Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 8
a titi da kyar Direba ya gyara."
Yaranta mata duga guda 4, suka yayyame ta, kowa son ya dauki Bebi yake yi.
Babu 6ata lkc. Direba ya kwashe kaya suka rankya.
Tunda daga mota, har gida Antin Jordan ke balbala tsiya akan abinda ya faru.
Dakin ta daban, aka ware mata ita da Bebin ta, bayan an gama duk kayaniyar ganin juna har da maigidan ya tofa na sa albarkacin bakin sa.
Sai dai nasihohi yayi mata akan ta aje hankalinta waje daya, kar ta sa wa ranta damuwa.Daki ta koma ta yi wanka, ta yi alwala ta yi sallolinta. Gefen gado ta zauna tana tanunanin yanayin da suka hadu da Sakina, fara'a kamar gonar auduga, amma tashi guda ta sauya fuska, saboda mijinta ya nuna ya santa.
Ta yi dan murmushi, ta ce,"Allah sarki Antina, alkhairin Allah ya kai miki."
Ta sa hannu ta jawo jakar Bebi, ta daukko lambar da Sakinta ta bata a rubuce, ta sa hannu ta yayyaga, tana fadi a ranta,"Sa ran ki a inuwa Maman Husna, kullum ni da mijinki haduwar [Aiport] ce, rabuwar (Airport)." Ta matse a hannun ta, ta wuce bayi ta watsa (Dosbin).
-----------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Washe gari da wuri Naseer ya nufi Kaduna. Shi kadai kuma ya tafi, wannan karon zuciyar sa ta bushe, matar sa kawai yake son ta dawo.
Shi yasa ya kwashe duk wani tunanin dake ran sa a game dake ran sa a game da tinkarar Alhj.
Yayi fakin, ya fito kai tsaye falon yayi sallama.
Mariya dake goge-goge, ta amsa sannan, ta durk'usa ta gaishe shi ya ce,"Hau sama ki kira min Ummi." Ta ce,"Tana ma kicin, bari na kira ta."
Ya zauna Mariya ta wuce. Jin kadan ta dawo ta ce,"Ga ta nan zuwa." Ya share minti 5 nan, kafin Ummi ta iso falon.
Ya mike kai sunkuye ya ce,"Sannu Ummi." Bata tanka masa ba, ta wuce ta haye sama. Yayi tsaye nan kirjin sa na harbawa.Bai sake ganin kowa ba, wucewar minti 30 har ya gaji da tsayuwa ya koma ya zauna.
Can Alh.Basheer ya tinkaro falon.
Ummi na rike da jakar sa suna maganganun su.
Naseer ya kuma mikewa yayi tsaye irin na marasa gaskiya. Ko inda yake Alhj bai kalla ba, jakarsa ya karba. Ummi ta ce," A dawo lafiya." Ya ce,"Amin." Ya fice.
Ummi na ta wuce kicin, ta ci gaba da hidimomin ta.
Naseer yayi kamar ya nutse a kasa, jiki babu kwari ya biyo bayan Alhj, amma kafin ya karaso.
Alhj ya shiga mota. Deriba ya tayar. Haka ya tsaya kamar dolo, yana kallo aka bude get.
Motar ta fice. Ya wuce ya shiga ta sa, ya bi bayan sa.
Ofis ya ga sun nufa, shi ma ya bi su. Yana zuwa zai wuce sakatare, ya ce,"Alhj ya ce ka dan jira shi a nan tukuna."
Ya ce,"To." Ya zauna.
Shi kansa sakataran dauke da mamaki yake, domin bai ta6a yi wa Naseer iso ba wajen Alhj.
Yana nan zaune Alhjn ya kira waya, ya bada izinin Naseer ya shigo.
Ya mike ya tura kofa, ya sjiga Alhjn na ta aikin sa bisa (Laptop), bai ko kalle shi ba. Ya duka ya gaishe shi, ya amsa a dakile.
Yayi shiru, haka shima Alhjn bai dube shi ba.
A haka ya daure ya fara magana,"Abba, na san babu abinda zan gaya maka wanda zai faranta maka rai, amma duk da haka ina mai gurfanar da kai na gare ka a matsayin mai laifi.Ka yanke min duk hukuncin da ya dace dani, wanda zai sanyaya maka rai, har ka huce ka ban Nusaiba, in koma da ita.
Da sunan Allah na ke wannan rokon Abba, ka taimake ni don son Manzon mu.
Yayi shiru. Shi kuwa Alhj sai a aikinsa yake yi.
Kamar ba zai tanka ba, wucewar mintoci, kafin ya ce,"Ka na iya tafiya, zan neme ka."
Ya durk'usa guiwa 2 ya ce,"To shi kenan, na gode Abba.
Kuma ina k'ara neman afuwa akan kuskuran da na yi.
Ka gafarce ni Abba."
Ya ce,"Ka je zan neme ka na ce."
Ya mike yana fadin,"Na gode, a tashi lafiya."
Bai amsa masa ba ya fice.
Alhaji ya sauke numfashi, ya dafe goshinsa, bai san dalilin da yasa son Naseer yayi masa yawa a zuciya ba, duk lokacin da ya gan shi kaunar sa karuwa take.
Dole ce tasa ya yanke hukuncin nan, saboda ya kar6o wa Nusaiba 'yancinta.
Ofishin su Yakubu Naseer ya nufa, can bargar dawakai, amma wurin na kulle babu kowa, sai mai ba dawaki abinci.
Bai tsaya 6ata lkc ba, ya damko hanyar dawowa gida, yana tafe wasi-wasi ne fal cikin ransa, wata zuciyar na saka masa zai yi wuya Nusiba ta dawo, wata kuma na tabbatar masa za ta dawo ne, tunda ya ce zai neme ka.,
Ai kai d'an gaban goshin sa ne. Daya iso shago, ya tsaya wajen Sageer.
Bai dawo gida ba, sai karfe 1,abu na farko sada fara gani, shine babu motar Nusaiba dake lullu6e a wajen.
Gabnsa ya fadi, ya fito da sauri ya fada cikin gida.
Zarah na zaune a barndar sasan su, tana ta faman goge kwalla."Menene wai?
Ban ga motar Nusaiba ba a waje!
Murya na rawa ta ce,"An kwashe kayanta, ka ga shi kenan ta faru, ta k'are, tuntuni na ke gaya maka, ka je ka k'i................
Ya katse ta da masifa,"Don Allah isa haka, kar ki kara 6ata min rai!
Ko yanzu daga ina na ke? Ya ce zai neme ni? Ai shi kenan tunda baya son ta dawo!
Ya nemi waje nan ya zauna dabas, ya cire hula zufa ta keto masa.
Zara bata iya kara komai ba, ta ma tashi ta bar wajen.
Umma na jin sa, kanzil ba ta ce da shi ba.
Bayan sallar la'asar, yana kwance dakin sa ya rasa abinda ke masa dadi, kamar an kwaso son Nusaiba an kara cusa masa cikin zuciya, sannan a 'yan kwananin nan da bai ga Ameer ba, duk kewarsa ta ishe shi.Gaba daya abubuwan sun dagule masa, domin ya sani ba za su ta6a daidaitawa da Abbansa ba, muddin Nusaiba bata dawo cikin gidan nan. Ya runtse ido, ya dafe kai kamar ya kwarma ihu. Zumbur ya mike ya kwashi makullai, ya fice ko Zarah bata sani ba, ya fada mota. Ya sake yi wa Kaduna tsinke. Yana zuwa. Sakatare ya ce Alhj ya tashi.
Yana kokarin fitowa daga get. Motar Yakubu na shigowa. Suka tsaya kowa ya fito gaba dayan su, babu mai walwala a fuska. Yakubu ya fara magana,"Ko ka ji abinda ya faru?" Ya ce,"Na me ? Ya ce,"Na rufe (Dabai Riders) mana.
Alhj ya rufe kulob, yadda yake gaya min ma ya sa dawakan a kasuwa har an samu masu siya." Salati Naseer ya fara yi, kafin ya ce,"Saboda me? Ya numfasa ya ce,"Wallahi ban sani ba, amma tun faruwar wannan al'amarin na ku hankalin Alhj a tashe yake. Iyaka kokari na, akan ya sauya shawara, amma ya ce ra'ayin sa ne.."
Naseer ya k'ara tarus! Idanuwan sa suka kawo kwalla, ya ce,"Yakubu ban san yadda zan yi ba, dazun nan na zo na yi magiya gun sa, ya ce in je zai neme ni, wai ina zuwa gida. Na tarar an kwashe kayan Nusaiba kaf. Lambarta ba'a samu.
Kuma ni na san rufe kulob din nan, duk baya rasa nasaba da matsalar nan, wata kila yana ganin ta dalililin Polo ya hadu da ni.Ban san abin yi ba Yakubu? Ya ce,"Gaskiya ne. Magana kan ta gama lalacewa. Ka san komai Alhj zai iya yi saboda Nusaiba, kar ka manta ita ce 'yar sa kawai. Sannan duk abinda ya faru, kai ka jawa kanka, domin ba karamar asara ka yi ba. Sai ka yi addu'a Allah ya sa hakan shine alkhairi. Gida ka nufa?
Ya kada kai,"Ina nan sai na ga abinda ya turewa buzu nad'i. Yakubu ya ce,"To sai ka dawo,"Goodluck." Na gode." Naseer ya fice, shi kuma ya karaso wajen sakatare, ya aje abubuwan daya zo da su.
Gidan Naseer ya nufa. Alhj na tare da baki. Yayi sallama ta gaishe su. Alhj ya bi shi da kallo. Ya ce "Dama na zo ganin ka ne, bari in jira ka." Ganin mutane a wajen yasa ya amsa." To ina zuwa."Naseer ya fita, motar sa ya zauna yayi ta ji Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 Ajinisa Yake3-04 Posted by ANaM Dorayi on 05:24 AM, 23-Nov-15 Under: Ajininsa yake _______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
Zan yafe maka komai, ya wuce har abada, amma sai ka kawo min takardar Nusaiba."Kansa cikin giuwa, ya girgiza kai, ya ce,"Ba zan iya ba Abba, ka yi hkr." Ya ce,"Wannan ba hukunci na ba ne.Nusaiba ce ta buk'ata ta kuma bar min sallahu jiya kafin su wuce Jordan.." Ji yayi numfashinsa ya shake gaba daya, yana neman faduwa.
Ya kasa motsi, balle ya ce wani abu. Ya ci gaba da cewa,"Na ba ka nan da jibi ka zomin da takardar, daga nan zan maka bayanan wasu abubuwa da suka kamata ka sani.
Ka na iya tafiya dare yana k'ar yi." Ya dago idanuwa jajur! Ya ce,"Ummi ku taimake ni, ku ba ni lambar ta mu yi magana, na san zata saurare ni. Amma a raba auran a haka, abin babu dadi.."Abba ya ba shi amsa,"Ban son dogon nace Naseer, raina k'ara 6aci yake yi. Kwanciyar hankalin na da kai shine ka kawo min takardar Nusaiba. Yadda ba ka so, haka ita ma bata so, shi kenan magana ta k'are babu lallai babu tilas."
Ya sunkuyar da kai, yayi shiru. Ummi ta ce,"Yakamata ka tafi, dare ya fara yi Naseer, muna sauraronka."Yayi wawan ajiyar zuciya, ya mike da kyar ya ce da su,"Sai da safe,gaba daya suka amsa,"Allah ya kai mu, a gaida mutan gidan."Bai k'ara komai ba, ya sakko a hankali ya tafi.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Karfe 11 dare, ya shigo gida,. Zarah na zaune a falo ta ci uban tagumi, ya turo kofar ya shigo." Ta mike tsaye da sauri ta tarbe shi."
Yayana!
Kai kuwa ina ka shiga yau?
Bai tanka ba, ya wuce kujera ya zauna, ta bi shi hannun kujerar ita ma ta zauna. Ganin yayi zuru- zuru, yasa tausayinsa ya rufe ta.
Ta nunfasa ta ce,"Ina ka je yayana? Ya ce,"Kaduna na koma." Ya aka yi to? Ya mayar mata da abubuwan da Alhj ya ce,yayi shiru ta rasa ta cewa. Ya kwanto da kan sa bisa cinyoyinta, shi ma ya yi shirun Ta dafa kan sa ta ce,"Kai yanzu me ka shawarta."Ya ce,"Na hukara Zarah. Allah na gani na yi ikayar kokarina. Abinda ya fi damuna maganganun da Alhj yayi. Ba k'aramin dafa min jiki suka yi ba, sbd a zahiri Alhj masoyina ne.Sai kin ga yadda ya cika hotuna na a falonsa, kya rantse da Allah ni ne dan masu gidan.
Ni dai na yi abin kunya, ban san ta yadda zan yi in wanke kai na ba."
Ta ce,"Gaskiya ne, amma duk da haka ka tuntubi su Umma ka ji ko za ta ce wani abu." Ya mike ya wuce bayi, yayi wanka ya ji sanyi a jikin sa, sannan ya kwanta.
Zarah na k'ara kwantar masa da hankali.
Da safe ya shiga wajen su Umma ya gaishe su.
Abba bai amsa ba, ya tashi ya koma cikin daki.
Daga can yana jin duk bayayin da yake wa Umma.
Yana gamawa ta ce.
"To ne menene nawa a ciki? Duk abinda ka ga ya dace, ka yi, tunda wannan 'ya ba ta mu bace, k'arewa ma ka ce bata k'asar.
Ka ga da gaske Abbanta ya ke yi." Yayi dan jim kafin ya mike, ya bar falon.
Umma ta bi shi da kallo, tausayin sa ya dan kama ta, ta kada kai ta ce,"Kai ka jawo wa kan ka."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Sati 1 Naseer yayi yana sintiri Kaduna, wai ko ya sanmi sauyin baki daga Alh.Basheer, amma sam babu.
Yau daya je ma. Alhj cewa yayi yau ce rana ta karshe daya ba shi, idan bai kawo takardar ba, to kar ya sake zuwa gun sa, kuma duk abinda ya biyo baya, kar ya ce yayi masa wulakanci.
Babu yadda zai yi, a daren ya rubuta takarda, saki 1 ya sa a ambulan ya rufe.
Washe gari ya isa gida, ya sami Alhj yana shirin fita.Bayan sun gaisa Alhj, na kallo irin ramar da Naseer din yayi. Ummi ta zo suka gaisa. Yasa hannun aljihu ya ciro ambulan, ya tsugunna ya mika wa Alhj. Ya kar6a, ya buda, ya karanta, bai ko karasa ba, ya rufe saboda irin lausasan kalaman da ke cikin takardar.
Ya dube shi ya ce,"Magana ta kare Naseer, kuma duniya da lahira na yafe maka abinda ka yi min. Son ka a cikin jini na yake, na rantse da Allah ba zan iya cire shi ba, saboda haka ka saki jikin ka, kai da na ne.
Magana ta 2, ita ce,"Gida da motocin da na ba ka, mallakin ka ne, ba na bukatar su. Abinda na ke son ka da shi ne, ka dauki Zarah ku koma can da zama.
Wannan umurni ne a matsayin na Babanka."Gaba daya tsigar jikinsa suka tashi yar! Idanuwansa suka kawo kwalla.
Ya zamo daga kujera ya ce,"Na gode Abba. Allah ya saka da alkhairi."
Ya ce,"Koma ka zauna. Yanzu yaushe za ka kammala karatun ka? Ya sunkuyar da kai, kunya ta rufe shi, ya rasa me zai ce? Da kyar ya daure ya ce,"Ai dama ban fara ba."
Da mamakinsa ya maimaita ,"Ba ka fara ba? To da ka ce min ka na zuwa?
Ya sunkuyar da kai, kamar ya ratsa kujera ya shige. Alhj yayi dan murmushi ya ce,"Allah da iko yake, yanzu yaushe za ka fara? Kidimewa tasa ya ce,"Gobe." Ummi ta ce,"Gobo kuwa? Ba dai gobe- gobe ba, ai kuma sai an sake nema ko? Ko kuwa ka na da "(Admission) ne a hannun ka?
Ya girgiza kai,"A'a.Duk sun lura a daburce yake, saboda haka Alhj ya ce,"Shi ke nan, ka je ka yi duk abinda ya kamata, idan ka sami ( Admission) din ka kawo min." Ya ce,"To na gode Abba."
Ya kosa ya tashi saboda tsarguwa, zufa ce kawai ke kwararo masa cikin riga.
Yana samu aka sallame shi, jikin sa na rawa yayi godiya, ya fice.
Alhj ya dubi Ummi ya ce,"Kawai Allah ne ya dora min son yaron nan, ba don haka ba, inda na ke ma idan aka ce ya zo da kudi ba zai zo ba."
Ta ce,"Ya za'ayi, ga kuma zuri'a a tsakani, dole a rage wani abin." Ya numfasa yana kada ambulan, sannan ya mika mata,"Karanta ki ji bayanan dake ciki." Ta kar6a ta karanta, ta yi dan murmushi ta ce,"Allah sarki da alama ya saduda Alhj."
Ya ce,"Kyale ni da shi dai."
Ta ce,"Na kyale."
Kowa ya ji abinda Alhj yayi, sai ya sanya masa albarka.
A hakikanin gaskiya Alh.Basheer mutum ne wanda ba'a samun su a wannan zamanin, sai an shekara ana bincike cikin mutanen kirkin da ake wa zaton suna da halin mutan da can. Karshen soyayya Alh.Basheer ya nuna wa, Naseer shi yasa Naseer din ke k'ara nadama kan nadama, so da kaunar Nusaiba ke k'ara dabaibaye zuciyarsa.
Kewar ta ke jefa shi.
Nisan tunanin ta musamman lukutan daya samu a asibiti yana jinyarta.Ya kan rink'a ganin kamar wata sabuwar rayuwar soyayya ce suka yi a tsakanin su, wacce yake mafarkin ci gaba da irin ta.
Malam Balarabe kuwa kalaman godiya sun kare a bakin sa.
Washe gari daya tafi Kaduna, ba tare da sanin kowa ba, don nuna girmamawa ga Alh. Basheer. Tabbas ya nuna halin girman, dole a jinjina masa. Haka shi ma Alhjn ya roke shi akan ya daina fushi da Naseer, tunda ya tuba, to ya kamata ya karbi tuban sa, sbd fushin sa tamkar dafi ne a gare shi.
Malam Balarabe ya amince, yayi farin ciki ya kuma zubda kwallan bakin cikin rabuwar auran Naseer da Nusaiba.
Ba 6angaran su Malam Balarabe kadai bakin cikin rabuwan auran ya dama ba, ita kan ta uwar gayyar, yau ta tsinci kanta cikin wani yanayin da bata gane masa ba, a tun lokacin da sako ya zo mata ta waya daga Nijeriya cewar ta fara iddar ta.
Zaune take dirshan bisa gado, ta takure kanta, tunanin yayi mata yawa.
Tana tambayar kan ta, ita kuma haka Allah ya kaddaro mata? Mutuwar aure ita ce matsala ta farko da ke ci mata tuwo a kwarya, a rayuwarta.
Ta tsani, ace anyi aure ya mutu, sai ga shi yau ya tabbata akan ta.
"Kaddara!
Ta fada a ranta hawaye, suka kubce.
Ta dawo tana zargin kan ta,"Watakila Naseer ya so ya gaya mata wata magana lkcn da ta wayi gari ta gan shi tare da ita asibitin, amma ta ki ba shi dama.
Yi hakuri ki ba Bebinmu nono. Haba 'yar gidan Abba."
Tabbas rarrashin ta yake yi, amma ta dauke kai, ta nuna bata san abinda take yi ba.
Alhalin ta warke, hankalin ta ya dawo jikinta.
Da kenan amarya, amma, a yanzu ina mai tabbatar miki yayanmu yayi nadama, ko bai gaya min da bakin sa ba, ni na yi imanin yana son ki.
Ba ki ga yadda ya fita hayyacin sa ba.
Lokacin da lalura ta kama ki, kuma ya kula dake yadda ya kamata!
Ta toshe kunnuwanta ta daga kai.
Idanuwanta tamau a rintse, hawaye suka ci gaba da sauka.
Istaharar ta ta tabbata gaskiya.
Bata sami isashen barci ba, sbd a yanzu take tunanin ya kamata ace ta ba Naseer dama shi da ita sun yi magana.
Yanayin daya suka kwana ita da Naseer, domin a ranar suka koma Hanwa. Yayi sintiri a sashin ta iya yadda ya ishe shi, wanda a da bai ta6a shiga cikinsa ba. Tun Zarah na taya shi sintirin, har ta hakura ta sakar masa. Daga ranar ya daukar wa kan sa alkawarin zama lafiya da kowa, zuwa k'arshen rayuwarsa.
Idan ba shi gida, yana shagon dinki ne, daya samu Abba ya fara amsa gaisuwar sa, kuma bin sa yake sau da kafa.
Komai bai zartarwa sai abinda ya ce. Haka yake bin Alhj, bai ketare umurinin sa. A haka aka share watanin 2. Mamakin sa 1 shine. Alhj ya ki dawo da wasan Polo, shi kuma yana jin nauyin yi masa magana.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
A 'yan tsakanin ne. Fa'iza ta haihu da namiji k'aton gaske mai kama da Babansa. Ranar suna, ya rada masa Mohammad. Zarah gidan sunan ta wuni duk da ta wayi gari baya jin dadi.
Tun daga ranar jikinta ya k'i yi mata dadi,
tsoro ya fara kamata, sbd fargaba daukan ciki.
Lalurar ta ta fara bata tsoro.
Lalai kuwa, abinda take wa tsoron ne ya samu.
Shi kan sa Naseer tausayi take ba shi, shi yasa wannan karon murnar sa raggiya ce.
Zarah na tsakiyar laulayi, aka biya kudin jarrabawar (External)
Naseer ya biya duka WAEC da NECO.
Daga nan Sageer ya shawarce shi daya fada makarantun bada (Lesson), don ya k'ara wanke masa kwakwalwa.
Babu musu, ya nema ya shiga guda 2, yana zuwa.
Ranar da za'a kai Zarah daurin mahaifa, ranar ce suke da jarabawar farko. Hankalin Naseer ba'a kwance yake ba, babu yadda zai yi.
Haka nan ya hakura suka tafi tare da su.
Umma da Inna Sageer ya kai su a Jeep din sa.
Shi ya tafi jarabawar sa da Civic.A saukake yayi jarabawar sa, duk da ba shi cikin nutsuwa, babu tambayar da ta gagare shi amsawa.
Yana tashi ya wuce asibiti abin sa, ya duba Zaraha, sannan ya dawo shago yayi ayyukansa. Can yake zama su ci su yi hira, zuwa karfe 9 ya dawo gida.
Zaman sa shi kadai yana kara taso masa da kewar Nusaiba, a lkc irin wannan can baya, duk da ta san baya maraba da ita cikin dakin sa, ta kan shigo har ta tambaye shi ko yana da bukatar wani abu.
Shi yasa ya dauki filo ya nufi sashin ta cikin dakin barcinta, ya jefa pilo bisa kafet ya kwanta.
Nan ya kasance wajen barcinsa, kodayaushe, yana laluben inda zai ji motsinta.
Watannin 3 sakamakon jarabawarsa ta fito.
Allah da ikon sa gaba daya sakamakon Naseer masu kyau ne.
Yayi matukar sa'a.
Allah ya kubutar da shi daga sharrin hukumar jarabawa da yanzu abin yake neman zama kasuwanci.
Ko ma ince ya zama din."
Magidanci na fama da kansa, duk da haka ya dage da karma-karma ya biya zunzurutin kudi, sai jarabawa ta fito, ace yaro bai ci ba, alhali da kokarin sa da komai.
Sannan ya dage wajen neman taimakon makarantun (Lesson), tunda daman makarantun gwamnati sai a hankali.
Ba duka (Syllabus) ake (Covering) , ba, balle yaro ya san makamar jarabawarsa.
Allah ya sawwake.
Ilimi ya zama wahala ga 'ya'yanmu talakawa.Shi kam Naseer yayi sa'a kamar yadda Allah ya halicce shi, shi mai sa'a ne a rayuwarsa.
Da rawar jikinsa ya kai wa Alh. Basheer takardun ya gani.
Yayi murna kwarai, daga nan ya shiga neman makaranta, don samun (Admission).
Sageer na taimaka masa.
Ba jimawa ba, ya sami Poly ta hannun Sageer din, Babu kudin kirki a hannunsa a wannan 'yan tsakanin, sbd zaman Zarah a asibiti.
Ya zauna yana tunanin yadda za'ayi.
Ba tare daya takurawa kowa ba.
Abin mamaki yana zuwa Kaduna, ya nuna wa Alhj,("Admission) din, kamar yadda ya umurce shi, cewar da ya samu ya kawo masa ya gani.
Take nan ya ware dubu 50 ya ba shi, ya ce ya je yayi hidimar makaranta.
Allah mai iko.
Tun daga ofid har ya dawo gida, godiya yake wa Alhj cikin ransa.
Ya kawo wa Abbansa, suka sa albarka shi da Umma, balle Zarah da take jin tausayin sa, sbd hidimar da yake sha a asibiti, ga kuma makaranta ta kunno kai.
Lallai Alhj ba karamin taimako yayi ma su ba.
Ciki lafiya, ba ka lafiya, ya kama karatun sa a (Poly Computer Science) yake karantawa, kamar almara yake ganin abin.
Lokacin kuwa cikin Zarah ya shiga wata 7.
Zullumi ya ishi kowa, musamman ita mai dauke da cikin.
Kusan kullun da ciwon mara take kwana.
Bata dai yin magana ne kawai.
Saboda ciwon ba wai ya tsananta ba ne.
Sati 2 da fara karatunsa, abinda ake gudun ya faru.
Ta haifi da namiji.
Aka sanya shi a kwalba kwana 7. Ya ce ga garin ku nan kuma shi ya ci sunan Alhaji, watau Mohammad Basheeeeeeeeeeeeerrr­ rrrr!!!!!.......
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Labarin haihuwar Zarah har Jordan, amma da aka ce ya koma. Jikin Nusaiba yayi sanyi, ta dubi Ameer yana ta rarrafen sa, yayi k'atob gasket, dauki da nishi jajur, ga suma baka wulik! Kamar kan Babansa.
Tausayin Antinta ya kama ta, ta yi tagumi ta ce a ranta,"Allah sarki Antina." Ta numfasa, Ameer ya rarrafo gun ta, ya dafa ta ya mike, ta sa hannun ta dauke shi ta rungume.
Tabbas ta sani dole Naseer ya sa Ameer a ransa.
Ta k'ara matse shi jikin ta, tunanin ta wai ace Naseer ya tada k'ayar baya, dan sa yake so a ba shi. Abinda ba zai samu ba kenan, yadda ta shaku da Ameer.
Ai mai raba ta da shi, sai wanda ya bata shi. Ta yi dai yi masu addu'ar Allah ya ba su mai albarka."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
BAYAN SHEKARA DAYA
Shekara guda da rushe(DABAI RIBERS),sauran kolub-kolub din wasannin polo sai kawo wa Naseer takardun gayyata suke, suna neman ya koma kungiyoyinsu.
Gayyata har da Ghana, Kamaru, Benin Republic, da sauran kasashen makwafta, wadanda suka san Naseer, suka kuma san irin rawar daya taka a wasan tsern Polo.
Amma sam ya ki amsa kiransu, duk da ya san dumbin alkhairin da zai samu a can. Sam-sam zuciyarsa ta fita daga wasan Polo tunda Alh. Basheer ya bar harkar.Hakan ya gaya wa Yakubu ranar da ya same shi da wata takarda da ta zo ta hannun sa daga Sakkwato. Magana ta kawo magana, suna hira tsakanin Yakubun da Alhj.
Shi kuma yake ba shi labari.
Saboda haka Alh.Basheer ya kira Naseer yayi masa magana. Baya ketare umurinin Alhjn, amma wannan karon Naseer kad'a kai yai ya ce,"Abba karatuna ya fi min wannan wasan, kuma ban jin zan iya wasa da wani (Polo club) a halin yanzu.
Alhj ya bi shi da kallo, tsaf ya kasa ganeme yake nufi.
Yayi dan murmushi ya ce,"Shi kenan tunda ka kawo zancen karatu. Allah ya bada sa'a."Ya ce"Amin. Alh.Basheer ya dade yana nazarin maganganun Naseer kuma yana tausaya masa, domin ya saba da Polo.
Yana sha'awarsa, bugu da k'ari wasan Polo A JININSA YAKE.Abinda kuwa daka saba da shi zai yi wuya ya fice maka a rai, sai dole. Alhjn bai yanke hukunci ba, tukuna, amma yana nan yana nazari a kai.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Al'amarin Nusaiba kuwa a birnin Jordan, ba yabo, ba fallasa a yanayin jikinta. Ta kasa samun natsuwa a ranta, saboda yawan zancen aure da Antin Jordan ke yi mata, tunda Ameer yayi wayau sosai, yana gudun sa ko'ina gwanin sha'awa.
Kullum amsar ta ita ce bata da wani bazawari tsayayye ko a Nijeriya, balle kuma a nan Jordan da babu wanda ta sani kasancewar ba fita take yi ba.Idan ba (Shopping) ba tare da yaran gidan da Direba. Ta damu kwarai domin ba ta san dalilin da yasa Antin ta damu da yin sabon aurenna taba. Shekara 1 kacal da mutuwar auranta.
A yammacin yau (Shopping) din za su da yaran gidan.
Kowace ta shirya cikin dogayen kaya kala daban- daban.
Direba ya aje su katuwar (Super market) din da suke saba zuwa.

Chapter 5 of 8