Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 6
biye dashi a baya. Shigarsu keada wuya sai dalibai suka dauki ihu baki daya 'boss! Boss! Suka daga Nafi'u sama suna yawo da shi acikin ajin da kyar suka ajje shi. Nafi'u ya dubesu sannan yace "Ga Boss nan a gabanku". Ya nuna Nuraddin da dan yatsansa hannunsa na rawa. Har yanzu ganin mahaukaci yakewa Nuraddin Nafi'u ya zagaya ya nufi gurin zamansa, a ganinsa kowanne lokaci zai iya hawansa da duka. "A'a yau kuma guduna kake yi?" Nuraddin yace, sannan ya fashe da dariya. "karyar banza ashe dai gabama da gabanta wai Aljani ya taka wuta, ka kake cewa wai ko shedan ne mutum baka tsoronsa." anya kuwa nima xan iya bin Nuraddin domin jiyo muku abinda zai faru? Sai kuma mun sake haduwa daga Aljani Ya Taka Wuta!....6 - - - - Dajin yayi shiru bakajin komai sai motsin ganyayyaki bishiyoyi dake gogayya da juna sakamakon iskar dake busawa cikin wasu lokuta kuma akwai jefi-jefin kukan tsuntsaye da sautin ruwan dake gudana cikin koramun dake zagaye da gurin. - Nuraddin yaci gaba da tafiya, amma har yanzu jikinsa rawa yake, domin daya daga cikin kawunannan masu gemu daya gani, yaso yayi kama da kan malam mahmud, malamin arabiyarsu, ni kuma wanda na gani yaso yayi kama da kan mai karanta labarin nan hehehe. - Bai dade da fara tafiya ba sai yazo daf da inda hanyar ta rabu gida biyu, hanyar datayi gabas, itace zata kaishi har zuwa makaranta. A daf da gurin tsakanin wasu bishiyoyi guda biyu, wata katuwar tsamiyace mai duhun ganye. Anan ne to Nuraddin yaga abin mamaki.Yana zuwa inda hanyoyin suka rabu, sai ya mike cikin sauri yabi wacce ta nufi gabas din ba zato ba tsammani sai bishiyar tsamiyar dake tsakanin bishiyoyi biyun ta girgiza sannan saita tunbuko daga cikin kasa, jijiyoyinta a waje tsirara, sannan saita nufi tsakiyar hanyar da Nuraddin kebi ta dasa kanta a hanyar. Nuraddin yayi turus ya tsaya cikin kaduwa, yayi kamar ya koma da baya, to amma idan ya koma da baya din ina za shi? Jikinsa na rawa sai ya karkata yabi daya hanyar data nufi kudu lokaci guda sai bishiyar ta sake tunbukewa ta tashi sama sannan ta sauka a tsakiyar hanyar daya fara bi ta sake dasa kanta. Nuraddin ya sake yin turus ya tsaya akaro na biyu, sai dai wannan karon lokaci guda ya juya a razane zai gudu, sai yaga bakin labulen duhun nan ya sauko a gabansa da sama bakinkirin babu hanyar gudu. Ga yamma tayi bakinkirin babu hanyar wucewa ga gabas bishiya ta tare hanya. Nuraddin ya juya nan, ya juya can yana neman hanyar gudu lokaci guda kuma kwakwalwarsa nakokarin tuno addu'a kowacce irice ma, sai dai rabonsa da rike addu'a ma, tun yana karatun dare a waje babansa. A dai-dai lokacinne wata katuwar mage ta keto da gudu daga cikin bakin duhun daya rufe bayansa, ta nufi kan katuwar bishiyar. Hawan magen keda wuya sai bishiyar tayi girgiza nan da nan ta rikide ta koma wata irin halitta mai zako- zakon hakora kamar kibiya, gashin kan halittar tamkar kayoyin aduwa. Halittar tana da kofato, sannan abin mamaki kuma shine dukkan jikinta a lullube yake da gashi kamar tunkiya.Nuraddin ya dubi jibgegiyar halittar ya rufe idanunsa yana mai fatan dama mafarki yakeyi, sai dai kuma arufe idanun nasa ma bai hana shi ganinta ba. Ya sake bude idanun nasa ma bai hana shi ganinta ba. Yasake bude idanun har yanzu dai tana nan shirim! A gurin tana dubansa da jajayen idanunta masu kamar garwashin wuta."Bance kada na kara ganinku a hanyar nan cikin dare ba"? Ta bugawa Nuraddin tsawa hayaki na fita daga bakinta kamar salansar mota."kai kafi kowa taurin kai ko"?Nuraddin yayi tsaye yana kallonta, yana kuma sauraronta. Tun abin na bashi tsoro harma ya soma bashi haushi."shin baka ji kashedin da nayi maka bane"?"Banji ba"! Nuraddin ya samu kansa yana mai cewa. Bai san lokacin da kalmar ta subuce masa ba, amma ya gama yanke kauna cewa wannanitace kalmar karshe da zai furta a duniya, jira kawai yake yaji tayi sama da shi ta jefa a cikin wangamemen bakinta mai kama da kofar gari.Shiru-shiru baiji komai ya faru ba, babu kuma alamar motsin komai a dajin sai sautin zubar yayyafar ruwan da har yanzu bai daina zuba ba. Nuraddin ya bude idanunsa a hankali, ga mamakinsa sai ya hanyar wayam babu matar nan ta bace haka nan bishiyar tsamiyarnanma ta koma inda take ta zauna. To amma lokacin da Nuraddin ya waiwaya bayansa, saiya ga har yanyu duhun dake bayansa bai yayeba. Wannan shiya dada tabbatar masa da cewa har yanzu yana cikin hadari, domin ya san mai zako-zakon hakoran batayi nisa da inda yake ba.Daga inda Nuraddin ke tsaye yana jiyo rugugin aradu jefi-jefi a can wani bangare na cikin dajin. Ba'a dade ba sai aka sake kwatsama wata aradun mai karfin gaske wannan karon ma har tafi wadanda akayi a can baya tsoratarwa. Walkiya mai hasken gaske ta biyo bayan aradun. A cikin'yan dakikun ne to Nuraddin ya fara ido biyu da wata kyakyawar sura. Walkiya ta haskaka wajen, Nuraddin yakai idanunsa ga ruwan dake gudu a gefen hanyar, a cikin ruwanne to yaga kyakyawar fuskar ta tana masamurmushi."Yau na gamu da gamona". Nuraddin yace cikin zuciyarsa. A daidai wannan lokacinne sai yaji wani irin ni'imtaccen kamshin turare ya mamaye gurin, sannan ne to ta bayyana a gabansa a zahiri kamar an jehota daga sama, fuskarta na sheki da annurh, hasken kyakykyawar fatar jikin budurwar shiya haskaka dajin. Kyawun budurwar bashi misaltuwa ga dan adam. Doguwa ce ba can ba'yar shafalfal mai tsukakken jiki da kyawun girar idanu, fatar bakinta narai narai dasu jajaye suna kyalli kamar ka taba jini ya fito, gashinta abin kallo da daukan hankalin duk wani da namijin duniya.... Aljani Ya Taka wuta!.....7 - - - "Jarumi Nuraddin". Tace dashi tana haskaka fuskarsa da tattausan murmushin Allah kashe ni dan dadi.Nuraddin ya dubeta duban nutsuwa tun daga sama har zuwa kan kafafunta. Hakika duk halittar dake jikin budurwar babu makusa, tunda yake bai taba ganin halitta mai kyawunta ba, ko shakka baya yi, yasan ta ninka Badawiyya kyau nesa ba kusa ba. Ga mamakin Nuraddin sai yaji duk tsoro da fargaba sun sake shi lokaci guda kamar cirar kaya.To amma fa duk wannan kafin idanun Nuraddin ya kawo ga kasan kafarta ne. Ko da idanunsa suka kawo ga kafarta, sai kamannin sha'awar dake fuskarsa suka sauya,suka rikide zuwa tsoro da fargaba. Ba wani abune yasa jikinsa sanyi ba, sai ganin kyakykyawar buduwar dake gabansa bata da tafin kafafu irin na bil'adama, maimakon hakan, sai kafta kaftan kofato irin na giwa.Kai Allah wadan naka ya lalace. Nuraddin yace cikin zuciyarsa lokacin da yaga kofaton. Ga doki hardoki amma kofaton na sakainane. Ya sake cewa da kansa.Buduwar ta dubeshi yayin data tabbatar ya kare mata kallo, sannan ta fara matsawa kusa dashi.Nuraddin ya yi tsalle gefe guda don gudun kada ta taka shi da kofato."kada kaji tsorona Nuraddin, domin yanzu tsakanina dakai babu cuta ko cin amana, sai so da kauna da amincewa, duk duniyar nan a yanzu babu wanda nake kauna sai kai, ba dan komaiba kuwa sai dan ganin kaine mutum na farko daya fara ganina a mummunar kamata bai sume ba".Ta danyi shiru ga barin daddar magana cikin murya mai kama da sarewar mutanen hindu, sannan taci gaba da ce.Dubeni da kyau Nuraddin, kyakykyawa ce kana sona? Nuraddin ya dubeta tun daga kan kyakykyawar fuskarta har zuwa kan kofatonta jikinsa na rawa ya sake dubanta yace."Tabbas babu wani dam adam dazai ganki yace baya sonki, amma idan yana da hankali babu abin dazai sa ya kusanceki ballantanamaharya soki da wadannan kaba- kaban kofato a kafarki. Ya nuna kofaton dake kafarta, sannan ya dada ja da baya kamar wanda ake bi da wuta.Budurwar mai kofato, ta dubeshi sannan ta hade fuska tace"da wani ne ya fadi haka bakai ba saina tsotse jininsa na shanye bargonsa, sannan na karairaya kashinsa na watsar a bayan duniya.Tsohon lokaci buduwar tana kallonsa kawai batace dashi komai ba. Jikin Nuraddin ya fara tsuma domin tunaninsa rikidewa zatayi zuwa jibgegiyar halittar nan ta dazu,to amma ga mamakinsa sai budurwa ta haskake shi da wani tattausan murmushi.Ka daina jin tsorona Nuraddin, ai na riga nayi maka alkawarin bazan taba cutar dakai ba, kuma ni mai kokari ce gurin cika alkawari, ba kamar ku bane bil'adama.Budur war mai kofato ta ja baya, sannan saita durkusa kasa, kyakykyawar doguwar rigar dake jikinta mai sheki da kamshin gaske ta sauko ta lullube kofaton. Kusan tsahon dakiku ashirin, sannan ta sake mikewa tsaye. Tun kafin doguwar rigar ta gama dagewa sama Nuraddin ya hango santala- santalan kafar kyawawan gaske, baitaba ganin tafif kafar mace mai kyawunsu ba.Daman ku'yan Adam gajen hakurine daku da tun farko ma kayi hakuri, sannu a hankali zaka ga surar da baka taba ganin irinta a jikin wata'ya mace ba a duniyar nan. Ta danyi shiru tana karkada awarwaron dake hannunta kan taci gaba da cewa."sunana AMAL'yar sarkin Aljanu. Mahaifina shike sarautar duk aljanun dake wannan nahiyar, muba kananan Aljanu bane. Dan haka inaso ka kwantar dahankalinka da sannu zan kaika ku gana da mahaifina, mutumin kirki ne, kuma nasan dole ne ma ya kaunaceka in dai na bashi labarinkadomin yana son jarumi irinka.Budurwa Amal ta daga hannunta sama, sai farantan abinci da kayan marmari iri-iri na sauka a gabansu. Ba'a dade ba sai wata katuwar rumfa ta alfarma ta sauko daga sama ta kare musu ruwan saman da har yanzu yake zuba kadan-kadan.Amal ta zauna, amma Nuraddin yakimotsawa daga inda yake, har yanzu gani yake kamar zata sake rikidewa zuwa wata halittar mai ban tsoro.Zauna mana Nuraddin, ko har yanzutsorona kake ji? Haba nuraddin ka yarda mana da alkawarina, ai ni dakai yanzu mun zama daya.Jin haka, shiyasa nuraddin ya koma can gefe guda a cikin rumfar ya zauna akan lallausan kilishin daya mamaye duk cikin rumfar. Nuraddinya dan lallatsa kilishin da hannusa, laushi tubus kamar katifa. "Matso kusa dani mana Nuraddin". Tace dashi a tausashe.Nuraddin yayi karfin hali ya matso kusa da ita ya zauna jikinsa na rawa, har yanzu tunani yake zata rikide.Amal ta dubi Nuraddin sannan tayi masa murmushi, ta dada matsawa daf da shi, har yana iya jin hucin numfashinta mai kamshin turare a fuskarsa.Ashe suma aljanu suna numfashi irin na dan adam. Nuraddi ya fadi cikin ransa."Kayi min murmushi mana Nuraddin ko baka sona ne"?A karo na farko da Nuraddin yayi koka ri, ya jefeta da wani dan saurayin fatalwan murmushi.Amal ta dafa kafadarsa tace."Nuraddin kana sona kuwa"? Aljani Ya Taka Wuta!......8 - - - Wanene zai iya dubanki a haka yace baya son kyakykyawa kamarki? Ai kowa yana son mai kyau indai kafa babu kofato". Nuraddin yace da ita yana duban fuskarta mai sheki.Amal tayi shiru tana sauraronsa, sannan sai ta rankwafa ta dora kyakykyawan kanta akan kafadarsa tace."Naji dadi Nuraddin, wallahi nima ina sonka matukar so, naji dadin cewar kaima kana sona". Ta danyi shiru, tana wasa da gashin kanta akan kafadarsa.Nuraddin ya dimauce, saboda ni'ima da kamshin turare dake tashi daga cikin gashinta."Ina so ka sani cewa daga yau kayi sallama da talauci har abada, muddin kana tare dani, ni'imar duniya kam ka hadu da ita, duk abimda kake so ka ambace kawai ka samu masoyina, sannan kuma nayi maka alkawarin idan jarabawarku ta karshe tazo, kada ka dami kanka da wani karatu, domin nida kai zamu yi jarabawar zan bude maka tafin hannuna duk abinda kake bukatar sani yana nan a rubuce, sai dai kuma ina so ka sani cewa kai kadai kake da ikon ganina."Amal ta danyi shiru sannan taci gaba da cewa."To, Nuraddin nidai kaji alkawarina saura naka Nuraddin, ina so kayimin alkawarin idan duk nayi maka wadannan abubuwan dana yi maka alkawari zaka aureni"?Amsa kuwar tambayar ta daki dodon kunnensa a bazata, hakika al'amarin ban mamaki na faruwa gareshi cikin daren nan. Nurdaddin yasa hannunsa a karo na farko ya dafa kyakykyawan hannunta yana tunani. Ni Nuraddin yau da auren aljana? Ya fadi cikin ransa. Koda yake ba aibu bane na aureta, indai har zata mayar dani mai arziki, to daman duk duniya ma me ake nemainba kudin ba? To kuma gashi sun zomin a bulus, in kuwa hakane mezai hanani aurenta. A lokacin ne to Badawiyya ta fado masa a rai. Hakika yana son Badawiyya matukar so, domin ta dade tana wahala akansa iri-iri dan me yanzu dare daya zai mata haka, don kawai ya hadu da aljana mai siffa biyu, mummuna da kyakykyawar siffa, waya sani ma ko nan gaba in ya sake ya aureta ta sake rikidewa. Amma dai bari na fara cin bulus din kafin na yanke shawara. Tabbas bazan taba barin Badawiyya ba mai sona tsantsa, ba dan jarumta ta ba, ko rashin tsorona. Yace da kansa a zuciya, sannan sai yace a fili."Zan aureki Amal".Amal ta dago kanta dake kan kafadarsa ta dubeshi tace"da gaskeNuraddin? Don Allah da gaske zaka Aureni"?Dagaskenake Amal, ai na fada miki babu wani mutum dazai ce baya kaunarki a duniyar nan Nuraddin yace yana duban fuskarta."Alkawari fa Nuraddin, nasan halinku na'yan Adam baku da alkawari.""To, shikenan Nuraddin, tunda ka amince gobe saika shirya mutafi na kaika gurin mahaifina ku gana, sannan kuma shima kayi masa alkawarin zaka aureni". Gaban Nuraddin ya fadi, jin cewa za'a tafi dashi gurin sarkin Aljanu, ya dubeta a tsorace zaiyi magana sai ta daga masa hannu."Nasan abinda kake tunani, indai idan wannan ne, kada ka damu kanka, domin babu wani aljani daya isa ya tabamin bakona ballantana kuma masoyina". Ta danyi shiru sannan tace."kayi kokarin rike alkawari Nuraddin, domin bana son mai karya alkawari, kuma daga yau bazaka sake ganinaba cikin mummunar siffata ba ta farko. Nayi maka alkawarin hakan". Amal tace sannan saita mika dan karamin dan yatsanta na dama tace tana murmushi."mukul la".Nuraddin ya mika dan yatsansa suka kulla alkawari sannan sai Amal ta cire daya daga cikin zoben zinariya ukun dake hannunta, ta kama dan yatsansa ta sa masa zoben ta ce."Daga yau in kana son ganina, sai ka murza wannan zoben,zaka ganni nazo, sai dai kuma inason ka sani cewa bana zuwa da goshin magariba, bakuma na zuwa da asuba, dan haka kada ka murza zoben a wadannan lokutan dan bazaka ganni ba, sannan kuma babu wani aljani daya isa ya tabaka inhar kana tare da wannan zoben koni dana baka shh kafi karfina, nima daga wajen mahaifina na gajesu. Guda ukune daman gashi nan na baka daya ka kula dashi da kyau kada ka sake ka baiwa kowa, domin yanada matukar amfani da daraja. Mahaifina ya taba rantsewa yace duk dan adam din da aljanu suka taba ya haukace koya nannade, ma'ana sassan jikinsa suka shanye, to dazarar anjika masa zoben nan a ruwa yasha zai warke kamar wani abu bai taba samunsa ba, sannan kuma in har kana tare da zoben nan babu wani aljani daya isa ya tabaka, koda kuwanice kamar yadda na fada ma tun farko.Tayi shiru tana jujjuya kanta akan kafadarsa, tana mayar da numfashi."Gobe sai mu hadu dakai anan kamar wannan lokaci, sai mu tafi nakaika wajen mahaifina, domin ya dade yana damuna akan na samo miji, to gashi na samu".Amal ta miki tsaye ta dubi Nuraddin zaune tace". Rufe idonka".Cikin mamaki sai Nuraddin yabi umarninta. Alokacinne yaji tace."To nuraddin sai goben kenan, Allahbamu alheri kana iya bude idanunka".Bude idonsa keda wuya ya ganshi zaune akan gadonsa. ...ALJANI YA TAKA WUTA CIGABAN LABARI part {11}... Cikin mamaki, sai yayi sauri ya dirgo daga kan gadon yana waige waige, domin a tunaninsa Amal ce keson cigca da wasa da hankalinsa. Nuraddin ya dubi sauran gadajen dake daki, sai yaga duk abokan kwanansa ne wadanda ya sani kwance suna bacci abinsu. Ya leka tagar dakin, sai ya hango farfajiyar makarantar kamar dai yadda ya santa, ciki mamaki sai ya dawo ya zauna a bakin gadon, sannan ya rufe idanunsa da tafukan hannayensa. Nuraddim ji yake kamar ya farka daga wannan mummunan mafarki. Adai dai lokacinne ya tuna da zoben data bashi, cikin gaggawa ya dubi dan yatsansa. Tabbar zoben nan yana sheki. Nuraddin ya murza zoben. "Menene kuma"? Amal ta sake bayyana acikin daren, sanye da doguwar rigar bacci tana murmushi. Dakin ya game da tattausa kamshin turare. "Ko baka jin baccine nazo na tayaka hira"? Tace dashi tana murmushi. Nuraddin ya juya ya dubi sauran yaran dake kwance a dakin suna ta sharar bacci, gabansa na faduwa yana ta addu'ar Allah yasa kada wani ya farka ya ganta a dakin. "kada ka damu dasu, ai baza su iya ganina ba, bakuma zasuji hirarmu ba, koda wani ma a cikinsu ya farka to a kwance zai ganka kana bacci". Tana gama fadin haka sai ta jefeshi da tattausan murmushi ta bace. Awashegarin ranar, acan kofar makarantar misalin goma sha biyu na rana musa mai gadi ne keta jayayya da wata kyakykyawar yarinya dake tsaye a gabansa. "Kacd dashi Badawiyya ce keson ganinsa". Ta ce dashi cikin kaguwa. Ai ba fadar sunan ne wahala ba, abin da nakeso ki gane shine neman mutum daya ciki duban dalibai cikin wannan uwar ranar mai kamar ta tashi Alkiyama ba karamin aiki bane". Mai gadi yace. Badawiyya ta kule, sannan sai wani tunani yazo mata nan da nan sai ta juya ta dubi direbanta tace dashi. "Dauko min jakata". Cikin sauri direban ya tura hannunsa ta cikin budadden gilashin motar, ya laluba kujerar ta baya ya daukowa Badawiyya jakarta. Badawiyya ta bude jakar, sannan ta dauko "yan wasu adadin takardun naira hamsin-hamsin tace da maigadin. Ga wannan kasha ruwan sanyi, amma don Allah taimaka ka nemomin shi". "Ai dole ne tunda kin bada maganin rana! Maigadin yace yana rawar jiki. "yaya kika ce sunansa"? "Nuraddin Abubakar". Badawiyya tace. Maigadin ya ruga da gudu, ya nufi cikin makarantar, zuciyarsa tana mai mamakin abinda ya hada wannan kyakyawar yarinyar mai kwarjini ga karfin mayen karfen kudi a tattare da ita da wannan watsattsen shaidanin yaron Nuraddin. Abin da ya faru a daren shekaran jiya ya tambara Nuraddin a duk fadin makarantar kai harma cikin gari, dalibai kuwa har kanana "yan aji daya babu wanda baisan shiba, domin ko yau aka kawoka dalibi makarantar sai an baka labarin Nuraddin. Ba'a dade ba sai ga mai gadin sun dawo tare da Nuraddin, sanye da kayan makaranta farare, da koriya Hula. Nuraddin ya dubi Badawiyya cikin Mamakin abinda ya kawota bayan kwanansa uku kacal da rabuwa, tabbas ba lafiya ba. Amma ga mamakinsa sai yaga tundaga nesa Badawiyyi ta fara masa murmushi. "Wallahi Nuri tunda ka taho bana iya barci, tunaninka ne ke damun zuciyata, shiyasa nace bazan iya ba gara na lallabi direbanmu ya kawo ni na ganka, yanzun ma kaga ko sani ba'ayi a gida ba". Nuraddin ya dubi abar kaunarsa cikin mamaki, so da kaunarta suka dada kwarara a cikin zuciyarsa. "kina nufin abinda ya kawoki kenan kawai ki ganni"? Badawiyya tayi murmushi, sannan ta gyada kai tace. "Ai ya wuce kawai Nuri, domin tunda ka tafi nake Mafarkinka, wallahi 'darling' duk inda zani dakai nake yawo a zuciyata, gaskiya ni dai ina ganin daka gama sakandire zamuyi aure, ko kana sami damar ganinka kullum a kusa dani, inka shiga jami'a ma take tafiya da matarka. Nuraddin ya fashe da dariya. "Lallai kam kinyi dabara, kinga naji dadin zaben kala-kala acan jami'ar naji ance canne gidan mata". Badawiyya ta harareshi tace. "kama fara mana"! Ta danyi shiru, kana ta dubi dan yatsansa ta girgiza kai tace". Koda yake ma dai nasan Maza baku da tabbar. A ina kuma ka sami kyakykyawan zoben nan, watace ta baka"? Badawiyya tace tana murmushi. To sai dai kuma lokaci guda murmushin dake fuskar Nuraddin ya subuce daga fuskarsa, gabansa ya fadi. "Au! Menene na wani bata rai, don kada nace a bani, to duk abinka saina karbi zoben nan a kalla dai inna dube shi yake tunamin dakai, ya dauke min kewarka". Nuraddin yayi shiru yana dubanta cikin taraddadi da fargabar abinda zai biyo baya, lokaci guda kuma maganar Amal ta fado masa *kada ka rabu da zoben nan domin yana da matukar daraja da amfani ga bil'ada". To, amma ai Badawiyya ma masoyiyarsa ce, kuma tayi masa wahalhalu da dama a rayuwarsa, duk dayake dai haduwa daya kawai sukayi da Amal amma ta mayar da shi mai arziki. Tun safe yake kashewa abokansa kudi, dayasa Hannu a aljihu sai kawai ya yita zaro kudi, kai duk abinda yayi niya idan yasa hannunsa a aljihu saiya dauko. To koma dai menene Badawiyya ita ta fara wahala akansa kafin kowa. saida yamma. Aljani Ya Taka Wuta!......12 ' ' - Hakika zoben kyakykyawane kamar Nurinta. Tambayar kawai da har yanzu takasa ramun amsarta itace. A ina Nuri ya sami wannan kyakykyawan zobe? Ita dai ta san kudin da ta bashi bai isa ya saya masa irin wannan kerarren zoben ba. Amma bari ya dawo zan tambaye shi. ' Badawiyya ta fadawa kanta kana ta kuma duban zoben, sannan sai ta kama zoben ta murzashi tana murmushi, a ganinta zoben kamar Nurinta ne. Da ba goshin bane, da Badawiyya tayi kaduwar da bata taba yin irinta a duniya ba, domin tana murza zoben mai shi zata bayyana a gabanta. Badawiyya tayi sa'a domin'yar sarkin aljanu Amal bata bayyana da goshin magriba, amma da zarar magriba ta wuce zata iya bayyana a sa'ar da aka murza zoben, ta koma kan daya daga cikin dogayen kujerun alfarmar dake dakinta ta fara cire kayan dake jikinta tana jefawa akan kujerarta. ' Al'adar da ta samawar kanta a duk magaribar duniya take son farawa.Al'adar a kullum kwanan duniya shine wankan magariba. Koda yake wasu lokutan in har bada wuri zata kwanta ba, ta kan bari har sai lokacin barcinta yayi saita shiga wankanta. Amma idan har Nuraddinyana nan Nuri Darling a yadda takankira shi, wankan magariba wajibi ne a gareta ba mustahabi ba. A duk sa'ar da Nuraddin ya dawo hutun makaranta, takan shiga wanka tun karfe bakwai na yamma. Wankan da shafe-shafe da kuma kyale-kyalenta, takan shafe akalla sa'a guda tanayi. Da zarar ta gama saita nemi guri ta zauna cikin annashuwa, annuri na fita daga fuskarta, yayin da daddadan kamshi madaukaki ke hurowa daga jikin kyakykyawar halittarta, taci gaba da jiran abin kaunarta Nuraddin wanda idan yazo suka fara hira basa rabuwa sai karfe goma shabiyu na dare. Aikin kenan kullum kamar karatu, har kuma sai Nuraddin ya koma makaranta sannan sai duk soyayyar ta koma kan hotonsa. - Badawiyya ta fito a hankalin tana rangwada, ta daura farin zani iya kirji, gashin kanta ya warwatsu akansantalelen wuyanta mai kamar na barewa. A duk sa'ar data motsa sai ruwa ya fantsamo daga cikin gashinta. Fitowarta kenan daga al'adarta ta wankan magariba.Ta zauna a hankali akan daya da cinwasu kujeru takwas masu numfashida suka zagaye dan madaidaicin dakinta, kana ta janyo wan dan karamin teburi fari mai tafiya akan kananan tayoyi. Wannan teburin shine dan dakon kayan kwalliyar Badawiyya. Sannu a hankali tana tafe tana rausaya har takai ga wani tangamemdo madubin kwalliya ta fuskanceshi. Daga cikin madubin tana iya hango kofar dakin da zata kaika har falon cikin gidan.Badawiyyata dauki wata 'yar doguwar kwalbar rob, wacce ke dauke da lallausan man shafawa mawadacin kamshi, ta matso man akan tafin hannunta na hagun. Sannan tasa na dama ta fara shafawa. Agogon dake jin bangon dakin ya fara rera sarewa, karfe takwas na dare, Badawiyya tayi murmushi data tuna da abin kaunarta Nuraddin. Ta daga hannanayenta izuwa fuskarta ta farashafa lallausan man, sannan ta lumshe idanuwanta cikin annushuwa tace.NURI DARLING!!! Bata dauke hannayenta daga fuskarta ba, ba ta kuma bude idanunta ba, domin ji take kamar hannayen Nuraddin ne ke lullube da fuskarta. A haka taci gaba da tunaninta. Sabanin al'adarta ta yauda kullum a ka'ida Badawiyya bata wanka karfe takwas na dar har sai idan abin begenta Nuri yana gari, amma yau sai gashi tayi saboda dalilai biyu. Na farko mafarkin da tayi a daren jiya na matar nan mai mummunar halitta wacce ke kokarin kwace mata Nuri. Hakan shiya sata wanka yau tun kafin karfe takwas na dare. Domin a tunanin Badawiyya koda Nura baya nan, kamata yayi ace tana raya lokacin hirarsu. Wannan shine dalilin wankanta domin tayi alkawarin zatayi kwalliya ta zauna tasa hoton Nuraddin a gaba tayi ta hira koda kuwa bazai amsa mata ba,ba kuwa zata daina kallonsa ba har sai sha biyun dare wanda shine ka'idar lokacin rabuwarsu da Nuri darling.Dalili na biyu kuma shine tana tunanin idan takai sha biyu batayi barci ba, da wahala ta sake mafarki da mummunar matar nan mai kokarin kwace mata Nuraddin. Hakika mafarkin ya tayar mata da hankali. Domin Badawiyya bata da wani abokin gaba a duniya da ya wuce wanda zai rabasu da *NURI DARLING*.Da farko da tayi mafarkin mata mummuna ce amma sa'ar data farka ta sake komawa barcinta, sai matar tazo mata a siffar kyakykyawa. Abin bakin cikin kuma ga Badawiyya, surar matar a wannan lokacin tafi tata kyau nesa ba kusa ba. Mafarkine kawai amma duk da haka ya tayar mata da hankali.Tunaninta ya katse sakamakon sauyin yanayi dataji a jikinta. Haka kawai ba zato ba tsammani, sai taji jikinta ya fara rawar sanyi sannan taji wani abu mai kamar iska ya na kada gashin kanta, sannan abu mafitashin hankali da figitarwa shine lallausan man datake shafawa a fuskarta sai taji yayi sanyi kalau tamkar tana shafa kankar adai dai lokacin ne taji karar budewar kofa kuu!Ina vaxan iya ganin wannan tashin hankalin ba. Wani abu yayi ta kururuwa cikin kwakwalwarta yana cewa kada ta bude idanunta, saidai kuma mai gargadi ya makara....... - """ALJANI YA TAKA WUTA CI GABAN LABARI {Part 13}""" Nuraddin yaci gaba da tunani, sai gashi kuma lokaci guda Amal na barazanar zata mayar da burin wani shudadden mafarki. Bazai yiwu ba, yace a ransa. Nakoma matsiyaci, tabbas ba zata sabu ba bindiga a ruwa. Nuraddin ya dubi amal ya sunkuyar da kansa kasa yace da ita a tausashe. "kin kasa fahimtata Amal, abinda nake son ki gane shine, so nake mu rabu da Badawiyya cikin salama, ke yanzu kina ganin bayan abinda tayi min ya dace na watsar da ita gefe guda"? Nuraddin ya girgiza kai sannan yaci gaba da cewa. "Daga yanzu Amal zan rike dukkan alkawarin danayi miki, kece baki san zuciyata ba amma wallah tunda na doraki a idanuna naji begenki ya lullube tsokar zuciyata, dan haka ina son ki kwantar da hankali nayi miki alkawari idan na koma gida, da zarar mungama jarabawarmu ta karshe, zanyi kokarin mu rabu da Badawiyya. Ni kaina nasan ba dai dai bane ace "yar talakan mutane tana takara da 'yar gidan sarkin aljanun duniya mai kyawun sura kamarki". jin hakan keda wuya, sai wani tattausan murmushi na farin ciki ya subuce daga bakin Amal. Ta sunkuyo da kai a hankali zata sumbace shi, sai ta tuna she bai riga ya aureta din ba. Cikin sauri sai ta dauke kanta ciki jin kunya, kana tace dashi. "Alkawari fa Nuraddin"? "eh alkawari, kada kiji komai ai sanin kanki ne ba daya kuke da Badawiyya ba ai ko ba'a gwada ba linzami yafi karfin bakin kaza, duk da yake dai itama kyakykyawa ce acikin mutane, amma ai gaba da gabanta wai aljani ya taka wuta". "tsokana fa kenan"? Amal tace tana dariya wallahi wannan karin maganar taku ta mutane ta fita daga bakinka". Nuraddin ya fashe da dariya, sannan ya juya firgigit yana leken taga don kada wani yaji sautin dariyarsu ya shigo ya ganshi shida yar sarkin Aljanu. "kada ka damu da wadanda suke waje, domin ko sun shigo ma baza su iya ganin mu ba, kai dai kawai shirya mutafi mahaifina na can yana jiranka. Nuraddin yayi ajiyar zuciya hakika yana tsoron zuwa garin da babu kowa sai aljanu, amma yanzu ya tabbata Amal bazata bari a cuceshi ba. Nuraddin ya mike tsaye a tsorace yace "mutafi". Nuraddin yabi umarninta. Rufe idonsa keda wuya yaji tace bude. Yana budewa sai ya ganmu a cikin wata katuwar alkarya mai dauke

Chapter 2 of 6