Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 8
dama ku gani zan rike Nusaiba iya rayuwata.
Ta dube shi a dage ta ce,"Bakin alkami ya riga ya bushe maka Naseer, domin jiya da daddare su M.Umar da M.Lawar sun zo. Amma Abbanka ka ya rantse, ya masu, babu ruwan sa a cikin maganar ka.
Haka ni ma bai lamunce min ba.
Saboda haka ka makara, dabara kuma ta rage wa mai shiga rijiya. Ina fatan ka gamsu. Yayi zuru kafin, ya numfasa ya dube ta ido sun kawo kwalla.
"Shi kenan Umma, na gode. Abinda na ke son ki rokin min Abba, shine, don Allah yayi hkr, idan na gaishe shi ya rinka amsawa. Ni zan fita, ga wannan koda Ameer yana bukatar wani abu." Ya ciro dubu 2, ya aje bisa hannun kujera ya tashi ya fice.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~­ ~~~~~~~~~~------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Karfe 9 ta gota kadan Jeep din su Hajiya Zulai ta yi fakin kofar gidan su Naseer. Suka fito Ummi na rike da hannun Nusaiba. Ummi ta yi sallama tsakar gida. Umma ta amsa daga falo, a lkcn kuwa ta kammala shirya Ameer tsaf!Yana ta tashin kamshin hoda. Bata dauki murya sosai ba, don haka ta ce,"Maraba, ku shigo mana." Ummi ta yaye labule. Umma ta mike baki har kunne,"Hajiya!
Ah!
Nusaiba!
Sannun ku da zuwa."
Suka zauna a kujera Umma ta mikawa Ummi Ameer, ta karbe shi. Sai ta wuce firj za ta dauko kayan sha.
"Dama kin bar shi, kin san safiya ce." Duk da haka ta kawo da Jus din kananan kwali da kufuna 2.
Bayan sun gaisa, Umma ta tambayi Alhj? Sai Ummi ta ci gaba da cewa,"Ba wani abu ya kawo mu ba.
Ameer mu ka zo tafiya da shi, ya zauna wajen uwar sa ta shayar da shi. Ko dama 6acin rai ne yasa aka aje shi."
Kwalla suka cika idanuwan Umma ta ce,"Gaskiya ne kuwa, na ji dadi, domin a gaba daya wannan al'amari Ameer shine abin tausayi.
Shi kuma wancan sakaran, ai kyale shi ya gasu, duk da cewar ya ce yayi nadama." Ummi ta yi dan murmushi ta ce,"Ai ba'a soyayya dole, mu ma mun san haka shi yasa Alhj ya ce a gaya masa, tana jiran takardarta, ko zuwa jibi. Insha- Allah za mu turo mota akwashe kayan ta a dauki motar ta."
Umma ta goge kwalla ta ce,"Ba laifi, ki yi hkr Nusaiba kin ji? Allah ya amfana miki dan ki. Ta dan sadda kai ta ce,"Ba komai Umma.
Idan kuma na yi miki wani laifi, ki yafe min." Ta girgiza kai,"Baba abinda ki ka yi min Nusaiba, Allah yayi miki albarka."
Ta ce,"Amin." Ummi ta ce,"To bari mu je, za ta debi wasu kayan kafin a zo kwashewa." Umma ta ce,"To bari in kawo maku wani makullin, ya fita da na hannun sa."Nusaiba ta ce,"Ina Antina Umma?
Ta ce,"Ita ma ta tafi."
Suka dubi juna, kafin Ummi ta tambaya,"Saboda me?------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------ Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 Ajininsa yake 3-03 Posted by ANaM Dorayi on 11:46 PM, 21-Nov-15 _______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
Fa ce,"Ita ma ba za ta zauna ba.
Sai Nusaiba ta dawo.
Kin ga ya 6ata 2 kenan, sai wani gyaran Allah.
Nusaiba ta dafa kirji ido waje, sun kawo kwalla, ta dubi Ummi ta ce,"Me yasa Antina za ta yi haka? Ai ni ba zan ta6a dawowa ba, yakamata yayi ta gane wamman.
Ummi mu je in debi kayan, mu wuce wajen ta."
Suka mike, Umma ta kawo makulli. Nusaiba ta debi kayayyakin da take son diba. Abubuwan dake firj din ta duk ta kwaso ta kaiwa Umma. Bayan Direba ya zuba kaya a mota, suka sallami Umma suka rabu suna daga wa juna hannu.
Babu Abinda zata yi, Nusaiba ta hana ta tafiya, babi abinda za ta iya yi.
Duk iya kaunar da take wa Nusaiba data zauna dakinta, dole ta kyale.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Babban abin godiya ma shine, da suka tausayawa baWan Allah suka zo da kan su suka dauke shi.
Shi yasa take ta yi wa Allah godiya, ba 6ata lkc ta kira wayar Abba a kasuwa, ta shaida masa. Ba karamin farin ciki yayi ba, domin rabon sa da fara'a tin asubahin jiya. Sai kuwa yau da aka ce su Hjy sun zo da kan su sun dauki Ameer.
Cikin gidan su Zarah su kai sallama yanzu. Inna ta amsa. Ta leko daga dakin Malam Umar. Ah! Nusaiba! Maraba. Fit Zarah ta fito daga dakin Inna, baki har kunne,"Amarya! Antina." Zarah ta matso suka rungume juna." Kin dawo ko amarya?
Ta daga ta dube ta,"Haba Antina, zo mu je daga cikin in gan ki."Ta kama hannunta suka shige daki. Inna ta ce,"Ke Hajiya shigo nan, kafin su gama ganawar. Ina fatan dai na dawo mata da amaryarta ne, mu huta." Bata ce komai ba, suka shige, tana 'yar dariya.
Nusaiba ta dubi Zarah,"Me yasa haka Antina? Bai kamata ki yi wa yayanki haka ba." Ta ce,"Ni kuwa a waje na hakan ya kamata, domin ciwon 'Ya mace, duk na 'Ya mace ne. Na kuma shaku dake amarya tafiyar ki za ki ta jefa ni cikin wani yanayi na dacin rai."
Ta dafa kafadar ta, ta ce,"Kin fadi gaskiya,"Antina, kuma na san ki ni nuna min iyakar kaunar da ba duka mace za ta nuna wa abokiyat zamanta wannan kaunar ba.
Allah ne ya kaddaro zan sami Ameer, amma ke ce sila Antina.
Ban mancewa har ta kai ki ga rasa na ki cikin. Ina so ki sani Naseer, yana da halayya masu kyau, yana da kula tare da tsare hakki, ni ce kawai da bai so yake nuna min banbanci.Bai damu da ni ba, balle ya kula da hakkoki na. Kar ki damu Antina, ba laifin yayanki ba ne. Allah ne bai sa masa soyayyata ba, saboda haka na ke rokon ki idan ya zo daukan ki, ki yarda ki bi shi, domin ke ce rayuwar sa.
Ke yake so, da ya ke yake ra'ayin zaman aure. Abin alfaharin ki ne a wannan zamanin da ki ka sami miji kamar Naseer, mai tsayuwa akan alkawarin soyayya. A karshe ina son ki sani, har karshen rayuwata ba zan ta6a mancewa da ke ba Antina. Hasalima dole wata rana Ameer wajen ki zai dawo, kin ga har yanzu mu na tare ke nan. Kin hakura ko?
Abinda ya fi ba Zarah mmk, shine ashe Nusaiba na sane da abinda ya faru kafin Naseer ya shiga dakin ta. Gaskiya Nusaiba mai hakuri ce, irin wanda sai an sha bincike kafin a sami irin sa. Ta zura mata ido cike da kwallan tausayi. Allah na ganin bata son rabuwa da amaryar ta.
Nusaiba ta kamo hannun ta, ta dora bisa kan ta,"Ki yi min Alkawarin Antina, a yau za ki koma dakin ki, ba gobe ba, kin ji? Ta goce da kuka, suka rungume juna, haka wahayen ya kubce wa Nusaiba,"Za ki koma ko? Ta dago ta goge kwalla ta ce,"Zan koma Amarya, amma kema ina rokon ki idan a an dai-daita da su Abba, don Allah kar ki kafe ki ce ba za ki dawo ba.Ta yi dan murmushi, ta ce,"Shi ke nan, bari mu zo mu tafi, sai mun yi waya, shi kenan na ji, alkawarin za ki min kamar yadda na yi miki." Ta yi dan jim, kafin ta ce,"Ai ba laifi na bane Antina, ke ma ba za ki yarda in zauna inda ba'a so na ba."
Ta kada kai.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Da ke nan amarya, amma yanzu ina mai tabbatar miki yayanmu yayi nadama, ko bai gaya min da bakin sa ba, ni na yi imanin yana son ki, ba ki ga yadda ya fita hayayyacin sa ba, lkcn da lalura ta kama ki kuma ya kula da ke yadda yakamata.
Ta ce,"Anitina ki na so ki gyara yayanki ne kawai, amma ni na san tausayine irin na musulunci. Kin san musulmi mai imani ya kan tausayawa dan- uwansa a lkcn daya shiga wani hali.
A bar maganar nan Antina, ki yi min addu'ar Allah ya zaba min abinda ya fi zama alkhairi."
Ta numfasa, hannun ta bisa kafadar ta,"Zan miki amarya. Allah yasa alkhairin a gidan yayanmu yake."
Ta mike tana dan murmushi, ta fito ba tare da ta ce komai ba, sbd bata son maimaita zancan. Dakin da su Ummi suke, suka yi sallama. Inna na rike da Ameer.
Zarah ta nufi gun sa, ta dauka, Ummi ta ce,"Zo nan. Ta wuce wajen ta da Bebi a hannun ta, ta tsugunna gefenta, ta dafa kafadar ta, ta ce," Zarah ba'a wasa da aure, hkr za ki yi ki koma dakin ki kinji?Kan ta sunkuye tana dan ta6a kuncin Ameer, ta amsa da kai, sannan ta ce,"Wallahi Ummi Naseer ya gane kuskuren sa, tun jiya yake kuka, yana bin mutane ya samu aje masa biko. Abban sa ne ke fushi da shi, ya ki bada hadin kai.
Don Allah Ummi, ku yafe masa ku bar amarya ta dawo."
Ta ce,"Babu abinda Innar ki bata fada ba yanzu, amma Naseer ya riga ya rushe katangarsa.
Alhj na da saukin kai, sai dai idan ka ta6i shi, nan ne za ka gane ma yana da zafi.
Saboda haka ku taya mu addu'a. Allah yayi masa zabi." Zarah ta yi shiru idunwanta suka kawo kwalla. Ummi ta mike, ta ce,"Allah yasa mu gana." Duk suka tashi suna fadin Amin.
Har mota suka rako su, sannan Zarah ta mikawa Ummi yaron. Ta dubi Nusaiba, kowacce hawaye ya zo mata, suka rungume juna. Da sauri Nusaiba ta shige mota, haka ita ma Zarah ta ruga cikin gida, bata son ganin tafiyar Nusaiba.
Hawayen ta suka yawaita, tana sharewa, wasu na sauka. Direba ya damki hanya. Nusaiba ta yi shiru cikin mota, ta sak'a wannan, ta kwance wancan a game da maganganun Zarah. Tabbas su Abba sun gaya mata Naseer yayi dawainiya da ita sosai a cikin kwanakin nan 50 da ta samu kanta a wani yanayi.Sai dai babu wanda zai tantace me Naseer ke nufi cikin ransa? Ko ita ma Zarah hasashe ta yi, domin da bakinta ta ce bai fito fili ya gaya mata ba.
A cikin tunanin ne ta ji Ummi na fadin,"Ke ba shi nono ya sha, ya farka."------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Ta dube su firgigi. Ummi na masa mika tana cewa ka sha barci ko? Nusaiba ta mika ruwa aka ba shi, sannan ta karbe shi, ta mika masa nono ya kama yana sha.
Nan da nan so da kaunar sa suka kara shiga zuciyar ta har bata san lkcn da fa kura masa ido ba.
Karo na farko da ta tantance kamanin danta.
Tamkar Ameer na farko. Haka kuma hoton Naseer take gani zahiri bisa cinyoyinta. Tsigar jikinta ta tashi yar!
Saboda kyan surar yaron nan, musamman daya buda ido tar!
Yana dube-duben sa.
Ya sha sosai. Ta juya shi daya gefen, nan ma ya sha mai isar sa. Bai koma barci ba. Ummi ta karbe shi, ta ci gaba da renon mai gida.
Jimawa kadan Kausar ta kira wayar Ummi, ta mika wa Nusaiba ta ce,"Ungo Kausar ce." Ta kar6a da saurinta, ta danna O.K."
"Hello."
Ta ce,"Hello Nusaiba ya karfin jiki? Alhamdulillahi."
Ta ce,"Ya maganar Bebi ne? kin san Allah jiya ban yi barci ba." Ta ce,"Bisa hanyar komawa gida muke yanzu, mun je an dauko shi.Ta nisa ta ce,"Better. Ai ni ba zan iya ba, ka aje a jariri, ai ka cuce shi.
Shi me ya sani? Ta yi dan murmushi,"Kausar kenan."
Ta ce,"Tare ku ke da Ummi ko? Bari in yi shiru, idan kin kebe, kya kira ni. Ku sauka lafiya." Ta ce amin. Ta kashe waya.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~­ ~~~~~~~~~~------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Sun iso gida 2 rana. Alhj na falon kasa. Suna isowa Ameer yasa a kafada ya haye sama, yana fadin "Ku hayo sama in gan ku."
Suka haye suka bar Direba na shigo da kaya. Mariya na taya shi. Bayan sun natsa a zaune.
Alhj ya dube su ya ce,"Bayan tafiyar ku. Yakubu ya zo min da maganar Naseeer, haka shima M.Balarabe ya kira ni a waya, kodayake yana min godiya ne akan dauko Ameer da aka yi, har ya ce zai zo musamman yayi min godiya.
Nace ya bar shi kawai, ta wayar ma ya wadatar, na kuma ji dadi. To koma dai menene, ban son mutane su dame ni akan maganar nan.
Lokacin da zan ba Naseer 'ya ta ban yi shawara da kowa ba.
Shi yasa ban son kowa ya sanya min baki, duk hukuncin da na yanke. Na riga na yanke shi. Saboda haka na kira wayar Fatima, na gaya mata za kikoma Jordan, ni zan kar6ar miki takardarki ki a wajen Naseer.
Ina fatan hakan yayi dai-dai.
Idan kuma akwai gyara ina jin ku?
Ummi ta ce,"Zabin Nusaiba ne, me ki ka gani? Ta ce,"Hakan ya ma fi Abba na.
Hankalina zai fi kwanciya."
Ya ce,"To shi kenan.
Insha Allahu nan da kwana 3 za ki bar kasar nan.
Allah ya kawo miki mai son ki, ki aura."
Ummi ta ce,"Amin."Sun jima suna hira nan, kafin Nusaiba ta dawo dakinta, duk bata da kuzari a jikinta, ita kanta bata san dalilin ba. Ta dan kwanta don ta huta. Sai ga Ummi da Ameer ya sake tashi barci.
Ta kar6e shi. Ummi ta fice.
Bayan ya gama sha tashinfidar da shi, ita ma ta kwanta tana fuskartar shi. Rike yatsun sa ta yi tana dan kada su, tana murmushin jin dadi. Sai da ta ci abincin rana, sannan ta kira Kausar suka kebe. Ita ma Kausar din ta goyi bayan Alhj akan komawar Nusaiba Jordan, domin a ganin ta zatafi samun nutsuwa.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Al'amarin Naseer kuwa, bayan ya baro wajen Yakubu, don jin yadda suka yi da Alhj, ransa 6ace ya isa gidan su Zarah.
An riga anyi sallar la'asar. Yana shiga Inna ta yi masa albishir da cewa su Nusaiba sun zo, sun dauki Ameer. Take nan yayi wa Ubangiji sujada, yayi godiya gare shi, sbd tsabar tausayin da Ameer ke ba shi.
Nan da nan wani yanki na 6acin ran sa ya goge. Sai da ya natsa. Inna ta sake fadin,"Sannan su zo nan sun rarrashi Zarah, ta ce za ta koma, nan ma kai take jira, dama kuma ko ba ka zo ba, ni zan maida ta anjima." Ya numfasa, kaunar Nusaiba ta k'ara shigarsa.
Yarinya mai hankali, haka kawai ya tsaneta. Ko me yasa? Ya karkada kai ya ce,"Inna na gode. Ina Zaran take? Ta zo mu tafi." Ta ce,"Tana nan a ciki tana jin ka." Ya mike daga inda yake zaune, ya shiga dakin. Tana zaune bisa kujera, jakarta na aje gefe.
Ya tsaya kan ta ya ce,"Sai na miki dukan musulunci tukuna, bari ki gani." Ya nad'e gefen rigar sa, ya tsula mata." Ni ki ke ba wuya ko? Ta 6alla masa harara. Ya mammare kuncinta. Idanuwanta suka kawo kwalla, sbd Nusaiba da ta fado mata rai.
Ya tsugunna ya kama kunnuwan sa 2, ,"Na tuba." Ya zura mata ido, tana share kwalla," In dai amarya ce, ki kwantar da hankalin ki. Insha Allah za ta dawo. Taso mu tafi." Bata tanka masa ba, ta mike tana ci gaba da share fuska, ya dauki jakar tayo waje, ya biyo ta.
Inna tana zaune, suka sallame ta, ta k'ara jajja masu kunni, suka tafi.
Ko cikn mota ta k'i magana, ya dubeta, yayi d'an murmushi,"Zarah manya,
yanzu ke ma ko tausayina ba kya ji, ina ku ke so in sa raina?
Ta yamutsa fuska, a karo na farko, ta ce da shi.
Oho?
Ai dama wanda bai ji bari bari ba, zai ji hoho!
In banda son kai ma, wa ka ke zaton zai tausaya maka?Ya ce,"Ke mana sanyin raina. Ina ganin ai saboda ke hakan ta kasance, sbd sonki kadai na aje wa zuciya ta. Bai kamata ki juya min baya ba, idan duka duniya sun dora min laifi.
Kalaman sa suka sa jikinta yayi sanyi, ta yi dan shiru kafin ta ce,"Na san haka yayana, amma lokacin da kowa ke gaya maka gaskiya, bai dace ka ki daukar maganar na gaba da kai ba.
Yanzu ina amfanin abinda ya faru? Ya kamo hannunta ya ce,"Wallahi babu, ban ta6a gane ni ba ni da wayau ba, sai wannan karon Zarah. Abin kamar almara na ke ganin sa."
Ta ce,"To yanzu menene abin yi? Ya ce,"Gaskiya ban sani ba, domin Yakubu ya je, amma Alhj ya ce mai kama da ni ma bai son gani, balle ya ji wata magana akan bikon Nusaiba.
A karshe ya ce masa ya riga ya soke ni a rayuwar sa.
Kin ji bayanin Alhj, sbd haka ni ban da wata dabara."
Ta yi tagumi, kafin ta ce,"Tabd'i!
Kai yanzu in tambaye ka tsakanin da Allah, ka na son amarya ta dawo? Ya dube ta ya ce,"D'ari bisa d'ari na zuciyata ke kaunar Nusaiba ta dawo, sbd ta yi min abinda ba zan ta6a mancewa da ita ba a rayuwa."
Ta ce,"To ka gwada wannan dabarar ka gani. Ka ajiye wani tura mutante wajen sa, ka tafi da kan ka, ka ce masa, sai ka ga abinda ya ture wa buzu nadi.!Duk wata bak'ar magana da wulak'anci, ka jure shi, da kansa zai hakura, yana ji, yana gani zai sakar maka 'yar."
Yayi d'an murmushi,"Zarah ke nan, bai saurari manya ba ma, sai ni uban laifi? To zan gwada. Amma ni kunya ma na ke ji mu hada ido da shi." Lallai ba sokake ta dawo ba, kunya ai murje ta ake yi." An gama Zarah,"Allah yasa amarya ta dawo, ko don in huta da ciwon kai."
Ta 6allo masa harara, ya dube ta yayi murmushi,"Ai kin ga na dan sami sauki, ko hararar na rinka sha ta isheni jin dadi." Ta d'an buge shi a kafada,"Allah za ka sani yayana."
Ya take birki a kofar gida, ta dauko jaka a kujerar baya, ta fito ta riga shiga gida. A falon Umma ya isketa.
Umma na mata fada. Ya zauna gefe ya ce,"Umma sun zo sun kar6i Ameer ko?
Cikin rashin kulawa ta ce,"Sun zo."
Ya ce,"An gode ma su."
Ta yi biris da shi ta ci gaba da mgnr ta da Zarah. Jimawa kadan ta koma sasan su, ta yi share- share da goge-goge.
Har dakin Nusaiba ta gyara shi, ta goge zuciyarta na saka mata lallai amarya za ta dawo da zarar Naseer ya je da kan shi.
Kwana 3 kenan Naseer ya kasa zuwa Kaduna, sbd kunya da jin nauyin Alhj. Yau kan Zarah har kuka tayi masa, tana hada shi da Allah da Manzon sa.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Yayi shiri tsaf!
Ya biya ya dauki Sageer suka danki hanya. Gida suka fara zuwa. Mai gadi ya ce ma su babu kowa cikin gidan, duk sun yi tafiya.Daga can ofis suka nufa, sakataransa ya gaya masa Alhj ya tafi Abuja.
Kai abinda babu sa'a. Haka suka dawo jiki babu kwari tare da mamakin ina za su je kuma gaba dayan su har da Nusaiba?
Koda suka dawo irin tambayar da Zarah ta rink'a yi kenan.
Har ta k"arawa Naseer haushi ya ce,"Wai ina zan sani ne Zarah da ki ka dame ni da tambayar nan?
Haba!
Yayi tsaki, ya tashi ya bar mata gidan, don sai su yi fada.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Karfe 10 na safiya su Alh. Basheer na filin jirgin. An gama bincike, an tantance Nusaiba da Ameer tare da kayayyakin ta. Suka yi sallma da su Ummi, ta wuce tana hawaye sabeda Ameer bisa kafadarta, hannunta daya yana kan Beby. Sai dai jirgin da za su shiga, sai sun dan jira shi, ya gama hutawa.
Kamar yadda aka bada sanarwa.
Duk fasinjojin da ake tantance su, na zaune falon, kafin a ba su umurnin shiga jirgi. Nusaiba ta zo ta zauna kusa da wata mata.
Ita ma rungume take da Bebi cikin shawul, ga wata yarinya a tsaye gaban ta, za ta kai shekaru 4.
Tana zama, ba ta yi aune ba, ta ga yarinyar nan a gabanta, tana ta6a Ameer,"Bebi! Mamanta ta juyo tana murmushi ta ce,"Husna ba kya ji ko? Ba na ce ki tsaya waje daya ba? Ta ce," Umma kin ga Bebi mai kyau? Zo ki gan shi."
Suka fara dariya.
Nusaiba ta ce,"In ba ki shi ne ku hada da na ku? Ta ce,"Eh.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Ya sunan shi? Ta ce,"Ameer, ke ya sunan ku? Ta ce,"Adnan.
Mamanta ta ce,"Oh ni, kin ji dadin halinki Husna."
Ko a jikin ta, sai k'ara kwanciya take jikin Nusaiba, tana wasa da kuncin Ameer.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------
Tun daga nan hira ta goce tsakanin Maman Husna da Nusaiba.
Kamar minti 15, aka sanarwa fasinjoji. Su wuce su shiga jirgi.
Tare suka sa6a yara suka wuce, ita fa Husna bata yarda ba, son Ameer take yi, don haka Nusaiba ta kamawa jaka tana bin ta da gudu.(First class) dukkan su za su zauna, sbd haka ga kujerar Nusaiba, ga ta su. Adnan da Manan sa. Su dai ba su yi sukuni ba. Sai da barci ya kwashe Husna. Sun sauka lafiya, ga 'yan tarbar 'yan uwan su nan fululu kowa na jira. Nusaiba ta dudduba, bata hango Antinan ba, haka Maman Husna ke fadin,"Husna kin ga Abbanki bai zo ba ko?
Tana rufe baki ta yana kira,"Husna! Ta kwace hannun ta, ta bi 6angaran da ta hango shi." Abba!
Karo na farko da Nusaiba ta dubi Abban Husna, sam bata gaskanta idanuwan ta ba. Ta kara duban sa da kyau, babu ko shakkar Ibrahim ne.
Jikin ta duk yayi la'asar saboda al'ajabin sake haduwar ta da Ibrahim, wanda tuni ta mance da shi a duniya. Suna tafe Maman Husna na fadin,"Sai yaushe ke nan?
Ta ce,"Ai ina hada layi na, za ki ji kira na. Ai ba zan yi wasa da lambar da ki ka ba ni ba, dole ne in kira Husna."
Suka yi dariya. Nusaiba yanke tabi wani 6angare,"Bari in jira su Antina a nan. Ta ce,"Ah! Ba za ki sallama da Husnar ta ki ba." Ta ce kyale ta, ta ga Abban ta, ta mance da ni." To shi kenan, sai na ji ki." Ta wuce inda su Husna ke tsaye da Abban ta, duk da cukuikuye shi, ta hana shi sukuni.
Babban yaron dake tare da shi, ya rugo ya rungume Maman su, shi ma zai kai shekara 6 ko 5 da rabi. Nusaiba na tsaye duk ta kosa Antinta su zo.......Ta bar wajen. Don bata son Ibrahim ya gan ta, kawai ji tayi Husna na rikota tana fadin,"Zo ka gan shi Abba, Bebi mai kyau."
Gabanta ya fadi, ta waigo cikin tsarguwa, suna hada ido da Abban Husna ya ji kamar zai fadi, sbd faduwar gaba. Bai san lkcn da yayi zuru, ya zuba mata ido ba.
Ta shiga dan yake, tana wa Husna magana,"Ke wai ba mun yi sallama tun a jirgi ba?
Tsayuwayar Maman Husna wajen yasa Ibrahim ya dawo duniyar daya tafi, yayin da Husna ke fadin,"Abba na zai ga Bebi mai kyau.
Ka gan shi? Suka fara dariya, ya kar6e shi ya dan daga sama ya ce,"Good day handsome Bebi!
Yayin da Nusaiba ta juya tana tambyara sunan yayan Husna, ya ce,"Imran." Ta ce,"Uhnmm..............Sunanka da dadi." Husna ta ce,"Ni ma sunana da dadi. Ta kama habarta ta ce,"Sosai ma, ke mai babban suna ma ba'a fadi, shi yaya ake kiran ki Husna."
Dadi ya kamata har da yi wa Imran gwalo.
Ibrahin ya numfasa, ya dubi matar sa ya ce,"Gaskiya wannan haduwa tana da ban mmk. Ai dole ayi dalla-dalla. Wannan ita ce,"Nusaiban da na ta6a ba ki labari. Nusaiba ga Madan din na Sakina." Mamaki ya kama Maman Husna, take nan kishi ya kulle ta. Ta dan daure fuskata ta ce,"Ka ce min wacce ta kusan zarar min da kai.
Nusaiba ma ta gyara fuska, ta ce,"Ki bar maganar nan Maman Husna ta riga ta wuce." Ya ce,"Sai zumunci ko? Yana da kyau, ina fatan kin bata adires, kafin ta koma, za ta kawo mana Ziyara."Sakina ta gyada kai tana yamutse fuska,."Na dai bata lambar waya."
"Mts, ina ganin ya kamata mu wuce Abban Husna, na fara gajiya wallahi."
Ya ce ,"Tunda ba'a zo daukan ki ba, why not ba za ki bi mu, mu sauke ki gida ba? Sakina ta kauda kai yayin da Nusaiba ke 'yar dariya, tana fadin,"Ku bar shi Allah na gode. Ai na san za su zo."
Ta mika hannu ta kar6i Ameer a hannun sa.
Ya maida hannaye aljihu, ya numfasa, amma bai iya cewa komai ba.
Ta shashshafa kan su Husna ta ce,"Sai anjima ko Husna!? "Bye-bye Bebi, sai ka zo gidan mu." Suka yi sallama da Sakina, ba wata walwala a fuskarta, ganin haka Ibrahim yayi gaba rike da hannayen yaran sa.
Sakinta ta bi bayan su cike da kishin babu gaira babu dalili.
Nusaiba na nan tsaye, duk takaicin al'amarin ya dameta ta, kamar minti 5 da wucewar su.
Antinta ta iso,"Allah sarki Nusaiba, sorry,"Wallahi sharrin mota ne, cak ta tsaya mana

Chapter 4 of 8