Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 9
ace ubanmu ne daya za a daukeki a baiwa wani ina kallo ba?" Na ce "Kai Yaya Almu mu bar maganar nan kawai, tana sawa gabana yana faduwa, zuciyata tana harbawa da sauri." Ya yi maza ya ce "Uhm to gara mu bar ta, bari mu yi wata me sunan wannan abincin da za ki yi mana? Na cc mishi "Stuffed chickcn onc" Na yi mishi lakabi da "one" din ne don zan iya yi maka su kala- kala don haka ran da zan sake yi maka wani zance maka stuffed chicken No 2, don in bambance maka su, ya saki wani irin lallausan murmushi ya ce ai na yarda da ke Rabi na san ke gwanar girki ce na kuma san za ki iya tattalin mijinki za ki iya tarairayarshi ki reneshi in na zauna na yi tunani na tuna tsananin kwadayina game da shimfidata sai in ga to ina ma dai ke ce wacce zan rinka shimfidewar? Kin sanni ina son mace mai sura irin taki, ina son komai naki Rabi ina Son duk wani yanayi naki in da za ki yarda da shawarar da na kawo da kin yi mamakina da kin ga irin tarairayar da na yiwa shagwabarki." Na yi ajiyar zuciya mai karfi na ce Yaya Almu ka yi hakuri ka san ban saba yin irin wannan maganar da kai ba." Ya cc "Gaskiya ne Rabi gaskiya ne, to koya 36 mun girki in mutum zai yi stuffed chickcn one, me za1 bukata? Na soma yi mishi bayani cikin sauri don ban son ya sake kawo wancan hirar tashi na ce mishi dankwalcliyar kaza katuwa kamar wannan ya ce na ganta, na ce to ga nama cikin cup madaidaici, butter cokali shi da na ture wadannan gefe na sake jawo wani hadin na shiga nuna mishi na ce sai kuma wannan naman saniya cup daya da Rabi ferarreen dankalin turawan da aka yanyanka shima cup daya madaidaici ga butter cokali takwas, murmushi biredi cup daya, kwat guda biyar sai albasa guda biyu suma. Ya ce To amma Rabi wannan irin girki naki ba zai saki kiba ba?" Na yi murmushi na ce "Ai kuma na iya abincin rage kibar iri-iri." Ya cefo mu yi magana gaskiya Rabi kin san ba zai yiwu ina kallon alheri da idona kuru-kuru in barshi ya wuceni ba, ni fa gaskiya na fi so ki zama matata ni bana son yin kanwar da ke in kima bukatar yayu ga su Zubairu nan ga su Junaidu da su Kabiru ke har su Hamza da su Musa sun gimeki ki yi dasu, ni ki bar ni kawia in zama mijinki uban 'ya'yanki, ki haifar musu masu yawa, ki yi musu tarbiyya su zama mutanen kirki na cc a'a.ba za a yi haka ba kai, dai ka je ka auri Uwalenka, nima in auri Mustaphan wurin Itinmu yallabai dama ni ina son shi don ina sha'awar tebarshi tana ba ni sha' awa ka sanni ina cikin maie masu girmama teba da ganin darajarta be zan iya 37 zama da wanda ba shi da ita ba. Nan da nan na ga Yaya Almu ya tsuke fuska alamar zuciyarshi ta so su shi kuwa na yi maza na koma kan aikina na kamashi gadan-gadan na dauko turmin karfen da na riga na wanke na kife don ya bushe shi da tabaryarshi na zuba naman nan na soma dakashi tare da ferarren dankalin nan sai da ya yi laushi tukuna na kwasheshi cikin wani kwanon silba mai dan fadi na juyre murmushen biredi akai da kayan yaji da yankakken albasa na sa kwai da ruwa cokalin cin abinci guda biyu na cakudasu da kyau sannan a dauko dankwaleliyar kazar nan da ba a cire komai a jikinta ba sai kai da kafafuwa na yi ta cusa kwababben naman nan a cikinta sai da na cikata tam ta yi matukar yin nauyi sannan na kawo zaren lilo na daurcta da kyau Yaya Almu yana bayani ta hanyar rike mun ita sannan na kawo blucband na yi ta mulketa da shi kafin na bude 0ven na sakata a ciki ta soma gasuwa na ce m1shi minti arba'in da biyar za ta yi a wannan wutar don haka bari in yi wannan hadin ka gani ya ce mun to. Na dora wancan naman cup daya na yi mishi hadin farfesu mai ruwa sosai na zuba kayan hadi su kayan kamshi shima na rufe sannan na koma na sake shiryawa Baba abincin darenshi na ka'ida tawon laushi miyar yauki na tuka mishi tuwon alkama miyar busasshiyar kubewa, na dawo kan kazar nan na ce wa Yaya Almu ai ka ga bayan minti arba'in da biyar din 38 nan na sake rage wuta ta yi kasa sosai na tsawon minti talatin ya ce Eh na gani na ce to yanzu komai ya kammala bari in cirota ta gani na ciro kazar ta yi shar gwamin sha'awa sai wani kamshi ke tashi daga cikinta na juye farfesu a kanta cikin kwanon dana sanyata mai kyau na' kawo murfi na rufe. Yaya Almu ya ce bari in kai mana wannan ke kya taho da sauran. Na ce mishi to. Na shiga falon, na samu Baba yana tambayar Yaya Almu kai ka yi sallar Magariba kuwa Lamido?" Ya ce "Eh Baba itama mai girkin ai ta yi balle ni na bi ku sallah ana idarwa ne dai na fito ban tsayya ba." Na isa wurin ajiye abinci na ajiye kwanukan da na zo da su kamshi ya gauraya ko ina Baba ya kalleni cikin murmushi ya ceUwata in kina mun irin wannan liyafar a za ki sa in fasa yin bikinki a bana ba kuwa?" An zauna gaba daya ana cin abincin rana cikin raha, Baba ya sakc cewa da can duk tsawon lokacui uwata ta iya irin wadannan girke-girken amma ba ta ciyar da danta da su ba ta boye abinta sai ta je gidan mijinta ta yi ta shirya mishi gara, miji ya fi uba ne uwata? Na kalleshi cikin ladabi na ce mishi "A'a Baba, ya yi maza ya ce "A'a ya fi miji ya fi uba daraja uwata don kuwa shi ta dalilin biyayyar da ki ka yi mishi ne za ki shiga aljanna, uwarki ba ta taba gaya miki haka ba?" 39 Na ce Ta taba." Ya ce "Yauwa to ita ai mai girmama aurenta ne." Na idar da sallar isha'i, bayan na yi wanka sai na zauna na yi kwalliya bayan na gama shafe jikina, na gyarashi yanda ya kamata, doguwar riga har kasa na sanya na wani yadin material bluc, Umma ce ta zo mun da yadin daga Dubai tsawon rigar ta sanya har ba a iya hangen siket dinta dake jikina, wuyan rigar an yi adon zare dan kadan na daura dankwalin a kaina sannan nakawo sarka da 'yan kunne bluc da warwaro da zobe mahadinsu na sanya, farin zaren da aka ratsa da blue wajen yiwa wuyan rigar ado ya sa na yi amfani da farin gyale dan siriri sosai na sanya farin takalmi da jaka na kara fesa wani turen na yi matukar yin kyau na fito na shiga dakin Baba inda duk aka hadu ana ta hira na je na zauna kusa da Baba a kasa sai dai ban tsoma baki cikin hirar tasu ba, ian dai ji ne kawai don ta yi mun kama da hirar manya da suka gama ne yaya Junaidu ya yi wa Baba sallama ya ce mishi za su tafi, za su bi Jirgin karfe goma. Baba ya yi musu addu'a, suka yiwa Umma Amarya sallama suka fita. Yaya Almu ya ce mun zo mu je ki rakani mu kaisu airport mu dawo. Baba ya kalleshi ya ce "Kai Lamido ba ka ce gobe kana case a court ba ne, ya ce eh zan yi Sammako in tafi ya ce to shi kenan ke uwata tashi ki rakashi, na bi bayan Yaya Almu wanda shima ya sha kwalliya cikin farin boyel. 40 A hanya muna dawowa ya dan wiawayo kadan ya kalleni ya ce mun "Ina son ki fa Rabi kin san ai ba zai yiwu in yi ta yi miki haka-haka ba, ko? Na ce "E to haka ne amma ai ka san ni kuma da wuya in yarda ka san mene ne so?" Da sauri ya tambayeni don me? Ina da shekaru talatin a duniya ki ce mun ban san so ba? N acc to kwanan nan ka gama son Aina'u har kana zama kana rera mata wakoki kana siffantata da siffofin ban mamaki kace wai kai a haka kake ganinta a irin son da na san kana yi mata, ni na dauka in ba a baka ita ba suma za ka yi ta yi sai na ga ka shanye kemadagas ko a jikinka sai ka koma son Uwalen da aka ce za baka ko yau da safen nan akan sonta ka ke shi ne nima yanzu za ka ce kana sona? Ya ce "E ai ina sonki din ne." Na ce "To kar ka sake gaya min haka abin da na sani shi ne kai wana ne ubanmu daya don haka ni ban taba yin wani tunani game da kai ba, yallabai kadai nake so shi ne yake bani sha'awa tebarshi kuma tana burgeni tun ba in naga ta turo cikin babbar rigar nan tashi ba." Yaya Almu ya buge mun bakina da karfi da bayan hannunshi na sa hannu na taba labban nawa na ga jini don haka da karfi na rinka kurma mishi ihu har muka iso gida ban yi shiru ba yana tsayawa na bude kofa na fito ban saurari maganar da yake yi mun na nufi falon Baba ina ihu ga shi na yi sa'a labban nawa 41 sun kukkubura shi kadai na smau a ciki na durkusa gabanshi ina ihu ya zubawa bakin na wa ido yana kallo. "Yi hakuri uwata ai kin wuce irin wannan kukan mai karfi yi shiru ki gaya mun me ya fasa miki bakin naki haka?" Na bar kuka na ce mishi Yaya Almu da kanshi ya lcka ya kirashi ya shigo, ya kalleshi ya ce me ta yi maka haka? Ya ce rashin kunya ne da ita Baba ba zaka gane rashin kunyarta ba sai na ce maka Baba daga shekaran jiya zuwa yau sau biyu Umma ta bugeta. Fuskar Baba ta yamutsc alamar ranshi ya baci da jin bayanin na Yaya ALmu ya kalleshi cikin 6acin rai ya ce lallai ne ka gaya mun abinda ta yi maka mai tsananni wadda ya sa ka yi mata wannan abin bayan ta yi kwalliyarta mai kyau dubi abinda ka yi, na ce ka duba waiwaya ka gani me ta yi maka? Yaya Almu bai boye ba ya ce maganar mutumin wurin Antinsu take yi mun. Baba ya kalleni cikin nutsuwa ya cc me yasa haka uwata? Na kalli Baba cikin nustuwa na ce Baba dama ana aure tsakaninw ad akanwa ne? Ya yi maza ya ce Babu na cc a to to shi Baba sai ya rinka yi mun wata magana na ce mishi ni da shi ai kaine ka haifemu, ya ki. Baba ya ce to kai me ya sa ka ki Lamido? Yaya Almu ya sake maida bayanir shawarar daya bayar, Baba ya yi murmushi ya ce to amma uwata ai ina ganin kamar lallai Lamido yana sonki tunda har zai iya kawo wannan shawarar a tsakaninku ban ga abinda zai sa ki 42 ki yarda ba, na ce msihi a'a baba ni na fi so ace Yaya Almu dani dukanmu 'ya'yanka ne bana so ka rasa kowa a cikinmu bana so ace ba kai,, ka haifi Yaya Almu ba haka nan zan yi bakin ciki in har aka ce mun ba kaine mahaifina ba nan da nan na soma yi mishi kuka baba ya shigå rarrashina har na yi shiru na share hawyaena na kalleshi cikin nustuwa, bayan fitar Yaya Almu na ce mishi Baba waye Mustaphan da aka ce z aka baiw ani? Ya zuba mun ido ya ce Lamido ne na sake buda baki cikin karfin hali na ce mishi Baba su waye suka haifeni? Da gudu hawaye suka rinka zuba daga idona, Baba ya sake kallona ya ce mini, "Kina tuhumar umarki ne? Na yi maza na ce mishi, 'A'a." To don me ni za ki yi mini wannan tambayar kin taba ji an ce miki ga dan'uwanki ya zo? Na yi maza na ce mishi, 'A'a Baba." "To don me shi Lamido ba za ki hada shi da su Junaidu ba, me ya fi su? Me ye bambancin shi da su? Da Lamido da Junaidu da su Zubairu duk daya ne kar ki damu kan ki da cewar shi yaya yake, muhimmin abin shi ne ke tawa ce wani muhimmin abin kuma shi ne Ummanki ce uwarki al'amarinki mai girma ne a wurina, don haka jna fata za ki kar6i mijin da na zabar miki da hannu bibiyu in dai ba ba kya son shi ba ne." Na durkusa gabanshi na ce mishi, "Zan bi umarninka da hannu bibiyu Baba ko da ba Yaya Almu ka zaba mini ba, balle Yaya Aimu sanin halin shi da 43 alherinshi da na yi ne ya sa na ke tsoro kar a ce shi ma ba na ka ba ne?" Ya ce, "To kar ki ji komai ni kowa nawa ne." Na ce mishi, "To Baba." Shigowar Umma Amarya ya katse hirarmu don kuwa dare ya yi nisa hakán nan shigowa ta yi da shirin kwanciya. Washe gari kuma fitowa na yi ban ga Yaya Almu ba. Wajen karfe goma na shiga falon Baba, saboda na yi barcin safe, na gaishe shi na zauna nan muna karyawa. Ya ce mini, 'Ai Lamido ya zo zai tashe ki wai ku tafi na ce mishi ai ko don dukan da ya yi miki jiya ba zan barki ki bishi ba kin ga kuma har yanzu labban naki a kumbure suke, ki rinka kiyayyye maganar da za ki rinka gaya mishi, kin ji ko?" Na ce mishi, 'To Baba." Da La'asar sakaliya sai ga Yaya Almu ya dawo alamar dai yana-fitoa daga kotu, arport ya je ya dawo Lagos. Na kalle shi na yi murmushi, Baba ya taya ni murmushin, shi kuwa ya kule. "Ai dariya ma kike yi mini?" Baba ya ce, Za ta yi mana ai ba ka da jarumtaka ne na dauka fushin da ka yi da safe ba za ka dawo ba sai kwanaki bakwai din da nan diba sun cika." Yaya Almu ya sunkuya ya ce, 'Baba sauran yan matan fa suna can suna ta shirye-shiryensu." Baba ya ce, 'Haka ne to gobe in Allah ya kai 44 mu sai ku tafi tare." Hankalina a kwance yake lokacin da na dawo gida, ba ni da wata damuwa cikin raina, sabdoa tsoron da nake ji din an kawar mini da shi, ni ce dai yar baba ta asali ta cikinshi shi kenan bukatata ta biya. Yaya Almu kuwa na san shi ne mijin da ya dace da ni, zabin da Baba ya yi mini din zabi ne na tsananin kauna zaton da nake ji cewar shi din uba daya mu ke shi ya hana ni yi wa kaina sha'awarshi, ko a hakan kuma ina kishin kalaman shi kan matar da zai aura. A yanzu kuwa son shi nake yi da iyakacin raina, illa iyaka dai na ki yarda in nuna mishi hakan. A falon Umma muka fara sauka mun same ta da baki sosai, kawayanta ne da na dade da sanin su a duk lokacin da hidima ta taso mata, kuma sune farkon masu zuwa kan lamarin nata, don kuwa aminanta ne na kut da kut. 'Ashe bikin Adawiyya ya tashi? Abin da sabbin shigowa falon suke gaya mata kenan. "To wai ni Furera Adawiyya ce kawai za a yi bikin ta ne? "Har da su Junaidu fa cikin masu aure nan. "Amma bakwa ambaton kowa sai Adawiyyah." Umma ce mai, gayawa wata kawar tata haka. Ta ce, 'A'a to wannan ai ke ya shafa mu kam ai auran yar mu muka sani za mu yi bikin 'yar fari kuma yar auta." Gaba daya suka kwashe da dariya. 45 "Kin fara tsuma mana ita kuwa? Don na san halin ki." Umma Hauwa'u ce mai wannan maganar. Irin wadannan kalaman sune suka yi sanadiyar fitata daga wurin Umma na ce bari in je in gaida Umma Karama da sauran mutanen da aka wajabta mini gaishe su a gidan. Sai dai ina shiga sashin Umma Karama na soma jiwo abin da ya birkitani ya fiddani cikin hayyacina, ya katse mini farin cikina, ya sani na Ji tamkar yawo nake yi a sama. "Wai a kan wannan shegiyar 'yartata. To shegiya mana wane ne ubanta? Nan gidan ubanta ne? Shi Lamido dama a mallake yake a hannunta, don abin da yake mata ya wuce biyayyaya tasan ma bauta daga kawai na ce ban yarda hadin da ya ce zai yi tsakanin Lamido da yarta ba, don hakan tamkar neman mallaka mata komai na shi ne tun da za ta mallaki Lamido shi kuma kamata ya yi a ce kowa na shi nc a gidan don haka Aina'u ce ta dace da shi, ita ce yar dangi ba wannan yarinyar da ba a san asalinta ba. To ba a san asalinta ba mana, mene ne asalin na su da Uwarta?" Rantsuwa mai tsammanin karfi na ji Umma Karama ta yi kafin ta sake jaddadawa wanda take magana da shi diu cewar ni şhegiya ce daka kawai tafi karfin Alhaji. Dafe kirjina na yi da hannu biyu ina fadin, "Na shiga uku." Na juyo da sauri na fita na nufi dakinmu zan je in dan kwanta in huta, saboda kai tsaye ba zan 46 iya fuskantar Umma da wannan zancen ba. Ina tafiya inan kara jaddada mamakina game da hadani aure da yaya Almu da aka ce za a yi. Ina shiga dakin mu na wuce Aina'u da Basira, na fada kan gadonmu na kwanta na dafe kaina, saboda sarawar da yake yi. Bayan na dan nutsa ne na ji hirar da suke yi sosai, ashe wai Ummana suke zai shi ya sa ba su samu damar amsa gaisuwar da na yi musu ba. "Cikin shiege ina jin ta yi ta haife ta, tun da shi kam baba ai kowa ya san yaya Aimu dan shi ne." Maganar Basira ne wannan da ta yi matukar kashe mini jiki. Tabbas in har za a cire mutum daya tsakanın ni da yaya Almu a ce wane ne wanda ba baba ne ya haife shi ba? To ina ganin kamar ni ce za a cire. Son kai ne kawai ya hana ni yin wannan hukuncin, to amma kuma zai yiwu a ce ni shegiya ce a ce ba a san asalina ba? Ina cikin wannan kidmane na ji Aina'u ta fige zanin gadon da nake kwance a kai tana tambayata. "Kin shimfida gadon ne da kika zo kika hau kai?" Na ce, 'A'a amma ko ban yi shimfida yau ba ai akwai ranakun da nan ke yi, ban zo na kwanta akai ba. " Ta ce, Ke kar ki kawo mini iskanci kin ji?" Ni uwarki ma yanzu ba girmanta nake gani ba, balle in ji tsoronta. Kan mu rabu kuma zan nuna mata asirin da ta yi wa baba da Umma Amarya da su yaya Almu, ni bai kama ni ba, don haka daina nuna mana wata 47 gadara, don an riga an yi iska abin kasa ya riga ya bayyana, mun riga mun gane nan ba gidan ubanki ba ne cikin she.......... " Kan ta kai karshen maganar tata ban san yanda aka yi ba ganí na kawai na yi a tsakar gidanmu muna cin uban dambe ni da Aina'u. Na kuma san danben ne ya fito da mu daga dakin na mu. Damben mai tsanani ne sosai, don kusan su biyu ne a kaina. Yaya Zubairu ne ya turo kofar wurin namu da saurin shi ya zo ya raba mu, na kalli Aina'u na ce, "Karya kike yi ki ce ba kya jin tsoron Umma don kuwa ko ni zan yi mata maganinki ba kuma ke ba na gaba da ke ma tafi karfin su. Ke Adawiyya ku wuce mu je." Umarnin da yaya Zubairu ya bayar kenan. Muna fitowa muka gamu da Umma Karama za ta shigo wurin namu, cikin sauri watakila labarin damben namu aka kai mata, shi ya sa ta zo da kanta. Can wurimta yaya Zubairu ya kai mu. Muna shiga wurinta ta kalle su cikin takaici ta ce musu, "Ku biyu ita kadai amma ji abin da ta yi muku? Ji ki Basira, ji fuskar ki tabarya ta kwada miki ko?" Ganin yaya Zubairu a bayanta ya sa ta y1 maza ta yi shiru cikin jin kunya. Sai kuma ta shiga yin tada wai za ta ji abin da ya hada mu. Aina'u ta ce mata ji kawai ta yi kawai ta yi na rufe ta da duka. Ta ce, "Eh. to dole mana samun wuri ne kansa bako ya fi dan gida 48 iko a gida." Ta kalleni ta ce, "Amma ai kin san su Aina'u ko Sa'a sune sun fi karfin duka a wurinki, don su nan gidan ubansu ne, ke kuwa fa kina tambayar uwarki asalinki? " Ban ji kunyarta ba na ce, Ba na tambaya ba kuma zan tambaya ba, don girmanta yafi gaban a tuhume ta, na kuma san inda duk ta samo ni ni 'yar halak ce, don Umma ba ta yi kama da mai yin halin banza." Ina maganar ina kuak sai na ji yaya Zubairu ya yi mini tsawa, "Ke Adawiyyah kar in sake jin kin yi wata magana." Ta ce, 'A'a kar ka ce za ka ce mata komai ni uwarta ce daidai da ni." Tana fadin haka ta figi gyalenta ta wuce wai wurin Umma za ta. Yaya Zubairu ya bi bayanta yana cewa, 'Umma kar ki jc mata wuri ki yi hakuri ki dawo wurin ki." Ba ta kula shi ba. Da gudu na wuce na tafi wurin Umma na yi sa'a duk bakin nata sun tafi kan ma in ce zan ce mata komai sai ga Umma Karama ta shigo. Wadansu irin maganganu take yi masu tsananin zafi da gore- gore wai tana rama zagin da na yi mata. Umma tana jinta ba ta daga ido ta kalleta ba, balle ta buda baki ta tanka mata, in banda da ta ga za ta nufo falonta na farko ta shigo inda take zaune ne ta ce mata, "Kar ki karaso nan, saboda ba na so ranki ya kara 6aci, in dai kika tsaya anan to za ki yi ki gama lafiya." 49 "Me za ki yi?" Ta shiga dura ashar. Ana cikin haka sai ga su yaya Junaidu dukkansu sun shigo ga alama yaya Zubairu ne ya kira su. Yaya Almu ya ce, 'Amma Umma wannan abin ai shi ne abin da ba zai yiwu ba ko? A ce wata zata tashi ta je wurin wata ba don mu'amular arziki ba sai don ta je ta ci mutuncin ta, yanda babu mai yi miki haka. Hakan nan ba zai yiwu ki yi wa wata ba in Rabi ta yi miki rashin kunya, sai ki gaya mini don ba ki taba kawo kararta na kyaleta ba." A fusace Umma Karama ta ce mishi, 'Ai lokacin ba ta gama da kai ba ne, amma yanzu da ta fara tura maka ita kuna kwana me za ka iya? Me zan ce maka jiya da shekaranjiya duk a ina ku ke? Ina ce kuna can küna holewarku." Ban san lokacin da yaya Almu ya sulale ya bar wurin ba, ya bar Umma Karar1a tana ta faman fadin maganganunta har ta yi ta gaji ta juya ta fita, saboda ta gaji da zage-zagen da take yi. Ba wanda ya tanka mata. Bayan fitar ta ne yaya Kabiru ya kalleta cikin sanyin jiki.ya ce mata, "Ki kara hakuri Uma." Ta yi murmushi ta ce To ya ya zan yi? Ina na kula ta muka yi kuma ai ni ce a kasa, Adawiyya ce ai ta jawo jta ta yi mata rashin kunya." Yaya Zubairu ya yi maza ya ce mata, "A'a Adawiyya ba ta yi mata komai ba, Umma ke dal kawai ki yi hakuri." 50 "Ba komai." Umma ta ce da shi. Da daddare rannan ina kwance a bayan Umma ita ta ce in zo in hau bayanta in kwanta. Ina kwance a bayan nata tana tambayata. "Jikinki dumi Adawiyya ko ba kya jin dadi ne?" Na ce mata na yi kwance cikin ruwa mai zafi ne Umma. A hankali ta soma yi mini hira cikin nutsuwa, "Sai kin zama jaruma kin zama mai hakuri kan zaman da za ki yi da Babangida, shi kam ba ki da matsala da shi, don kuwa babu wani wanda zai so ki kwatankwacin son da Babangida yake yi miki. To amma, yan'uwanshi su ne matsala." Na ce mata, "Umma." "Mene ne?" "Kin yarda in tambaye ki wani abu?" "Uh, uh kar ki tambayeni komai yanzu barci ya kamata mu yi." Na ce mata, "To." Na kara matsawa jikinta na jingina kaina da bayanta. Sannan na shiga barci. Dare ya yi nisa lokacin.da na ji Umma tana kiran sunana cikin salati da tsoro ta. "Adawiyya! Adawiyya!!." Na bude idona a hankali ina kallonta cikin rawar jiki a dalilin tsananin zazzabin da ke kadani kar! kar!! Kar!!! Na zuba mata ido ina kallonta cikin yanayin rashin lafiya. A hankal na bude baki na ce mata, "Ki yi hakuri Umma dazu na ji tsoron gaya 51 miki ne su Anti Basira sun cijeni da karf." Umma ta ce, "Cizo?" Ta shiga salati tana kuka. Yayin da take yaye ruhuwar tawa, don ganin inda cizon yakc. Nan da nan ta shiga kuka mai tsanani tana cewa, "Ya ya zan yi da ke Adawiyya? Ya ya zan yi da wadannan mutane da suke shirm tosa mini ke a gaba? Ba ki kuma yi musu komai ba, laifina ne kawvai ya shafe ki, kiyayyar da suke yi mini ne za su dawo da ita kan ki." Ta sa hannu ta dauki wayarta. Y aya Junaidu ta kira. Har cikin dakin Umma ya shiga, ta nuna mishi jikin nawa, ya ce, 'A'a wannan al'amari Umma hakuri fa za ki yi kawai tun da dai an kusa rabuwa ba kuma zai yiwu ki ce za ki yi wa yara wani abu ba, tun da dukkansu ya'yanki ne." Ta ce, "Haka ne." Cikin daren jiya Junaidu da Umma suka kai ni asibiti aka yi mini allurai, suka dawo da ni. Kwana biyu ina jinyar cizon da su Aina'u suka y1 mini, amma ba wanda ya sani, don yaya Junaidu ya ce kar a gayawa kowa, a yi shiru kawai. Rannan yaya Almu ya kirani, na same shi

Chapter 3 of 9