Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

murmushi tace
“morning balqis, yau kece da kanki?” murmushi balqis tayi tana faɗin “ayyuka ne su ka yima Aunty laatifa yawa shine tace nazo nayi attending wannan shari'ar dan bata so tayi missing”

“good,laatifa ba dai aiki ba” barrister ta faɗa,ƴan matan nan ne suka ƙaraso wurin su, mai niƙab ɗin ce ta gaishe da balqis yi tayi kamar bata san da ita take ba,saima kyauda kai da tayi tana kallon gefe, yamutse fuska mai kama da barrister tayi tana faɗin “Abun ma yar haka ce ko Aunty balqis” murmushi balqis tayi kamar ba ita ba tana faɗin
“miye kuma yumnah shagwaɓa” bubbuga ƙafa wacce aka kira da yumnah ta shiga yi tana turo baki da faɗin
“mom kina jin Aunty balqis ko, ba zata daina ce man haka ba”
“bana cike da wannan shiritar taki yumnah,balqis nayi ciki”

barrister ta faɗa tana yin gaba, bin bayanta yumnah da wannan budurwar dake sanye da niƙab su kayi yummah na cigaba da shagwaɓarta security guard ɗin na biye da su.

murmushi kawai balqis tayi tana komawa wurin aikinta.


Yan jarida na ta so suyi magana da barrister amma security guard ɗin ta sun ƙi ba su dama,amma saboda ƙwaƙwa irinta ƴan jarida ana ture su amma suna jefoma barrister tambayoyi.



A bakin ƙofar office ɗinta security
su ka tsaya macen dake ɗuke da jakarta da rigarta ce ka ɗai ta shiga ciki sauran securitys ɗin kuma su ka zagaye office ɗin yanda ko ƙuda bai isa ya gitta ba tare da sun ƙwamushe shi ba.


Wani irin haɗaɗen office ne naji da faɗa, yasha expensive desk da leather chair's masu shegen kyau ,barrister zulaihat kujerarta ta nufa ta zauna,akan desk ɗinta securityn ta ajiye mata hand bag ɗinta sannan ta rataya mata coat ɗinta jikin office suit hanger,wasu files ta ciro daga cikin briefcase ɗinta ta shiga dubasu tana ƙarasa haɗa hujjojine kafin lokacin shiga court ɗin yayi.


saman sofa dake cikin office ɗin yumnah su ka nufa su ka zauna sai a lokacin ne ɗayar ta yaye niƙab ɗin dake fuskar ta, masha Allah na furta da ganin kyakyawar fuskar matashiyar budurwar wacce a shekaru bazata wuce sha tara ko ashirin ba kusan sa'anni ne da yumnah.

damuwace ƙarara akan fuskarta, murmushi yumnah tayi tana faɗin
“yanzu dan Allah da ki ka cire wannan abun ba kiji daɗi ba?” kallon yumnah kawai matashiyar tayi ba tare da tace komai ba
“zaki fara wannan shirun naki ko, mom kiyi mata magana mana ta saki jiki da ni ko dan taga na damu da ita” yumnah ta faɗa tana wani ɓata fuska, girgiza kai kawai barrister tayi tana cigaba da aikin dake gabanta ba tare da tace ma yumnah komai ba.



“mom kema shirun zaki man?” ta faɗa tana turo baki kamar zata fashe da kuka

“yumnah wai miyasa ke baki san lokacin da mutum ke son magana da lokacin da bai so ba, baki san halin da take ciki bane zaki dameta?”

a hankali ta kama kunnenta tana faɗin “sorry mom, zama da damuwa bashi ke maganin matsala ba, that's why nake son ta ɗan saki jikinta” kallon matashiyar tayi tace

“sorry NAINARH idan na takura maki, inaso ki saki jiki ne kawai”

murmushi wacce aka kira da nainarh ta saki
“karki damu baki takura man ba, nagode da kulawar ki a gare ni”

martanin murmushi yumnah ta mayar mata tana buɗe hand bag ɗin data shigo da ita, ciro wayarta ƙirar iPhone 14 pro max tayi dialing wata number,waya ta shiga yi cike da shagwaɓa.



miƙewa barrister tayi da sauri security ta matso tana harharɗa files ɗin dake kan desk ɗin tana maidawa cikin briefcase, ganin haka ne yasa su yumnah miƙewa da sauri nainarh na maida niƙab ɗinta tana ɗaurawa, kallon su barrister tayi tace “ina zaku?” yumnah tace “mom ba time yayi ba”
“eh, ku zauna anan duk yanda shari'ar tayi za kuji” duƙar da kai nainarh tayi alamar ba haka taso ba


matsowa barrister tayi ta dafa kafaɗar “sorry nainarh ba dan wani abu yasa nace ku zauna nan ba sai dan tsoron abun da zai biyo baya acikin court, nan sai kin fi samun tsaro”

“shikenan mom,amma ba za'a neme ni ba?” nainarh ta faɗa
“babu mai neman ki, idan yiwuwar hakan ma ta taso za'a zo a tafi dake ne, fatana dai ki kwantar da hankalin ki” gyaɗa mata kai kawai tayi.


Komawa su kayi su ka zauna barrister kuma su ka fice,security tunda su ka ji alamun buɗe ƙofar office ɗin su ka gyara tsayuwar su tana fitowa su ka nufi cikin court ɗin har lokacin yan jarida basu daina binta da jefo mata tambayoyi.





ciki su ka ƙarasa security guard biyu ne suka shiga cikin court room haɗi da macen sauran su ka tsaya a waje, lokacin da su ka shiga court room ɗin a cike take,duk wani mai ruwa tsaki ya hallara suna zaune a mazaunin su yan jarida sun saita kamarorin su jiran a fara kawai su ke, balqis na daga zaune saman chair daga can baya,Attorney tables da aka tanada domin su ta nufa zama tayi security na ajiye mata briefcase ɗinta daga gefenta su ka tsaya,gaishe da ita attorneys ɗin su ka shigayi tana amsa masu cikin kulawa , mutum biyu ne a cikin su ko kallon in da take ba suyi ba,wata macece da wani namiji,fuskar ko wanen su a haɗe take kamar an aiko masu da saƙon mutuwa, namijin ya jingina da head board ɗin chair ɗin da yake zaune hannunshi riƙe da ƙwallon wasan chess yana wasa da ita saman desk,murmushi saki tana faɗin “good morning BARRISTER HASHIM” sai a time ɗin ya juyo masha Allah na faɗa kyakyawa ne na gaske fatar jikinshi chocolate color ce, kallonta yayi da wasu lumsassun idanuwanshi, kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kai yana faɗin “morning” kamar irin anyi mashi dolen nan,girgiza kai kawai tayi tana buɗe briefcase ɗinta ta fito da files da laptop ɗinta dake ciki......
_*Episode 3_4*_



*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘


_________________________



Prison officers ne su ka shigo su biyu sai mata guda biyu ma'aikatan prison sun sako wata mata a tsakiyar su yayinda police maza gudu biyar ke a bayan su kowanen su riƙe yake da bindigar sa,uniform ɗin prison ne a jikin matar inda a gaban rigarta aka rubuta number 106 da farin fenti’ black ɗin hulace a kanta,hannunta a sanye yake da handcuff, kanta a duƙe yake har su ka ƙarasa cikin court ɗin, kusa da brisster zulaihat matar ta zauna yayin da police ɗin su ka tsaya a bayan su.

ƙus ƙus ne ya fara tashi a cikin court room ɗin wasu na tausaya ma matar yayin da wasu ke kiranta da munafuka in sha Allah asirinta sai ya tonu.

shiru su kayi sun kafe juna da ido kowa na so yayi ma ɗan uwansa magana amma ya kasa daga brisster har mata,ƙwalla ne ya taru idon matar da sauri brisster ta miƙa mata handkerchief tana faɗin “karki kiyi kuka, in sha Allah yau gaskiya za tayi halinta” jinjina mata kai matar tayi tana goge hawayen dake zuba a idonta, brisster ma dauriya kawai take amma itama kukan take son yi kawai ta daure ne dan karta ƙara karyama matar zuciya.

A hankali matar tace “ina nainarh?”
“suna office ɗina ita da yumnah, na hanata shigowa nan ne dan ban san wani abu ya faru da ita” jinjina kai kawai matar tayi da ka ganta ka san tana cikin matsananciyar damuwa.

ɗaya daga cikin prison offices ɗin ne yace “hajiya za mu iya tafiya?” miƙewa matar tayi su ka nufi in da aka tanada domin zaman su,zama tayi matan su ka sata a tsakiya.

miƙewa su kayi gaba ɗayan su saboda shigowar alƙali,saida alƙali ya zauna tukun suma suka zauna,bayan koto tayi tsit, miƙewa judicial Assister yayi ya gabatar da ƙara bayan ya kammala ne alƙali ya buƙaci da lawyer masu ƙara ya fito.

Cikin ƙwarewar aiki clerk yake typing duk wani abu da ake furtawa a cikin court kama daga sunaye mutane har zuwa yanda shari'ar ke tafiya ga DAR (digital Audio recording ) box a gefenshi tana ɗaukar komai.

miƙewa tsaye brisster hashim yayi wasu files dake gabanshi ya ɗauka yana ajiye chess ball ɗin dake hannunshi, fitowa yayi daga inda yake zaune yana wani gyara zaman coat ɗin dake jikinshi,papers ɗin dake hannunshi ya miƙama judicial Assister, juyawa yayi ya miƙama alƙali.

“my lord wannan rahoton gawar marigayi ne wanda ƙwararon likitoci su ka gudanar tare da horoton cctv camera dake gidan shi, sai bincike da ƴan sanda su ka gudanar akan shatin hannun hajiya Asma'u da aka samu a jikin bindigar da aka kashe marigayi da duk wasu wayoyi daya amsa kafin faruwar abun,sai sunayen witness”

yana gama faɗa ya koma mazauninshi ya zauna yana ɗaukar ball ɗin shi ya cigaba da juyata saman table.

miƙewa mom tayi cikin taƙon kamala ta fito tsakiyar court,ɗan rissinar da kai tayi tana kallon alƙali alamar girmamawa, jinjina mata kai alƙalin yayi,takardar dake hannunta ta miƙama judicial Assister tana faɗin
"my lord wannan sune jadawalin shedo da nayi ma court alƙawarin kawowa"

tashi judicial Assister ɗin yayi ya miƙama alƙali takardar, amsa alƙalin yayi yana ɗaukar glass ɗin shi ya manna a ido, ya ɗan ɗauki tsawan lokaci yana duba duka takardun harda wanda brisster hashim ya bada kafin yace“zaki iya tafiya” godiya tayi mashi tana komawa ta zauna.

“idan malam Aisha tana kusa ta matso gaban koto” Alƙali ya faɗa, a hankali matar ta miƙe daga cikin mutanen dake zaune saman chair, jikinta sai rawa yake daga ganin yana yinta bata cikin natsuwarta,ƙarasowa tayi ta tsaya a cikin witness stand, tashi mom tayi ta nufi in da matar ta tsaya.

ƴan jarida nan su ka fara ɗaukar komai, tasowa balqis tayi ta dawo inda mutane su ke hannunta riƙe da abun magana,juyawa tayi saitin da attorney su ke karab idanunta su ka haɗu da na brisster hashim wani ɗan iskan kallo ya watsa mata wanda yasa ƴan hanjin cikinta kaɗawa ita kaɗai ta san ma'anar wannan kallon daya watsa mata , da sauri ta duƙar da kai tana juyawa ta bar wurin da sauri, gyaɗa kai yayi yana maida hankalinshi ga Alƙali.


Rantsuwa Alƙali ya fara sa Aisha tayi akan zata faɗin gaskiya, kafin ya ɗaura da cewa “court na san sanin cikaken tarihin ki?”
kasa magana tayi saboda wani irin rawa da jikinta yake har sai da Alƙali ya sake magana “kina ɓata ma koto lokaci" da ido mom tayi mata alama data kwantar da hankalin ta, magana ta fara cikin rawa rawar murya dake nuna rashin natsuwarta

“suna na Aisha Usman shekaruna 42 ni ƴar asalin garin faskari ce dake jahara katsina,nazo Abuja ne ta dalilin wata ƙanwar mahaifiyata itace sanadiyyar fara aikina a gidan marigayi”


“malama Aisha tsawan wane lokaci ki ka san marigayi da matar shi hajiya Asma'u?”

“tsawan shekara goma sha biyar”
“ko zaki iya faɗa ma court yanda zamantakewar gidan take tsakaninki da masu gidan?”

“mutanene masu karamci da san al'ummah ko da kuwa ya kasance na ƙasa da su ne, duk tsawan shekarun dana ɗauka tare da su basu taɓa nuna man cewa wai ni ƙasa nake da su ba, hajiya Asma'u ta ɗauke ni tamkar ƙawarta kuma ƴar uwarta,haka marigayi tamkar ƴar uwarshi ta jini haka ya ɗauke ni”

ƴan rubuce rubuce Alƙali yayi kafin ya ɗago yana faɗin “ko zaki iya bama court labarin yanda kisan marigayi ya....” tun kafin Alƙali ya ƙarasa magana tayi saurin ƙatse shi jikinta na rawa tace “wallahi ni ban san komai a game da kisan marigayi....”

desk Alƙali ya buga yana faɗin “nan court ce, ki san yanda zaki riƙa magana, laifi ne Alƙali na magana ka tari numfashin shi, ki kiyaye”

“tuba nake” ta faɗa

tunda Alƙali ya fara magana gaban matar nan ke faɗuwa, tama kasa ɗagowa ta kalli Alƙalin ko mutanen dake cikin court ɗin,brisster hashim kuwa da wannan matar tunda Alƙali ya fara gabatar da ƙara ya mida hankalin shi kan Alƙali ko motsin kirki ba yayi ƙwallon chess ɗin dake hannunshi ma ajiyeta yayi.

tambayar Alƙali ya sake jefa mata, kawai sai gani a kayi tafashe da kuka abun yayi matuƙar ɗaurema brisster kai hajiya Asma'u kuwa jikinta sanyi yayi zuciyarta ta karaya, ta san da wahala ta ƙubuta, Aisha ka ɗaice shedar da take ganin zata iya taimakawa wajen faɗar gaskiya.

wicked side smile brisster hashim ya saki, yana kallon macen dake kusa da shi su ka kashe ma juna ido, da yawan brisster's ɗin dake wurin sun jin daɗin yanda abun ke tafiya ƙalilan ne abun ya taɓa zuciyar su.

sai da ta gama kukan mai isarta tukun Alƙali yace“koto na saurarenki”

“wallahi ni ban san komai ba, hasalima bana garin abun ya far.....”

da sauri brisster zulaihat ta tari numfashin matar tana faɗin
“my lord!, shaidata ta shiga halin ruɗani, tana tsoron magana a gaban court sabo....”

da sauri matar tace “babu ruɗanin da na shiga, kuma ba wai ina jin tsoro ba ne , gaskiya ce nake faɗa, bana nan abun ya faru” matar ta faɗa with full confidence,mamaki kamar ya kashe mom, saboda Aisha tana Abuja komai ya faru amma a gaban koto tace bata nan, brisster hashim har ƙara gyara zama yake abun yana tafiya yanda yake so.

“laifi ne katse shaida yayin bada amsar da Alƙali ya tambaye shi, brisster ki kiye”

“tuba nake” ta faɗa

“ina ki ka je a lokacin da abun ya faru?” Alƙali ya jefa mata tambaya

“naje garin mu domin duba jikin ɗana da ke fama da ciwan daji ( cancer ), kuma hajiya Asma'u da kanta ta bani izinin tafiya ita da mijinta”
“ A ranar yaushe ki kayi tafiyar?”

“na tafi garin mu ranar laraba a washe garin ranar Alhamis nake samun labarin abun da ya faru”

“mi yasa baki dawo ba da ki ka samun labarin abun da ya faru da ubangidan na ki?”
“saboda lalurar ɗana, jikinshi ne yayi tsanani shiyyasa ban samu damar zuwa ba”


ƴan rubuce rubuce Alƙali yayi kafin yace “zaki iya komawa ki zauna, kotu za tayi bincike akan bayanan da ki ka bata, lawyer masu ƙara ko kana da tambayoyin da za kayi ma malam Aisha” miƙewa brisster hashim yayi yana gyara zaman coat ɗin shi, cikin takun ƙasaita ya nufi tsakiyar koton, cikin maganar ƙasaita yake faɗin “my lord, ina so zanyi ma shaida wasu ƴan tambayoyi”

izini Alƙali ya bashi
“godiya nake” ya faɗa yana matsawa in da Aisha take tsaye

“malam Aisha ina so zanyi maki wasu ƴan tambayoyi,ya zamantakewar iyayen gidan naki take, shin kafin mutuwar cp ko a kwai wani saɓani da ya taɓa shiga tsakaninshi da uwar ɗakin ki, ko akwai rashin jituwa tsakaninsu, wasu dai Abubuwa maka mantan haka???”

“babu yallaɓai,a kwai fahimta a tsakaninsu, marigayi yana matuƙar kyautata ma matar shi hatta mu ƴan aiki ya ɗauke mu da matuƙar daraja”

jinjina kai brisster hashim yayi yana faɗin “ita fa uwar ɗakin taki, ya nata halayen su ke, bata da wasu ɗabiu marasa kyau wanda baku jin daɗin su???”

ran brisster zulaihat ne ya fara ɓaci da irin tambayoyin da brisster hashim kema Aisha

“gaskiya babu”
“koda a ɓoye bata da su?” ya sake mata tambayar, miƙewa brisster zulaihat tayi rai a ɓace “objection my lord”

“sustained”Alƙali ya faɗa yana bata izini

“lawyer masu ƙara kamar yana son tursasa witness ɗina akan dole sai ta faɗi abun da bashi ba”

“brisster hashim ka kiyaye” jinjina kai brisster hashim yayi

“malam Aisha a ra'ayin ki ne ki ka tafi gida ko kuwa uwar ɗakin kice ta nuna dacewar tafiyar ki a wannan lokacin?”

“Itace tace ya kamata na tafi na duba jikin shi , da tace man haka sai nace mata zan shirya ranar juma'a ko asabar naje amma sai tace na shirya gobe na tafi da farko naƙi amincewa da tafiyar a washe garin nace kawai zan tura masu kuɗin su fara amfani dashi kafin zuwa ranar juma'ar na tafi, amma sai ta zaunar dani ta nuna man dacewar na tafi a goben shine na amince”

“da tace ki tafi a lokacin ba kiyi wani tunani ba ko akwai dalilin da yasa tace kije?”

Miƙewa brisster tayi tana ɗan dukan table ɗin dake gabanta “objection my lord”

“Overruled”Alƙali ya faɗa

komawa tayi ta zauna tana cizon yatsa na rashin bata dama da Alƙali yayi, side smile brisster hashim ya saki

amsar tambayar da brisster hashim yayi mata ta bashi

“banyi tunanin komai ba, saboda idan ahalina suna cikin matsala ta kan fini shiga damuwa akan halin da nake ciki,shiyyasa banyi zargin komai ba”

jinjina kai brisster yayi “mudi mai gadi ya sanar da koto cewa akwai wani matashin saurayi dake yawan zuwa wurin uwar ɗakin na ki, baki taɓa tunanin mike kawoshi wajenta ba , ko miye alaƙarta da shi ???"


“sunan sa Abid, ɗan ƙanwarta ne dake zaune a ƙasar waje, yana yawan zuwa wurinta duk lokacin da yazo suna samu saɓani da marigayi saboda kwata kwata jinin marigayi bai haɗu dana Abid ba, saboda Abid yaro ne mara tarbiya baya girmama na gaba da shi , gashi duk lokacin da yazo sai ya takura ma yarinyar su , hakan yasa marigayi baya son yana zuwa gidan, ita hajiya sai ta nuna ba taji daɗi ba kan nuna kyara da tsangwama da yake akan yaron, a ranar da mu kayi magana kan tafiyata ya zo gidan har saɓani ya shiga tsakanin shi da marigayi ya dake shi, abun yayi matuƙar ɓata ran hajiya har su ka samu saɓani da marigayi, bayan mungama magana da ita naje ɗakina na wanke kayan da zan tafi da su na zagaya baya zanyi shanya na hangesu ita da Abid suna tattauna wasu maganganu wanda ban san mi su ke tattaunawa ba, nayi ƙoƙarin naji abun da su ke faɗa amma abun ya gagara saboda tazara dake tsakanin mu,bayan na koma ɗakina cikin dare naji Abid ɗin yana waya a bayan ɗakina kamar yana faɗama wanda suke waya saɓanin da su ka samu da marigayi bana jin mi na ciki wayar ke faɗa masa na dai ji yana faɗin a cikin satinnan ya kamata suyi aiki a kanshi ko zai daina mashi shiga hanci da ƙudindine, na tsorata da jin abun daya faɗa har na kasa bacci , washe gari tunda safe na samu hajiya da maganar amma sai ta nuna kar na damu da abokan kasuwancin shi yake waya”


tunda Aisha ta fara jera wannan jawabin gaban hajiya Asma'u ke faɗuwa bata taɓa sanin komai dake faruwa a gidan Aisha na sane ba sai yanzu.

“abokan ka suwanci, ko kin san wane irin ka suwanci yake?, sannan wane saɓani ya shiga tsakanin shi da marigayi?”

“gaskiya ban san kasuwanci da yake ba, amma na taɓa jin labari a wurin mai gadi cewa yaron yana harkar kayan maye , kuma dukiyar da yake juyawa ta hajiya Asma'un ce ”

jinjina kai brisster yayi
“wane saɓani ne ya shiga tsakanin shi da marigayi?” ya sake maimaita mata tambayar
“gaskiya ban sani ba”

juyawa brisster hashim yayi ya kalli Alƙali “my lord , tun ranar da mai gadin gidan ya ba police duk wasu bayanai akan yaro suka tsaurara bincike sai dai kash bayan kwana biyu da fara binciken na su aka samu gawar shi yaron a cikin gidan shi anyi mashi kisa makamancin na marigayi,hakan na nufin hajiya Asma'u ta tura Aisha gida ne dan ta samu damar aiwatar da shirinta ba tare da wani ya ganota ba,sannan ta sallami ma'aikatan gidan dan kar su ga abunda zai faru,Abid ya ƙi bata haɗin kai ne shiyyasa ta tura makasan da su ka kashe cp su ka kashe shi dan kar ya zame mata matsala”

“Objection my lord”
jinjina mata kai Alƙali yayi alamar amincewa

“my lord lawyer masu ƙara na son tabbatar da laifi akan wacce nake karewa ba tare da ƙwararan hujjoji ba”
“brisster hashim ka kiyaye”
“tuba nake”

jinjina kai Alƙali yayi kafin ya ɗauki pen ɗin shi yayi ƴan rubuce rubuce

“lawyer masu ƙara ko kana da sauran wasu tambayoyi da za kayi ma malam Aisha”

“su kenan tambayoyin da nake son yi mata” brisster hashim ya faɗa, tsaki brisster taja a zuciyarta tana faɗin
“ko ina amfanin wannan tambayoyin”

“lauyan wanda ake ƙara ko kina da wasu tambayoyi da za kiyi ma malam Aisha?”

miƙewa brisster tayi “eh my lord” dama Alƙali ya bata, fitowa tayi brisster hashim kuma ya koma mazauninshi.

“malam Aisha a bayanan da hajiya Asma'u ta bada da kuma binciken da muka gudanar ya tabbatar mana da cewa kina a gidan a ranar da abun ya faru , hasalima kece ki ka fara sanar da su zuwa mugayen mutanen da su ka shigo gidan”

“wallahi brisster bana garin ita da kanta tace naje, munyi maganar da ita yau washe gari tunda safe na tafi”

murmushi gefen fuska brisster ta saki tana faɗin “ƴan uwan naki su su ka bada shedar cewa a ranar ba kije garin naku ba sai a washe garin ranar da abun ya faru”

shiru Aisha tayi ba tare da tace komai ba
“malama Aisha ke koto ke saurare?”
“ranar na tafi sai dai ban samu isa garin ba sai cikin dare,hakan yasa basu san da zuwa na ba sai washe gari”jinjina kai brisster tayi tana juyawa ta kalli Alƙali

“my lord malama Aisha ta sanar da koto cewa bata nan abun ya faru, a binciken dana gudanar ya tabbatar man da tana a cikin komai ya faru”

“binciken koto zai tabbatar da hakan, kina da sauran wasu tambayoyi da za kiyi mata”

“babu sauran wasu tambayoyi da zanyi mata”

“malam Aisha zaki iya komawa mazauninki kafin binciken koto ya kammala”
“godiya nake” ta faɗa tana ɗan rissinar da kai,barin witness stand ɗin tayi ta koma mazauninta ba tare da ta bari sun haɗa ido da brisster ba ko hajiya Asma'u.

brisster wurin zamanta ta koma itama,haka shari'ar ta cigaba da tafiya duk wasu jadawalin sunayen witness ( sheda) sai da Alƙali ya kira su gaban koto yana masu tambayoyi bayan ya kammala masu ya ba brisster's dama suma suyi masu nasu tambayoyi, ko wane sheda da kalar amsar da yake ba dawa a kan kisan marigayi CP,hajiya Asma'u tun tana sa ran kuɓuta har ta sadaƙata tasan bazata taɓa kuɓuta ba daga yanayin amsoshin da shedun ke ba court,brisster ma gwiwowinta sun sage bata taɓa shari'a irin wannan ba tana shari'a akan kisa amma kuma bata taɓa rashin nasara ba amma wannan shari'ar na neman tafi ƙarfinta , shedun da take taƙama dasu gaba ɗaya sun juya mata baya,duk wanda aka kira a cikin su abu ɗaya su ke faɗi hajiya Asma'u ta kashe mijinta kuma suna bada ƙwararan hujjoji wanda dole koto ta yarda .


brisster hashim kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha yasan zaiyi wuya yau bai yi nasara akan brisster zulaihat ba abun da ya daɗe yana jira kenan tsawan shekaru.

Magana Alƙali ya fara, tsit kotun tayi kowa na sauraron hukuncin da court zata yanke “binciken kotu ya tabbar da malam Aisha bata nan a ranar ashirin da ɗaya ga watan biyar”

Ajiyar zuciya Aisha ta sauke tana dafe saitin zuciyarta, brisster wani mugun faɗuwa gabanta yayi hajiya Asma'u kuwa tuni hawaye sun taru a cikin idanunta

“bayan kammala haɗa duk wasu hujjoji da binciken koto dana likitocin dake kula da gawar marigayi CP ya tabbatar da hajiya Asma'u itce ta kashe CP” tunda Alƙali ya fara magana brisster hashim ke sakin murmushi, brisster zulaihat kuwa banda faɗuwa babu abun da gabanta ke yi.

“kotu ta yanke ma hajiya Asma'u hukuncin kisa ta hanyar rataya tare da biyan tara ta naira milayan hamsin”

Wani irin murmushin farin ciki barisster Hashim ya saki yana kallon ƴan uwan shi wanda hukuncin yayi masu dai dai,a ɗayan ɓangaren kuwa barisster Zulaihart wani irin tashin hankali mara misaltuwa ta tsinci kanta, da dama mutanen dake Court ɗin abun yayi masu daɗi yayin da wasu ke tausaya ma Hajiya Asma'un.

ana cikin jimamin hukuncin da court ɗin ta yanke sai ga saƙo daga fadar shugaban ƙasa na nemama Hajiya Asma'u sassaucin kotu daga rataya zuwa ɗaurin rai da rai tare da biyan tara ta nera miliyan ɗari saɓanin hamshin.

Ran barisster hashim idan yayi dubu ya ɓaci ba haka yaso ba yaso hukuncin kisa aka yanke mata ta hanyar rataya bai so ɗaurin rai da rai ba amma idan ya tuna ba wai zata fito bane sai hankalishi ya

Please Login or Register in order to submit comment