hana ku iyayen yara faɗar ra'ayin ku ba,ranar da aka tsaida tayi maku ko da mai abun cewa a cikin ku?” Abbah ya faɗa yana bin su da ido.
dady Ahmad da dady Mustafa wanda sune wakilan Irfan da Noor su ka yi saurin cewa
“babu wata matsala Abbah,duk lokacin da aka tsaida rana hakan yayi,Allah ya nuna mana lokacin bikin lafiya” da Ameen su dady su ka amsa,mom fatilah sai wani cika take tana batsewa,ji take kamar ta shaƙi wuyan uncle Mustafa da yayi maganar.
kallon dady da uncle mutallaf Abbah yayi
“ku fa hakan yayi maku?” dady ya bashi amsa da “ai ƴaƴan su ne Abbah,duk hukuncin da suka yanke yayi”
“to Masha Allah hakan yayi, shi kuma Waseef sai munji daga dangin mahaifin Kairiyyah,muji su kuma yaushe ne za su sa ta su ranar,sai ku iyayen su mata idan da mai abun cewa to” Abbah ya faɗa, tunda Abbah ya faɗi haka uncle mutallaf ke jefa ma mom fatilah wani irin kallo mai cike da gargaɗi amma sai ta kauda kamar ma bata san yana yi ba,tsit parlorn yayi babu wani wanda yayi making any move har Abbah ya fara tunanin ko ba mai abun cewa ne a cikin su,mom fatilah tana son magana amma uncle mutallab yaƙi bata space ga Noor daketa faman haɗata da Allah kan karta hanata farin cikinta
“kamar yanda muka haɗu haka Allah ya nuna mana ranar Auren lafiya” Abbah ya faɗa da Ameen duka su ka amsa.
kallon ya

Please Login or Register in order to submit comment