Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tumtum yayin da ƴaƴan shi ke kewaye dashi sun saka shi tsakkiya,fira suke cike da nishaɗin.


su goma ne ƴaƴan Abbah dady shine babba daga shi sai uncle Ahmad daga su sai uncle Mustafa da uncle Ubaid daga su sai uncle mutallaf daga shi ne sai barrister Hashim da Aunty mariya daga su sai Aunty Safeenah da uncle Khamis daga su sai Aunty Adama ita ce Autar Abbah.


gaba ɗayan su ne a parlorn uncle Khamis ne kawai babu shima baya ƙasar ne tsawan shekara 19 kenan rabon shi da ƙasar,shi ka ɗai ne a cikin su baya da Aure.


Dady na daga hannun daman shi yayin da dady Ahmad ( mr president ) ke kusa da shi sai
Uncle Mustafa, Uncle ubaid da uncle Hashim, ɓangaren hagu kuma Aunty mariya,Aunty safeenah da Aunty Adama ne sai uncle mutallaf dake tsakiyar su,Irfan da Waseef na daga saitin kan Abbah zaune,gaba ɗaya hankali su na kan Abbah dake basu labarin yarintar su dady cike da nishaɗi.



sallamar mom ce ta katse masu firar da suke,gaba ɗayan su suka kai duban su gareta, murmushi ne ya bayyana akan fuskar Abbah da alama yaji daɗin zuwanta,kaf cikin surikan sa babu wacce yafi so sama da mom,tamkar ɗiya haka ya ɗauketa,idan ka cire barrister Hashim da Aunty Safeenah babu wanda baiyi farin ciki da zuwanta ba,da sauri Aunty Adama ta tashi fuskatar ɗauke da murmushi ta nufo mom.


hugging ɗin juna su kayi hakan ba ƙaramin ɓata ran Aunty Safeenah yayi ba,kauda kai tayi gefe tana jan tsaki, cike da kewar juna suka gaishe da juna,cikin parlorn su ka ƙarasa,wurin Abbah mom ta nufa fuskarta ɗauke da murmushi.


zama tayi kusa dashi “in wuni Abbah,mun sameku lafiya?”
“lafiya lau Alhmdllh,ya gidan ya kuma aiki”
“lafiya lau” Masha Allah Abbah ya furta,duban ta ta kai ga dady Ahmad cike da girmamawa ta gaishe da shi,cikin kulawa ya amsa mata yana tambayar Yumnah.


ɗaya bayan ɗayan tabisu tana gaishe da su,cike da kulawa su ke amasa mata in ka cire barrister da Aunty Safeenah da su kayi kamar ba su san da su take ba,hakan kwata kwata bai dameta ba dan idan da sabo ta saba da halin su,dady baiji daɗin hakan ba ya rasa miye matsalar ƴan uwanshi da matar shi.


“Ashe abun da ya faru da Asma'u kenan?, ubangiji Allah yayi mata mafita,Allah ya kuɓutar da ita,su kuma wanda su ka da baibaye ta da sharrin Allah yayi gaggawar tona masu Asiri” Abbah ya faɗa

da Ameen ya Allah Abbah su ka amsa banda uncle Hashim da yayi tsit kamar baya parlorn


“Allah ya kuɓutar da ita ya kyauta gaba” a cewar uncle Ahmad da Ameen su ka amsa suma,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga yi mata jaje in ka cire Aunty Safeenah data miƙe ta nufi ƙofar fita, barrister Hashim kuwa lumshe idonshi yayi kamar mai bacci .


“saffenah!!” Abbah ya kira sunanta,dakatawa tayi da tafiya ta juyo tana fuskantar shi

“ina zaki kowa na nan?”
“zan shiga wajen mama ne,naga an gama firar zumunci tunda har bare sun fara zuwa shiy...”

bata ƙarasa ba sakamakon tsawar da dady ya daka mata
“Abbahn ki ke faɗama haka?,maza ki dawo ki zauna kafin ranki ya ɓaci” murmushi kawai mom tayi bata so dady yasa baki ba.

rai a ɓace ta nufi wajen zamanta zata zauna
“jeki kawai” Abban ya faɗa,babu ko kunya ta juya ta fice,kauda kai kawai dady yayi da alama baiji daɗi ba,kallonshi Abbah yayi yana sakin murmushi haɗi da girgiza kai.

A bakin ƙofa Aunty Safeenah taci karo da su Yumnah, fuskar su ɗauke da murmushi su ka gaishe ta,ta amsa ma kowa amma banda Yumnah da Nainarh da tabi da wani irin kallo mai wuyar fassarawa.


hankali Nainarh ba ƙaramin tashi yayi ba da irin kallon da Aunty Safeenah tayi mata,duk sai taji wani iri dama ba tayi niyyar zuwa ba Yumnah ta jawota tasan dama ba dole bane dangin Yumnah su sota ba.


ganin yanayin data shiga ne yasa Fa'iza kamo hannunta cikin nata,da murmushi akan fuskarta tace “muje ko”
tura ƙofar parlorn tayi su ka shiga bakin su ɗauke da sallama,gaba ɗaya parlorn su ka kai duban su gare su.


Amsa masu sallamar su kayi in ka cire uncle mutallaf daya kafe Nainarh da ido ko ƙyaftawa baya yi uncle Ahmad ma kallon sani yake mata,har suka ƙaraso cikin parlorn uncle mutallaf bai janye idanunshi daga kanta ba har sai da Abbah yayi mashi gyaran murya tukun yayi sauri kauda idoshi daga kanta ya kalli Abban,hararar wasa Abbah ya watsa mashi.


saurin duƙar da kai yayi duk sai yaji kunyar kamashin da Abbah yayi yana kallonta yasan Abbah zaiyi tunanin wani abu shi kuwa har ga Allah kama tayi mashi da wacce ya sani.


zama su kayi kan rug carpet ɗin cikin kulawa su ka gaishe da su suna amsa masu,nuna Nainarh Abbah yayi da hannu
“in ku ka samu wannan mai kama da mariyata?” gaba ɗayan su suka kai duban su ga Nainarh sai da Abbah ya faɗa su kaga kamaninta da Aunty mariya in ka cire mom da dady dan su sunfi ganin kamaninta da Carol ƙanwar mom,sai yanzu uncle mutallaf ya fahimci da wacce take mashi kama.


kallo ɗaya Irfan da barrister suka yi mata suka kauda kai
“ƴan mata yaya sunan ki?” Aunty mariya ta faɗa tana kallon Nainarh
“NAINARH” ta bata amsa,jinjina kai Aunty mariya tayi “masha Allah, Nainarh suna mai daɗi” Aunty mariya ta faɗa, murmushi Nainarh ta saki a hankali ta furta “nagode”



juyawa Aunty mariya tayi ta kalli mom,fahimtar abunda Aunty mariya ke nufi ne yasa mom faɗin “ɗiyar Asma'u ce”

“Allah sarki” Abbah ya faɗa cike da jin tausayin Nainarh,babu wanda baiji tausayinta ba jin itace ɗiyar Hajiya Asma'u, barrister Hashim kuwa ko a jikinshi.


“sannu kinji Nainarh Allah ya kuɓutar da mahaifiyar ki” a cewar Abbah ,gaba ɗaya parlorn su ka amsa da “Ameen ya Allah” fira suka shiga yi cikin kwanciyar hankali.


Noor tunda su ka shigo Irfan ke Binta da wani irin narkaken kallo,itama tunda ta zauna hankalin ta na kanshi,wasu alamomi yake mata da ido wanda daga ita sai shi su ka san ma'anar su,sosai su ka shagala da kallon juna ƙarshe da su ka gaji tashi Irfan ɗin yayi ya nufi ƙofar fita shida Waseef ,zambur ta miƙe tabi bayan su babu wanda ya lura da ita sai Yumnah da Kairiyyah dake kusa da ita.

A parlor Waseef ya tsaya Irfan kuma ya nufi back yard,wassef na zaune sai ga Noor,nufoshi tayi cikin takun sauri “ya Waseef yana ina?”


“back yard” ya bata amsa,da sauri ta nufi ƙofar da zata sadata da back yard ɗin gidan, gyara zaman shi yayi kan sofa yana ciro wayar shi daga Aljihu.



tun daga nesa ta hango shi ya jingina da wall gaba ɗaya hannuwanshi na cikin Aljihun wandon shaddarshi, idanunshi a lumshe suke kamar mai bacci,a hanzarce ta ƙarasa in da yake tun kafin tayi magana ƙamshin turarenta ya sanar da shi isowar ta,a hankali ya buɗe idanunshi a kanta.


wani irin kallo ya shiga binta da shi yayin da ita kuma ta marairaice mashi fuska kamar zata sa mashi kuka.



“shine daka shigo kayi kamar baka ganni ba ko?” ta faɗa a shagwaɓe,buɗe mata hannuwanshi yayi alamar ta zo gare shi, ba tayi musu ba ta nufe shi,faɗawa tayi jikin shi, hugging ɗin juna su kayi tightly kamar za su koma abu ɗaya.


matso da baƙin shi yayi saitin kunnenta,magana ya fara yi mata kamar mai raɗa
“duk laifinki ne miyasa kin san tare za ku zo da dady baki faɗa man ba,kin san yanda nayi kewarki kuwa?”

“ina so nayi surprising ɗin ka ne shiyyasa”ta faɗa a shagwaɓe
“kinyi missing ɗin na?”
“sosai ma,har gani nake kamar bama sauri da muna tafiya”

“amma shine baki nemi ni ba ki ka zo part ɗin Abbah?”
“saboda na san anan zan same ka”
“da ban zo ba fa?”
“nama san bazaka ƙi zuwa ba”


raba jikin su yayi yana jan hannunta su ka nufi wasu haɗaɗun chairs dake back yard ɗin,zama yayi saman ɗaya daga cikin kujerun yana nuna mata ta kusa da shi,maƙe mashi kafaɗa tayi alamar bazata zauna ba,hannunshi ya miƙa mata babu musu ta kama jawota yayi zuwa jikinshi yayi mata mazauni akan laps ɗin shi, murmushi ta saki tana lafewa a jikin shi.


shafa doguwar sumar kanta dake a buɗe ya shigayi yayin da ita kuma tayi lamo har wani lumshe ido take.



*😳 Irfan⁉️*



idan mu ka koma parlorn Abbah,sun jima suna fira sai da lokacin zuwa masallaci yayi tukun su ka tashi,ficewa mom tayi tare da su Aunty Mariya da su Yumnah, wani ɗan corridor dake kallon parlorn Abbah su ka nufa.


wani irin hamshaƙin parlorn ne su ka shigo,yaji kayan alatu kamar a gidan sarakai,ga wasu jigunannun sofas masu rai da lafiya har set biyu.


Aunty Safeenah ce zaune saman sofa mai mazaunin mutum uku yayin da mamy ke hakimce kusa da ita ta ɗau wankan less ɗinkin riga da zani kamar ko wane lokaci zaka samu fuskarta da makeup,sofa dake kusa da su Hajiya fatilah ce matar uncle mutallaf tare da Hajiya Halima matar Uncle Ubaid sun ɗau wankan tsadadden less mai shegen kyau,fuskarnan ta su tasha makeup hannuwan su a cike su ka da ƴan hannu da zobba na zallar zinari.


Mama Ameena ce hakimce saman sofa mai mazaunin mutum biyu dake kallon ƙofar shigowa parlorn,super atamface a jikinta anyi mata ɗinkin riga da zani kalar na su na tsaffi,ta dafka uban ɗaurin ɗankwalinta kamar koda yaushe.


cikin parlorn su mom su ka nufo bakin su ɗauke da sallama,tsuke fuska mama tayi lokacin da idanunta su ka sauka kan mom,taɓe baki mamy tayi tana kauda kai.


Amsa masu sallamar su kayi in ka cire mamy dake cin ɗaci sai wani buɗar hanci take,
har gaban sofar da mama take zaune mom ta ƙara so,cikin girmamawa ta gaishe da ita,cike da izza tana wani yamutse fuska ta amsa mata a taƙaice,lamarin yaba Nainarh mamaki ita da abun ya zama sabo a idonta amma duk wanda ke parlorn yasan cewa babu jituwa tsakanin mama Ameenah da mom kwata kwata bata sonta.


Mama Ameenah matace ga Abbah,ita ta haifi Aunty Adama,ita ka ɗai ta rage a matan Abbah,kwata kwata bata ƙaunar mom.


“mun same ku lafiya?”
“ga zahiri kuwa kin gani” mama Ameenah ta faɗa tana nuna kanta da hannu, murmushi ne ya bayyana akan fuskar mamy da su Hajiya fatilah da alama abun yayi masu daɗi.

shiru mom tayi ba ta sake cewa komai ba,gaishe da mama su Yumnah su kayi, a taƙaice ta amsa masu tana sauke idonta kan Nainarh da duk tasha jinin jikinta.

“ita kuma wannan ina aka sameta?” mama Ameenah ta faɗa tana nuna Nainarh da hannu,faɗuwa gaban Nainarh yayi,gaba ɗaya parlorn duban su suka kai ga Nainarh.


“ɗiyar Aminiyata ce Hajiya Asma'u” mom ta faɗa,jinjina kai mama tayi
“ziyara ta zo maki ko mi?”
“A'a wani iftila'i ne ya faɗama mahaifiyar ta,to shine na daw...” bata ƙarasa ba mama tayi saurin dakatar da ita
“to sai aka yi yaya,zama mi take cikin zuri'ata,ita mahaifiyar ta ta bata da dangi ne da bazaki barta a hannunsu ba,?”


“ba haka bane mama,zaman...”
“dan Allah dakata mana Zulaihart, wai sau nawa zance karki sake kirana da mama,banda jaza masifa ina ni ina haihuwar dangin sheɗan wanda Allah ya tsinemawa,ko nayi maki kama wannan tsohuwar banzar mai yawo ƙwauri waje??”

ƴar dariya mamy tayi tana kallon su Hajiya gaje
“Allah ya huci zuciyarki” mom ta faɗa tana tashi, ta nufi ƙofar fita daga parlorn, Yumnah idanunta har sun cika da hawaye bakomai yasa bata son zuwa part ɗin Abbah ba idan ba ranar Friday ba sai dan saboda wannan cin mutuncin da mama kema mom,tashi tayi tana kama hannun Nainarh da duk jikinta yayi sanyi.


Fa'iza ma ranta ba ƙaramin ɓaci yayi ba,tashi itama tayi ta bi bayan su da kallon mamaki mamy tabita har ta fice daga parlorn.

rai a ɓace Aunty Adama ta kalli mama Ameenah
“gaskiya wannan abun mama da ki ke a gaban ƴaƴa da jikokin ki bai dace ba,haba dan Allah da shekarunki zaki zauna yara na zugaki kina abu irin haka”


“kamarya yara na zugata, mi kike nufi Adama?”mamy ta faɗa rai a ɓace
“da mahaifiyata nake magana ba dake ba,karki ƙara sa man baki,kuma duk abunda take akwai mai zugata sama da ku ne?”


tsantsar mamaki ne ya bayyana a kana fuskar mamy wai yau ita Adama ke faɗama haka “lallai Adama Ni kike faɗa ma haka saboda Zulaihart?”


“fiye da haka ma sai ta faɗa maki mabaruka,gaba ɗaya ku babu mai hankalin data san abun da ya kamata,mama shekarunta sun ja tunaninta baya yake komawa,maimakon ku zama masu bata shawara idan kunga za tayi abun da ba dai dai ba amma saboda son zuciya kullum cikin birkita mata tunani kuke,babu wanda yafi bani haushi a cikin kuka sama da ke Safeenah” Aunty Mariya ta faɗa rai a ɓace tana kallon Aunty Safeenah


“ni mi nayi Aunty mariya,babu ruwana fa a cikin wannan abun?”
“dama zaki ce haka mana,akwai wanda ya ɗaure masu gindin yin abunda su ka ga dama sama dake,kina ƙanwar mazajensu ko kunya bakiji”



“da Allah ya isa haka mariya,ni ya kamata Ku rufe da faɗa ba su ba,kune za ace ma ko kunya ba kuji,kun fifita bare sama da ƴan uwanku musulmai,ko da yake ke barewa ai baza tayi gudu ɗanta yayi rarrafe ba”


“ko mi zaki ce mama a shekarunki wanan abun da ki ke bai dace ba” Aunty Mariya ta faɗa tana nufar wata ƙofa,da harara mamy ta bita har ta shige ɗakin,tsaki Aunty Adama taja tana bin bayan su mom.


“aikin banza dana wofi, kullum da an taɓa wannan dangin sheɗan ɗin sai su rufe mutane da faɗa kamar wasu ƴaƴan cikin su” Hajiya Gaje ta faɗa tana sake jan wani tsaki
“gaba ɗaya zanyi maganin su ne daga su har ita” a cewar mama Ameenah


“wallahi mama karki bari yarinyar nan ta zauna,ta maidata can dangin uwarta,haka kawai zata jajubo ma mutane gayyar tsiya inji ba uwarta bace ta kashe mahaifinta ba” Aunty Safeenah ta faɗa sai wani huci take.

“rabu da ita ai Tahir ɗin zai zo ya same ni,zanji idan shi ya bata damar ajiye wanann annobar a gidan shi”



mamy ranta fes kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,dama ta san muddin mama Ameenah taga Nainarh sai tasa an koreta daga Estate ɗin gaba ɗaya.



first floor mom ta koma, bedrooms ɗin dake floor ɗin ta nufa, toilet ta shiga yayin da Yumnah da Nainarh su ka zauna saman arm chairs ɗin dake bedroom ɗin, Nainarh hankalinta duk a tashe yake da abunda ya faru a part ɗin mama Ameenah,tunaninta yanzu wace irin rayuwa za tayi idan ta koma hannun dangin mahaifinta,kwata kwata basa sonta musamman yanzu da suke zargin mahaifiyarta da kashe mahaifinta,bare ace dangin mahaifiyar ta da ba nan suke ba,yanzu ita ya za tayi kenan...⁉️ _*Ep 21_22*_



*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘


______________________________



sosai tayi nisa a duniyar tunani har mom ta fito daga toilet yumnah ta shiga bata sani ba,prayer mat Fa'iza ta shimfiɗa ma mom ɗin, wurin da Nainarh take ta nufo.


dafa kafaɗarta Fa'iza tayi, saurin kallon fa'izar tayi,murmushi Fa'iza ta sakar mata “ ina ta magana kinyi nisa a tunani baki ji,karki damu da maganar mama Ameenah babu in da za kije kina nan a tare da mu, ki kwantar da hankalin ki kinji”


murmushi kawai Nainarh ta sakar mata ba tare da tace komai ba, turo ƙofar ɗakin Aunty Adama tayi ta shigo,duban su suka kai gareta, cikin ɗakin ta ƙaraso, zama tayi kan chair ɗin da yumnah ta tashi tana fuskantar Nainarh, fuskarta ɗauke da murmushi tace


“kiyi haƙuri da halin kakar taku wasa take babu in da za kije, kina nan tare da mu har Allah ya kubutar da mahaifiyarki kinji”
murmushi Nainarh ta sakar mata
“nagode sosai Aunty, Allah ya bar zumunci”
“kar ki damu,ai yanzu munzama ɗaya, zansa yumnah ma ta kawoki gida ki zo man ziyara, ai zaki zo ko”
“Eh in sha Allah, nagode sosai Aunty”



“shikenan, tashi ki shiga toilet ki ɗauro Alwala ki zo kiyi sallah” da to ta amsa mata, tashi tayi ta nufi toilet ɗin, kusa da Yumnah ta zo ta kabbar sallah, bayan fitowar Nainarh Fa'iza ta shiga,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga gabatar da sallar zuhur, bayan da su ka kammala ne su Yumnah su ka fice aka bar mom da Aunty Adama a ɗakin.


main parlorn su ka nufa,a zaune su ka samu kairiyyah da Noor,ƙarasawa su kayi cikin parlorn, kusa da kairiyya yumnah da Nainarh su ka zauna.


suna a nan zaune parlorn Aunty Nafeesa da Aunty Nadiya su ka shigo,sun ɗau wanka Abaya maroon color yayinda Enaaya da Aneesarh su kayi ankon Pakistan dress riga da wando white color ,rigar da wandon sun sha adon sparkling stones,sunyi rolling Veil ɗin kayan a kan su,simple makeup ne a fuskarsu, kamar ko da yaushe eyes ɗinsu manne suke da sunglasses mai shegen kyau.


basu jima da shigowa ba Laatifa da Balqis su ka shigo tare da mom maryam da mom maimunatu, suma ankon Abaya su kayi yayinda mom maryam da mom maimunatu suka ɗau wankan tsadadden Swiss less naji da faɗa.



mom maimunatu ta so su shiga part ɗin mama Ameenah Amma mom maryam tace babu inda za ta sai dai mom maimunatu taje ita ka ɗai,duk yanda mom maimunatu ta so su shiga su gaishe da mamah ƙin zuwa mom maryam tayi sai ma tashi da tayi ta nufi bedroom ɗin da su mom su kayi sallah, itama sallah tayi.




*Queen Kainart💫*



A jere danƙara danƙaran motocinsu su ka shigo cikin estate ɗin yayinda motocin securitys Armys ɗin su suka sako su a tsakiya,katafaren parking space ɗin dake part ɗin Abbah suka nufa, daidaita parking ɗin su kayi, durowa security Armys ɗin su ka shiga yi daga motocin su,cikin girmamawa su ka shiga buɗe masu car doors, motar farko
Abbah ne ya fitowa hannunshi riƙe da sandarshi mai shegen kyau sai ɗayan ɓagaren dady ya fito, motar bayan su dady Ahmad ne da dady mustafa su ka fito bayan ta su sai tasu Uncle ubaid da Uncle mutallaf su ka fito daga nan sai Uncle hashim.



bayan motocin su sai na jikokin Abbah,a mota ɗaya ya Naeem da zaabith su ka fito motar bayan su ya Adnan da ya usman, ya Ahmer ne su ka fito bayan tasu ne sai ta su Irfan da Waseef su ka fito waseef riƙe da hannun Jamal a front seat na motar da su ka fito Aman da Ammar su ka fito su ukku sun sha ankon white jallabiya harda Arb turban a kansu ba ƙaramin kyau su kayi ba kamar ka sace su ka gudu, motar bayan su Fa'iz da Yazdan ne su ka fito sun ɗauki wankan farar shadda kamar sauran, kawunan su a sanye su ke da huluna hakan ya ɓoye tarin sumar dake kansu.



gama fitowar su kenan daga motocin su motocin her excellency salima suka kunno kai cikin estate ɗin,da katawa su kayi har motocin su ka ƙaraso parking space ɗin, sai bayan da su ka gama daidaita parking ɗin tunkun ɗaya daga cikin securitys ɗin ya buɗe mata car door ta fito,masha Allah na furta a sanye take da lafaya white color ta yafa gyale saman kanta, fuskarta ɗauke take da simple makeup kyawawan eyes ɗinta a manne su ke da farin shade mai shegen kyau.



wurin Abbah ta nufo cikin takun ƙasaita yayinda PA ɗinta ke take mata baya, cikin girmamawa ta gaishe da Abbah, da kulawa ya amsa mata
“ina ki ka baro man Amaryata na ganki ke ka ɗai?”
“ bata jin daɗi ne”
“subhanallah, mike damunta?”


“ta dai ceman zazzaɓi na damunta, da tare zamu zo to sai da muka shirya kuma taji bata iya zuwa jikin ya ɗanyi zafi”
“ya salam, to Allah ya bata lafiya, Allah yasa kaffarane” gaba ɗayan su da Ameen su ka amsa


“dr ya dubata kuwa?” uncle Mustafa ya faɗa
“eh dr James ya dubata”
“mike damunta yace?”
“zazzaɓin ne kawai” mom salima ta faɗa
“zazzaɓi kawai ne a wajenki?,ni dama na san Zaabith bazai iya kula man da ƴata ba,idan baza ku iya kula da ita ba ku dawo man da ita zan sa ƙwararren likita ya duba man lafiyar ɗiyata” ya faɗa yana zaro wayar shi daga Aljihun wandon shaddar shi.

Uncle Ahmad har ya buɗe baki zaiyi magana Abbah yayi saurin dakatar da shi dan ranshi ya ɓaci ya rasa miyasa Almustafa yake mashi haka, kullum gazawar su yake gani a wajen kula da ƴarsa,gaba ɗaya zuba mashi ido su kayi suna kallon ikon Allah, Zaabith duk yasha jinin jikinshi yasa bazai wuce rashin mutuncin da yayi mata bane ya haddasa mata zazzaɓi.



dialing number dr fawar yayi, bugu biyu yayi picking “hello fawar kana hospital ne?” on the other handa dr fawar ya amsa mashi da “Eh sir, kana buƙatar wani Abu ne?”
“kainart ce ba lafiya nake son kaje ka duba man ita”
“ok sir”
“thank u” ya faɗa yana rejecting call ɗin.


“amma kasan cewa gidan gomnati ba wurin shigar kowa bane haka kawai ?” Uncle Ahmad ya faɗa yana kallon Uncle Mustafa da yayi kicin kicin da fuska


“Irfan kaje kayi mashi rakiya zuwa Villa ɗin,idan kun isa ka kira ni ina son na san mike damunta da gaggawa”
“in sha Allah Uncle” Irfan ya faɗa yana nufar ɗaya daga cikin motocin da suka dawo,driver seat ya shiga, suna anan tsaye yayima motar key ya nufi main gate ɗin estate ɗin.


babu wanda Uncle Mustafa ya kalla a cikin su ya nufi ƙofar shiga katafaren garden ɗin gidan, murmushi kawai hajiya salima ta saki,Uncle Mustafa yanda mataƙar tsaurin akan ƴaƴan sa, bai haɗa soyayyar da yake masu da komai ba, zai iya ɓatawa da kai saboda ƴaƴan shi shikuma tashi ƙaddarar kenan son ƴaƴa,shiyyasa Kainart ke mugun tsoron ya san irin zaman da suke da Zaabith dan ta san muddin ya sani abun bazai yi kyau ba.



“bari na shiga ciki Abbah”
“to salima” Abbah ya faɗa, enterence ɗin shiga part ɗin Abbah ta nufa
“muje ko Abbah”dady ya faɗa
“kuje gani nan zuwa” da to suka amsa mashi,ƙofar shiga garden ɗin su ka nufa, dakatar da Uncle Ahmad Abbah yayi.


“zo Ahmad” dawowa yayi in da Abbah yake tsaye, kamo hannunshi Abbah yayi cikin nashi, wata ƙofar shiga garden ɗin su ka nufa daban da wacce su dady su kashiga,wasu irin shuke shuke ne a wajen masu matuƙar kyau da ɗaukar hankali,ga wasu tsuntsaye masu ban sha'awa dake kai komo a cikin garden ɗin.



wasu ƙayatattun benchs dake ƙarƙashin wasu rukunin bishiyu su ka nufa,zama su kayi suna fuskantar wasu killatattun ruwa,kai tsaye baza'a kira su da swimming pool ba ga wasu tsuntsaye dake shawagi saman ruwan abun gwanin ban sha'awa.


“na san ba kaji abunda ɗan uwanka yayi maka ba,amma ina so kayi haƙuri kayi mashi uzuri” Abbah ya faɗa
“Abbah amma mi yasa kullum Al'mustafah yake ganin gazawata akan ƴar sa,ina iya bakin ƙoƙarina wajen ganin wani abu bai faru da ita ba”


“haka ne Ahmad,amma kafi kowa sanin halinshi,yanada saurin fushi ga zuciya musamman akan ƴaƴanshi shi kalar tashi ƙaddarar kenan shiyyasa nake son kuriƙa yi mashi uzuri idan yayi wasu abubuwan,yanzu na san yana can hankalinshi duk ba'a kwance ba saboda rashin lafiyar ɗiyarshi,da ƙyar yau yayi bacci mai daɗin,kayi haƙuri da ƙaddarar ɗan uwanka”



“shikenan Abbah komai ya wuce a wajena, Allah ya bashi ikon cinye ƙaddarar shi”
“Ameen ya Allah,ya fama da mutane,ina fata komai yana tafiya daidai??”


“Alhmdllh Abbah komai yana tafiya yanda ya kamata”
“masha Allah,labari yana samuna har gida daga mutane daban daban,suna kawo man labarin yanda komai ke tafiya,kuma Alhmdllh naji daɗin yanda kowa daya buɗe baki yake faɗin Alkairi a kanka,Na yarda da tarbiyyar ka da gaskiyar ka da riƙon amanarka,nasan yanda kake da tausayin talaka ina so Ahmad ka ƙara fiye da haka, kazama adalin shugaba kamar ɗan uwanka,ina fatan yanda ɗan uwanka yayi ya gama lafiya har yau ƙasar nan bata manta da ayyukan Alkairin sa ba,ina so kaima kowa ya buɗe baki ya faɗi Alkairin ka ko bayan saukar ka”


“in sha Allah Abbah zaka sameni fiye da yanda kake tunani”
“haka nake son ji,Allah yayi jagora”
“Ameen ya Allah” fira su ka shiga yi Abbah na ƙarfafa mashi gwiwa akan mulkinshi da bashi shawarwari.



Idan muka koma ɓan garen su dady wani ƙaton dinner hall su ka nufa dake cikin garden ɗin,gaba ɗaya zagaye yake da glass daga waje kana iya hangen abunda ke ciki,wasu irin zungura

Please Login or Register in order to submit comment